Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yaba da amsa Umma tace, dan uwan shi don Allah gyara hausan ki mana.
Kada ki sa mashi bakin jini da zargi ga mutane, ace ko tare suke shaye shaye dashi.
Imirah yace haba Maji, may kuma zai kai Sadauki gurin ni tunda harkan mu ba daya,ba dashi.
Maji tace Allah sarki ai zatona yana tare da kune a can kasuwan, kasuwan kan ba gidan yan maye bane ai.
Ba ta dai juyo ba ta koma part din ta inda dama daga itace sai Bintu su Maryam basu dawo ba tukun.
Ba,a jima ba suka shigo dawowan su ke nan daga makarant alokacin, sai suka shiga neman abinci.
Maryam da tafita waje ta samo ruwan sanyi don sai sun saye basu da fridge a part din su.
Nan ta samu Umma nata fada dan may za,ace wai Sadauki dan uwan Imirah ne ganin maryam bai hana ta fadan da takeyi ba.
Maryam na dawowa take cewa halan anyi wani abin ne wai naji Umma na tafada wai dan shaye shaye don rainin wayo za,ace dan uwan tane.
Bintu ce tabata amsa tace kin san basu da tunane da mama take fada wai don ta tambayi yaya imiranah yaya sadauki da,bai shigo gida,ba tun da safe yau.
Ikon Allah shine kuma abin fada inji Amirah cikin nuna mamaki karara a fuskan ta.
Komai fadan su dai ai ba,a raba anta da jini ko? Don basu san cewa wata rana suma abin zai iya shafan su ba ko,
Nan Amira take ta fada ran ta a bace basu san shigowan shi ba sai ji sukayi ana cewa wai kedawa ke fada haka ne Mira,
Tace hmmm ashe ma ka dawo yaya nida su Umma mana da basu so a zauna lafiya.
Nan take fada mai abinda ya faru shiru yayi baice komai ba suma dai din hakan ne.
Maji tafito da alwala tana mashi kallin mamaki tace kai ina ka,shige yau haka ne.
Yace maji wallahi ina cikin gari kayan mune ya iso shine naje nai clearing din su a gurin da ake saukewa.
Kaya kuma wasu irin kaya ne haka yace cikin wasa yana wuce kayan yan kwallo mana maji.
Kai kan da kwallo Allah ya inganta kawai, don ya zama maka jinin jiki ko?
Fatima kawo mashi abinci kinji tun safe mutum bai karya ba yana gurin zancen kwallo kawai aranshi.
No Maji gaskiya,abar abincin nan don sha dan drinks a can kada naji yunwa saidai anjima da dare zanci.
Yaro ke fadin wai ana sallama da Umar UF a waje, inji wani mutum.
Mikewa yayi yafita saida Maji tai mamaki take cewa a ranta yau kuma Sadauki akewa sallama a gidan nan.
Allah dai yasa mutumin kirki ne ba abokan shashancin shi bane suka fara biyo shi su mayar dashi ruwa.
Amira ce ta sako zancen abinda Umma takeyi na kokarin raba su da yan uwan su don ganin su basu da komai wanda yakai ace sun hada alaka dasu.
To koma maye ai dai ai su yan uwanku ne kuma duniya ta sani to may ye abin damuwan kai a ciki uwar ta,basu amsa.
Kafin tai magana sai ga sadauki ya shigo yana zama yake cewa Amirah gobe zaku shiga school ne da safe.
Wani abin kake so ne yaya, ya na,gyara zama yake cewa bani amsa mana kafinki min halinku na yan Nigeria.
Tace idan da abinda zanyi sai na bari sai jibi ko na shiga yace dana gode sai yai shiru daga haka bai kara magana ba suke tahiran su kan wata yar uguwar su.
Dawowan Alhaji yasa Maji fita tabar su don zuwa gaidashi kamar yadda ta saba, Sai da ya mike, tsaye bayan fitar mahaifiyar su, yake cewa don Allah Amira gobe ku kwashe kayanan gaba daya kufita dashi kafin nine na safe.
Amma kada ki fadawa maji yau sai goben kawai taga kuna kwasa please angama yaya tace mashi do ita kadaice a falon lokacin su maryam da Bintu suna ciki.
Maji na,shigowa bata ga sadauki ba take cewa,a,a shi kuma wanan din ina,ya tafi ne wai,?
Bai faci abinci ba yau gaba daya Amirah tace yako fita ina ganin saida safe ke nan, nan Maji tasawa maryam da Bintu kira tace su zo sukaiwa yayan su abincin shi a dakin shi.
Tai hakane don tagani idan yana gidan ko yafita don in fita yayi to gaskiya zancen ya fara baci ke nan kuma.
Zun dauki abincin zuwa part din samarin gidan tun daga,nesa,suka gane yana cikin dakin nashi don wutan dakin da yake kunne a lokacin.
A hankali ta kwankwasa kofan don itace a gaba maryam hankalinta yana kan wayan ta.
Sadauki wanda yake zaune dakin shi yana karatun wani littafi mai ban tausayi yaji nocking din kofan shi mamakine ya kama,shi don dama har ya rufe daki ko.
Don haka ya taso ya bude don yaga wanda ke kwankwasa mai kofa a wanan lokacin haka.
Daga shi sai yar singileti da gajeren wando irin da maza ke kwanci dashi da dare idan zasu shiga kwana.
Bintu ce yagani da kayan abinci a hannun ta ya zuba mata ido baice mata komai ba.
Ganin yadda yake yasata dukar da idon ta kasa tana cewa Mama ce tace mu kawo maka abincika nan.
Dan guntun tsuki yaja yace banace na koshi ba shine sai an biyoni dashi har nan kuma.
Bai sanda maryam suke ba,saida taimagana daga bayan Bintu tace kasan maji in bakaci ba hankalinta bai kwanci ai.
Maryam na koshi wallahi yanzun na,rage yawan cin abincin nan sosai don gudun kada nai nauyi da yawa na,kasa yin wasa kuma.
Yace shiga ki aje min daga ciki, yadan jaye mata a hanya Bintu ta shiga ta aje mai a bakin katifan shi da sauri tafito bata sab yana gap da ita ba sai ji tayi tayi karo dashi.
Tsaki yaja yana fadin ke dai yar kauye ce wallahi ko baki ganine zaki tureni haka kamar baki da ido.
Yi hannkuri ta fadi cikin dan muryanta kamar zatayi kuka shi dai ya kauce mata ta,wuce ta gaban shi yai tsaki yace yar kauye kawai da ita.
Maryam dariya take take cewa kai Bintu ke dai matsoraciyace wallahi kamar wace za,a kama ko tai laifi.
Har suka shigo gida Maryam tana mata dariya take basu Maji labarin abinda ya faru.
Maji tace wallahi in yana kiramin yarinya da yar kauye sai na bata mashi rai Allah, duk wanan kokarin da yarinya ke mashi baya gani.

Washegari kamar yadda ya umurci Amirah dayi haka,tayi don ta,tayar da Bintu suka,fara aiki don ita a,zaton ta fenti zai sa ai ma,shiyan nasu.
Matan gidan kowa tana fita daga gidan daya bayan daya zuw gurin aikin su inda suke gulma a ran su cewa, kullun sharan daki kamar wani tsiyane cikin shi.
Mani dai a zaton ta gyara kawai yaran keson yiwa shiyan don karan kan su kawai.
Tara da yan mintina sukaji muryan sadauki yana cewa wasu mutane ku shigo dashi nan.
Set ne na kayan gado tare da masu hakawa aka,shigowa Maji din dasu nan masu aiki sukansuka fara aikin gyaran guri kamar yadda ya dace.
Labule sabbi, kujeri set masu dan karen tsada, fridge sabo dal dashi a kwalin shi, TV plastama babban size din sai center carpet mai laushi duk a falon.
Dakunan ta duka ukku an saka sabbin gadaje a ciki don shi ana shigo da kayan ya fita abin shi waje, bai shigo ba,balle maji da imani ya cika ta tambaye shi inda wanan abinda bata taba mafarki ba ya fito masu.
Kafin karfe biyu masu wanan aikin da yake aikin su ne har sun gama komai ko nan su Amira suka karasa sauran gyaran da yarage masu.
Sai uku ya shigo gidan da ghana most go manya manya har guda hudu niki niki dasu aka zube su a falon Maji.
Maji tace Sadauki zonan cikin damuwa da rudani take tambayan shi ina ka,samo wanan kaya haka.
Ya lura cewa ta,shiga tashin hankali yasa shi zama kasa gap da kujeran da take yace Maji ko kin manta kin gura danki tilo guda sadaukar da ranshi wa kasanshi ne.
Yace abinda kika yarda shine alherin shi ya fara zuwa maki a yau din nan duk abinda zan samu ga,wasan da nakeyi Maji nakine ke da yan uwana gasu nan.
Sai mahaifina da kuna kakannina da suka nuna min hanya madaidaiciya da ta dace dani.
Don haka kwantar da hankalin ki Maji dankine ya,fara kawo karfi lokaci yayi da zamu fara shiga mutane muma ayi damu.
Maji yau ina matan gidan nan suke?
Duk sun fita gurin neman na kasu da rufin asirin diyan su, amma ke kina gida kina masu bautan da basu gani har abada.
Idan na samu bakiji dadin ba Maji ai ban haihu ba gare ki.
Wasu hawaye ne masu dumi suka zubo mata don abin kamar a mafarki take ganin shi a ranta.
Ji yayi ta dafo kan shi abinda ta dade batayi mashi ba tun yana yaro in zasu tafi makaranta take mashi haka.
Takance Sadauki Allah ya tsare min kai Allah yabada sa,a Allah ya daukaka min kai Allah ya albarkace ka da arziki ta hanyar alheri.
Yau ma da yaji ta dafa mashi kai yasan maka manci haka za,ayi sai yaji tace.
Allah nagode ma daka azurta min Sadauki ta hayan daka zaba mashi a rayuwan shi.
Ya Allah ka tsare min shi ka kare min shi daga duk wani abincutarwa da kuntatawa a,rayuwan shi Allah ka albarka ta min wanan yaron fiye da tsamanin mai tsanmani,
Ya Allah ,,,,,,, sai kawai kuka mai karfi ya subce mata ta kasa karasawa abinda tai niyar fadi daga karshe sai a cikin ranta tafadi Allah ka,azurta shi da zuria masu albarka.
Bintu ce mai karfin halin amsawa don duk kuka suke adakin gaba dayan su har ita Bintu din dake kallon ikon Allah.
Saida sukaci kukan shi ne ya,fara yin shiru cikin su yake cewa Amira dauko jakarcan na baya ki bude.
Tajawoshi dakyat zuwa gaban su inda ta bude turamay zannuwane irin na kasar ghana ciki makil dasu.
Yacd tajawo dayan kuma shima dogayen riguna ne na yan mata acikin sa su takalma da hand bags, nan suka,rude suka shiga fitarwa,
Dai dayan shadda ne ciki masu tsada suma dayan kuma kayan kantine nashi da yan kanneshi kana yasayo masu.
Nan ya,ware wa kowa naahi kason kamar yadda yasayo su tun can ghana din.
Maji tai matukar jin dadin haka a,ranta don yafara da yaddaya dace duk da nagari yayi yasamu yan uwa su sheda.
Tasan Allah ya hore mata da nagari wanda yasan zafinta da darahan ta a idon duniya ke nan.
Yace ban sayo maki kayan kitchen ba don ban san kayan da kuke so ba sai a saya a nan kawai.
Maji tace a,a dakata ko wanan ma sun isa haka wallahi.
Saidai banji ka fadi may kaiwa mahaifin ku ba har yanzu don baiyuyuwa ace ni kai min haka amma shi banji nashiba.
Yace Maji na Baba daban ne nasan ya dade yana son harkan noma don haka noma nake son yafara bana sosai akwai kudin da zan bashi wanda zai dan isheshi yafara dasu.
Allah yai maka albarka sadauki takara fadi a fil kowa yace amin cikin jin dadi da farinciki.
Gardama ya fara a tsakanin Amira da maryam gurin rabon kayan su nan ya fitarwa kowa da wanda ya sayo mata ya mika masu.
Bintu dai tana gefe tana kallon ikon Allah da jin dadin uwayen dakin ta ganin farin ciki ya sauka masu yau.
Maji tace ban fa gane ba sai duk suka joyo suna kallonta don jin may zatace dashi.
Tace naga kayan su Amirah amma banga na diyana,ba mana ko ita ba yar uwarka,bace.
Shiru sukayi gaba daya don su sai a lokacin kan su ya kawo wuta ga hakan.
Shiru yayi bai bata amsa ba kamar badashi takeyi ba ma sai da takara tambayan shi ne yake cewa ban sayo da itaba Maji.
Don may sadauki shiru yayi kawai yana dakilar wayan shi bai bata amsa ba.
Ta juta gurin su Amira tana ffadin ku miko min kayan nan a,kasa uku kowa ya kwasa.
La Mama don Allah kibar masu watarana idan ina da rabo za,a sayo dani ai.
Ba zaiyuyu ba gaskiya ku miko min nan kawai kunji tafada cikin bacin rai yace Maji bar masu sai a sayo mata a nan.
Amma maji bata saurare shi tai masu jan ido suka miko kayan inda ta raba daidai ta cirewa Bintu suna ta bata rai don may za ai masu haka.
Waya ma dole bai basuba saida dare ya shigo da guda hudu sai dai na Bintu baikai nasu kudi ba.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,

A LOKACIN MU KE,,,,,


Yau kwana arbain da,wasu yan kwanaki da tafiyan Sadauki don haka a wani yammaci Alhaji ya dawo kasu Maji ta tafi gaishe shi yake ce mata.
Maijidda kunyi waya da Umar yau kuwa tace bai kira mu ba don kasan kiran shi nada wahala ta nan.
Indai ba shine ya kiramu ba ni ban faye kiran shi ba gaskiya, ya dan juyo yana kallonta ciki kada kai yace haba maijidda ya wuce ki kashe dubu daya da dan kai gurin jin lafiyan shi kawai.
To Alhaji kudin fa ai yazama cacan kudi kulun gaskiya ace dubu dubu haba dai idan dai ya kira muji lafiyan shi ai.
Yace tau yace min insha Allahu gobe zai karaso gida don yau jirgin su ya,sauka Nigeria da safen nan.
Wani irin murmushin jin dadi Maji ta sauke a lokaci guda afili kuma tace Allah ya kawo muna,shi gida lafiya.
Alhaji ya amsa mata da Ameen yace da farko naji tsoron tafiyan yaron nan amma kinga da muka,bar ma Allah zabin shi gashi har sunje sun dawo lafiya.
Maji tace a hankali Alhaji nafika jin tsoro don ina gudun yaje ya kara hinjire muna a can.
Ai kawai al,amarin daga Allah ne maijidda don dai ni san ba wai rashin tarbiya bane ya jefa yaron nan cikin wanan yanayi.
Jerabawa ne kawai daga Allah ya zo min ta hanyan shi wanda mafi yawan mutane yanzu kowa da kalar tashi jerabawan da,ake jarabtar shi dashi.
Allah ya sauwaka Maji ta fadi a fili tareda mikewa don tabar dakin don tasan idan takai wani lokaci a ciki yana iya zama masu matsala da maigirkin ranan watau mama Asiya.
Ta koma dakin ta ta samu yaran ta kowa da waya a hannun shi suna dakala.
Sai Bintu ce da bata da waya ta ke zaune tana karatun littafin islamiyan ta da take bita.
Shigowan ta yasa su dan dogo kai suna kallon ta don sun saba idan ta je gaida Baban su tadawo suna kallon yanayin ta idan bada bacin rai ta,shigo ba don gudun ace yayan su ya aikata wani abin asha kuma.
Sai dai sunga tsatson farin ciki a fuskan ta inda kafin su tambaya take ce masu Amirah ance gobe insha Allahu yayan ku zai dawo garin nan yau sun sauka lagos gobe zai karaso gida da yardan Allah.
Gaba dayan su dadin wannan labarin sukaji don sun san tun da har yakai warhaka kuma ance sun dawo komai ya tafi normal insha Allahu .
Ba kamar yadda suke daridari ba da farko don gudin kada yaje yai shaye shayen shi a koro masu shi.
Washe gari tun da safe suka fara dan gyaran wuri da kuma yi mashi abinci na musan man dan taron shi.
Maryam ce da Bintu suka gyara mashi dakin shi tsab don komai sada suka fitar suka share suka goge mai sabon zanin gado maji tabayar suka shimfida mashi.
Wanda karfin aikin ma duk Bintu ce tayi shi ita kadai maryam sai karatun ta take a cikin wayan ta kawai.
Ganin suna aikin yasa yan sa idon fahintar kila mai dakin zai dawo ke nan.
Mama Asiya ce ta fara samun Umma da zancen cewa yau naga mutanen ki sai wani jin dadi sukeyi harda gyaran wuri.
Nafisa tace da zan shigo dazun naga suna,gyara dakin yaya sadauki ai.
Muga atsiyar da ya tsinano masu a can ai sai rawan kafa suke wai yatafi ya dawo.
Wanan dan shaye shaye may kike zaton zai ita tsinano masu a can, ai yadda yaje haka zai dawo tsula dashi dan ganye kawai.
Ranan sai kawai aka kafa dandali a tsakar gida don gulma katuwar tabarma suka shimfida wa kan su nan aka baje ana ciye ciye ana hira wai.
Maryam ce tashigo gidan tana cewa yau kan gulma yakai gulma a gidan nan bakiga har tabarma,aka baza ba manya da yaran su a tsakar gida don kawai aga may yaya zai dawo dashi.
Ni dai Allah ya kawo min shi gida lafiya yasa wanan tafiyan ta zama mai silar shiryuwan shi.
Suka amsa mata da Ameen maji.
Sun zage sai faman goge gogen falon su da babu komai sukeyi don dai ya haske kawai.
Sun gama dan har wanka sunyi lokacin suna zaune falo suna dan hira jefi jefi tsakanin su.
Suka jiyo muryan shi ya shigo gida da sallama a bakin shi, kamar muryan yaya sadauki naji a,waje Amira take fadin haka.
Hamdala Maji tayi a fili tana fadin shine ba kama ba ai taji dadi don ko ba komai ta tsinkayo canji ga yanayin shi sosai don gashi ya shigo gida har da sallama a bakin shi yau.
,Nan sukayo waje don taron shi da saurin su hae suna karo da junan su.
Kamar yadda ya tafi
daga shi sai yar jakar shi wanan karon ma haka yadawo masu sai yar karaman jakar daya goya a bayan shi.
Daga inda matan gidan suke zaune da yaran su suna shan rake suka tsura mai ido kawai.
Shine yake ce masu sannun ku da gida mama daga haka bai karasa ba ya juya zuwa part din mahaifiyar shi.
May na fada maki Asiya na fada maki tsula ya tafi tsula zai dawo muna rabu da dan matsiyaciya kawai masu gadon tsiya ta ko ina.
Dariya suka sa dasu da yaran su a lokaci guda wanda sai da ran sadauki ya dan sosu don yasan dariyar a kan shi ne.
Sai dai ya dake ya rugumi kannen shi da suka sheko suka rugumay shi suna mashi sannu da zuwa.
Banda Bintu wace take tsaye daga gefe sai dai da murna a fuskan tana cewa,
Sannu da zuwa yaya cikin yar muryan ta ko bai jita bane yadai ja kannen shi suka shige kawai abin su ciki.
Bayan su tabi suku suku da ita tana dan dariyar yake a fuskan ta.
Inda MMaji take zaune ya isa cikin farin cikin shi ya zauna kasa tare da sa kan shi saman cinyarta yana cewa Maji yaya na samay ku?
Murmushi maji tayi tace anya Baba na kwallo kaje kuwa kaga yadda duk ka canza min a lokaci guda.
Murmushi yayi yace kai haba dai maji kwallo ko naje wallahi ban ramay bane?
Sai tai dan murmushi wanda rabon haka a tsakanin su ya matan lokacin shi.
Maji ta,waiga inda Bintu take rakube tana cewa, Fatima kawo wa yayanki ruwa ko yasha Amirah tace da abinci ko gaba daya.
Nan suka shiga kitchen din tare wanda Bintu ta fara dauko abin shan da suka shirya mashi takawo mashi.
Ta duka ta aje zata juya yake cewa ke wata irin bakauya ce kinga mutum ya dawo baki iya gaishe shi ne.
Amira dake aje tire din abinci take cewa aiko ta gaida kai yaya sai dai in bakaji bane.
Maji tace kadawo ke nan ko hutawa bakayi ba zaka fara takura min yarinya ko.
Ya juya inda suka aje mai kayan abinci a gaban shi yana fadin kai kai kai Amira duk ni kadai wanan abinci haka mai yawa.
Ga,wacce tayi su nan ai da yawa tana nuna mashi Bintu dake can gefe kujera a zaune kasan ties a dakin.
Amira tace ta ba bako yake ba yau ai batai laifi ba ko don ance bakon ka annabin ka.
Sosai yaji dadin wanan karamawan da kannen shi da mahaifiyar shi sukai mashi haka wai duk shi sadauki keda wanan taron.
Shigowan hjy Kubura dakin shi ya katse hiran jin dadin ganin shi da suke yi a lokacin
Tashigo da fara,a a fuskan ta tana cewa yanzu su Anwar ke fada min wai bakon ghana ya dawo ina shigowa.
Murmushi yayi yana cewa mummy mun samay ku lafiya ko?
Lafiya kalau sadauki yaya hanya yaya can kuma I hope komai normal.dai ko ?
Inda dane Maji zatace tsakani da Allah tazo taron shi amma yanzu data rage ta, sai take kallon makirci ne ya kawo ta kawai.
Nan ta kare kitihin ta ta fita daga dakin daga inda Bintu take zaune tabi da kallon makira kawai ita da maji da suka san komai.
Maji bayan yaran sun kaure da hira tadan fito tsakar gida tun daga inda su mama suke zaune aka jefo ta da hausa.
Tsula ke nan wai tafiyan sundundun madundun yadda aka tafi haka aka dawo zaban kunya.
Dan nagada ai bai iya gado ba dama taya za,ace kagaji abu kuma ka ketare shi.
Maryam dake bayan Maji bata san tafito waje zubar da bawan lemun da suka,sha ba, sai jin muryan ta maji tayi daga bayan ta tana cewa.
Mu dai mun gode ma Allah ai yaje lafiya ya dawo lafiya yan bakin ciki da suka so kada ya dawo sai su mutu.
Da sauri Maji ta juyo kanta tana cewa ke maryam ban son rashin kunya fa da suke zancen su sun ambaci sunan wani ne.
Sadauki da suke daki suna jin amsar da maryam ta bayar sun san akwai magana a waje sai sukai shiru daga ita har sadauki din lokaci guda.
Maryam ta shigo tana turo baki gaba tana cewa yan bakin ciki kawai dama nasan sheri da ganin kwam ya,zaunar da su ai a gurin kuma sun gani.
Maji ta shigo dakin don haka maryam din tai shiru don tasan in taji tana mita,yanzu zata balballeta ne da fada.
Sai da maji ta zauna ta dube su a nutse take cewa abinda nake so daku maryam shine.
Duk wacce taji a na,sake magana a gidan nan inda ba sunan mu suka ambata ba kada wacce ta kara tankawa kowan su.
Amirah tace Maji su wasu irin mutane ne da son fitina daga dawowan mutum zasu fara sakewa mutane magana kamar suna jirace da shi.
Maji tace suna jirace mana ba hassada bane kawai rudin shedan ai komai mutum zai iya yi don jan fitina.
Fitana,suke so don sunga yadda yaje haka ya dawo masu shine abin dariyar

Please Login or Register in order to submit comment