Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

guri inda muka shiga gaisawa da mutane dake jiran mu a haraban.
Can na hango anty Amira da wani dogon mutum a tsaye daga gefe daya na zare hannuna daga rikon da sadauki yai min na nufi gurin ta.
Da dan sauri na na rugumota a jikina itama dai ba laifi ta riko ni din tana dan murmushin yake a fuskan ta.
Nace anty nayi missing din ku mun samay ku lafiya tace mun dai yi missing din dan uwan mu kawai Bintu.
Nasan magana ta fada min don tana fadan haka bata tsaya ba ta wuce zuwa gurin sadauki mutumin yabi bayan ta tabar ni a tsaye nan.
Naji an dafa kafada na ina juyawa anty maryamce tace kada ki damu don ko kin saba da halinta yanzu ai.
Shigowan su Nafisa ya katse muna zancen mu nan suka rugumoni da farin ciki suna fadin kai matar yaya kin bamu kewa wallahi sosai.
Barin Nafisa da mutumin da take tare dashi wanda ta gabatar mai a matsayin wanda zata aura wai.
Yayi ya nufo inda nake tare dasu nafisa nan suma suka shiga gaidashi tare da mashi sannu da zuwa suna mai taya shi murna samun karuwan da yayi.
Hannuna ya kama zuwa kofan shiga gidan namu wanda yake a rufe a lokacin don za, abude shi da addua don shiga ciki.
Malaman da aka gaiyato ne suka bude gidan da addua tare da fatan gamawa da duniya lafiya.
Mun shiga gidan da farinciki gaba daya mutane sai yaba kyau da tsarin gidan suke yi.
Abincin da aka girka don taron mu aka shiga ci kowa sai da ya wadata yaci ya koshi zuwa yamma mutane suka dinga watsewa daya bayan daya kowa a cikin farin ciki.
Ganin an dan rage yawa sai yan gida tsiraru suka rage ba yawa yasa na juya gurin anty maryam nace zan dan shiga ciki anty .
Tare da ita muka shiga dakin da yake a matsayin mallakina wanda yasha kayan alatu sosai na zamani don komai daga waje aka shigo dashi a gidan.
Yana zaune tare da Amira da Bashar dasu yaya sagir da yaya Abdul suna hira.
Muna mikewa ya bini da wani irin kallo na so da kauna yana cewa maryam ki barta ta huta please koma may ye ai zata labarts maki idan kun natsu.
Don nasan bakunan nan naku tab yake da gulman da kowan ku ya tara ya tsiyayawa dan uwa.
Nace kai haba dai yaya kana iya raba anta da jini ni da anty maryam sai Allah fa.
Yace ai na gani na kuma sani don gashi ta haki zaki barni a nan ni kadai.
Kai kade kuma yaya inji Amira yace kin san na saba da matata yanzu bamu raba second a tare.
Amma wanan da kike gani naga yau tana son nisanta ta dani idan ban yi niya ba.
Amira ta kawar da kai gefe daya don ta fahinci i yanzu ba karamin ji dani yaya sadauki yake yi ba har bai iya boye feeling din shi a gaban kowa.
Ga wani irin kyau da haske dana kara tare dani ga wani annuri da take gani yana fita tare dani.
Lalai kam Bintu tayi sa, a da dace a rayuwan ta na jajircewa da tayi ta mallaki zuciyan sadauki da ma ruhin shi a baki daya.
Lalaikam shima din yayi dace samun Bintu a matsayin matar aure a gare shi don mace mai kyau da addini rahama ce ga namijin daya samay ta.
Kalli yadda ta koma yana wani ji da ita da dan shi wanda ko dan kukan yaron bai son ji komai nasu gwanin burgewa.
Gaskiya yayi sa, an samun mace mai kyau a rayuwan shi da Rahama ce ai bazai wani jin dadin nunata haka ba a duniya.
Ba Amira ba kowa ya kalle mu zancen zuci yake a kan mu don ko mun dace da junan mu sosai.
Don sadauki za, ace mutum ne mai sa, a a rayuwan shi ga dukiya mai tarin yawa Allah ya daukaka shi dashi.
Ga mace ya samu mai kyau da tarin addini tare da ita ta gyara mai rayuwan shi don duk wanda ya ganshi yasan ya watsar da halaiyar shi ta da can baya.
Hassada dangin shedan tuni Amira ta mike tana fadin ita zata tafi gida sai anjima kuma.
Sadauki yace haba Amira tun yanzu ki tsaya mana har ayi sallah sai ki tafi gida tunda ba koranki ake ba?
Tace no bari kawai na tafi don naga kamar kana son hutawa ne da iyalin ka tafice tana cika tana batsewa a ranta.
Ya gurgiza kan shi yabita da kallo don yasan abinda take nufi akan Fatiman shi ne take wanan cikar haka tana batsewa ita kadai.
Sun dan jima suna hira akai kiran sallah suka mike zuwa sallah nikan muna dakina mun baje da maryam muna hiran yaushe rabo da ita.

****** ********* ******
Bamu samu jan mu ba sai bayan karfe tara kowa ya watse yarage daga mu sai iyya a gidan da take ta faman gyaran guri.
Ya fito daga dakin shi a cikin jallabiya baka mai gajeren hanni yace haba iyya wanan aikin yai maki yawa fa gaskiya.
Nace a nemo muna wasu masu taimaka wa agidan mutum biyu aikin ki kawai ke yanzu shine kula da Matar gidan da yara ba ruwan ki da wanan aikin kuma haka.
Tace haba Alhajina har ina aikin yake a nan ai ba sai an nemo wasu ba zan iya ko ni kadai.
Yace a, a iya na gama magana ko gobe ne insha Allahu masu aikin zasu fara zuwa sai ki gwada masu komai daya dace suyi.
A lokacin na fito ina saye da wani dogon riga dinkin shi simple ne irin na zama gida mai launin jikin kura, kaina da hula dana daure gashina a cikin sa.
Nan nake cewa , a, a iyya baki huta ba hakana har yanzu don Allah ki huta kibar aikin nan haka har da samay ga Amir kuma goye a bayan ta tare dashi take aikin.
Tace wai na dan rage kayan nan kafin safe kada gurin ya kwana haka da kazanta.
Badai tsabta ba kan Iyya don mace da bata haihuwa dama ance tsabta gare ta sosai haka ne ya kasance ga iyya din don yar ta daya a duniya.
Kima tayi aure sai dai ba wani dadi a gidan auren don wahala take sosai sunan ta suwaiba.
Yatana da yara uku ga mijin bai wani aiki sai dan buga bugan da yakeyi kawai iyya tasha min magana akan wanan zaman na Suwaiba haka nan.
Haka yasa na sa a raina zan wa yaya magana akan wanan matsalan don ya kamata a taimaka ma rayuwan su don Iyya gaskiya ba laifi mace ce mai rikon gaskiya da amana.
Fruit muka zauna muka dan sha muna hira yaso fita da daren zuwa gida don yaga iyayyen shi sai dai yana tare da gajiya.
Waya naji sunyi yana ba baba hakkuri sai da safe zai shigo ya duba su insha Allahu.
Bamu jima ba muka shige ciki muka kwanta iyya ta bukaci na bar Amir a gurin ta wanda naji dadin hakan.
Don ko banza an kunsa yaye shi ma a lokacin don haka yana bukatan dan jayewa daga gare mu.
Don ya manta da nono da sauri a cikin sauki batare da ya wahala ko ni na wahala ba.
Washegari ma masu zuwa muna sannu da zuwa sun kara cika muna gida ba wani hutu sosaia lokacin don jama, a kada su ce ina masu fadin rai
Kowa haba haba nake da zuwan shi don duk abu daya ne ya kawo su da mai kudi da tallaka sunzo ne don nuna farin cikin su gare mu.
Na fahinci mutane mu suna a cikin wani hali na haula, i don wahalan da ya ishi mutane haka yasa duk wanda yazo naga yana da dan rauni nake taimaka mai wasu zan basu sabulai da kudi wasu kuma sun fi karfin karban kudi a gurina sai dai na basu tsaraban abinda ya dace dasu wanda ankawo min abubuwan da zan rabawa mutane dake shigowa taron mu.
Sai bayan kwana biyu da dawowan mune na fahinci an canza muna ma, aikatan mu dana saba dasu abaya.
Ma, ana anbarsu a tsohon gidan mu da muka taso haka yasa banji dadi ba nai magana da yaya yace zai duba al, amarin.
Da yamma kuwa sai ga Atiku da iyalin shi sun zo taron mu na tare su da farin ciki nake tambayan su yaran su sukace suna lafiya.
Tare ma suke da maigidan su yana waje nace a, a shine zai tsaya a waje ku shigo dashi mu gaisa mana.
Amaryan shi ta fita ta shigo dashi nan muka gaisa nake tambayan shi mai yasa bai dawo nan inda muka dawo ba.
Yace hajiya ance nan kayan aikin ku duk yanzu na naura ne bazan iya aiki dashi ba nace haba haba basai a koya maka ba.
Gaskiya daga gobe gaba dayan ku har su baba musa duk a nan zaku dawo da aikin ku sabbin a kai su wancan gidan.
Nan ya shiga min godiya nake tambayan shi Aliyu fa suke ce min yana nan gida kudin makaranta yai tsaye tunda maigida baya nan.
Banji dadin jin haka ba nace gobe yazo da yaron za, a san abinda za, ayi akai insha Allahu.
Nakawo tsaraba da kudi na basu shi kuma mijin na bashi kudi ga sayi shinkafa dashi.
Nan ya dukar da kai sai hawaye ya fara zubo mai yana cewa hajiya ban san irin godiyan da zan maki ba keda maigidan ki akan irin taimakon da kuke muna a rayuwan mu ba.
Ga yaron nan Aliyu maigidan ki ya taimake mu a baya an mashi aiki ance da ba, ai aikin ba haka zai koma dan luwadi shima don abin zai ta damun shi idan bai yi ba.
Yanzun ko kinga zancen ya koma tarihi a sanadinku ke da maigidan ki da kuka taimakawa rayuwan mu.
Nace haba malam atiku babu komai ai duk yiwa kaine may ye amfanin kana tare da mutum baka taimaka mashi ba.
Munyi sallama dasu zasu tafi sai ga maigidan ya dawo nan suka tsaya suna gaisawa dashi.
Yace malam Atiku hajiya tace sai a dawo daku gidan nan ko nai magana da Bashar yace duk zaku dawo nan da aiki daga gobe insha Allahu.
Nan ya shiga godiya nace ai na manta maman Aliyu don Allah ina son kuyi min wani taimako keda abokiyar zaman ki.
Sai gaba daya hankalin kowa ya dawo a kaina nace ina son don Allah duk safe a dinga dama muna koko da kosai ana kaiwa makaran tan dake da almajirai sadaka da yamma kuma ina son duk ranan jumma, a a dinga dafa shimkafa da wake buhu daya ana kaiwa sadaka a wanan makarantan.
Don haka sai kuyi min lissafin abinda kuke bukata daga kayan aiki da kulan da za, a dinga zubawa sai naji na aiko maku da kudin.
Kara zubewa sukayi a gurin suna min godiya cikin jin dadin wanan ci gaban da suka samu na rayuwa.
Tunda dama manejin rayuwa ne sukeyi ba wani sana, an da sukeyi yanzu zaune kawai suke a gida dan abinda mijin su ya samo ake amfani dashi.
Munyi sallama dasu akan zanji sako daga gurin maigidan su idan ya zo gobe aiki.
Suna fita sadauki ya juyo inda nake zaune yana sauke ajiyan zuciya yace wanan sabon hikimar kuma ta maynene queen ?
Nace godiya da neman kariya ga ubangijin mu yaya na kasan duk wanda Allah yai ma baiwa ya kamata ya gode masa.
Sai nake ganin yaran almajirai masu bara a titi zamu taimaka da dan abinda zasu ci suji dadi a ransu muma muji daga ni, imar su.
Yace haka yana da kyau sai kuma may kike gani ya dace ayi don kudin kwallon da na samu wanan karon ina son inyi amfani dashine a sadakatuljari,a
Nace akwai magidanta mabukata yaya da abinda zasu ci da iyalinsu yake masu wuya akwai kuma marayuwa da ke neman taimako don Allah ya kamata ayi awani abu akai yace insha Allahu angama queen.
Na kuma gode da wanan shawaran taki zan duba nasan abinda za, ayi na taimako ga alumma daya dace ayi.
Sai da mukai kwana uku na shirya na tafi gaida su mama don lokacin mutane sun dan tsagaita shigowa muna sosai gaida mu.
Wanda wasu gulma ne kawai ke kawo su gidan don suga yadda gidan namu yake ne.
Shiga nayi na alfarma dagani har Amir da Iyya muka tafi gidan namu sadauki ne ya jamu a mota.
Mun samu su lafiya sai dai gaskiya duk akwai sauyin canji a tare dasu mama ce kawai zaka kalla kasan bata da wani matsala a tare da ita.
Amma sauran gaba daya duk sun wani jemay kamar basu ba Umma duk kiban nan nata yanzu ya tafi tsufa ya taso mata sosai tare da ita.
Ga furfuran dole daya bata masu kansu ita da mama Asiya yanzu kana ganin su kasan suna cikin wani bakon yanayin da basu saba ba a baya.
Mama tai matukar farin ciki sosai da ganin mu ta shiga haba haba damu a gidan.
Kaunata dake gurin ta ta murje tayi kyau da ita sosai harda tsayi naga ta kara min da haske ga sabon da naga sunyi da mama sosai yanzu.
Itako yar bakin rai na kusa awa daya a dakin bata fito ba tana can tana ji da kanta a daki don suna da wata yar dattijuwan da ke masu komai a shiyan su basu ko kauda kara sai matar ce mai aiki.
Can tafito tana wani cika tana batsewa nace a, a anty Amira ai na zata kin fitane ban san kina ciki ba wallahi.
Ta zauna tana cewa ina ciki na kwanta ne ina jin shigowan ku bandai fito bane kawai.
Nace Allah sarki mun samay ku lafiya tace Alhamdullahi a takaice inda Amir yake zaune yana wasa ta kalla tace my boy kaine wai kazama wani bulele haka dakai?
Nace anty aiko yama ramay sosai don tun shekaran jiya da muka dawo bai faye lafiya ba baya son cin abinci sosai sai anyi da kyat yake dan shan tea.
Ai dolr kuyi kiba kuna cin gashin kanku kun manta da kowa kina kokarin raba muna dan uwa damu.
Nace kai haba anty ni na ma isa na rabaki da yayan ki kin dai fada ne kawai ra,ayinki.
Amma ai tsakanin ki da yaya sai Allah tace lalaikan gani nan bari nan takalmin kaza.
Murmushi yayi daga inda yake zaune kusa da mama yace wai ke yaya zance da mukayi ne na ma,aikacin bakin da kikace min kin samu.
Ta wani lumshe ido tare da bin lafiyan kujeran da take zaune akai tace yana nan yaya.
Naga baka da lokaci ne ai sai na matan ka yanzu shi yasa ban fito ma da zancen ba ranan da kazo.
Yace kin san Fatima yanzun queen ce lalaba abata nakeyi a hankali don banson ganin bacin ranta akan komai.
Haka kuma duk wanda yai niyar bata mata rai wallahi sai inda karfina ya kare akan mai shi don bazan dauki rozarci akan iyalina ba ko kadan.
Tasan da ita yake wa warning don haka taja bakin ta tai shiru tana sauraren shi har ya kare zancen shi.
Yace mata ki fadawa mutumin yazo mu gana gobe da dare karfe takwas don kafin aiki ya taso min idan son samu ne ma har aurwn nake son ayi akafin lokacin.
Sai ya mike tsaye yana fadin shi zai fita nace don Allah yaya rogo nake so da zogala na dade ina son cin sa tun muna turai nake kwadan shi wallahi.
Na juya gurin mama ina cewa mama akwai man shanu ai ko ?
Tace akwai shi fatima yace yau kuma abinda kuke son ci ke nan kuma kayan yan kauye.
Abinda aka samu a turai ina shi ina kwadayin abincin yan kauye kuma maimakon yai kwadayin kayan sanyi.
Mama tai murmushi don sai yanzu ta fahinci wanan mugun kyau din da nayi bana banza bane ashe dama tai hasashen hakan amma sai taga ai Amir ko shekara daya bai kaiba watan shi ma na takwas ke nan da haihuwa.
Ko iya sai lokacin tagane ciki gare ni tace kai masha Allahu uwar dakina Allah ya raba ku lafiya yasa wanan karon ba dan zama asibiti bane kuma aka samu kamar maigidana cewa Amir.
Au ita yanzu cikine kuma da ita ina ruwan naga banza wai kina nufin kiyi saurin cika gida da diyan ki kafin wata ta shigo ko may?
Banza kuma Amira wai ke wata irin shashan yarinya ce mara wayo haka dake ?
Abin arziki ya samu maimakon kiyi farin ciki da karuwan da aka samu amma mugun halinki yakaiki ga hasashen banza kuma.
Kai maji nidai ba dama nai magana akan Bintu sai an zageni don tabi ta hada mutane da ku baku ganin kowa sai ita haba maji.
Nace nima anty wallahi ban so cikin nan yanzi ba Allah dai ne ya kawo shi don ban manta da wuyan da nasha ba gana wanan din.
Amma to yaya zanyi Allah ya riga da ya kawo shi basai na yi hakkuri ba da ikon Allah.
Amira kada fa naji kinzo kina karamin murya naba yara suzo maki weekend na hanaki kice zakiyi fushi ya fada mata hakana.
Komai Amira tai mai yana kokarin shanyewa ne don ya fahinci ita haka Allah yayita da bakar magana.
Shi kadai ne kawai nasu ke zuwa masu daya koshi don baya biye mata ne kwai suke zaunawa lafiya amma ita haka take da kowa ba dadi nata kalar rayuwan ke nan kuma ita.
Shi dai ya fita da yaji fadan mama ya tsanan ta akan Amira din yana cewa haba mama kiyi hakkuri da yar sister na ta dai kusa wucewa tabar maki dakin ki itama ta huta hakana kamar kowa.
Bai dade da fita ba sai ga yaro da rogo cike da zogala nan na zauna da kaina na shiga gyarawa hankali kwance kowa sai da yaci banda Amira da take ta faman fushi ita kadai.
Mukan sai faman hira muke da mama da su iyya da yar aikin mama din don mama bata dauke ta wata yar aiki ba can.
Ina basu labarin abubuwan mamaki da na gano a tafiyan mu da irin daulan da na gani a gidan Abu sifiyanu mai kudin duniya.
Duk sun natsu ina ta basu labarin irin daukakan da yaya sadauki ya samu a duniya ta wasan kwallo.
Tsukin Amira mukaji ta mike fuuu ta shige ciki cikin bacin rai dama kuma don ta kule ne nake kara bada labarin tunda na gane ita yar hassada ce a rayuwan ta.
Don maganan da tayi kan cikin dake jikina ya bata min rai dakewa kawai nayi kada mama ta fahince ni ta kara mata fada.
Baba ya aiko yana kirana nan na mike na saka gyale na nufi dakin shi nan na samay su zaune da mummy kusa dashi.
Na shiga da sallama na tare da gaishe shi yake cewa yanzu kubura take fada min cewa kun shigo ina barci nace takiraki mu gaisa.
Nace eh baba ance ka samu barci shine nace a barka tunda anan zamu wuni mun samay ku lafiya ko ?
Yaya karfin jikin naka kuma yace Alhamdullahi Fatima ai iyayyen ki gasu nan suna bani kulawa sosai wallahi.
Kinga ita wanan ma yanzu ta aje aikin ta don lalura na itace take min komai ita da hauwau.
Jiki kan naji sauki sai dai tafiyan da ban iya yi ne kawai har yanzu matsala koshi likita yace insha Allahu da sannu zan dan iya fara takawa.
Nace Allah ya nufa baba ya amsa da Ameen Fatima yaya maigidan naki kuna dai lafiya ko?
Nace lafiya muke baba ai tare ma muka shigo dashi ya tafi ys dawo ne yabar mu anan.
Fatima Allah yai maku albarka a rayuwan ku ina mai alfahari da kasancewar ki mata a gurin sadauki.
Don nasan wani abin tare da taimakon ki ne yake yin shi a rayuwan shi yasa Allahda Annabinsa sukace ku auri mataye na gari don ku sama ma diyan ku uwaye na gari a rayuwan su.
Ke alheri ce sosai Fatima a rayuaan dana wanda ina matukar alfahari da hakan ko yaushe kasancewan shi tare dashi yasa sadauki gaba daya ya sauya daga sadaukin da muka sani a baya.
Duk wani mumunan halaiyar shi yanzun yazama tarihi a gurin mu da bakece ya aura ba da sai dai muce Allah ya kyauta kawai.
Gashi natashi kudi suna shigo mai ta ko wani hanya may zai sashi tunanen gyara wani mugun halaiyar shi can na baya da basu da kyau da ai saidai kawai yaci gaba da gurbatacen rayuwan shi babu mai kwabon shi a kai.
Amma duk irin kokarin da kikeyi a kan shi ina da labarin komai a kunne na Fatima.
Allah dai yai maku albarka yasa ku gama da duniya nan lafiya yabaku zuria dayyaba masu maku biyayya kamar yadd kuke muna.
Na amsa cikin kunya da Amin baba na gods nima da kuka mai da rayuwana haka don kune silar komai da nake ciki a yanzu.
Yace kai haba dai Fatima ai mune dai da godiya a kanki yadda kikai muna biyayya haka yau gashi ya zama muna alheri ga baki dayan mu ko.
Haka dai nabar gurin baba yana ta saka muna albarka da fatan gamawa da duniya lafiya a rayuwan mu kamar yadda ko wani da ke bukatan addua ga mahaifan shi kullun.
Sai dare ya dawo ya kwashe mu muka bar gidan zuwa gidan mu cikin farin ciki a ran mu yadda iyayyen mijina suke zuka ma rayuwan mu albarka haka.

Muna hanya nake cewa ashe mummy tabar aikinta ne akan rashin lafiyan bab ?
Yace wallahi fa haka sagir ya fara fada min da kuma naje gun baba din shima yake fada min haka din.
Nace ai ko ta kyauta wallahi don haka shine zama tare yace ai zan duba akan al, amarin don asan abin da za, ai mata akan haka din.
Nace yaya bafa mummy ba kawai dukkan su sun bukatan taimako wallahi don alama ya nun sun a cikin wani hali wallahi ba dadi da ganin su.
Yace nima nai tunanen hakan amma banji kince komai ba shi yasa nai shiru nima.
Nace kai haba yaya nice kuma zanyi magana akan taimakon iyayyen mu yace bakece P A ba ke ce ya kamata ki tsara abinda ya dace a kan su ai.
Nan na shiga zaiyano mai abinda ya dace ai masu din don a taimakawa rayuwan su har muka kai gida kowa ya shiga part din shi don watsa ruwa ajikin mu ko zamuji dadin hakan.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: I'mIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA

Please Login or Register in order to submit comment