Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har ta zauna kusa da ita bata san ta zauna ba, tana taɓa ta ta zabura.


“Wayyo Allah na”


“Ke lafiyan ki?”


“Wallahi wani littafi ne nake karantawa mai shegen dariya”


“Littafi kuma ai ke Allah be raba ki da karatun littafai ba”


“Wallahi Anty Namra yayi daɗi kamar me, da zaki karanta kema da kin sha dariya”


“Idan na samu time zan karanta, meye sunan littafin?”


“Noor na Khadeeja Candy”


“Okay ni dai ara min wayarki wani abu”


“Ke dai ce zaki kira Asim ba wai kiyi wani abu ba”


“Naji ni dai bani”


Sai da tayi saving ɗin page ɗin, sannan ta miƙa mata wayar tana zolayarta. Namra dai bata ce mata komai ba ta tashi ta fice tana faɗin.


“Ina fatar da Akwai kuɗi a ciki”


“Kai kaji ki da wata magana, manyan Babe's irin zasu zauna waya ba kati, taf mune tare da manyan samarin garin nan fa, kin san ko dan karya dole a saka mana manyan kati ”


Da dariya Namra ta fice, ta koma ɗakinta. Takardar ta ɗauko ta saka Number ta danna kira. Ringing biyu zuwa uku yayi picking da sallama.
Sai da ta lumshe ido ta buɗe da murmushi sannan ta amsa masa.


“Wa'alaikassalam. Asim”


“Namra...”


Daga cikin wayar tana jin lokacin daya sauke ajiyar zuciya, sannan yace


“Namra wai Abban ki ya yarda na aure ki?”


Kai ta ɗaga masa kamar yana gabanta, hawaye suka silalo mata.


“Ya yarda Asim, shiyasa na neme ka”


“Alhamdulillah”


“Ina kaje Asim? Ashe zaka iya tafiya wani guri ka bar ni?”


“Namra idan mun haɗu zamu yi magana”


“Yaushe zaka zo?”


“Ba zan iya zuwa gidan ku da sunan hira ba, sai dai mu haɗa ta layin su Azeema”


“Okay gobe da ƙarfe tara dan Allah”


“Allah ya kai mu I Love You”


“I Love You More”


Daga haka ya kashe wayar. Sai ta rumgume phone ɗin tana murmushi tare da hawaye.


KALSOOM POV.


Kusan kullum sai Doc. Hilal ya kirata a waya sun gaisa, sai dai fira ce be cika zuwa ba sai jefi-jefi. Sau biyu ya taɓa kawo mata ƴaƴansa suka gaisheta ita kuma tayi musu goma na arziki.
Ana sauran sati biyu biki Doc. Hilal ya nemi ta bashi list ɗin abubuwan da zata yi na biki. Bata rubuta wasu abubuwa masu yawa ba, bayan abubuwan da al'ada ta tana da.


Batayi wata hidima ba duk da kasancewar ƙannenta sun so tayi, amman bata biye musu ba, wai ita ta girmi wannan yanzu.
Kala kusan arba'in da huɗu yayi mata, duk masu kyau da ɗaukar hankali, kowa ya gani sai ya yaba, wasu na faɗin haƙurin da tayi yanzu zata ci riba.


Ranar laraba aka saka amarya lalle a daren ranar akayi wankin amarya, washegari alhamis akayi ƙunshi da kitso, friday akayi walima, Assabar aka ɗaura aure Kalsoom da Doc Hilal.
Daddy yayi mata nasiha mai ratsa jiki, gwaggwanin suka mata jan kunne akan rayuwar gidan aure kamin Momy ta ɗora da nata. Kuka sosai Kalsoom tayi a lokacin da aka fito da ita za a saka ta mota zuwa gidan mijinta. Duk wanda ya gani zai yi zaton bata son auren ne.


Da ƙafar dama ta shiga gidan aurenta tana ƙorar shedan kamar yadda Momy ta faɗa mata. Sai da aka zaunar da ita a saman gadon aurenta sannan ta tsagaita kukan.
Batayi zaman minti ashirin ba abokan ango suka shigo tare da ango, sai zolayarsa suke, anyi siyen baki da wasu abubuwa da al'ada ta tanada sannan suka yi musu addu'ar zama lafiya.
Har gurin ƙofa Hilal ya raka abokansa, yayi ma ƴan'uwan amarya da wasu daga abokanta sallama sannan ya rufe ƙofar.


A maimakon ya koma ɗakin Kalsoom, sai ya nufi ɗakin Rashida dan duba halin da take ciki.
Zaune ya tararda ita ƙasan carpet tana wani irin kuka kamar ranta ze cire, wata cousin ɗinta na kusa da ita tana bata haƙuri.


“Habiba ɗan bamu waje”


Ya ƙarasa faɗar yayinda yake zaunawa kusa da ita, janta yayi izuwa ƙirjinsa ya rumgume ta sosai.


“Shiiiiiiiii. Wannan hawayen ban ga dalilin zubar da su ba Ammyn Rafiq, kin san ba ɗan bana son ki bane yasa nayi aure sai dan sauwaƙe miki wasu abubuwan, a maimakon kiyi farin ciki sai kuma kiyi kuka?”


“Ina son Hilal ina kishin naga wata a tare da kai, zan iya mutuwa Hilal”


Ta faɗa tana ƙara narke masa a jiki. Saman kanta ya shafa ya sumbanci shi sannan yace


“Allah ya sassauta miki wannan kishin Pyar, I Love You so much amman ina son ki so abunda nake so”


Kuka tayi sosai har sai da maƙoshinta ya bushe sannan ta sassautama kanta, har kuma lokacin Hilal na rumgume da ita yana rarrashinta.


“Pyar”


Ta ɗago kai ta kalleshi da kumburarin idanuwanta.


“Karki sa damuwa a ranki kin ji? Mijinki yana son ki matuƙa, kuma baya da niyar cutar da ke”


Ta ɗaga daga jikinsa.


“Tashi kaje kar na shiga mata haƙƙi”


“Zanje amman sai kin yi min alƙawarin zakiyi bachi!”


“Zan yi”


Babbar rigarsa ya cire, da ita ya gyara mata fuskarta, ya goge majinar data ɓata mata gaban riga sannan ya kai bakinsa cikin nata yana kiss.


Ya ɗauki lokaci mai tsawo yana kiss ɗinta da shafa wani ɓangare na jikinta, har sai da ya tabbatar ya kashe mata jiki, sannan ya ɗaga ya kalleta.


“Good night Pyar”


“Good night”


Sai ya sumbaci goshinta.


“Dream me i love you”


Ɗan murmushi ta sakar masa kaɗan. Sannan ta sake shi ya tashi, ya baro mata ɗakin zuciyarsa cike da zumuɗin zuwa gurin Amaryarshi.


Da sallama ya shiga ɗakin yana murmushi, sai ya zauna kusa da ita ya kai hannu ya yaye lulluɓin dake kanta.


“Wannan Amaryan bakinta da tsada yake, har ta kasa amsa sallamar angonta”


Hawayen daya gani a fuskarta ya tada hankalinsa. Dan be yi zaton macen data kai kamar Kalsoom idan anyi mata aure a zamanin nan zatayi kuka ba.


“Wannan hawayen na minene My Queen? Ashe yau ba ranar farincikin mu bace? Ai kamata yayi mu gode Allah ko?”


Ita kanta bata san hawayen minene take ba, na farincikin yau Allah ya gwada mata aurenta, ko kuma na yanayin da take ciki na baƙincikin rabuwa da iyayenta.
Matsawa yayi daf da ita sai ya kai tattausan hannunsa ya share mata hawayen, ya kwantar da ita jikinasa, yasa babban yatsansa da mai bi mata yana mata saƙa a jiki.


“Ranar yau ba ranar kuka bace ranar murna ne, ranace da zaki gode Allah kuma ki shirya karɓar angonki da kyakkyawar tarba”


Notse kanta tayi cikin ƙirjinsa, jikinta na amsa saƙon da ƴan yatsunsa suke kai mata. Tana jin wasan ya canja salo sai ta zame jikinta, idonta cike da nauyin kallonsa.


Murmushi yayi yana wani lumshe ido yana buɗe, sannan ya janyo ledar dake gefensu ya buɗe ya ɓalle lemun dake cikin kwali ya ɗauko cup ya zuba mata. Duk yadda taso ta ci da kanta ƙin yarda yayi a dole ta haƙura yayi feeding ɗinta, ba dan tana jindaɗin yadda yake bata ba, abun ka da wanda be saba ba.


Bayan sun gama, ya riƙa hannun tana mursa lallen dake hannu tare da yaba.


“Amman wanda tayi miki lallen nan ta iya lalle gaskiya, yayi kyau sosai”


Yadda yake taɓa hannun nata yasa tsigar jikinta tashi. Duka hannayensa yasa yana luddar hannun nata, a ɗan space ɗin dake tsakanin fingers ɗinta yasa one finger ɗinsa yana mata tafiyar tsusa, sai kallon yanayinta yake, gaba ɗaya idonsa sun koma kamar ba nashi ba.


Janye hannunta tayi ta miƙe tsaye.


“Bari mu tashi mu yi sallah”


Murmushi yayi ya dantsi bakinsa, sannan ya tashi ya nufi bathroom ɗin.
Tun da sunayi sallah godiya be yarda ya kai hannunshi ya sake taɓa jikinta ba, in banda kayan bachi daya ciro a closet ya miƙa mata sai shima ya saka nasa. Sannan ya hau saman gadon ya kwanta ya bata baya, be juyo ba sai asuba.


Bayan sun yi Sallah, ta hau gado ta kwanta, shi kuma ya fita dan duba uwargidansa.
A kitchen yaji motsinta, hakan ba ƙaramin bashi mamaki yayi ba, da sauri ya nufi kitchen ɗin ba dan zuciyarsa ta yarda da ita ɗince a kitchen ba.


“Wow Pyar me kike yi?”


Ta juyo ta kalleshi da murmushi, fuskarta acan-acan da kwalliya kamar ita ce amaryar.


“Breakfast nake haɗa muku”


Ya zagaye ƙugunta da hannayensa, zuciyarta cike da jindaɗi.


“Seriously Pyar? Amman gaskiya kin kyau mana, so faɗa min jiya kin yi bachi?”


“Nayi bachi mana, ai nasawa rai na zan iya ne”


“Good girl”


Yaja hancinta, wanda hakan yasa ta dariya.


“Amman ni dai Doc Ina jin tsoro, kar yarinyar nan ta amshe min kai, wasu ba aure Allah suke ba burinsu kawai su fitar da matar gida su maye gidan da ƴaƴanta”


“No no no, wannan yarinyar ba irinta na auro miki ba, tana da tarbiya fiye da tunanin ki”


“Allah yasa”


“Amin”


Sai ta ɗago kai ta miƙa masa bakinta sukayi kiss, sannan ya rumgume ta a kafaɗa kamar wani ƙaramin yaro.
Har ta gama soya dankalin rumgune yake da ita ta baya, sai da ta fara jera kayan abincin sannan ya sake ta da nufin zuwa ya tashi Kalsoom.


Har lokacin bachi take hankalinta kwance. Da murmushi ya ƙarasa kusa da ita, zanen bachinta ya fara yayewa, yasa hannunshi ta ƙasan wandon bachinta ya soma shafa ƙafarta zuwa cinya.


Wani yarrr taji, sai tayi saurin buɗe ido ta tashi tana kallonsa. Murmushi yayi ya hau saman gadon ya ɗora kansa saman wuyanta.


“Good morning Queen ina fatar kin tashi lafiya?”


Kamin ta amsa ya zira halshensa yana lasar wuyanta, ya kai hannunshi saman ƙirjinta, ya soma murza breast ɗinta a hankali, lumshe ido tayi zuciyarta cike da ƙyamar abunda yake mata. Tana jin ya fara ƙoƙarin ɓalle bottom ɗin rigar bachinta tayi saurin riƙe hannunsa, ta buɗe ido ta tashi.


Sai shima ya miƙe tsaye yana murmushi.


“Je kiyi brush zamu ci abinci”


Bata tace komai sai kawai tayi murmushi, ta nufi bathroom, shi kuma ya fice ya nufi nashi ɗakin dan wanke bakinsa.


Bayan ta fito ta ɗauki mayafinta na jiya ta rufa a jikinta sannan ta nufi falon. A lokacin Hilal har ya hallara a dinning yana riƙe da hannun uwar gidansa.
Yadda taji abu ya soki zuciyarta sai taji kamar karta ƙarasa kusa da dinning ɗin, sai dai tayi ƙarfin halin ƙirƙirar murmushi ta ƙarasa tana gaisawa da Rashida.


Rashida da kanta ta zuba ma Hilal abinci sannan ta zuba ma Kalsoom, sai ta zuba ma kanta.


“Ina Ezzah?”


Ƙalsoom ta tambaya. Sai Rashida tayi murmushi tace


“Suna bachi around tara da rabi zasu je islamiya, idan na tashe su yanzu zasu dame mu ne kawai”


Ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin zaunawa, zamanta keda wuya sai hawaye ya gangaro ta idonta ya wanke mata fuska, da sauri ta tashi.


“Am sorry”


Sai ta nufi ɗakinta. Sai Hilal yayi saurin tashi ya rufa mata baya. A take yanayin Kalsoon ya canja har ta haɗiye wasu yawu da ƙarfi, ta sauke ajiyar zuciya tana kallon yadda abincin ya fita ranta.


NAMRA POV.


Tara saura mintuna Namra ta saci jiki, ta nufi gidansu Azeema. Sai da ta kusa ƙarasa sannan wani tunanin yazo mata.
Sai ta yanke tafiyar ta dawo gida, a lokacin an buɗewa Abban gate zai fita, taji kunyar ganinsa sosai sai dai sa'arta ɗaya dawowa ne tayi ba fita ba da fita ne da me zata ce masa?


Lokacin data kawo kusa da shi ya zuƙe gilashin motarsa yana mata wani kallo.


“Daga Ina mike?”


Ta ɗanyi jikiri gurin bashi amsa saboda tunanin ƙaryar da zata masa.


“Az- Azeema ce bata da lafiya shine yaje na dubata”


“Da izinin wa?”


“Anty”


“To kar na sake ganin kin fita ke kaɗai”


Be jira amsar ba ta ya ɗagarda gilashin motarsa, direba ya jashi yayi suka yi gaba.
Ta hanyar kitchen ta biyo ta shigo falo, sai rabon ido take idan wani be ganta ba.
Al-hamdulillah falon ba kowa hakan ya sata jindaɗi, cikin natsuwa ta nufi ɗakin Anty Amarya.


“Wa'alaikissalam”


Ta amsa sallamar Namra a yayinda ta aje kofin tea dake hannunta saman bedside drawer.
Kusa da ita Namra ta zauna tana tauna maganar da zata mata.


“Anty kin ga jiya ai Maryam ta bani wasiƙa ko?”


“Uhm”


“Asim ne ya bar min ita wai yazo be same ni ba, shine ya rubuta min number wayarsa, sai na kira da wayar Maryam, yace min mu haɗu a gefen gidansu Azeema”


Anty Amarya ta girgiza mata kai


“A'a ke yanzu girman ki ne a ganki a ƙofar gidan wa su kina fira? Yazo gidan ku mana, sai kace wani baƙo”


“Wai shi yana jin ba daɗi idan yazo nan gidan”


“Cinye shi zamuyi? Ai ko yanka namansa ake dole ne yazo nan indai yana son ki”


Shiru Namra tayi tana nazari. Anty Amarya ta mire baki.


“Uhm- Allah dai yasa kina son Asim ɗin nan yana son ki kamar yadda kike son sa”


Murmushi kawai Namra tayi, ta kai hannu ta ɗauki wayar Anty Amarya dake gefenta.


“Bari na kira shi”


Sai ta tashi ta fita. Ɗakinta ta dawo ta sake ɗauko takardar ta saka number ta kira. Ringing tayi har ta katse be ɗauka ba, sai da ta ƙara kiransa sannan yayi picking.
Tana yin sallama ya gane ta.


“Namra gani a gurin ban gan ki ba”


“Ina gida Anty tace ba sai dai kazo gida”


“Namra ina jin tsoro, bana son zuwa gidan nan naku kallon wulaƙanci ake min”


“Kazo mana babu koma ma, Hajiya tana part ɗinta, Maryam da Hindatu sun tafi makaranta, Abbah ma ya fita”


“To gani nan zuwa”


“Gidan ka shigo kaje gurin Garden”


Daga haka ta kashe wayar, ta mayarwa Anty Amarya.

“Anty ga wayarki na gode”


“Ke kin hallaka taki wayar ko?”


Murmushi tayi, ta juya ta fice. Firjin ta buɗe ta ɗauki lemu da kofuna, sannan ta nufi garden zuciyarta cike da zumuɗin son ganin masoyinta.


A-ƙalla ya ɗauki mintuna goma shabiyar, sannan ya iso, da faɗuwar gaba ya buga ƙofar gate ɗin. Sai mai gaɗinsu ya buɗe masa yana tambayar wanene.


“Nine ko Namra na ciki?”


“Eh tana ciki”


Mai gadin ya buɗe masa ƙofa, yana mamakin ganinsa.
Gidan ba baƙonsa bane, dan haka be sha wahala ba gurin ɗaukar hanyar da zata sadashi da garden ɗin. Namra na hango shi ta miƙe tsaye ta rumgume tana murmushi, ta hannayenta, idonta ya cika da ƙwallah.
Shima murmushin yayi yana kallon yadda ta rame tayi baƙi kamar ba ita ba.


“Namra ashe zan ƙara ganin ki?”


Bata bashi amsa ba sai kawai ta nuna masa kujerar dake facing ɗin nata. Bayan ya zauna sai ta zauna tana share hawayenta.


“Asim ina ka tafi?”


“Katsina naje gurin wani Ƙanen Mahaifina ina riƙa masa aikin jima da yake yi”


“Haba Asim shi kenan sai ka gudu ka bar ni kana ganin kamin adalci kenan?”


“Namra idan kika aure wani ba niba, mutane zasu min dariya, ban san da wane ido zan ɗaga kai na kalli mutane ba”


“Matuƙar kace zaka biye ma dariyar mutane ba zaka iya aikata komai ba Asim. Nima dana biye dariyar mutane da ban yarda na aure ka ba, yanzu ka watsar da karatun ka, abunda nake da yaƙinin shine zai taimaki rayuwarka”


“Ba karatu ne a gaba ba yanzu, faɗa min da gaske mahaifinki ya yarda muyi aure?”


“Ya yarda shiyasa yace na nemo ka, kuma ina jin ba zai sa mana date da nisa ba”


“Al-hamdulillah Allah mun gode maka, amman Namra kina ganin zaki iya zama da ni?”


“Ba zan iya zama da kai ba na amince zan aure ka? Ya kake wannan maganar kamar ba Namra ce a gaban ka ba?”


“Ina ganin kamar yanayi na da naki ba ɗaya bane”


“Ba mu da banbanci ai duk mutane ne. Asim Amira ta ɓata”


“Haka naji kuma ni ake zargi da sace ta ko? Kamar yadda aka zarge ni da sace ki”


Ta share hawayenta.


“Waya faɗa maka?”


“Ai abun duniya baya ɓoyuwa Namra, kuma kin san akwai munafukai da yawa a duniyar nan. Shiyasa na yanke shawarar barin garin gaba ɗaya, ko da mun yi aure a Katsina zamu zauna tun da ban da gurin aje ki a nan, amman can family house ne akwai ɗakuna da yawa, sai dai na ƙasa ne”


“Amman Asim kana ganin zaman mu a can zai yiyu? Karatun ka fa?”


“Na riga na yafe karatu Namra. Kuma zaman mua can zai fi, saboda har ga Allah nan bana da gurin aje ki, kuma kin ga nan idan mun ci za'a gani, idan ba mu ci ba ma za'a gani, kuma abu kaɗan za a zo gidan ku a faɗa, can kuma babu wanda ya san ki, kuma kin ga ɗan zuwan nan da nayi, ina kama masa aikin jima nima ina samun nawa, kin ga ko dashi zamu iya cin abinci kamin Allah yayi mana wata hanyar”


“Amman Asim shi yace zai baka gida a can? Ni dai zan fi jindaɗi mu zauna nan”


A take ya canja fuska.


“Ko be yarda ba ni zan roƙe shi ya bamu gurin zama, kuma ni a tunani na Namra ko a ciki wuta nace ki zauna zaki iya zama in har kina so na”


“Ina son ka Asim, kuma zan zauna a duk inda ka aje ni, yanzu kaje ka samu magabatan ka suzo su ga Abba”


Murmushi yayi ya sauke ajiyar zuciya.


“Zan yi haka Inshallahu, na gode sosai”


Ba suyi wata doguwar hira ba suka yi sallama, ko lemun da ta kawo masa be sha ba.
Cikin rashin jindaɗi ta nufi shiga falo, har ta nufi kitchen ta aje lemu na ɗauke da kalaman da Asim yayi mata. Idan tace ba zata iya zama a can ba zai zargeta, sai dai har ga Allah bata jin zamanta acan ɗin zai fi.
Bata yarda ta labarta ma Anty Amarya komai ba, sai kawai ta shige ɗakinta tana shawarta zucuciyarta, da nema musu mafita.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa17.html




🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺

Wattpad @
KHADEEJA CANDY


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


Wannan shafin sadaukarwa ce ga SANAH S MATAZU. Namra da Kalsoom sun ce a gaishe ki😘


NOT EDITED ⚠️


*PAGE - 17*


KALSOOM POV.


Sun ɗauki dogon lokaci kamin su fito. Ko da suka fito har Kalsoom tayi nisa da cin abincinta.


“Sorry mun bar ki kina cin abinci ke kaɗai”


Rashida ta faɗa tana ƙoƙarin zama. Kallonta kawai Kalsoom tayi ta cigaba da cin abincinta. Hilal ya lura da yadda yanayin Kalsoom ya canja hakan yasa ya zauna a kujerar dake daf da ita ya ɗauki abincin ya mai da agurin.


Sosai da sosai hakan ya sosa ran Rashida, for the first time in history jikin mijinta yana gugar jikin wata mace. Wasa da riƙayi da abinci ta kasa ci. Hilal ya lura da yanayinta amman be kulata ba har ya gama cin abinci tare da Rashida. Tashi Rashida tayi zata kwashe kwanukan sai ya riƙe mata hannu.


“Bar su kawai je ki shirya kan ki zan kwashe kayan, nima na iya aikin ai, amman kamin nan zauna zamu yi wata magana”


Ba musu ta koma ta zauna. Sai da yaja dogon numfashi sannan yace


“Rashida Kalsoom ina son ku bani aron hankalinku, Ban auri Kalsoom ba dan na wulaƙanta Rashida, kuma ban auri Kalsoom ba dan bana son Rashida ba, yanzu nauyin ku duk ya hau kai na, dan haka ina fatar zaku taya ni sauke nauyin da Allah ya ɗora min, ba wai ku tada min hankaliba, zan fu kowa jindaɗi idan kuka haɗa kanku.


Zan iya zama abun kwatance idan kuka kwantar min da hankali, ba zan iya gane wace tafi so na ba sai ta sai ta hanyar kwantar min da hankali da kuma kyautatawa. Bana son wani rashin jituwa ya shiga tsakanin ku, kuma ban da ɗauka anyi ance duk wanda take ganin ba ayi mata dai-dai ba zata iya magana”


Kalsoom ce ta fara magana bayan ya kai aya.


“Inshallah zaka same me mai biyayyah, ni ɗai indai gefe na inshallah ba za a taɓa samun matsala ba, kuma ina fatar wasu abubuwan da zanyi a cikin rashin sani Ammyn Rafiq zata tunatar da ni”


“Inshallah ina fatar nima zaki tunatar da ni Allah ya bamu haƙuri zama da juna, sai dai sai kin yi haƙuri dasu Ezzah saboda basa jin magana”


Rashida ta faɗa tana mai jin sassauti a zuciyarta.


“Ba komai Ai yara na kowa ne, yaran ki ai nawa ne”


Hilal ya jidaɗin yadda yaga sun ɗan sake da juna, yasan nan gaba komai ze wuce kishi ne kawai wanda ba a rasa ba.


Bayan sun ɗan yi fira ta tashi ta nufi ɗakinta, Rashida kuma ta nufi ɗakin yaranta, dan ta tashesu.
Shigar da tayi a ɗakin ya bata damar kallon irin dukiyar da mahaifinta ya zuba mata, ta jidaɗi matuƙa sai da ta ƙare ma ɗakin kallo sannan ta ɗaga hannu sama tayi ma Allah godiya. Sannan ta nufi bathroom ɗinta tayi wanka, cikin koriyar atamfa ta shirya ta tsaɓa ado. Sannan ta ɗauki wayarta ta kira Momy da Daddy ta gaishe su.


Guraren biyu da rabi Salma tazo gidan, aiko Kalsoom kamar ta haɗeye ta, sai duk taji kamar ta daɗe bata ganta ba.
Ɗakinta ta kaita ta kawo mata abinci da abun sha. Sai da Salma ta ci ta ƙoshi sannan ta kalli Kalsoom tana dariya tace.


“Komai mai lokaci, yau dai gashi na ci abincin gidan Kalsoom”


Kalsoom tayi dariya. Salma tace


“Ya dai zaman ku babu wani matsala dai ko?”


“Eh toh babu matsala zuwa yanzu, ban sani ba dai ko gaba. Amman a yadda na lura kamar yana son matarsa da yawa”


Salma ta saki baki.


“Kalsoom kenan ke kin fi son ki auri mijin da zai riƙa wulaƙanta uwargidansa? Irin wannan mijin ai ba mijin aure bane, idan ya gama da ita akan ki zai yo.
Kuma Hilal ai dole ya so matarsa tun da matarsa ta gina masa sonta a zuciyarsa, kema ki gina naki mana, yana son matarsa cikin bata bashi lokacinta bata kula da gidanta a yadda ya dace, me kike tunani idan ke kika masa duk abunda yake so?


Aure ba abun wasa bane Kalsoom sai kin kai zuciyarki nesa, babu ruwanki da sashenta indai ba har ta kama bane, wani abu da gangan zata yi dan ki gani amman ki riƙa kauda idonki dan samawa kanki masalaha.
Ban da nuna masa ke maki son matarsa, wallahi komai take miki karki nuna masa baki son matarsa balle kuma ƴaƴansa, sai dai idan tayi miki wani abun na laifi ki nuna ɓace ranki ki yi magana dan ƙwatar yancin ki. Karki kuskura zagin matarsa gaban idonsa, kina ida kina haka ko da ita ta nuna masa bata son ki ita zai riƙe da abun a zuciya ba ke ba


Kuma ki kama ƴaƴansa ki riƙe kamar naki, babu ruwanki da ƴan anyi ance, ban da ɗaukar zancen maƙota, ban da biye son zuciya, duk wani kishi da zaki ji ki danneshi ki sawa ran ki sassauci, ban da faɗin sirrin miji, musamman na al'amarin auratayya. A duk lokacin daya buƙace ke ki nuna masa kin fisa buƙatarsa, ki sake jikinki ki yiwa mijinki duk abunda yake so. Ke ai baki da matsala da wannan matar tun da bata da lokacin kanta ma, yara kuma kullum suna islamiya da boko kin ga ai gidan ma kusan naki ne ke ɗaya


Ƴan uwansa ki kama ki riƙe ki maida su kamar naki, ki girmama mahaifansa, ki girmama abokansa, ki tarbi kowa da far'ah idan kina da abun basu ki basu, ki zama mai yawan alheri, gidan ki ya kasance mai ƙamshi da tsafta, abincin ki ko yaushe a ready.
Kin ga waɗannan abubuwan da na faɗa miki? Sune mallaka na musamman wanda mu mata basu san da ita ba, idan kina wannan wata mace ba zata iya gane kan mijinki ba, sai dai kiji ana ta mallake shi ai baya da magana sai nata”


Kalsoom tayi dariya tana mamakin yadda Salma take jero mata waɗannan bayanan kamar wata tsohuwar mace.


“Salma.yaushe kika ɗauki wannan karatun?”


“To ai ke sabuwace mu kuwa mun tsufa a lamarin, ke bari na baki wani sirrin, idan zaki bawa mijinki abinci ki laɓe a inda ba zai ganki ba ki riƙa karanta masa Bismillah kafa shirin da tara ko sha tara, ki tofa masa a ruwa ko wani abu kamar alawa haka ko dabino, a lemu ma zaki iya amman idan kin ƙanƙare, sannan ki karanta masa Hal'ata alal insanu har zuwa samin'an basira, sai maimaita sami'an basira sau bakwai ki tofa masa a abinci, ki yawaita lalle idan mijinki mai son lalle ne, ko kuma ki karanta ayatul kursiyo ki tufa masa a ruwa, kuma ko yawaita cin fruits da tsarki da ruwan ɗumi, ki riƙa masa shagwaɓa dan zama suna son shagwaɓa sosai, hmmm ƙawata sauran soyayyar ki nemeta gurin Allah kawai, amman sai kin ba labari”


Taɓawa sukayi, Salma ta ɗora


“Ai shiyasa bana da shakku akan mijina, nasan ko aure yayi

Please Login or Register in order to submit comment