Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ban sani ko ku kunayi a gidan ku shiyasa kake ganin duk mata haka suke.
Dago kai yayi ya kalleni yace dakata kada wautanki ya kaiki ga zagin gidan mu yanzu na koya maki wayyo a gurin nan.
Shiru nayi don nasan zai iya idan na kara magana na fara shan dan faten da na zuba a plate a hankali.
Banyi ko rabi ba naji na koshi sai na fara juya cibin kawai ina wasa dashi a plate din a hankali.
Yana kallon abinda nakeyi bai min magana ba har yagama ci na mike zan fara kwashe kayan.
Yace shiyasa baki kiba oya maza ki cinye abincin nan kafin nazo na sure ki dashi yanzun nan.
Don bakin barna kinga banza yasa kika dafa da yawa kin san baki ci?
Na turo baki gaba nace nifa gaskiya na koshi don ban jin yunwa saboda ba abinda na hade balle yunwa ya damay ni.
Tsawa ya daka min yana fadin will you finish it my friend ?
Dole na dan fara turawa kamar zanyi amai ga nauyi da kunya da suka cikani lokaci guda.
Ganin saura kadan ya mike ya bar gurin na zaci fita zaiyi amma sai naga ya koma saman kujera three seater ya kwanta tare da dora kafan shi daya saman kan kujeran.
Kitchen na shiga na wanke kayan da muka bata na kara gyara gurin da mukaci abinci na juya zan shiga daki naji yace.
Waye dan gadin gidan ki kina daki ina falon ina maki gadin gida maza ki dawo nan ki zauna mara kunya kawai.
Nace ikon Allah nifa ba boya bace don naga kana son mayar dani kamar wata wacce ka sayo.
Yace amma ke yarinya ce karama ba,a fada maki cewa sadaki na biya bane lakadan ba bashi ba kikazo gidan nan ne ba wai.
Don haka ina da right din da sai abinda nake son za,ai min a cikin gidana idan kuma kince ba haka ba sai na kira maman naki da taci kudin sadakin nawa tazo nan tabani abina yanzu.
Don ba zan biya kudina ba don bukata na kuma a kun tata min a banza yadda nace dole shi za,ayi a gidan nan kinji na fada maki daga yau.
Haka na dawo falin na zauna ina jiran wani sabon cin mutunci daga bakin shi kuma.
Bai min magana ba sai wayan da yake ta bugawa ana kuma bugo mashi wanda akasari murna ake mashi kan auren da yayi.
Sanyin A C da yai yawa a falon yasa na dan takure a guri guda har barci ya daukeni a zaune ban sani ba.
Jin kaman nai barci a inda nake zaune yasa shi juyowa yaga ina barcin kuwa.
Ido ya kura min har tsawon wani lokaci yana bin ko ina na jikina da kallo har tatsun hannu na da kafa sai da ya kare masu kallo lokaci mai tsawo.
Nikan sai barcina nake hankali kwance jin kaman an tabani yasa ni farkawa furgigit idon shi a kaina.
Na turo baki tare da gyara wuyana da yai min tsami nace ni dai in mutum yana maita ne ko shan jini wallahi kurwa na kur akan shi.
Dariya yayi yace yar kauye kona kara maki karfin A C din ne don naga kinji dadin hakan har da sake min baki kina barci.
Nace inda bamu dashi ne a dakin uwata sai kai min gori dafin abin kafin kayi kudin ka kaganta dashi.
Yace ai nasan shi ya jawo ki yanzu tunda can kauye babu shi anzo an samu na banza ana sha nan.
Nace dakata wallahi gida gidane haka uba ubane kada ka kara zagan min gidan iyayye na nima.
Yace idan an zaga may zakiyi nace na rama aiko yayo kaina cikin tako daya duk yunkurin mikewan da nayi nagudu sai da ya cin min gurin.
Nan ya matse ni saman kujeran muna shakan nunfashin juna yace ki rama din ina sauraren ki.
Shiru nayi ina fadin ka sake ni kawai mugu sai kara matseni a kirjin shi da yayi bai sake ni ba.
Wani irin bugawa naji kirjin na yi fal, fal gashi kuma bai sake ni daga jikin shi ba.
Nace cikin karfin hali mugu kawai ka sake ni wallahi ko na fadawa mama cin amanan da kake min yanzun kuwa.
Yace go ahead kirata yanzu tunda baki da kunya ki fada mata na matse ki ko ?
Sai da ya gaji don kan shi ya sakeni daga jikin shi na tashi da sauri nai daki ina fadin mugu kawai ni bari ma na cire kayan nan don sun haramta gare ni daga yau.
Yace wallahi duk kika cire kayan nan sai na tube ki zindir a gidan nan naga tsiya.
Ke har wata mace ce can da kike ganin kamar kina da wani ajine wai?
Daki na koma na zauna a bakin gado idanuwana suka ciko da hawaye don takaici.
Nace a raina may kullun yake nufi da fafin wani har mace ce da za,a gani aji sha,awan ta ko may ?
Muryan shi naji daga falo suna gaisawa da wasu haka yasa da sauri na saita kaina nasan baki mukayi a gidan.
Ashe yan uwan mamane suka zo gaida mu da kuma yi muna sallama washe gari zasu koma gida.
Shi ya shigo yana fada min zuwan su tare da jamin kunne na saita kaina in har na bari suka fahinci wani abu har naja sukai mashi fada sai na yabawa aya zaki.
Nafito ina murmushin dole nace lah mama kune ashe sannun ku da zuwa.
Maimakon na zauna saman kujera sai na zube kasa ina gaida su a cikin girmamawa.
Masha Allahu Baba kaikan wallahi kayi dacen mata a rayuwan ka yarinya haka da ladabi, yaushe yaran yanzu masu rawan kai zasu tsaya yiwa sarakai wanan gurmamawan haka.
Baba don girman Allah ka rike matar da daraja ku mutunta junan ku, ku rufawa kan ku asiri a tsakanin ku.
Darajan miji shine na mata yadda ka mutunta matar ka haka duniya zasu mutunta maka ita.
Ke kuma Fatima don Allah basai mun fada maki ba don yaran yanzu boko yasa kun san komai na rayuwa zaman takewan aure sai dai idan kun ki amfani dashi kawai.
Don haka kin dai ga yadda uwar ku take rayuwan ta a gidan ku idan kinyi koyi da halin yayan mu da kika zauna da ita babu wani rayuwan da zai gagareki hakkuri a duniyan nan.
Don haka yi nayi bari na bari abinda duk mijinki bai so kin sani, don kun zauna guri guda gwargwado kin san halin shi yasa naki.
Gaba dayan ku idan kuka ba da kunya uwar ku kuka tozarta ita da taga dacewan hakan ta hada ku.
Komai yaya bata boye muna ba na hadin da tai a tsakanin ku kuma ku yanzu bazaku taba fahintar manufan ta ba sai nan gaba.
Don haka ku taru kuba mara da kunya ku kashe ku bisa a tsakanin ku ba komai ne ma ita yayan sai taji shi ba tsakanin ku duk abinda zakuyi ku boye sirin auren ku tsakanin ku don gujewa shigan ta wani hali.
Kai kuma Baba don Allah duk wani abin kurciya da akayi sai abarshi a matsayin kurciya ne yanzo kakai ga tara iyali nan zuwa badi war haka in Allah ya kawo rabo sai kuga mun dawo taron suna gidan nan kuma.
Nan dai sukai muna nasiha ma ratsa jiki suka zauna nan tare dani sai dare suka koma gidan mukai sallama cewa bazasu dawo ba kuma.
Har kofa na raka su suka tafi suna muna fatan alheri da samun zuria ta gari.
Suna wucewa na koma ciki wanka nayi tare da sallah ishai na zauna ina zikiri naji dawowan shi gida tare da rufe kofan gidan.
Hakan yasani sani bazai fita ba ko ina ke nan again ganin shi nayi tsaye da farar leda a hannun shi, na dago kai na dube shi ban san yaya akayi ba naji bakina yana mashi sannu da zuwa a lokacin.
Ledan ya miko min yace na dafa mashi liptop din dake cikin ledan naman kuma na kai mai falo saman dining zai fito yaci.
Inda ya aje min saida na shafa namike zuwa yin abinda ya sani na fara dafa ruwan liptop din batare da na tsaya karan ta kona maye ba.
Na fito na aje mai naman da zafin shi a table tare da ruwa da drinks mai sanyi.
Ina kitchen naji fitowan shi, falon ya zauna ya fara cin naman da na aje mashi.
Sai da na juye ruwan ga wani dan karamin flask na hado da cup na nufo falon yana zaune yana cin naman shi hankali kwance nace ga shayin na dafa.
Ya dago kai yace injin baki zuba sugar ba a ciki nace mai a,a hakana na dafa don ban san ko na may ye ba.
Da hannu ya nuna min na aje anan ina ajewa na juya zan shige yake cewa ke bazakici naman bane ?
Na koshi na bashi amsa a taikace yace may kikace ban fa son shegen gardaman nan naki kinji na fada maki.
Nace naci abinci a dasu mama na koshi dazun kafin su wuce don sai da nai masu girki sukaci da yamma.
Baice min komai ba na juya na shige na zaci daya gama zai shigane amma sai naji ya kunna TV dake falon ko da ban fita ba wasan kwallo akeyi a tv nace bissimillahi Allah nazo gidan masu yi.
Ni dai har barci ya kwashe ni ban san lokacin da ya shige ba sai tsakar dare na falka naji shiru na kara jan bargona na gyara rufe jikina da kyau.

****** ********* ******
Haka mukaci gaba da rayuwa a gidan zaman doya da manja ba wani abinda ke shiga tsakanin mu sai in yana bukatan wani abu zai shigo daki ya fada min.
Sai dai a nawa bangaren ina hankalina a tashe yake don ina ganin bazan iya cika alkawarin mama ba akan shi don a halin yanzu ban san wani rayuwa ma yake ciki ba agidan sunan muna gida daya ne kawai dashi.
Satin mu uku da aure na gama komai gashi hutun mu ya kusa karewa zamu koma school wani sati.
Sai ganin shi nayi dakin lokacin ina kwace na kifa cikina a saman gado ina sauraren kira,a a wayana kaina babu dan kwali na daure gashi na da ribon ta baya ,
Ganin ya shi ya shigo yasani saurin lalabo dan kwalina na daura akaina kallona kawai yayi ya basar kamar bai san may nakeyi ba.
Yace ke nazo na fada makine yau da dare zan koma gurin aikina don haka sai ki fada min abinda kike bukata a sayo maki idan na fita.
Nace ni ban bukatar komai sai dai Monday mai zuwa zamu fara school insha Allahu.
Yace gashi ke baki iya mota ba balle na bar maki motana kiyi amfani dashi sai kuma idan wani driver zan samo ya dinga kaiki.
Nace ai ko da kake daukata yar kauye ba wai doluwa nake ba yadda kake tunane don ni mota kuma yanzu sai dai na koyawa wani tuki.
Fatan kawai yanzu Allah ya hore min yadda ya horewa kowa na samu nawa na kaina insha Allahu.
Kallon mamaki take min kaman zaiyi magana sai kuma yai shiru kawai yafita daga dakin.
Duk da nace komai akwai shi a gidan amma sai ga kaya niki niki maigadi ya shigo dashi wanda kusan yan kayan lashe lashe ne a cikin kwalayen.
Sai da yai wanka yafito ina kitchen ina girka abincin dare ya zo bakin kitchen din ya tsaya yake ce min zancen motan da mukayi dazun na binciki maryam ta fada min ki gwane don kece ke jan ku zuwa school don haka ga motana nan zan bar maki ki fara amfani da ita kafin na duba wanda ya dace a sayo maki.
Ni zan shiga gurin maji nai masu sallama kagin dare yayi min sai ji nayi nace ni dawa zan zauna cikin wanan katon gidan haka.
Yace kedawa kikazo gidan nan dama baki san gidan yadda yake bane kika shigo kai tsaye.
Shiru nayi nace to don Allah ko na roka kanina musa yazo ya zauna dani kafin ka dawo.
Yace no kada ki fara min aanan tarkace inama laifin ki ce nace Amirah tazo ta zauna dake har na dawo.
Nace amma kana gani ita anty zata yarda tazo gidan nan saboda ni kuwa ?
Gidan ki ne ko gida na Amira fa yar uwatace kada ki man ta da hakan don haka ki barni da tsarina kawai.
Ya juya yafita na ce o Allah takawo ni gidan gwauna kaida sai dai obey the rules kawai ba jin views din mutum.
Ya samu mama zaune falo tana zaman kadaici na rashin mu tare da ita bayan mun gaisa take tambayan shi lafiya na yace ina lafiya kalau.
Tace da fatan dai ba wani matsalan komai a tsakanin ku ko?
Ya kai haba maji matsalan may kuma dai ni nama zo ne nai maku sallama yau zan tafi Spain ne muna da wasan da zamu buga har agentina zan tafi ina ganin kuma zan kwana biyu a can idan na tafi.
Da sauri mama tace ita matarka da,wa zata zauna tsawon wanan lokacin haka dake fadi?
Yace da cewa nayi ko Amirah zata koma can har na,dawo, amma ita kuma naji tana fadin wai ko za,a dauko mata kanin tane agida ?
Sai dai na kashe wanan magana don ban yarda da yan kauyen na su zo su zauna min gida ba suyi min barna.
Kana da hankali kuwa yan kauye kan tunda ka dauko diyan su ai kashiga ganin su ke nan a gidan ka.
Ina yaron kanin tane uwarsu daya kuma ba wani babba bane can fa shi yaron.
Kuma ma ita wanan malaciyar inba kwanciya ba may zata yi a gidan amma shi yaron ko wani aike ne ko aiki ai zata iya saka shi yayi mata ko ?
Kada fa kace zaka hanata zumunci da yan uwanta, tun yanzu dan sune gatan ta.
Ya ce maji ba wai zan hanata zumunci dasu bane kawai gani nayi dauko yaron kaman wani long process ne kuma yanzu.
Mama tace aa ka aje da zai kaita makaranta kuma don dazun maryam ke fada min wani sati zasu fara school insha Allahu.
Yace mun gama wanan magana ko zanbar mata motana tayi amfani dashi don ashw maryam ma ta koya mata mota ko.
Tace madallah ubangiji Allah yai maka albarka Allah ya baka zuria masu albarka da zasu tausaya maka kaima.
Yace amin maji nan ya ciro kudi masu yawa ya bata yace ta rike a hannun ta idan da bukatan wani abu a bayan shi sai ayi.
Yadda ya saba tafiya a gida ba tare da daukan kaya ba yauma haka yayi sai yar bakar jakar tafiyan shi kawai ya rataya.
Ina zaune falo don na kasa zama daki kamar mai tsoro yafito ganina zaune a falo tasa shi zama a falon shi ma yana waya ina ganin bashar ne don naji yana fadi ya biya ta gida yazo da Amira kafin ya wuce.
Sai da ya gama waya ya miko min kudi yana fadin karbi na nan nakali kudin tare da karba sai baice min komai ba.
Cikin karfin hali nace namay nene kuma yace ki rike a hannunki don amfani idan kuma ma da wani matsala bashar yana gari sai ki nemashi.
Ni gaskiya kudin nan sunyi min yawa ban da abinda zanyi dasu haka dubu biyu ma sun isheni saboda naga komai akwai a gidan ai.
Kallon mamaki yai min yace wanan kudin ne sukai maki yawa dubu darine fa kawai idan kuna son sayen wani abin fa bana gari.
Nace ni dai sunyi min yawa don ban saba kashe kudi ba komai mamane take saya muna na fadin cikin sanyin murya.
Ok sai ki aje a gurin ki idan na dawo sai na karba don ban saba alheri ba na karba ni.
Bashar suka shigo da Amirah sai wani shan kamshi take kamar an sata zuwan dole ne nake gani.
Amma tana ganin shi ta dan sake tana fadin yayana dazu shine kaje gida ina barci baka sa atayar dani ba sai dana tashi maji ke fada min kazo wai yau zaka koma.
Yace Amira ai ina ce baki gidan ne ma a lokacin da dake zanyi magana yanzun dai ga wanan nan zaki zauna min da ita har na dawo ba zan dade ba nake gani sosai sai dai kuma yadda tafiyan ya kaya min dai idan naje.
Kudi yabata itama madu yawa yace ina tsan mani akwai komai da zakuyi amfani dashi abinda babu dai ga Bashar sai ku tuntube shi kawai.
Bashar ya shigo ina gaishe shi yake fadin kaunata ashe yau wanan mayen ball din zai koma ya bar min ke ai yayi arziki hutun ku ya kare da kafanshi kafan ki wallahi.
Tsaki sadauki ya mashi yace dan Allah mu tafi ni ban iya shirmay ka da ka saba kaji.
Sai naga na mike nima da suka mike kallo na yayi cikin yanayin da bazan fahinci na maynene ba, sai suka fara tafiya daga ni har Amirah muna bayan su tafe.
Sheri bashar ke mashi wai ashe shine bakauye yana kira min kauyan ci murum zaiyi tafiya mai nisa shine zaiwa matar shi wanan sallaman haka.
Yace kai dai kasani jarababen banza ni yanzu ma har ina tausayawa maryam da wanan shegen jaraban naka da ka samo.
Yace ni matata ba irinka bane don chakwai muke abin mu ban kuntata mata bata kuntata min kaine aka bari da jan ajin banza kawai.
Suna shiga mota muna masu Allah yakai lafiya ya bada sa,an tafiya.
Sai da suka bace muka shigo ciki mai gafi ya rufe get inda suma naga ya tsaya ya basu wani abu.
Muna shiga ciki batai min magana ba naga tafara jan dan troler din ta ta nufi dayan dakin dashi nace ,a a anty ba anan zamu zauna tarw bane.
Ta wani juyo a wulakance ta dube ni tace ina ko kin mata ni bani zama da kowa daki dayane don ban son yawan takura.
Sai kawai taci gaba da tafiyan ta can kuma taja ta tsaya ta juyo duk ina tsaye ina kallonta tace Bintu kada fa ki manta gidan dan uwana ne nan ina da right din shiga duk inda naga dama batare da wani shamaki ba.
Kiyi hakkuri anty ni bada wani manufa nai magana ba gani nayi gidan nada girma mu zauna daki daya kawai shi yafi.
Tace to ba zan zauna ba sai inda naga dama zan zauna kuma kada ki kara cewa zaki min katsalandan ga al,amarina kinji na fada maki ko.
Ni dai nabita da kallon mamaki don ban san laifin da nai mata ba har muka koma haka da ita kaman wasu makiya can.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI DA ALLAH,,,


ALOKACIN MUKE,,,,,


Tunda nai wanan mafalkin na tashi jin kaina nake yana min wa ni irin ciwo gani banda sukuni a tare dani.
Haka na daure nai muna abincin rana tare da na dare a lokaci guda sai dai ina sake sake a raina kan mafalkin kabir da nayi may hakan ke nufi ne wai?
Kudi na fito dashi da abinci nace ma musa ya bayar min da sadaka a waje ya samu karamin yaro ya bashi.
Na gama shirya dining table da kayan abincin dana girka nashege daki na kara wanka.
Dogon rigan atamface a jiki dinkin shi mai hannu daya ya matse ni sosai rigan wanan dai kan sai zaman gida don da aka kawo dinki naita fada da anty maryam akan dinkin.
Ina fitowa ban san da dawowan shi ba sai ganin shi nayi falo kwance saman dogon kujera ya sa hannun shi daya ya rufe fuskan shi dashi.
Dagani tunane yakeyi ko may yake tunane oho sai da nakai daidai kan shi na tsaya daga bayan kujeran tare da dan rakwafowa saman kujeran nace.
Sannu da dawowa yaya kamar daga sama yaji murya na sai naga yai sauri cire hannun shi firgigit da sauri yana bude ido mukai arba dashi.
Cikin mamaki ya amsa min fuska a daure yana cewa yyawa nace akawo ma abin sha ne ?
Eh kawai ya,bani amsa na juya zuwa inda fridge yake, na dauko lemon five alive mai sanyi da cup.
A kasale ya mike zaune daidai ina isowa da drinks din a hannu na sai dana aje cup na bude lemon na fara tsiyayawa a cup din.
Na dauka tare da mika mashi sai naji ya sauke ajiyan zuciya yana karba daga hannu na.
Sai da na samu kujera na zauna ya kai cup din a bakin shi ya fara dan kurbawa a hanlali tare da lumshe idanuwan sh.
Sai da ya kurba kusan sau biyu naji ya ce may ya hada ki da Amira ne wai ?
Shiru nayi ina wasa da yatsun hannu na kaina a kasa sai ji nayi yace bake nake tambaya ba ne ?
Nace wallahi yaya ni ban san wani abu ya taba hada ni da ita ba.
Kwayar idona ya daga idon shi ya kalla don tabbatar da maganan da nayi yace kin tabbatar da hakan da gaske ba abin da ya hadaku bayan bana nan ?
Kai kawai na daga mashi da eh haka ne din amsa na .
Yace shi ke nan ai idan ma wani abu kikai mata ai zanji don zan dauki mataki akan hakan.
Don ba zan yarda matar da nake aure ta wullakanta min yan uwan haihuwa na ba ko kadan.
Dan murmushi nayi nace nima ai yan uwana ne don banda wanda sukafi a garin nan yanzu don may zan mata wani abinda ranta zai baci akaina.
Wanan kuma ai matsalar ki ce ni dai kin ji may na fada maki ai sai ya mike tsaye zai fara tafiya nake cewa abin yana saman dining tun dazun.
Sai nayi sallah zanci ya bani amsa ba tare da ya juyo gare ni ba nan nabi bayan shi da kallo kawai.
Dogon mutum ne sai dai ba irin can din nan ba kuma karfafa ne mai fadin kirji ga shi da dan dogon fuska da hanci irin zubin fulananin kasan sokoto sak dashi.
Musa ne ya dawo yana cewa anty na dawo dazun na samu bakya falo.
Sai a lokacin na dawo daga tunanen wanan zaman da baudaden mijina da nakeyi.
Don nidai yanzu ban san kuma wace irin kulawa ake so na bashi ba wanda yafi wanan da nake mai yana mai dani kamar wata shakatafi can.
Na saki ajiyan zuciya a fili tare da dan murmusawa nace ga abinci can fa na zubo maka ne musa.
Yace anty lokacin sallah yayi alwala na shigo nayi naje massalaci hakan yasani mikewa nima na shiga don nai sallah.
Bayan na

Please Login or Register in order to submit comment