Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dai kawai da mutum ya shiga yanzu za,ace ga abinda yayi kuma.
Aiken ki fa nayi Amira kika tsaya mai da naki ba,asin son raki haka Amira taja kafa ta,wuce zuwa sauran sassan gidan,
Inda Bintu take zaune maji ta dan kalla tana fadin yi hakkuri kinji har ta dawo muji ko canjin waye,
Andan jima kadan sai ga Amira ta dawo tana konkwami tana fadin wai, maman su Hadiza tace takawo ta aje ko na baba ne amma taki bata ga kudin tana kokarin mikawa mahaifiyar ta kudin hannun ta,
Amira mai yasa baki bata ba da kika dawo da kudin nan may zanyi maki dashi a nan ,
Maji cewa fa tayi wai zata ajewa Baba ni kuma nasan ba,bashi kudin zatayi ba shiyasa nace mata tabari na tambaya sauran shiya muji in ba nasu bane,
Yadda maji take magana da yar ta acikin lumana ba daga harshe ya ba Bintu shawa sosai sai faman bin su da kallo take yi, na sha,awa.
Yadda uwa takewa yar ta magana a cikin kwantar da hankali da fahinta,
Inda Bintu take a zaune Maji ta,waiga tana fadin inaga canjin Alhajine idan ya dawo zan tambaya muji in har ba nashi bane zan sa su dawo mata da kudin.
Bintu ta mike don fita daga dakin a daidai lokacin da Umar ya shigo dakin ke nan babu ko sallama.
Sai cewa yake ni zan tafi ball kada kuma ace ban fada ba natafi , yana,wani cicin magani cikin dakewa,
Haba babana kai wai yaushe ne zaka girma zaka shigowa mutane daki babu ko sallama kana wani shan kamshi da cin magani.
Kamar wan da zai tafi gurin wani abin arziki wai ball, ball din mai zai tsinana maka a rayuwanka ne wai,
Maimakon ya tsaya yaji karshen maganan ta,sai juyawa yayi kawai ya fita daga dakin,
A hankali maji ta sauke ajiyan zuciya tana furta Allah ya shirye ka babana,
Bintu dake tsaye ta amsa da Ameen Mama sosai har cikin ran maji taji dadin Ameen din da Bintu ta amsa mata dashi.
Mama ni zan tafi sai anjima ke nan zan fada mata yadda akayi, to kin ji yar albarka ki gayar min da Hajiyar masa din kinji ,
Bintu takai kofa Maji tace may ye sunan ki ne bakuwar hajiya ?
Cikin murmushi Bintu ta amsa da Bintu nake mama Allah sarki sunan mai kyau sunan mahaifiyar maigidan nan ke nan ai.
A waje ta samu wanan mai bakin ran yana tare mashin zai hau ko kallin shi batayi ba don tsoro ma yake bata, ita,

****** ********** *****
Kida ke tashi daga cikin waya daga daki yayin da uwar ke daga gurin wanke wanke tana wanke kwanukan da suka ci abinci dashi na daren jiya,
Ganin hankalin uwar yana ga aikin da takeyi yasa Raiha mikewa a hankali zuwa gurin da ta boye kayan harkan ta a ciki ta jawo wani kwalba ta kwankwada son ranta tai wani jan iska da tsuke bakin ta a hankali.
Ta koma saman gadon da ta tashi a kai, ba bata lokaci sai barci ya dauke ta a gurin.
Uwar na shigowa daki taga yadda ta kwanta daidai da ita, a hankali uwar ta kada kan ta don takaici tana dan kiran sunan ta ,
Ke Raiha Raiha fa wai bazaki tashi ki yi abinda zakiyi bane ki kwance haka galala tun safe kamar mara lafiya.
Cikin murya irin ta mashaya Raiha tace kai haba mama please easy please easy barci nake ji fa.
Ikon Allah barci dai barci dai kamar wata malalaciya sai kin tashi ki ce wai ke yunwa yunwa kamar zaki hadiye mutane, lokaci guda.
Nan uwar ta barta ta,tafi tana mita a kanta a lokacin ta gyara kwanciyar ta da kyau taci gaba da barcin ta.
Bata farka ba sai yam lis ta farka sai bandaki tafada tana sauri don fitsari da kashin da take ji a lokaci daya.
Bayan ta dauki lokaci tafito ne daga ban dakin shine ta debi ruwa a randa ta watsa don ta dan ji jikin ta ya sake mata don nauyin da yai mata a lokacin.
Tsab ta shirya cikin wasu kananan kaya ta,dauko hijjab din ta tayafa a kan ta kamar wata ta kirki can.
Inna ni zan fita tace a gadarance uwae tace ina kuma zaki yanzu ana batun yin magariba kuma ?
Ba nisa zan tafi ba zan dan je can kasan layin mu ne na,dawo .
To ki daiyi sauri kafin mahaifinki ya dawo bai samay ki ba.
Yanzun ai zan dawo ba dadewa zanyi ba Inna, tana fita ta tare mashi sai wani uguwa da ke da yawan mutane akasarin su duk matasa ne maza da mata birjit a gurin.
Kutsawa tayi itama tashige gurin can wani dan lungu wani gaye ne ta nufa yana zaune tsakiyan su sai busa hayaki yake,
Yana saye da,riga blue mara hannu a jikin shi duk mozuqu din shi sun fito wahe sosai.
Yana ganin ta tace yar halas yanzu fa nake zancen ki a,raina nace ko kayan basu kare bane har yanzu don tun shekaran jiya baki leko mu ba nagani,
Ina tafe ai na tsaya ne har na karasa sauran wanda ya dan rage min don gudun kada na tara kwalabe a dakin namu yai yawa.
Kasan gyatumar ba sanin kai tayi ba har yanzu bat da sau nake mata koda ta rutsani nakan ce mata maganin mura ne nake sha ai,
Shegiya baby watau dai a kwana kike sakata ke nan dai ko?
Kai ma kagane ke nan ai don abin sai da kwana don ba,a,bari ai saurin sani abin.
Nawa kiia zo dashi don kin san ranan ma na biyo ki canji dai ko?
Nawa ka biyoni brosha ina dari uku ne dai kawai ko?
To dari uku ba kudi bane dasu ne ai muke karawa muna business din ga,shegun kwalawan nan kullun sai kokari suke suga,sun kama mutane don kawai su caji mutum dan canjin kashi badon a,daina harkan ba.
Ni dai kaji miko min kaya na natafi don yau ba dadewa zanyi ba ina sauri ne.
Wasu kala za,a baki akwai fa,sabbin fitowa masu aiki sosai wallahi tace cikin tsiwa bani dai wanda ka saba bani kawai na,wuce na biya shagon Samuel na kara dan kwalabe a can,
Daidai lokacin Umar yazo baiyi magana ba,sai kudin da ya miko mashi yace kaibani nabar gurin nan don ban son sa ido da yawa.
Brosha amma kasan sai ka sallameni zaka sallami wani can ko?
Umar yana daga gefe ya harde hannayen shi a kan chest din shi ya zuba masu ido yana sauraren abinda sukeyi kawai.
Sanin ko waye Umar yasa brosha fara hado mai kayan shi don yana kai wata biyu baizo gurin ba yafi aikowa a,saya mashi,
Yana kokarin miko mai canji tare da kayan shine fam cike da leda, yaji muryan Umar yana fadin ka bata da sauran canjin sai wani lokaci kuma ya juya yatafi a bin shi bai tsaya jin may zasu ce ba,
Binshi da ido Raiha tayi tana,mamaki mutum haka ga alheri ga kuna ta hango jin kai a tare da shi.
Mtwee tace tare da juyawa tace kai bani na,wuce kaji ban son bata lokaci nace ma,
Aike yau kin taka sa,a wallahi haka yake in har yazo sai yai wa wani alheri a gurin nan, sai dai kuma ba kullun ne yake zuwa ba,
Tana karba ta juya tabar gurin don zuwa chemist ta sayo sauran abubuwan ta.
Tana fitowa yana,shigewa mota ya harba yabar erea din don gudun wani ya ganshi idon sani yasa yake zuwa wanan uguwar sayen kayan mayen shi can nesa da gida.
Ko da Raiha ta isa gida lokacin har takwas da rabi na dare.
A lokacin mahaifinta har ya dawo daga kasuwa sai dai yana daki shi yana rage kayan jikin shi.
Hakane ya bata daman shigewa ciki batare da yasan dawowan ta ba gidan.
Ganin ta kawai mahaifiyar ta tayi don haka hankalinta ya kwanta don tasan da zaran mahaifinta ya ji bata gidan matsala ya faru ke nan.
Tafito daga dakin mahaifiyar ta,a,daidai lokacin da mahaifinta yake kokarin zama a,saman tabarma a kofan dakin shi tana cewa baba sannu da,dawowa kawai ta,sa kai ta shige abinta,
Ashe tana gidan ai yanzu nake batun nace wai tana ina ne banji motsin ta ba uwar tace tana ciki ai tundazun, (Uwa ke nan,)
Nan ya zauna yana cin abinci suna hira da mahaiyar Raiha cikin so da kauna a tsakanin su,

****** ********* ******
Yaro ne daga kofan gida yake kwada,sallama yana cewa abani ruwan pure water, na naira goma.
Da sauri Hanne tafito daga dakin ta tana cewa shigo ka karba kaji ta bude dan fridge din ta ta dauko mai ruwa leda biyu ta bashi ta karbi kudin zuwa dakin ta,
Ba,ajima ba wata yarinya tashigo itma ta saye haka mutane suka gane cewa tana sayar da,ruwa ana dan shigowa gida ana,saye.
Nan tai shawaran ta fara dan kayan sanyi irin zobo da kunun ayya tana hadawa dashi ko zata kara cabawa ga samu,
Kudin ta bayar aka,sato mata kayan zobo da na kunun ayya ta hada.
Ba bata lokaci aka ganeta mutane suna shigowa,saye tun dai da,zafin ranan da,ke yawa a garin don ko baiyi sanyi sosai ba ana saye hakana.
Ance rai da kwadai don haka Hanne tafara shawaran canza fridge din ta zuwa wanda yafi wanda ke gare ta girma don ta kara bun kasa sana,an ta dashi.
Da maigidan ta yadawo ta fada mai ahawaran da tayi shiru yayi don baida na fadi, don baida na fadi saboda yasan cewa shi kan shi yana amfana da wanan sana,an data samu tana dan yi yanzu.
Saboda yana tare masu gurare da dama na yau da kullun a gidan har ma,da wanda bai zata ba don yan zu a lokaci ne muke inda mata suke bada nasu gudun mawa a gida fiye ma da yadda ba, zata ba a rayuwa




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: A LOKACIN NE


BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAIJIN KAI,
ALLAH NAGODE MA DAKA BANI WANAN DAMA NA RUBUTA WANAN LABARIN DA KE DAUKE DA YADDA RAYUWAN ZAMANIN NAN NAMU MATSALOLI DA ILLOLIN DAKE CIKIN WANAN RAYUWAN NA WANAN LOKACIN DA MUKE CIKI ALLAH KA BAMU IKON AMFANI DA FADAKARWAN DA ZAMU TSUNTA A CIKIN WANAN GUNTUN LABARIN,,,

IDDAN BAKI BIYABA DAN GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE BADA YARDANA BA,,,,,,

Zaune take saman sallaya a gurin da ta idar da sallah hannun ta ya na dauke da farar tasbaha tana ja a hankali sai dai a zahiri ne hakan a can cikin kasan zuciyar ta tunane fam a ranta tana tunanen ko a halin yanzu ina dan ta Umar ya shiga,
Kadan kadan tana daga kanta tana kallon agogon dake manne a,bangon dakin ta a hankali,
Karfe goma,sha daya na,dare saura agogon ya nuna mata a lokacin hankane ya kara sa hankalin ta, tashi sosai don tana tsoron kada ya shigo mata kamar yadda take zargin ganin shi
Tarasa gane wani haline dan nata yake kokarin jefa kan shi a ciki, ga yawan surutun kishiyoyi dake damun ta a a kullun,
Maimakon ace sun taimaka mata gurin kara bashi tarbiyan da suke ganin baida shi issashe sai kawai suka buge da gulma da kara mugun zance a kan dan nata wanan al,amarin ne ya ke kara sa jefa Maji a cikin tashin hankali, da damuwa a rayuwan ta gashi dai ita a nata fannin bata kasa da nasu yaran ba, gurin daukan su har a cikin zuciyar ta a,tsakani da Allah take masu komai,
Kara daga ido tayi takai duban ta ga agogon bangon dake manne a bangon dakin nata,
Karfe sha biyu saura yan mintina na dare ta gani haka ya kara tayar mata da hankalin ta,
Bata kai karshen tunanen taba taji an turo kofan dakin ta, da karfe inda sabo da hakan tasaba tasan ba mai mata wanan halin sai maigidan su,
Ba sallama sai cewan da yayi a hasale wai ina danki ya tafine ?
Shiru Maji tayi don ta saba da wanan kalman na danki a bakin maigidan nasu,
Kefa nake tambaya yakara fadi daga inda yake tsaye daga kofan daki rike da labulen dakin nata,
A hankali Maji ta dago kanta zuwa kalkon shi tace cikin yar murya siririya ban san ina ya shiga ba ba nima tun dazun nake zaman jiran shigowan shi don yaci abinci,
Wani wawan kallo ya watsa mata daga inda yake tsaye yace ai dama nasan da yardan ki yake wanan mugun rayuwan da take don ke ce kike daure mai gidin yake kara lalace wa ai kowa yasan hakan,
Hmmm kawai tace tare da fadin Allah ya kyauta malam amma ta yaya zan goyawa Sadauki baya ya dinga abinda yake alhalin nasan ba alheri yake koyawaba a rayuwan shi,
Wanan kuma ke kika sani don ke ce da hasara saboda ni ba shi kadai ke gareni ba ai,
Yana fadan haka ya gaura kofan dakin da karfi yafita daga dakin nata rai a bace,
A hankali maji ta sauke ajiyan zuciya, zuciyan ta yai mata wani tauri saboda kalamin da mijin ta ya fada akan dan tilon danta namiji guda da Allah ya bata a gidan sai yan kannen shi mata da ke bayan shi su uku rak Allah ya bata a gidan mijin nata,
Yayin da sauran kishiyoyin ta suke da yara fiye da nata a gidan
Maji itace mace ta uku a gidan malam habu dan kasuwa ne shi, sai uwar gidan su mama hauwa mai yara bakwai a gidan,tana aikin a women center,
Sai mummyn Asiya, wace itace Maji ke biwa, tana da yara biyar a gidan, tana aikin koyarwa sai amaryan su Anty Kubura da ke da yara hudu ita ma aikaciyar jinyace a wani asibitin gwaunati,
Daga cikin su maji ce bata wani aiki kwakwara don ita batai boko mai zurfi ba tana aji hudu secondary malam habu ya auro ta don haka bata da aiki sai yan buga bugan kasuwanci irin na mata da take a gida kawai,,
Da farko malam Habu yana matukar son Maji da kuma tausaya mata don bata da ilimi mai zurfi, sosai,
Amma yanzu matsalar dan ta, Umar ya wanda takewa lakani da sadauki don kasancewar shi sunan shi Umar faruk, kuma a matsayin shi na dan farin ta yasa take kiran shi da haka,
Rayuwan da Umar yake ciki a yanzu yafara kawo matsalar a tsakanin malam habu da matar shi Maji mai suna maimuna,,
Matsalar farko dai daga irin yanayin shigar shi na tufafin shi, don sam baya iya saka irin tufafin diyan hausawa na al,ada a jikin shi,
Sai kuma gashi ya bullo da dabi,ar son wasan kwallo a rayuwan shi don duk abinda yake da zaran time din zuwan shi filin wasan kwallo yayi dole yabar koma maynene zuwa gurin wanan wasan a duk safiya da marance, na kulli yaumin,
Malam habu yayi iya kokarin shi gurin ganin Umar yabar wanan wasan kwallon kafan da yake yawan fita tun yana dan karamishi,
Amma abin ya faskara duka zagi da bakar magana ga mahaifiyan shi bai sa Umar ya daina wanan wasan kwallon kafan ba da yakeyi
Yan uwan Umar duk yan kasuwa ne sai masu aikin gwaunati daga cikin su amma shi ba ruwan shi da shiga harkan kowan su
Iyakar shi yai wanka yafuta gurin abokai sai kuma zuwa wasan ball, da yake a gaban shi,
Maji tai nasihan rana taina dare amma bai sa Umar ya daina wanan halaiyar nashi ba

Fitan malam Habu daga part din Maji suka hade da Umar wanda ke shigowa gidan a lokacin wani wawan kallon da tsana ya watsawa Umar din,
Sannu Baba ina wuni yakai har kasa yana gaida mahaifin nashi a cikin ladabi da biyayya wanan gaisuwan yaran dakin maji ke da wanan tarbiyan a gidan kawai,
Uwaka na ce uwaka tare da kara mika mai dakuwa da hannun shi na dama yace yaron banza yaron wofi kawai mai ladabin shegu,
Da ban wuni ba zaka gan ni haka ina ka shige haka tun safe sai yanzu zaka shigo min gida, kana wani ladabin shegu haka dakai,
Baba bafa ko ina naje ba ina gurin training tun dazu yanzun kuma da zan dawo na tsaya gurin dantani mai shago muna hira a majalisasr su,
Training din uwar ka na ce training din tsiya jeka ai tunda rayuwan da kazaba wa kanka ke nan ni ba ruwana inka samo wahalanka kada ma kace ni Ubankane,
Umar dai yana duke a gurin da yake baidaga ba yana sauraren kalaman mahaufin nashi,
Malam habu ya wuce ciki fuuu yaba ta faman sababi da bambami akan umar din,
Daga kai yayi ya kai kallon shi ga kofan dakin mahaifiyan shi wace yasan daga gurin ta mahaifinshi yake yagama zazzaga mata tsiya ke nan a kan shi don haka yasa tafasa shigan da yai niyar yi gurin ta a lokacin,
Don yasan yanzu tana can ranta a bace akan rashin ganin shi da batayi ba yini guda zur ga kuma baba ya je yanzu ya zazaga mata balain shi da ya saba,,
Yashige part din shi ya fara dan rage kayan jikin shi, daga shi boxe din shi irin ta maza ya rage a jikin shi,
Dukawa yayi kasan gadon shi ya jawo wasu kwalabe cikin wani leda mai karfi daga karkashin gadin inda ya balli wasu kwaya dake cikin ledan ya bude wani kwalban syrup ya hade su tare ya shanye, a lokaci guda, ya fada saman kujeran shi tilo daya dake dakin,
A hankali ya fara zukan syrup din har sai da ya shanye duk ruwan maganin dake cikin kwalban gaba daya, ya wurga kwalban a kasan carpet din dakin,
Nan saman kujeran ya dan fara lumshe idanuwan shi a hankali yana rufe su ko may ya tuna sai kuma ya mike daga inda yake zaune zubur ya dauke kwalban daga inda ya aje su ya mayar gurin da ya dauko su,
Nan yaja jiki zuwa saman kujeran da ya fara zama ya kara zubewa sama da karfi har saida kujerar yai, dan kara don fada mashi da karfi da yayi,
Nan barci ya kwashe shi babu bata lokaci a gurin baifi mintuna ba sai ga Maji wacce ta kasa barci ta shigo dakin ganin ko ya dawo daga yawon da mahaifin shi yace ya tafi,
Maji ta dade tsaye a kan shi tana kare mashi kallo cikin mamaki tayi tayar dashi amma bai tashi ba dole tafita daga dakin tabarshi a hakana,
Zuciyar ta fam da kunci sai kuna dan zargi da ya fara darsuwa a zuciyar ta a hankali,
A haka ta kwana ranta babu dadi a cikin sa sai faman tunanen da takeyi har dare ya raba sosai a lokacin,

****** ********* ******
Zaune take a f
gaban mahaifin ta a cikin natsuwa take sauraren shi, yana mata zance akan zuwa birnin da zatayi gur8n kaunan shi dake can tana aure don ta matsa a kan Bintu tazo mata hutu ta dan kwana biyu a gurin ta,
Sam Bintu bata,son wanan tafiyan don dai babu yadda zatayi ne da umurnin mahaifinta da gaskiya bataje ba,
Don tafi son ta,zauna a kauyen su tare da mahaifinta don koda take mace ce itace kamar jagoran gidan nasu duk da kasancewar Bintu karamar yarinya ,
Haka take yawan aikin wahala a kan su samu dan abinda zasuci a gidan su kasancewar mahaifin nata ba,wani mai abin hannun shi bane,
Itace zuwa icce itace suyan awara da rana da safe kuma tana koko da kosai kafin ta dawo zuwa makarantan bokon da yake a ranta,
Yanzu gashi gwagonta ta birni ta matsa sai tazo gurin ta wai hutu wanda ita bata san dalilin da ya sa,duk tazo sai tai zancen zuwan Bintu gurin ta hutu ba,
Yan kayan ta,already ta,shirya su a dan jakar ledan ghana most go karama duk jakar ta tsufa sosai don har ledan jikin jakar ta dan tashi ya,wani dan takure daga jikin shi,
Kudi mahaifinta ya ciro daga aljihun shi dubu daya ya mika mata tayi kudin mota dashi,
Kallon kudin take tana mamaki inda ya samo har dubu daya yabata wai tai kudin mota dashi,
Hannu biyu Bintu ta mika ta karbi kudin cikin ladabi tare da fadin na gode Baba,
Bayan ta karba ne yake cewa tau Bintu ki saurareni kiji abinda zan fada maki da kyau,
Ki sani dai rayuwar birni daban yake da,tamu irin na kauye don haka kiyi taka tsatsan da duniya ki kama kanki ,
Ki kawar da idon ki ga duk abinda,bai shafeki ba a rayuwan ki ki tsaya inda gwagon ki ta tsayar dake duk da yake ke yarinyar ce nnatsatsiya amma nasan zakiga abin mamaki da zai iya canza maki rayuwan ki a can,
Don haka kiyi taka tsatsan da duniya baki dayan ta a yanzu babu gaskiya ki tsaya a matsayin ki na yar talkawa kamar yadda kika samu rayuwar mu, aciki tun farko,
A hankali Bintu tace insha Allahu baba zan tsare kamar yadda kace zaka kuma samayni da kiyayyewa insha Allahu,
Yace Allah yai maki albarka Bintu Allah ya tsare min ke da tsarewar shi ta karba da amin Baba idanuwan ta sun kawo hawaye kamar zasu digo dag idanuwan ta,
Shi da kan shi ya rakata har tasha inda zata samu motar da zai kaita, garin Sokoto,
Tana zuwa motar ta cika suka kama hanya sai Sokoto zuciyar ta fam da kunci a cikin sa,
Sai karfe biyu suka shigo gatin na sokoto a lokacin mutane suna ta haramar yin sallah azahar a garin,
Mai yar mashin ta dauka kamar yadda akai mata kwatance tace a kaita Sama road, a bakin shagon dantani mai yar mashin ya tsaya da ita,
Shi ta tambaya gidan Gwago Asmau mai masa ya nuna mata da kwatance tabiya mai mashin kudi ya tafi ta dauki yar jakar kayan ta zuwa gidan da akai mata kwatance, dashi,
Da sallama a bakin Bintu ta shiga gidan ta samu gwago zaune a tsakar gida tana gyara kayan yin masan ta,
Tana ganin Bintu ta fara fara,a tana cewa a,a,a wanake gani yau garin namu kamar Bintu,
Maraba da yar gwago sannu da zuwa sannu da zuwa tana mata maraba cikin jin dadi da ganin ta,
Daki ta nunawa Bintu ta,shiga da kayan ta daga cikin dakin tare da,samun guri ta dan zauna a takure daga gefe guda,
Gwago ta,shigo, dakin dauke da

Please Login or Register in order to submit comment