Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su gas, su tv, fridge, toaster da yan kayan kitchen electronics akwaisu a kitchen din.
Yan zuwa jai kaya suka dawo suna fadawa mama abinda ya faru a gidajen mi mama tace a daikai nata da ta saya muna hakk8n mune ta sauke muna ai.
Saura kwana hudu buki ya shigo cikin gidan duk gidan a lokacin cike yake da baki yan zuwa buki yan uwan hauhuwan maji da ga garin su sunzo.
Dakin ta ya samay ta da wata yarta ta dagin su mama take ce mai bayan sun gaisa dama ina son na gan ka don gobe ko jibi nake son akai Fatima gurin iyayyen ta don su ma suyi nasu bukin a can tunda ita yar fari ga mahaufin ta.
Shiru yayi bai dago kai ba tace don haka sai naji naka shawaran akan tafiyan nata don ban san ko kana da wani shiri ba ?
Yadago idon shi da suka canza launi yace maji ni wani shiri nake dashi duk abinda kuka tsara ai daidai ne.
Ta kara cewa ina son ka basu mota da sauran kayan da zasu bukata a can akai masu don zirga zirga da amfanin su.
Baiyi magana ba nan ma shiru yayi yana tunane wa maji ke son na tura wanan bakin kauyen ya kwana can gari ba wuta ba wani abin more rayuwa can.
Ranan da za ai kamu gidan mu ya cika makil da mutane yan uwa da abokan arziki ta ko ina na bangaren dakunan gidan.
Mata mu hudu ne maza ukku, sai dai a lokacin na bata tsarin abin don duk yadda akayi dani na fito zuwa gurin kamun naki futowa nashige bandaki na kulle kaina ciki.
Mama tace a kyaleni tunda bani son fitowa agan ni ai hakan ba ibada bane ga mutane yan gulma da basu sanni ba sun cika gurin don son ganin kwam.
Sai da naji ba kowa a shiyan duk sun watse sun tafi gurin kamu nafito na zauna a bakin gadon mu nai tagumi ni kadai a dakin.
Sai ganin mama nayi tashigo dakin abinda ya dan sani firgita ke nan zan tashi tace koma ki zauna abinki na fahinci baki son ai maki kamu a garin nan sai a gaban iyayyen ki ko?
Don haka kada ki damu gobe insha Allahu za,a tafi dake can zamu washe gari muyi maki naki a gidan mahaifan ki.
Kuma kinyi gaskiya don wanan halin naki yasa nake kara kaunanki Fatima a raina don baki dauki karyan duniya ba ke a ran ki.
Muna nan zaune tare da mama a daki har mutane suka fara shigowa tana kara yi min nasiha akan duk rayuwan da zamuyi na daure nayi hakkuri watarana sai labari insha Allahu.
Ganin mutane sun fara shigowa yasa ta barni ta koma dakin ta sai lokacin ne na dan sake jikina nan na fara shirin tafiya don tace da safe zamu tafi garin mu.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA YA KARANTA ALLAH NAGANIN KI ZAI KARABAN MIN BASHINA GOBE GARE KI,,,,


A LOKACIN MUKE,,,,


Amaryam kan ta tare gidan angon ta Atiku maria haka ta kwana a cikin bakinciki ranan don tashin hankali.
Washegari da safe ko kafin ta gama barcin ta data saba tafito ta samu har amarya ta fito ta gyara gida ta dora ruwan zafi a wuta.
Ganin maria ta fito lokacin tana tsaye tana tara kwanon da tukanen maria, da yaran ta suka bata tun safen jiya har yau.
Bingidan maria tayi da kallon yadda ya sha gyara ko ina, ina kwana ?
Amarya Sadiya tace mata, cikin haushi ta amsa mata tace lafia kawai,
Ta wuce zuwa bayi ta kewaya tafito tafara alwala duk abinda amarya keyi tana binta da ido.
Bazata gwada wa amarya sadiya shekaru ba itma dai sadiya din zasu zo sa,a daya da maria din.
Kafin duk yaran maria su tashi har sadiya ta dama kunu, ko sai ga maigidan ya shigo wanda tun fitan shi masalaci suna can suna zikiri bai dawo gida ba sai yanzu da gari yadan haska.
Yana shigowa ya samu sadiya ta zuba kokon da ta dama ga sabbin robobin da tazo dasu gidan.
Inda taimashi sannu da dawowa ta dauka takai katon roba mai kunu kofan Maria ta girke masu ta dauki nata da mijin ta tashiga dashi dakin ta.
Sai gata tafito da sabon bucket a hannun ta ta deban mashi ruwan wanka takai mashi bayi.
Zata fito ne ta samu maria ta idar da sallah tafito waje tace mata ga kokon ku nan a kofa na aje maku sai ruwan wanka dana sa su fito su fara wanka kada su makara zuwa makaran ta .
Wani kallon banza maria ta watsa mata tace da baki gidan wake basu ruwan wanka dama kada ki kawo min sallo da iyawa don gidan kika shigo.
Kuma ki koma ki dauki munafukin kokon da kika aje don mu baza musha abin sihiri ba wayasan inda kika fito da tarkacen tsiyan ki da zaki wa mutane sihiri kice wai kin dama.
Haba yar uwa gumbane fa akayo muna shi wanda zamu amfana dashi kwana biyu a gidan nan.
Munafuka mun san irin ku wazaki cuta sai dai shi daya daukowa kan shi, bata karasa ba Atiku yafito daga dakin amaryan nashi.
Yace ke Maria wallahi ki shiga taitayin ki idan kikace zaki tirka min tsiya agidan walle na lahira nafin ki jin dadi.
Ke ga kina iskancin ki nakawo ijjiya na saka maki ba fa fin karfina na kin yi ba.
Raga maki dai nakayi don wa yanga yaran dakin ka gani ko suma yaran ba tausayin na kikayi ba da kina tasaya masu da baki kaisu mahalaka ba ke illata masu rayuwan su.
Duk wace tace tashin hankali da diban albarka zata aza min agida bani daukon shashan ci yanzo don zama da mace ba dole na ba.
Aliyu kai, Aliyu ina kake na ?
Sai ga yaron ya fito yana sharan fuskan shi yace baba gani.
Yace ku tai zuwa sallah in kun dawo ku taho ku karya kutai zuwa makaran ta kajiya.
Sai amaryam tace gama ruwan wanka ceniya ga na aza masu suyi wanka sutai zuwa makaranta.
Yace ke baki kunya ba maria, yaushe kika tashi warhaka har ki dama masu kunu su sha suyi wanka da safiya haka.
Kuna na dai ko inke baki sha diyana sha sukai inga ta tsiya yau inkin isa, in tsiya kika so ko wane irina samunai ki kai ga Atiku.
Ya juya ya wuce bandaki zuwa wanka nan yabar maria na fadi ashe akwai wadda akai agidan ga don walle in mace tace makirci ta iya gida nai ta taho wallah.
Ni dai ba tashin hankali nishigo gidan ku yi ba aure na yakkawoni kuma ni tsakani da,Allah nika zama da kowa a rayuwa na don banda mugun nuhi akan kowa.
Amma fa ki sani inkice ba wanga zama kika,bukata a gare ni ba duk wadda kika so yinai zamuyi keji na hwada maki wallah.
Ta juya ta shige dakin ta tafara gyarawa kafin mijinta da ya,shiga wanka yafito ta saka turaren wuta daki ya dauki kamshin safiya.
Maria na jin kamshi har dakin ta rayuwan ta yai matukar baci tace a fili karuwan banza kawai.
Mamakin ta bai kai karshe ba sai da taga Atiku ya fito cikin wankakun tufafin shi Sadiya ta rako shi har kofan fita daga gidan ta kai tsugunne tana fadin.
Ya Allah ka tsare muna bawan ga na ka bashi sa,a da rabo na alheri, ka bashi sa,a ga abin daya fita nemowa yaciyar da mu ta hanyar halal ya Allah ranan taga dariyan Atiku har sai da hakoran shi suka baiyyana a fili.
Duk maria tana daga kofan ta tana kallon bakon al,amarin da ya shigo masu a gida.
Atiku yafita cikin jin dadi yana fadin Ameen Sadiya nagode nagode Alkah yasa ki zama min alheri a rayuwana.
Yana fita daga gidan maria tace wai sabon kicihi can muka fito har takalman ya tsinstinke indai namiji ayi dai mu gani gidan ga.
Sadiya kamar bataji may maria take fadi ba ta,share ta dakin ta takara gyarawa tsab tafito kofinan da yara suka sh koko kafin su fita ta tattara su ta wanke da sauran kayan da tai aiki dasu.
Kagin amarya tai kwana hudun ta maria ba karamin wahala tasha ba saboda Sadiya mace ce mai tsabta da mijin su ya dawo gida kayan da ya cire na aikin shi bata bari ya kwana bata wanke su ba.
Haka dakin ta duk da ba komai a cikin shi sai ta gyarashi sau kusan hudu a wuni.
Maria sai habaici da bakar magana take yaddawa cikin gida tai ta faman fada da yaran ta tana sauke haushin uban su, a kan su.

****** ********* ******
Wanka nayi don shirin kwanciya saboda ban tsaya dogon hira ba gobe mu da lecture mai zafi da zamuyi.
Dogon riga fari mai dan hannu na dauka na saka a jikina ina kokarin daure kaina sai ga mama tashigo dakin namu.
Tace dauka niyi ai keyi barci Fatima?
Nace a a mama yanzun dai naka shirin kwanci wani abu zan maki mama ?
Na tambaya cikin dan kallon ta a cikin ladabi da nake mata a koda yaushe in muna magana da ita.
Tace, dama magana naka son muyi dake inba ki komai ke jiya.
Nace walle mama mi nikai mashin ?
Kwacinya dai naka shirin yin yanzu don gobe muna da lecture da safe insha Allahu.
Ta juya tana fadin ki saman a daki na yanzun in ke gama.
Daga haka ta juya tafita daga dakin ina gama daure kaina nabi bayan mama dakin ta.
Na samay ta zaune a saman gadon ta sai dai yanayin ta kaman tana a cikin yar damuwa a lokacin.
Ganin na shigo takw ce min zonan ki zauna Fatima tana dafa gado daga gefen ta alama take min a gurin zan zauna ke nan.
A darare na zauna dan bakin gadon kadan dan nesa da ita, sai naji ta dafa hannu na daya tana fadin Fatima magana nake son yi dake don haka ki fahince ni kuma idan magana na da takura a cikin shi kada ki damu kanki don Allah Fatima.
Nace mama hwadi dai maganan ki ai babu komai walleh na fadi cikin murmushi don nasan dai kila laifi nayi zatai min magana.
Tace Fatima ina fatan bazaki fassara min magana ta ba da wani fasara gani ke dai kinka cancanci hakan shina yasa na aiwatar da hakan akan ki.
Tace, bakomai na ba so dai nakai ki auri sadauki don dai ta kin ka san halinai kuma kina iya hakkuri akan duk wani baudaden hali nai.
Kamar a mafalki naji zancen mama take duk da sanyin da dakin ta keyi na A C sai da naji zufa na karyo min.
Tace na san cewa keta zaki iya hakkurin zama da yayan ki kuma ki rufa mai, asiri ga duk wani rayuwa nashi.
Wanga dalili dana hwada maki shina yasa na yanke hukunci a raina keta zabina dama shi din.
Tace Fatima nasan cewa a ranki zaki iya cewa missa nai maki wanga mumunan zabi a rayuwan ki .
To maganan gaskiya gani nayi duk matan da yay aure babu komai cikin wanga aure nashi in ba tonon asiri ba a garai.
Har da nima uwatai, ke har yan uwa nai sai gori ya ishe su gidan ga.
Ba yau ba na dade ina wanan hwatan ni kadai a rayuwa ta, amma na rasa yadda zan hito maki da zancen.
Amma yanzu nasan ke dan tasa shekarun ki yakai ta fahinta shinasa naga gara na hwada maki dai don ki san abinda naka kullawa a tsakanin ku.
Wagga magana kuma da naka hwadi Fatima har tai kunnen Baban ku yasan da ita.
Shima dai ya nuna farin ciki nai akan zancen, sai naji muryan ta ya canza tana cewa cikin murya mai kuka.
Fatima Allah yasani ban yi wanga hadin don dai na cuta maki ba, nayi shina dai don samun farin cikin ku baki dai.
Nasan cewa har yanzu bawai ya bar shan abinda yakasha bana ke ma ke san da haka Fatima, hwada min faina bakiyi.
Don kina gudun bacin ran da zan shiga ciki nai shina yyasa baki son na sani.
Fatima ance wanda ya rigga ka kwance yana riga ka tashi na san komai da sadauki kayi, a rayuwa nai don nita na haifi abina,.
Nasan halin rayuwa nai sarai shi dai nayi don gujewa masifan da a ciki nai tunda ya boye min shina yasa nima nabar abin aboye kaman yadda kuka boye min din.
Shin Fatima macen da ka irin wanga halin ai ta san kan ta na inda baki san kan ki ba duk wadda naka gwada maki halarci sai kin tai kin hwadai wani gurin.
Ko ni ki hwada min nasan mi yaka ciki, amma kinka iya boye zancen sai kokari kikai kiga ya bar wagga har kan ke dai.
Fatima kiwa Allah ki taimaka min akan wanga yaron don ban san mi, Allah ka nuhi ga auren ku ba.
Nasan cewa na hada ki da aiki Fatima, amma gani nayi ke ta kadai ka iya tayani wanga kwaran ba tare da anjiya ba.
Sai tai shiru kuka ne yafi karfin zunciyan ta a lokacin don haka ta kasa ci gaba da maganan ta.
A hankali na zamo daga saman gadon da nake zaune tare da durkusawa daidai kafan ta nima dai din kuka nake sosai.
Kaina ta dafa tace nasan baki son wanga hadin da naka shirin maku don shi ba son kina yakai ba.
Amma na sani Fatima an, walleh sadauki sonki yakai so daina bai sani bashi, a ruyuwa nai.
Kuma in kunyi aure duk bari shikai da yardan Allah ba zai wulakantaki ba Fatima an kuma ni ban barin hakan ya hwaru tsakanin ku.
Jin tai shiru ni kuma ina duke na kwantar da kaina saman cinyan ta sai darzan kuka nakeyi.
May zan bata amsa dashi nace ban son mashayin dan ta ko may, ?
Inace bata kyauta min ba don batai man adalci a rayuwana ba duk da nasan batai min ba din ko may zan ce mata?
In ce, mama kin cuce ni da kika hadi da danki mara mutunci mara tarbiya lalattace ko may?
Ince bata kyautawa rayuwana don da itace ta haife ni da cikin ta bazata taba min wanan zaben da tai min ba ko may?
Haka yasa naja bakina nai shiru sai kuka nake yi wanda na rasa kukan mana wani cikin tunane na nakeyi?
Shiru itama mama din tayi tana nata kukan tana sauraren nawa da nakeyi cikin tashin hankali.
Fatima nasan zaki ce ban kyauta maki ba a yanzu don bazaki gane may nake nufi da wanan hadin da nayi ba.
Amma nasan nan gaba idan ina raye insha Allahu zaki gane haka kuma zaki gode min a rayuwan ki.
Fatima gida bai koshi ba ai ba akaiwa dawa muma nan mu na bukatan kki a cikin mu, don haka mi zai sa in bari wanan baiwan taki ya tai gidan wani ina kallo bayan muma nan muna da bukatan ki a cikin mu.
Ban iya cewa uffan ba har lokacin sai naji muryan mama tana fadin tai ki kwantawan ki keji indai kega da takura ki hwada min sai a hwasa.
Da kyat na mike na fara tafiya kuka yaci karfi na don haka dashi na fita dakin mama tabi bayana da kallo tace a fili.
Fatima am sai dai kiyi hakkuri don abinda ka hissheni na nakayi ke kadai ta ka iya halin wanga baudaden yaron da Allah yya ban.
Kuka sosai nake a daki ni kadai gashi uwayen kallo suna can falo har wanan lokacin suna kallo.
Maryam kamar an tsikare ta sai gata tashigo dakin dan wakan ta, sai ganina tayi a kwance na kifa ciki ina darzan kuka ni kadai a dakin.
Mi nika gani haka shin?
Missa may ki Bintu?
Sai ma kara sautin kukan dana dan yi ban bata amsa ba, itakuma bata fasa tambayana ba tare da zaunawa gap dani tana tabani.
Bintu baki hwada min ko missa may ki shi,?
Ko sai na tai na hwada ma maji ta taho ta tambaye ki da kan ta?
Ba amsa sai ta mike zuwa kiran mama don tazo ta tambaye ni da kan ta.
Riko hannun ta nayi nace cikin kuka anty don Allah ki dawo kada kitai wurin mama don tasan ko may nakewa kukan.
Shi wai minana dan Allah missa may ki kika wanga bakin kuka, wane irin bakar dabi,ata haka shin?
Cikin wanga dare ke zauna a daki ke kadai sai kuka kikai kaman wadda aka aikowa mutuwa?
Shi ko wani na yya mutu anka bugo maki waya wai ?
Na fada jikin ta nace anty na shiga uku na lalace anty mika shirin hwaruwa dani na wai ?
Shi wai mi an kayi na wai baki hwada min don Allah na sani ?
Gashi kece kan na kira maji ta taho tagane ki shin minana hallan?
Ina kwance a jikin ta nace anty na ga boni na lalace shi mi nai wa Allah da wanga bakin rayuwa ka shirin fada min ?
Wane irin rayuwa na ka son hwada maki ?
Wai yaya sadauki mama ka son na aura Anty yaya sadauki mutumin da duk duniya baida bakiyiya irina don dai ina hwada mai gaskiya.
Wani kallo ta watso min tace Bintu auren yaya sadauki na kika wa wanga kuka haka shi ?
Dama ba soyayyana kukai dashi bana ?
Da sauri na girgiza mata kai nace ba wani zancen arziki da ya taba shiga tsakanina dashi ni dai nasan kaman annabi da kafiri muke ni da shiya.
Maji na ta hwada maki haka ko wa?
Nace ita ta ttakirani dakin ta taka hwada min bukatan ta garan.
Yanzu kibar kuka Bintu muyi magana ta fahinta da keya don wanga kuka da kikai nima kuka na kason yi.
A hankali na sasauta kukan da nakeyi don inji may zata fada min, ganin na rage tace shin Bintu ke baki son yaya na ?
Nace walleh anty ban taba so nai ba a rayuwata mi zan yi da mutumin daya tsane ni a rayuwa nai?
Tace ke yanzu zaki iya hwada ma maji baki so nai?
Ta kura min ido cikin kuka nace walleh ban iyawa anty amma da ma mama na tai min wagga magana ba gaskiya hwada ma mai shi magana nakai.
Tace to ke gani.
Ni yanzu shawaran da nika baki shina hakkuri dai zakiyi kada maji ta fahinci haka gare ki.
A yadda nasan halin nai shina kashirin balgace auren da kan shi ke ga dai ke komi bai hito ta bangare ki ba.
Ko mi kki gani ga magana ta ?
Maganan ta dutse don shine mafita a gare ni nace cikin kuka anty na gode shawaran ki na zanbi don shina kadai mahita agaran.
Tace to ke gani amma a,a kika zama cikin daki ke dai kina wanga irin darzan kuka mi da baki kirani ba tundazun muyi shawara shin.
Tace ke ga yanzu in yya jiya nasan ba karamin rigima zaiyi a gidan nan ba, tun da shi arniya mai dan buje yaka so.
Wanan magana shine ya kwantar min da hankalina nan muka raba dare muna magana akan zancen har barci ya dauke mu zuwa asuba.

****** ********* ******
Tun ranan da akai zancen naji ban kara ganin shi bani haka nake ba walwala tare dani ko kadan yanzun ma idan na dawo daga school ban zama a falo ina dakin mu.
Don ni idan da hali badon na gudu mama tace ban mata diyyauci ba da na gudu daga gidan gaba daya.
Shima haka sadauki bai shigo ba gidan tun ranan da Baba yai mashi magana.
Haka ya gaji da fushin shi ga kiran da Amirah ke damun shi dashi tana tambayan shi ko yai tafiyane bata ga ya shigo ba don ita batasan dawan garin ba.
Maryam bata fada mata ba don ta fahinci Amirah bata kaunan hadi tsakanina da yayan ta don ita a ganin ta yayan ta yafi karfi wata Bintu can yar kauye can.
Don idan maryam na magana tana min sheri kan yaya Anty Amirah bata iya boye kin da take wa hakan a zuciyar ta.
Tashiga fada ke nan da maryam tana cewa kefa baki da wayyo don Allah may ye kuma na wanan magana ba dadi ina yaya zai kai wata Bintu can kuma haka.
Ina gani maryam din tagane zuciyar yar uwar ta ne yasa ta ki fada mata komai akan halin da ake ciki.
Mun tafito zamu school muka ganshi tsaye a kofan gida shi da wani mutum da gani dai mutumin ya girmay shi sosai.
Ina ganin shi na dukar da kaina kasa ban yarda na kalli inda suke ba inajin maryam tana gaida shi ni kan ban tsaya ba na wuce abina.
Sai dai shi muna fitowa idon shi akan mu don yana facing din hanyar fitowa daga cikin gida.
Ya ramay ya dan fada kadan sai dai ba kowane zai gane hakan ba sai wanda ya sanshi sosai zai iya gane hakan.
Ina tsaye tazo da motan ta ta dauke ni muka fara hanya, sai da muka dan yi nisa take cewa Bintu nace na,am anty.
Mayasa baki gaida yaya ba ?
Shiru nayi ba amsa tace indan kina haka maji bazata ji dadi ba gaskiya na fada maki ki nuna bakomai a zuciyar ki haka zai sa tafitar da zargin komai a kan ki.
Nace anty ni wallahi ban son ganin shi ma yanzu bakiji yadda nake jiba a halin yanzu dana gan shi a zuciyata.
Kada ki damu insha Allahu komai zai zama normal amma sai inkin bi shawara na fa.
Don haka dakikeyi kin san yafi wayo zai iya hada ki da maji laifin ya koma akanki don haka ki gyara halinki tun wuri har inkina son kanki da lafiya.
Ban tanka mata ba shiru nayi tare da kwantar da kaina ga glass din motan ta kawai.
Can tace dama ina son indan mun tashi daga makaranta na fara koya maki mota.
Da sauri na dago kai ina kallon ta nace, mota anty ni ina zan samu mota kuma?
Dariya ta kyalkyale dashi tace kin san abin Allah ne yar uwa da zakice haka?
Muna wucewa ya shiga gida bayan bakon shi ya wuce daga mamane sai Amirah zaune a falo suna karyawa a lokacin.
Amirah tana ganin shi take cewa kai yayana har zan kai cigiya da sanarwa gidan redio da talabijin a kan ka.
C U yace an fada maki ni raggone da zan bace ko ni bakauye ne da zanbace maku?
Ya juya gurin mama yace ina kwana maji cikin

Please Login or Register in order to submit comment