Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mota mu tafi da wanan bakin shirmay naka babu kunya da kake min.
Easy man, take it easy bani nakar zomon ba fa, kaga ni fa ban hanaka ba don ni ba motsoraci bane irin ka.
Wani harara yakai wa Bashar yace wallahi zaka kaini makura Allah da wanan halin rashin kunyan da ka tsiro wa mutane daga sama.
Bashar dai yaja motan shi yanawa sahiban shi bye bye, suka bar gurin suma suka juya zuwa cikin gida.
Airport ya kai shi nan ya shiga jirgi da ya tashi da sha biyun rana suka tafi Abuja, bai so buga wanan wasan ba amma halin da yake ciki yaji kawai gara ya je ya buga ball din shi ko zai samu sauki a zuciyan shi.
Duk da kwallon da ya buga bai hana shi jin abinda yake ji a zucuyar shi ba har yanzu.
Suna waya da mutanen gida amma bai, taba jin wani yai zancen yarinyar ba ko yaji an anbaci sunan ta ko a waya.
Gashi girman kai ba zai iya barin shi ya tambayi kowa labarin ta ba don sai yana ganin kamar abinda yai mata ne yake ganin bai kyautawa yarinyar ba.
Don yana gani ai kaman zaman kaunan shi yarinyar take a gareshi amma shedan ya rude shi yai mata haka.
Yace a fili, kai kai gaskiya ban kyauta why don Allah why har haka ya kasance a tsakanin mu ne wai.
Ya dan kai wa katifan da yake kwance nashi da hannun shi na hagu da karfi sosai har sai da ya dan jin zafi a hannun shi.
A haka ya kai har sati biyu acan suna da wasan da zasu buga sati mai zuwa amma ya juyo ya dawo gida haka kawai.

****** ********* ******
Ina gurin mama na zaune na sake raina ba abinda ke damuna yanzun in ba matsalan mijin ta ba da kulun a cikin tashin hankali suke a tsakanin akan ban kawo masu komai ba.
Amma nazo ina cinye mashi abincin gidan shi a banza shi gaskiya ba zai zauna da agola ba a gidan shi.
Naso na bar garin amma sai na dake na tsaya inga iya gudun shi ko zai kore ni ne ni kuma nasan yadda zan girgiza mashi auren shi.
Sai dai ya shigo yayi haukan shi ya fita babu mai tsinka mashi a cikin mu dan dama ma ita mama sukan kwasa dashi idan abin ya ishe ta.
Gidan kowa ban zuwa kullun ina gida zaune kamar wata matar aure can dani.

Ganin shi kawai sukayi da yammacin jumma,a ya diro garin nan suka gaisa mama take tambayan shi yaya akayi kuma ya dawo ba yace suna da wasa wani sati ba sai satin sama zai dawo gida.
Yace eh maji nadawo ne nai wani abu a garin kuma da akwai wasu takardu dana manta ban tafi dasu ba da zan tafi.
Yakai wani lokaci a zaune baiga giccina ba hakan yada shi sanin cewa har lokacin ban dawo ba ke nan garin.
Ya mike ya fita kaman wani mai jin kasala a lokacin, Bashar ya kira yazo idan an fito sallah su fita.
Ranan Monday maryam tafito a cikin shirin ta zata shiga makaran ta,a waye ta samay shi ya fito daga gurin exercise .
Sun gaisa yake tambayan ta ita wana har yanzu taki dawowa ba kun koma makaranta ba tace eh munyi waya da ita tace bata san ranan da zata dawo ba kila ma,
Fuska a daure yace ina ne garin su?
Tace, a yaya baka san garin su Bintu ba kai, duk zaman ta a gidan nan?
Yace don Allah malama fara bani amsan tambayana kafin kiyi min halin ku na yan kasa tukun na tambaya cikin tambaya.
Tace can rabah take nan dai tai mashi kwatancen yadda ake zuwa garin yace inda muka tafi gaisuwan wancan mutumin da tatashi aure kenan ya rasu ko tace mashi eh can ne ya amsa mata da ok good.
Zaka tafi garin ne yaya ta tambaye shi tare da kallon fuskan shi yace ban sani ba tambayan ki kawai nayi.
Sai batan kamar kwana biyu da tambayan maryam ranan da safe yace wa Bashar ya shirya zasu tafi wani dan kauye su dawo.
Sam Bashar bai kawo komai ba a ran shi nan yazi ya dauke shi shi yaja mota suka tafi.
Ban zuwa gidan kowa amma ranan haka kawai nace zan je na gaida kakanin mu kafin na tafi don saura kwana biyu na tafi.
Mun fita gida da kaman awa biyu suka shigo garin wani mai faci bakin titi suka tambaya gidan dan Amo shayi akai masu kwantacen gida.
Da farko da suka isa gidan yaso yai gardama ko banan ne gidan ba saboda ganin yadda gidan kaman ma yafi ko wani gida na uguwar lalacewa a shiyan.
Sallama suka ce ai masu da maigidan yaron da suka tura yace kai mai gidan kan yanzu ba,a samun shi gida yana can gurin moli.
Basu gane may yaro ke nufi yace yashiga yace wai bakine daga sokoto sun zo ganin Bintu.
Mamana tanajin haka tace, Bintu bata nan tafita amma ace su waye yace ace yaron hjy ne yazo tafiya da ita.
Jin haka yasa mama tace ace su shigo daga ciki ai su yan gidane nan ta tura yaron ya kirani gidan kakan nina, basu so shiga gidan ba amma dole suka shiga.
Shi dai bashar sai kallon ikon Allah yakeyi kawai don abin ba mamaki ba daure mai kai yayi.
Bin gidan yake da kallo da mamakin yadda dan adam ke rayuwa cikin wanan rubaben ginan haka da akoda yaushe yana iya rushewa.
Bai san cewa shigina in har akwai mahaluki a cikin shi ba Allah na karewa yadda yaso.
Tabarma mana ta shimfida masu daga dakin ta nan ma yai matukar mamaki wai dakin da ake rayuwane, acikin shi haka.
Ruwa ta debo masu acijin wani kufin silver ta sabo ta kawo masu bashar ya karbi ruwan ya dan kora a cikin shi.
Shikan bai san yaya zai iya kai wanan cup din a bakin shi ba gaskiya don tun bashar baisha ba yaji kaman yai amai.
Bayan mama ta dan fita dauko masu abin fitara ne Bashar yace wallahi kasha ruwan nan don ba haka ake neman aure ba.
Cikin tsawa yace Bashar you are very stupid wallahi.
Neman auren wa kuma can sai dai idan kaine kazo neman auren ban sani ba don kai baka raina mata naga alaman haka ?
May ye abin rainawa ga abinda mutum ke so a ran shi ?
Shiru yayi don mama ta dawo a lokacin tana mika masu abin fitaran tana fadin kuyi hakkuei akwai zafi wallahi.
Sai ga wata akuya tashigo nan ta hau saman tsadaddun takalman su ta sake mai fitsari a na shi.
A hankali yace oho shit da ido yaiwa bashar din signal ya kalli kofa abinda akuya take mashi.
Murmushin keta bashar ya sake mashi, yace don't mind my friend duk ciki ne ai.
Lokacin na shigo gidan da mamakin ko su waye aka ce sun zo nemana a lokacin daga sokoto.
Sam ban kawo cewa shine ba don sai ina zaton mamace ta turo wani ya dauke ni kila.
Ina bullo daga kofa mukai arba dashi zaune cikin fararen shaddan shi yaci starch.
Nai matukar mamakin ganin su a gidan mu dakin uwata musa ne ya hango akuyan tai fitsari akan takalmin dayan su ya shiga koran akuyan ya debo ruwa ya zubawa takalman.
A hankali na tsaya daga kofa ina masu sannu da zuwa, duk na shiga rudewa da ganin su.
Bashar yace min humm Bintu kinzo kinga mama shike nan kin manta da zancen an koma makaranta ko ?
Nai dan murmushi nace ban man taba yaya kawai dai ban tashi dawowa bane a lokacin nan.
Da sauri yaya sadauki yace sai yau she baki da hankali ne wai ana karatu zaki zo ki samu guri ki zaman ko a kauye.
Ganin zai sake layi yasa Bashar tare da fadin yanzu dai mama tace muzo mu dauke ki yau din nan don an koma school tun ranan Monday kin sani kuma.
A hankali nace yau din nan yaya yace eh haka ta bamu umurni shiyasa muka zo ai daukaki din.
Nace ni gaskiya ban shirya ba fa sai dai idan na shirya zan dawo anytime.
Kafin wanin mu yai magana sai mamana ke fadin may zaki shirya kuma ina kin yi wanki jiya kitashi kawai ku tafi tunda har kikaga hajiya ta aiko a dauke ki.
Ban so ba haka na shirya zan bisu su suka fara fita yakawo kudi masu yawa yabata yace tayi hakkuri babu kudi a jikin shine.
Sai da zantafi nace mama ki boye kudin nan kafin mijin ki ya dawo ya kwashe su kiba musa yakai maki gidan su kakale a boye maki su ku dan samu abincin abincin rana dashi.
Nakawo sauran kudin dake hannuna sunkai dubu goma nace tace ga abinda aka bata.
Mukai sallama dasu muka fara hanya ina baya sai tunane nakeyi kawai a raina.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN KARANTA KO KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NE SHEDAN MUNA BINKI BASHI,,,,

ALOKACIN MU KE,,,,

Mun kama hanya sai hiran su suke shi da Bashar niko ina bayan mota zaune a takure cikin damuwa.
Bashar ne daga inda yake zaune ya dan juyo yace min Bintu gaki kinyi shiru mana.
Nai dan murmushi yake kawai nace ba komai yace ko kina son a sai wani abune?
Kai kawai na girgiza mai nace idan mun kai wani kauye zan sai dan tsaraban da zan kai wasu mama kada naje masu hannu sake.
Sai faman gudu yake shararawa da mu har sai da naji tsoron gudun da yake da mu nace komai nashi dai na muggai ne ko kashe mu yake son yi ne wai ?
Kafin wani lokaci sai gashi mun fara hangen garin sokoto daga nisa mun da kara gaba nani ya taka burkin motan da karfi sai dana nan dan firgita bani ba har Bashar dake gaban mota sai da ya kalleshi.
Muna nan zaune shiru ya bude mota yafita zuwa gefen da nake zaune ya bude marfin mota fuska a daure yace nafito ina fitowa ya mayar da marfin motan ya rufe .
Ina tsaye jikin mota ya daro hannau shi guda saman kan mota dayan kuma ya sashi daga gefen kunkuruna sai dai mota ya dafa.
Take naji cikina ya kada min fuskan shi a daure tamau yace ke dakata kiji kada kikaga nazo na dauko ki naji wanan zancen a gida ran ki zai baci sosai wallahi duk kika bari maji taji cewa nine nazo na dauko ki sai na bata maki fiye da tsanmanin ki.
Nace baka son asani may yasa kazo ka dauke da ka barni mana har lokacin da na tashi dawow,,,
Bakina ya murde dakarfi yace ke baki da kunya ko ina magana kina magana who is the master?
Jin zafi a bakina yasa na dan zille na duka sai ya komane sai saman kirjin shi na fada.
Da sauri na kara dagowa hakan yasa muka tsaya muna facing din juna face to face.
Ya dan dade yana kallona sai ya kuta ya juya ya shiga mota yana fadin kinji warning din da nai maki wallahi duk naji zancen nan sai ranki ya baci dani wallahi.
Na shiga mota idona yai ja kaman zanyi kuka ina cewa ni wallahi wanan cin zalin ya isheni don anfika karfi sai a dinga cuta maka kawai.
May kike fadi yace sai lokacin Bashar dake muna dariya yace haba ka barta hakana mana please?
Ya tayar da mota muka ci gaba da tafiya, bai tsaya ba sai wani guri da ake sayar da kayan irin na kauye na ciye ciye.
Nan suka fita sai gasu da sayayan kayan tsaraba mai yawa irin na kauye ana lodawa a buth din motan.
Muka bar gurin nidai ban san may damay suka sayo ba a lokacin muna shiga gari a play over ya samu guri ya tsaya.
Can ya tare wani mai Napep yake cewa, ya kaini gida tare da mai kwatancen inda zai kaini, yabiya shi kudin shi nan mutumin ya loda kayana a cikin motan shi.
Su mama suna zaune sai ganina kawai sukayi a bazata kawai nan suka shiga cewa la Bintu ashe kina hanya ?
Yaran da suka shigo min da kaya na diban masu rake gyada dafafa na basu suna ta jin dadi suka fita.
Naje gurin mama na rusunna na gaida ita cikin jin dadi da gani tace Fatima shike nan kinje kin samu guri kin share ai har ina batun binki ne da banga kin dawo satin nan ba.
Nai murmushi nace mama ai zan dawo tunda an koma makaranta, tace yayasu wajen mamaki suna lafiya ko nace duk lafiya kalau mama suna gaida ku.
Ta kalli tsaraban da nazo dashi tace Fatima wanga tsaraba haka mai yawa fa dariya kawai nayi a raina nace aikin mahaukaci ne.
Nan muka shiga hira dasu anty suna min sheri wai naje naga mama na kasa dawowa.
Sadauki bai shigo ba sai da yamma lokacin ina cikin daki maryam ke fada mai Bintu fa ta dawo yaya.
Yace taga daman dawowa ke nan ta samu kauye ta zauna kaman wani birni can.
Tasa min kira na fito sai ganin shi nayi a zaune nace yaya ina wuni ?
Ya amsa a kasalance da lafiya?
Kinga daman dawowa ke nan ko ?
Murmushi kawai nayi mashi na karasa gurin maryam nace gani anty tace dama yaya na kiraki ku gaisa ta fadi tana dariya.
Na juya kawai na koma ciki, ina gyara kayana ban fito ba sai bayan magariba don nasan lokacin bai nan.
Ina cin abinci kawai sai gashi ya fado falon saudaya na daga kai na kalle shi ban kara ba.
Maryam ce take ce mai yaya adebo ma tsaran Bintu na kauye yace kai maryam kayan kauye ai sai yan kauye.
Daga inda nake zaune nace, muko dashi mukafi wayau kayan kauyen don yafi bada lafiya ai.
Yace ke yanzu lafiya kike ke nan a haka kamar a karya ki?
Kafin nai magana maryam tace a,a yaya aiko yanzu Bintu ta yi kiba in kuma tafi haka ai bata kyau.
Ni wallahi duk da mace ce amma nafi son mace haka silynder da ita sharp din mutum duk dress din da yayi sai yai ma mutum kyau.
Ga Bintu kuma dagowa ce ga wanan uban farin nata kamar yar larabawa da ita.
Kai maryam don Allah ya isa haka kada kisa kan Bintu ya fashe wanan dadin haka inji Amirah?
Maryam tace wallahi anty da har haushi nake ji idan mun fita da Bintu yadda matane ke yabata amma yanzu nima nasan gaskiya suke fadi.
Watarana fa muna alwala a makaranta wata na ganin gashin Bintu ta yanka salati wai ikon Allah yanzun ke kina da wanan gashin haka kike faman boyon shi ga hijjab kullun ?
Sai lokacin yaya yai magana yace, shiyasa ta bude ai don su gani su yi magana.
Nace kai haba yaya haka kawai zan bude kaina wa nake son ya gani kuma?
Ke kika sani dai tunda an gani an yaba din ai yadda kike son agani din.
Shiru nayi wani takaici ya kumay ni a raina nace ni wallahi wanan ai zargine kawai?
Yace nakara jin kin bude wani part dinki a jikin ki sai na bata maki rai gidan nan.
Dan Allah yaya ji yadda maryam ma take wani zuzuta fatima wallahi sai kace wata sarauniyar kyau can.
Su dai suka sani shedanun yara ne wallahi kin gan su nan shiya sa duk suka fita sai maza sun biyo su don suke kiran su.
Wanan sheri da may yai kama saboda Allah haba dai yaya kana biyewa Anty Amirah tana zuga ka kawai yaya.
Ni dai wani haushi da takaici bai bari na ko iya dago kaina ba a lokacin don irin takaicin da nakeji.
Amirah tace maza kan na zuwa har ana masu yanga da kuri kafin a dauki wayan su tafadi cikin dariya.
Kai haba anty ai wanan sheri ne kawai kike kulla muna gar wasu maza muke kulawa mu don Allah,
Baiyi magana sai shirun da yayi can ya dan bude abincin da aka aje mai agaban shi ya fara ci nikan na mike na shige dakin mu.
Amirah tace kibar gudu ai don kada a ci gaba da zancen zaki shige ko?
Shima bai bi ta kaina ba yaci abincin shi ya tafi abin shi kawai.
Ban san yaya akayi Bashar ya fadawa Anty maryam su suka daukoni daga kauye ba ranan da na dawo.
Amirah na falo ta dunkule saman kujera tana chatting maryam na zaune tana gyaran farcen ta.
Maji na zaune tana gyaran wayan ta da ke hannun ta ruwa ya dan zubo mashi da take sha.
Nafito da plate a hannu na da abinci zanci na zauna na fara ci ban dade ba sai ji nayi maryam tace.
A humm wai ashe ke Bintu yaya sadauki ne yaje har kauye ya dauko ki da zaki dawo?
Da sauri na dago kaina kalle ta cikin mamaki sai banyi magana ba don ina mamakin ina taji wanan zancen ita.
Amirah tace ke kan Maryam wallahi uwar sheri ne wata Bintu ne can yaya zai je har kauye daukowa?
Maryam tace au kina nufin karya nakeyi ke nan ko,ai ga Bintu nan shi in ba shi yaje tun daga nan ya daukota ba wallahi.
Kin ma raina yaya Allah shine zai tafi har kauyen nan mai uban nisa akan Bintu.
Don in nunawa Anty Amira na kai nace to anty maryam don ya dauko ni wani abune halan ni nace yazo ?
Ni da ban ko shirya dawowa ba amma yasa ni tasowa ba shiri saboda zuwan shi.
Bintu da gaske yaya ya dauko ki wai ko may?
Nace su sukaje sukazo dani ban ko shirya ba amma ya matsa min wallahi saida mama tace na shirya su zo dani.
O lalai ma yayana shine yai pretending kamar ma bai san komai ba a ranan da ta dawo.
Bake ne ba idan ana magana akan yaya da Bintu sai ki wani kakarw ki hana a fadi ni dai ban kara magana ba ina mamakin yadda maryam taji zancen ga kunya mama duk ya kamani lokaci guda.
Nace dama,na,sani kawai tun ranan in fada mata tare dasu nadawo da yafi min yanzu gashi anji ko.
Amirah bata bar zancen ba sai da ya shigo gida har kowa ya manta ashe ita abin yana ranta.
Yashigo cikin yar fara,an shi bayan ya zube saman kujera yake, cewa maji yau naga wanan kawar taki da tun muna tsohon gida kuke tare.
Maji ta dago kai tace wata kawana kuma ke nan yace ko yar Rabin isha ake ce mata ba ?
Au kace uwar goyon ka dai ai itace tai giyon ka lokacin tana amarya a unguwar na mu da anyi maka wanka sai gidan ta.
A ina kagan ta yace can wani unguwa naje duba wani tsohon gida da akai min talla tun kwanaki ban samu zuwa ba sai yau din nan.
Naji ance wai ba sadauki maji bane nan yace wallahi ban gane taba maji ta tsufa duk ta lalace sosai dagani tana cikin wahala.
Tace Allah sarki, tun lokacin da mijin ta ya dauke ta suka koma kauye ban kara jin duriyan taba.
Yace lalai na gan ta yau kan maji tace inji ka samu abinda ka bata ?
Yace dubu goma kawai na samu na bata banda kudi ga aljihuna a lokacin amma nai mata kwatancen gidan nan ai tace zata zo.
Yauwa yayana wai ashe kai ka dauko Bintu daga kauyen su ranan da ta dawo ?
Da sauri ya daure fuskan shi kaman bashi ke fara,a ba yan dakikoki kadan da suka wuce.
Yaba ta amsa da eh mu muka dauko ta wani abin ne akayi kuma ?
Inda nake ya kalla fuska a daure nima na daure nawa tare da dukar da kaina kasa.
Amirah tace da nace karyanr wallahi da maryam ke fadi dazun ban yarda ba wallahi.
Yace naga bata da niyan dawowa school ne gashi ankoma shiyada naje nazo da ita ai.
Daga haka yai shiru maji najin su batace kallaba ko wanan lokacin ban da cewa da tayi Allah yasa yar Rabi dai tazo gidan nan wallahi na dade ina tuna ta sosai wallahi.
Mikewa yayi yana cewa zan shiga daki maji duk nagaji yau wallahi zan dan huta.
Yana fita na sauke ajiyan zuciya a hankali don nasan nawa ya samay ni kuma tunda yai min gargadi kada na fadi.
Ban taba sanin yaya yana da nombana ba sai yau ina daki ina shirin sallah naji wayana na ruri.
Ina dauka naji yace ke ashe baki da hankali gulman ki hae yakai can ban sani ba dana ce kada ki fadi sai da gulman ki yakai kika fadawa maryam abinda na hana ki.
Na marairaice nace wallahi Allah yaya bani na fada mata ba ban san inda tajiba wallahi ko.
Sai naji ya kashe wayan dip nabi wayan da kallon mamaki tare da sauke ajiyan zuciya.
Kwanana biyu da dawowa ya sa kai ya tafi zuwa kashen waje gurin wasan su don can yafi dawowa a jike idan ya tafi.
Tafiyan shi, na dawo normal kullun ina cikin yan uwana muna mu,amulan mu yadda muka saba dasu.
Bamu da matsalan komai a gidan yanzu don gaskiya Alhamdullahi, mota kowan su na dashi, haka ma sutura duk muna dasu matsu tsada, waya kowacen mu babba take riko a hannun ta duk shi ta saya muna, gurin abinci sai wanda ran mu yake so zamuci, ga uwa uba makka da muka tafi kowan mu da hakoran makka a bakinta irin na adon mata yana walkiya.
Matsala guda yanzu shine matsalan gidan su maji na fitina a tsakani kullun ga Nafisa yanzun abinta yai kamari sosai gwanin ban tausayi da ita.
Idan iskancin ta ya ishi Baba haka zaifito tsakar gida yai masu tas ita xa uwarta, sai in Umma ta gajine takan tanka itama tace.
Ba kan diyana aka fara lalacewa ba ai a gidan kan suyi ai wasu sunyi kuma nasan hannu aka samin suka lalace.
Don haka koma waye na sani kada maishi yaga kamar yaci bulus wallahi indai nice bashi akaci wallahi.
Don sheri saboda mutum yaga nashi ya lalace sai ya mayar da dan kowa lalatace a gida.
Badai na su kawai duniya zata fada ba sai an fadi na mutum tukun.
Mummy tafito daga dakin ta tace kai amma dai hjy Atika tauhidi bai sheki ba wallahi.
Ashe shi wanda kike nufi hannu aka saka mashi ke nan a lokacin yazama haka bamu sani ba ko sai yanzu da yakawo akanki ne kika

Please Login or Register in order to submit comment