Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Jin haka yasa Sabuwa ta fara dan sake magana tana fadin an dai ji kunya wallahi .
Karshen muna funci ya baiyyana ace muna ba, a da lafiya amma sai ga shi an iya labewa da karamar yarinya har ana dirka mata ciki.
Abin kunya girma ya zube kamar wanan yar yarinyar za, a ce wai ta samu ciki da mutum irin Alhaji wanda kewa iyalin shi ikirarin baida lafiya bai iya komai da mace amma ya takure a gidin yarinya karama to ga abin boye ya fito fili ai kowa ya gani yanzu gaskiya ya baiyyana.

****** ********** ******
Tun lokacin da na fara period naga gaba daya na sauya wani girma ya zo min ga kayan dadin da nake samu ina ci iri iri gwagwadon halin yan kauye irin dadin su na kauye.
Wani lokaci sai nayi kyauta da wani abin ma na rabawa yaran cikin gida su ci don ban iya ci ni don ban saba da yawan ciye ciye ba a rayuwana.
Zaune nake a saman kujeran dakina nayi tagumi da hannuna na hagu na zurfafa ga tunane.
Sai ganin shi nayi ya shigo dakin na bishi da idanu kamar shima yadda ya bini da kallo don ganin yanayi na a cikin damuwa.
Guri ya samu ya zauna a bakin gado yana kokarin cire babban rigar dake jikin shi.
Yace may kuma ya faru na gan ki haka amarya, murmushin kake nayi wanda bai kai ciki ba a fuska na.
Yake cewa wai may ke faruwa ne ko anyi wani abin ne kuma bayan fita na ?
Nace babu komai tashi yayi daga inda yake ya dawo kusa dani ya zauna saman kujera two seater dani kai a zaune.
Yake cewa fada min mana may akayi ne wai naga yanayin ki ya nuna min kina a cikin damuwa.
Nace ba komai Alhaji tunane Inna ta kawai nakeyi.
Yace wani abu ya samu inna din ne kuma ?
Kai na girgiza mai alaman a, a.
Murmushi yayi tare da riko min hannuwa na wani irin yar naji har cikin zuciyana tare da jin nauyin shi na ganin ya taba min jikina karo na farko zamana dashi.
Ban kai ga karasa mamakina na ba naji ni ya kwantar dani a saman jikin shi yana dan shafana a hankali.
A take naji yanayina na neman gagarana zama a gurin da nake zaman tsara dashi.
Yace ki kwantar da hankalinki insha Allahu akwai shawaran da nakeyi akan ki idan har nakai karshe wata kila ma zaki koma gurin Inna din da zama na dindindin.
Da sauri na dago kai ina duban shi yace ki dai kara hakkuri kinji Rahama dan bani lokaci kadan.
Nace ni ban son komawa gidan mu gurin inna ta, zama na nan yafi muna komawa gidan su Inna yanzu hankalin ta a kwance yake don mama bata gani na balle ta tayarwa Inna da hankalinta .
Ni nan zan zauna gurin ka kana kula dani fiye da Inna ta da baba na ban cikin matsin mama kuma yanzu.
Dukar da kan shi naga yayi a kasa sai naga hawaye suna zubo mai sannu a hankali.
Cikin mamaki nai zubur na mike daga inda nake a zaune tare da dawowa gaban shi na tsugun na ina cewa .
Don Allah Alhaji idan har na fadi wani abinda ba daidai bane kayi hakkuri kayafe min naji zan koma gidan mu gurin Innata muyi ta hakkuri da rayuwan da zamu tsunta agurin mama.
Ji nayi ya tallafo ni daga gurin da nake a tsugune zuwa jikin shi ya rugumay ni yana dan shafa min bayana tare da fadin ya isa haka kiyi shiru babu inda zaki tafi kina nan tare da mu insha Allahu.
Wanan ranan ne muka fara kwanciya saman gado daya da Alhaji sai dai yana gefe ina gefe a kwance har gari ya waye .
Abinda ban sani ba ranan shi gare shi ko runtsawa bai yi ba sai faman tunanen duniya yakeyi.
Ya so it a mayar dani gidan mu gurin iyayyena don yana ganin yana kuntatawa rayuwa na sosai, amma kuma sai gashi ni da bakina nake fadin wanan zaman yafiye min zaman gidan iyayyena dadi.
Haka yasa ya fahinci daga ni har innata muna wani rayuwa ne na zaman ukuba a gidan.
Dole yabar wanan yarinyar yaga abinda Allah zaiyi akai don Allah kadai yasan dalilin wanan auren don shi baki sa,ata ba ko wace tafini shekaru bai da nufin karawa a rayuwan shi.
Sai gashi a lokaci daya Allah ya jarabce shi da kara aurena auren kuma yazo da kaddaran rayuwa gare shi.
Yadda na samu kwanciyan hankali na mirje nai kyau dani haka yasa Sabuwa tayar da hankalin ta duk ta fige tayi wani baki da ita.
Gashi ta sa a ranta cewa cikine a jikina yasa na koma haka dani lokaci daya.
Akwana a tashi hasaran mai rai yau nakai wata takwas da aure har lokacin ban sheda nayi aure ba a rayuwa na.
Iyakata naci na sha na kwanta nai kwana idan naso na shiga na taya matan gidan aikin su.
Ba mama da mama hauwa ba kawai nake tayawa aiki har sarakan su idan aiki yai yawa nakan kama masu.
Ban hakkura da zancen zuwa islamiya ba na kara tunawa Alhaji da kyat na samu ya yarda na tafi sai gashi ya sawo min hijjab har uku maya har kasa da nikaf na rufe fuskana.
Ranan da zan fara fita nasha sheri gurin matan gidan wai ni yar izzala ce shiyasa nake da mugun tsabta ashe.
Na dai yi murmushi nai masu sai na dawo nafice daga gidan dama Alhaji ya riga yai min register komai a school din.
Don haka ban sha wani wahala ba na gane ajina gwajin farko ya fahinci na dan yi nisa aka mayar dani ajin manya.
Sosaina dage ga karatu na ba wasako a gida nake banda abinyi sai karatu da yan aiyuka na.

****** ********* ******
A bangare Alhaji ya samu sauki sosai don tsare dokokin da yayi na likita har anfasa zancen yi mashi aikin da akace za, ayi da farko.
Hakan da yake ji yasa yake ganin ya samu sauki ya shiga kokarin gwada sa,anshi ya gani .
Ranan a cikin barci na dinga jin wani bakon al,amari ya na ziyarta na idan dai ba mafalki nakeyi ba to zan iya cewa kirjina, watau dukiyan fulani na ne kejin ana taba min a lokacin.
A hankali na zubura zubur daga mafalki kamar zan fasa ihu sai jin muryan shi nayi yana ce min kamar rada yi shiru amarya nine Alhaji ba kowa bane.
Na gyada kaina alaman na gamsu sai naji yana sauke ajiyan zuciya naji yana ci gaba da saukewa a hankali.
Bai kuma fasa abinda da hannayen shi keyi a saman kirjina ba har lokacin.
Sai faman rintse idanuwa na nakeyi don irin bakon yanayi da nake ji a lokacin.
Kama an fisge shi naji ya juya da sauri tare da rike maran shi da hannayen shi yana wani irin nishi kamar kugi a hankali.
Shiru nayi ina sauraren yadda yake fitar da sauti daga bakin shi cikin yanayin ban tausayi .
Can a kasan makogwaron shi naji yana kiran suna na a hankali da kyat sautin maganan shi ke fitowa a lokacin yana fadin naje na dauko mai ledan maganin shi da ya bari a dakin sabuwa.
Ban ki ba haka na daure cikin wanan Uban daren hana na wucw gurin mama hausatu na buga mata kofan dakin ta tare da cewa maganin shi yace na karbo mai a gurin mama Suwaiba.
Ita da kanta ta tafi dakin ta buga mata take cewa miko min ledan maganin Alhaji da ya bari a nan ta tambaya da sauri injin dai lafiya yaya ?
Lafiya kalau ya manta bai sha bane yace a dauko mashi ya sha ta karbo ta mika min na juya na bar dakin simi simi dani.
Nakai mai sai da ya hada ya sha zuwa can ya dan samu relief sai barci mai nauyi ya dauke shi nima na koma na kwanta zuciya na fam da tunanen abinda ya faru yan mintina da suka wuce a tsakanin mu.
Wanda har lokacin ina dan jin dan matashin kirjina yana dan min radadi.
Washe gari na tashi ina matukar jin nauyin shi da kunya akan abinda yai min a daren jiya gashi alama ya nuna yana dan jin jikin shi .
Amma haka ya daure yafita daga gidan zuwa gurin neman kudin shi daya saba yi.
Bai jima ba a waje jikin ya tsanan ta mai ya dawo gida ya kwanta min a daki gashi kunya da nauyi nake ji har lokacin ban iya hada ido dashi.
Haka yasa shi fahinta halin da nake ciki daga inda yake kwance na shigo dakin ne naji ya kira sunana.
Na amsa sai naji yace na gode daren jiya fa ko ba komai na dan more daga ni,iman da Allah yai maki ya fadi hakan cikin dan lumshe idanuwan agi a hankali.
Shi kadai yasan irin halin da ya tsinci kan shi a daren jiya sai dai yana gap da biyan bukatan shi a gare ni ne yaji maran shi ya rike mai sosai a lokacin.
Hakan ne yasa shi dole neman magani ya hadiye don samun saukin abinda yake ji.
Tambayan kan shi yake a zuciyar shi yayin da idanuwan shi suke a rufe yaushe ne zai samu ya more niiman da Allah ya hallata mai ga wanan yarinyar ?
Irin yanayin da ya tsinci kan shi da ace shi mai lafiya ne yasan cewa a daren jiya din Allah ne kadai zai kare bai kai ga mayar da ni cikakkan mace ba kamar yadda yake gurin yin haka a gareni a kullun.
Ganin da nayi jikin shi ya matsa mai yasa naje na fadawa sauran matan nashi halin da yake ciki.
Ba bata lokaci dakin nawa ya shiga ganin yan zuwa yi mashi sannu da jikin shi.
Nan sabuwa ke cewa Alhaji kana son matsawa rayuwan ka akan sai kaga ka burge wanan yarinyar a koda yaushe.
Idan baka bi sannu ba zaka halaka kanka da kan ka furin budurwan zuciya.
Sai ka dinga farwa yar karamar yarinya akoda yaushe yaushi zaka ganewa lafiyan ka tunda kaki na tsuwa da girman ka a koma ana taratara da kai kamar karamin yaro har may kake nema ne gareta wanda baka samu ba a baya.
Yana jin ta sai dai halinda yake ciki bai iya bata amsa a lokacin don jin zuciyar shi yake yana mai tafasa .
Ga zancen ta na kara kona mashi zuciyar shi akoda yaushe.
Shima laifi ne ga maganan sabuwa da take yawan nanata yana yawan kusantar Amaryan shi ne yasa matsalan shi ke yawan tashi koda yaushe.
Shi dai a gare shi yadauka kawai wanan wani jerabawa ne daga Allah kawai.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KIKA BAWA WACCE BATA BIYA BA ALLAHNA GANIN KI DON AMANA NE A GARE KI YAR UWA, , ,


Sannu sannu sai gashi lokaci yana ja a wanan lokacin duk wani dan matashin yaro dake gidan idan dare yayi muma shiyana muna karatu, wanda suke jin dadin hakqn anan zamuyi ta shirmay har dare kowaya watse.
Bayani nake masu sosai yadda zasu fahinta gakaratun da suke dan tsinta a gurina.
Wani lokaci kuma novel zan samu mai dadi da ma,ana da koyar da wani abinda ya shafi fannin rayuwan dan adam.
Zan dafa abinci na zuba a babban tire nan zamu taru muna ci muna hira muna dariya abin dai na kurciya zallah kawai.
Har zuwa wanan lokacin zama na da maigidan kamar kullun ne ya kan yi iya bakin kokarin shi don yaga yadda zai yi ya dan samu gamsuwa.
Sai dai hakan bai yuyu ba a gare shi don da alama matsalar shi tana nan mai bai gushe daga gare shi ba.
Don idan yaso ya kai gare ni sai naji yana zufa yana wani irin kugi mai fitar da wani sauti na ban tausayi.
Ni kaina nakan matukar jin tausayin shi idan ya shiga wanan halin don haka zai wayi gari ya wuni a wahalce dashi dashi.
Na fara fahintar wasu abubuwa duk da dai wayo na baikai na fahinta ba a lokacin amma sai nake fahintar ba gani kadai hakan ke faruwa ba har ga sauran matan shi musanman ma dai sabuwa.
Idan ya kwana a dakin ta zanga ya tashi wani lokaci ba dadi har aka fara dan rade radi a gidan abinka da gidan yawa.
Ranan mama da kanta take bugun cikina akan zancen take cewa dani wai amarya kuna dai biyewa wa maigidan yaki natsuwa har ta samu lafiya komai ya zama daidai ko ?
Nace mama na daina zama ne idan yana daki kike nufi?
Ta kama baki tace wane ni da fadar haka amarya rufa min asiri tace ni dama cewa nayi kawai ki dan kaurace mai ga shimfida irin ki dan rika ba da lokaci din nan .
Kin san shi namiji kullun a bukace yake da mace ba ruwan su da lafiyan su koda hakan kuwa zai masu illa ne.
Nace mama kina dai nufi idan yana daki na fito waje na barshi ya huta ya samu hutu sosai ko.
Nan dai ta gane shirmay na bai bari na fahince ta sai ta fito min fili tai min bayanin komai a baiyyane.
Cikin canza fuska nake ce mata gaskiya mama ni Alhaji bai taba nuna min wanan abin ba a tsakani na dashi sai mutunci kawai.
Kan ta ya daure ba don ta yarda ba don tasan hakan ma ba zai faru ba koda kuwa ace ni ba yarinya bace yaya zan zauna har wanan lokacin.
Karshe dai sai cewa tayi dani ki daiyi a hankali kinji kada ki yarda ace an samu wani matsala a kan ki kinji ya ta.
Nace to mama nagode Insha Allahu zan kula kamar yadda kikace din.
Sai gurin karima sarakuwan tane ranan take kara fayyace min yawan hasashen da ake mun a gidan kan lafiyan Alhaji.
Muna hanyan makarata ne take fada min komai tare da jamin kunne akan na kara kulawa sosai.
Tun ranan ban yarda ko dan tabanin da yake ya samu relief din da yake yi na daina bari yanzu.
Har abin ya fara dan damun shi da yai min magana ban boye mai komai ba na fara kuka ina fada mai abinda akace ina yi mai.
Ya gane anja min kunne ne akan haka yasa ya daina kada ya jamin bakin jini ga iyalin shi don su a ganin su nice ban bari ya samu sauki.
Ranan dakin mama hauwa yake ciwo ya murtuke shi a cikin dare aka kwasa sai asibiti.
Nan suka fara fahintar cewa ciwon ne dai bai bar jikin shi ba ba yadda suke hasashe bane.
Koda aka dawo dashi gida wanan karon andai dawo ne amma yana matukar jin jikin shi sosai.
Don yakai idan zaiyi fitsari ma kusan zakaji yadda yake faman nishi da kugi kafin fitsari yazo mai.
Wasa wasa ciwo sai gaba gaba yake mai ya ramay yai baki sai dan wuya takai ma yanzu bai fita kamar yadda yakeyi a baya.
Cikin haka ne ranan aka aiko babana yai faduwan mashi a hanyan shi na dawowa daga kasuwan kauye da yake zuwa.
Alhaji ya samu labari don haka yana dakin sabuwa yasa a kirani nazo na dan rusunna daga kofan dakin nata don ban yarda na shiga daga ciki ba don ta cikin dakn zaune a lokacin.
Yake cewa dani yanzu nake jin labarin abinda ya faru da mahaifin ki jiya shiyasa na kira ki.
Ki shirya sai zuwa ta rakaki ki dubo shi amma kada ku wuce goma ku dawo gida.
Nace na gode cikin murana wanan ne karo na biyu bayan aure na da naje gaida mahaifana.
Na farko tare dashi muka tafi ban ko kai minti talatin ba baba ya matsa min nafito muka koma gida.
Sai wanan daya bani bako mu tafi da zuwaira na dubo jikin mahaifina ko shi nasan don baya jin dadi ne da tare zamu tafi dashi.
Tsab na shirya cikin katon hijjab sai nikaf dana dora akai duk d dare ne amma na saka nikaf din na tare fuskana da shi.
Har mu uku muka tafi don Aisha ta biyo mu da taga zamu fita tare da zuwaira din.
Da sallama muka shiga gidan a tsakar gida muka samay su suna shan iska tare da baba.
Nan muka durkusa muka gaida su tare da mai yaya jikin shi da Allah ya sauwaka ya tsare gaba.
Sai can yake cewa wai Rahama ke ce ai ban gane kiba ikon Allah ya kuke ya gidan duk kuna lafiya ?
Yaya shi maigidan naku da na sa jikin dafatan ya samu sauki ko don ance jikin nasa ba dadi kuma ?
Bayan mun gama gaisawa da baba ne da tambayoyin da ya jero min na juya inda mama take tayi tsit tare da kura min ido.
Ko may take kallo hakana ban sani ba daga jikina na daiga duk da dare ta kura min idanuwan ta a kaina.
Nace mama mun samay ku lafiya yaya gida ashe baba kuma wani kaddarane ya samay shi haka?
A cikin basarwa take amsa min gaisuwa na a tsatsaye na gaida Inna ta dake zaune a gefe tana motsa kunu mai zafi data dama ina ga na baba ne.
Can na mike na leka dakin mama gurin su Lawisa suma ba wani karban arziki ne na samu a gurin su ba.
Na fito na shiga dakin Inna ta na samu kannena zaune suna dan hiran su, suna gani na suka hau murna.
Nace dasu ba wani bayan kun yadani ba ku zuwa gurina sai kace ba, a gari daya muke daku ba kamar wacce bata da yan uwa.
Nasir yace kiyi hakkuri mama ce ta fadawa baba ranan nan da muka tafi gurin ki shine baba yace kada mu sake zuwa gidan ki.
Lokacn Inna ta shigo dakin inda muke ta samay mu muka kara gaisawa da ita cikin mutunci.
Nan ta zauna a bakin gadon ta ganin Inna ta shigo dakin yasa su zuwaira da muke tare mikewa suna fadin amarya zamu tsaya kofan gida mu jira ki.
Nace haba ku zauna mana suka ce a, a muna dai waje har ki gama mu tafi ai.
Bayan fitan su ne Inna ta nisa take cewa yaran suna da da, a da sanin ya kama ta ne.
Nace cikin shagwaba Inna nikan dai yanzu ba kya sona nice kawai nake can cikin damuwa daku ?
Tace da akai may kuma nace ina ko su Nasir an daina tura min nagan su sai na tara abu don a kawo maku amma babu yaron da zan ba ta kawo nan na ciro wani babban leda daga cikin hijjab dina ina mika mata.
Kallon ledan takeyi tare da tambayan wanan may ne kuma a ciki ledan cike yake fam da tarkace iri iri dana tara don na kawo mata.
Bayan ta gama dan dudubawa ne race yarinya kardai ince kayan mijinkine kika kwaso muna haka na amfanin ki ?
Mijinki fa bai rage ni da komai ba yanzu don inba rashin lafiyan nan da ya kwantar dashi ba kusan duk sati da aiken da yake min daga gurin mamakin mai kuli.
Ni ban san irin godiyan da zanwa wanan bawan Allah ba gashi ya rike min ke da mutunci kullun yana yabawa da halin ki na tarbiya a garesu.
Ga kuma abin alherin da yake kawo muna don kinga yanzu banda talaucin dangin kayan miya sabulun wanka man shafi da sauran su.
Watarana ma har kayan girki kamar shine ya aje mu zai kawo muna da kudi ga hikimar da yayi na bi ta hannun mai kuli ya kai muna ta gurin ta sai dai ta aika nazo ko ta kawo min idan uwar ku tafita daga gidan.
Nisawa nayi nace mama shi Alhajin ne ke kawo maku wanan amma ni bai taba fada min komai ba wallahi.
Tace shine alherin arziki gashi yanayi ke da yakeyi kanki ma baki sani ba sai yanzu.
Nidai ko rike min ke da sukayi da mutunci ya wadatar dani wallahi tun har yau banji wani abin asha ba daga gare ki.
Murmushi nayi nace haba Inna baki koya min yin haka ba aikuma bazaki taba jin shi daga gare ni ba ai.
Nan dai nace Inna su Lawisa yaya nasu zancen auren ne naji shiru har yanzu ?
Tace kin ga yadda baki san komai ba nima haka iyakata dasu ido a gidan nan bana shiga zancen su suma hakan.
Sune ma ganina a wadace yake damun su kin san halin uwar taku da hassada da kyashi ai.
Yadda taso ta kawar dake a gabana taga na wullakanta sai taga sabanin haka ga taimakon da Allah ya jefo mijin ki a rayuwan mu yake muna.
Kedai kikara hakkuri akan wanda kikeyi mai hakkuri baya tabewa ga banza insha Allahu.
Nace insha Allahu ina tace idan ma tayi muna hakane da wani manufa to yanzu mu hakan ya zama muna alheri.
Don ya koma mata ciki kullun zaka ji ta tana sake magana da habaici a gidan nan.
Gashi Allah ba ai mashi wayo ita nata diyan ko tsohon ma Allah bai kawo masu ba sai zaman sa,in sa suke a tsakanin su da ita.
Muryan baba ne daga waje yake kiran Inna ta yana fadin ke Asiya bazaki sake yarinyar nan su tafi ba ga dare yanayi ko anan kike son ta kwana.
Shine ya katse muna hiran mu da inna na mike ina cewa inna zamu tafi zan shiga gurin mama na gaida ita kafin mu tafi.
Tace injin mijin naki yace ki shiga gurin nata don kada ki koyi wanan halin na matan yau da muke daukan hakan ba komai a rayuwan mu hakan ko shine babban koma a gobe kiyama.
Sai kiji mace ta fita da sunan zuwa gida daya sai ta biya gida goma ba da bakin mijin ta ba.
Nace Inna har na fito fa ya kirani yake cewa na, ratse na gaida mama altine din tace to tashi ku tafi kada dare yai maku.
Naba kanne na dari biyar nace su karya dashi da safe suka shiga murna itama inna dubu daya na bata na fita naba babana dubu daya mama dari biyar.
Sai sa min albarka baba da Inna sukeyi mama kan tun ce min da tayi an gode bata kara magana ba.
Gashi ko ranan da haka zata kwana ba ko sisi a hannun ta don yanzu yaranta sunyi wayo suke rike kudin su a hannun su.
Da kyat zata iya karban naira hamsin a gurin su don sai tasha mita kafin su bata wani abu.
Mun shiga gurin mama Altine tai murna kwarai da ganin mu tana ta ina aka saka dani.
Sai tambayana take yaya muke yaya abokan zaman nawa injin dai ba wani matsala ko ?
Tace nayi hakkuri na dage gurin kyautatawa mijina da sauran abokan zamana kamar yadda nakeyi.
Tace hakan da kikeyi shine samun kwanciyan hankalin ki a gidan don da kinje masu a tsaye ne ko shi mijin naku bazaki samu kan sa ba ai.
Bamu jima ba mukai sallama muka koma

Please Login or Register in order to submit comment