Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.


Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.


“Ni zan wuce”


Ya watsa mata wani kallo.


“Haka zaki fita?”


Ta ɗan kalli jikinta


“To ya zan yi?”


“Ban sani ba”


Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.


“Kuma kar ki cireta har office”


“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”


Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba


“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”


“Miyasa?”


“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”


“Okay”


Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.


“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”


“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”


Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.






__________________________________________
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

Website
www.khadeejacandy.com.ng


*PAGE - 34*


NOT EDITED ⚠️




ASIM POV.


“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”


Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.


“Mashallah har nawa aka biya ne?”


“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”


“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”


“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”


“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”


“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”


“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”


“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”


“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”


“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”


Asim ya sauke jiyar zuciya.


“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”


“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”


Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.




RASHIDA POV.


Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.


Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.


“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”


“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai an samu sperm ɗin wani”


“Amman ke yanzu dan baki da hankali sai ki bar shi yayi amfani dake? A maimakin kije can waje ki samo wani? Yanzu kin ja mana masifa Asmee”


Rashida ta ƙarasa maganar da kuka.


“Ba ni da tabbacin ina shi ɗin ko bana da, an ban yi gwaji ba, wata mata ce da take zuwa gurinsa aka ce ta kamu”


“Amman yayi ta neman ki ne har da yawa ne?”


“Kin san duk lokacin da kaje da buƙata dole ne sai sun nemi su kwanta da kai”


Kuka ta fara, yana ta dana sanin abunda ta aikata. Sai kusan azahar Rashida ta bar gidan bayan taja mata kunne akan karta kuskure da bari kowa yaji ciki har da mijinta.


Banki ta dawo zuciyarta cike da tunani kala-kala, masu sokanar tama ganinta da rigar likita, dariya kawai take musu ba dan ta kula da zancen su ba. Ta shiga office ɗinta sai zama ya gagareta, ga takardun data tarar an kawo ma tayi sigh ko kallonsu ba tayi ba. Ta juya ta fita, office ɗin Alhaji Bashir ta nufa. Bata nemi izinin shiga ba ta tura office ɗin ta shiga.


Hannunta ta miƙa masa kamar yadda ta saba yayi mata kiss, sannan ya zauna saman teburin ta ɗora sama ƙafarta ɗaya saman ciyarsa tana masa wani irin abu, kamar wata gwaggwazajiyar karuwa.


“Security Camera, dai a kashe take?”


“Ai nasa an cire min ita tuni saboda ke”


Ta ƙara matsarda ƙafarta, izuwa cikinsa.


“Bashir akwai wanda ka sani a Alex Hospital, ɓangaren Lab?”


Hannu ya kai ya naɗe wandon suit ɗin nata, ya fara shafa ƙafarta.


“Ba za a rasa wanda na sani ba, miya faru ne?”


Shiru ta ɗanyi tana tunani, idan har ta yarda ta faɗa masa, asirinta zai tono, tun da dole ne yayi ma matarsa magana, wata ƙila ma ya sake ta.


“Wallahi wata friend ɗita ce za'ayi ma gwajin kasan asibitin sun fi ƙwarewa, sama data su Hilal”


Ya ɗauko wayarsa yana wani lumshe ido


“Bari na kira Doc Sabo sashen jini yake aiki”


Ta sauka daga saman teburin ta dawo saman cinyoyinsa.


“Kar wani ya shigo fa”


“Babu wanda zai shigo sai ya nemi izini”


Sai da suka gaisa da likitan sannan ya haɗa shi da Rashida. Gaisawa kawai tayi da shi sannan ta sanar masa zata karɓi number sa, su yi magana.


Sai da ta saka number a wayarsa sannan ta sauka daga saman jikinsa, daman tayi samana hakan ne dan kar ya gano damuwarta tun da ta saba masa a duk lokacin data shigo office ɗin.
Duk da irin kibar da yake da ita bata hanashi saurin unƙurawa ba ya riƙo hannunta ganin zata wuce.


“Yau da wuri zamu tashi babu aiki da yawa”


“Eh amman zan je gida akwai abunda zan yi”


“Aiko dai yau na so mu haɗu”


“Gaskiya akwai abunda zan yi, yanzu fa haɗuwar mu zata riƙa wuya, ƙara kaje gurin matar kawai”


Bata tsaya jiran abunda zai ƙara cewa ba ta fice daga office ɗin.
Lokacin data dawo office ɗinta zaunawa tayi ta ƙare duka aikin dake gabanta, sannan ta ɗauki wayarta ta kira likitan. Bayan sun gaisa ta gabatar masa da kanta.


“Sunana Aisha bee Omar, akwai wani cousin ɗina dake fama da matsala sai yaje asibiti aka bashi gwajin jini, to ina son idan ya kawo ka min a yi masa a kira ni a sanar dani dan Allah”


“Amman miyasa Hajiya?”


“Idan ka kawo ka sanar min zan faɗa maka ko minene, ka turo min account number ɗin ka”


“A wannan Asibitin bama yin abunda ya tsaɓa doka, hakan kan iya ja mana ɓacin suna a asibitin nan”


“Ba taka doka zaka yi ba, ceton rai ne idan har ya kawo ka faɗa min dan Allah”


“Miye sunan shi?”


“Sunan shi Hilal”


“Okay”


“Karka Manta ka turo min account number ɗin”


“Alright”


Yana kashe wayar ya turo mata account number ɗin. Ta jidaɗin ganin number, ga dukan alama zai yi saurin bata haɗin kai, jiki na rawa ta tashi ta fita daga office ɗinta, ta je ta cikin bankin ta masa transfer 100k.


NAMRA POV.


Yau ba laifi ta samu bachi dare, duk da ba mai nauyi bane sosai, minti goma ashirin zuwa ashirin da biyar take farkawa.
Sai dai a duk farkawar da take, a zaune take ganin Mardiya tana kallonta kamar wata mayya, tun Namra tana dauriya ta koma bachi har ta gaji ta tambaye dalilin rashin bachin nata.


“Wallahi na kasa bachin ne mafarkin tsoro nake, kusan kwana biyu yanzu haka na ke”


“Kiyi addu'ah kawai ki kwanta, babu abunda zai same ki, ki karanta Ayatul kursiyu ƙafa uku ko wace da bismillah wallahi har garin Allah ya waye babu abunda zai same ki”


“Toh na gode zan gwada”


Ta faɗa da damuwar a muryarta. Komawa Namra tayi ta kwanta ba ita ta fake farkawa ba sai asuba.
A kulolin gidan ta ɗauka ta zuba musu ɗumamen tuwo da Maman Mardiya tayi, sannan tayi wanka ta ɗauka ta nufi asibitin.


Ko da ta isa ta tarar har sun siye tea a bakin asibitin sun karya. Mama bata wani sake da Namra sun gaisa ba, ciki-ciki ta amsa masa gaisuwarta, ta fice tama watsa mata wani kallo a kaikaice kamar wata kishiryarta.
Hakan be dame Namra ba, dan ita ta san muhalin data aje ta a yanzu, tun da ta fara fahimtar tafiyarsu.
Bayan kamar minti talatin da fitar Mama Asim ya ɗauko dubu goma sha biyar ya miƙa ma Namra.


“Ga wannan ki siye wasu abubuwan na gida, Mama zata siyo katifa da wasu kayan”


Namra ta jidaɗi sosai, daman zama gidan su Mardiya ya fara isarta, duk da tasan kuɗin ba zasu isheta hakan be hanata nuna farincikinta ba.


“An biya kuɗin maganin ne har wasu sun rage?”


“Eh ɗari biyu matar ta ara mana, Allah dai ya ba ni ikon biya”


“Amin, amman Asim shabiyar zasu isa siyayya kuwa? Ba mu da komai fa kasan komai ya ƙone”


“Haka nan za a matsa ayi Namra, bafa irin siyayar gidan ku zaki yi ba, ta talakawa zaki yi, kamin mu ga abunda Allah zai yi kuma”


“Toh Allah ya taimaka”


“Amin, likitan yayi min allurar ɗaya ɗazu, kuma yace ya kamata na ɗan fara taka ƙafar, koda ina riƙa wani abun ne”


“Aiko ya kamata ka fara tun yanzu”


“A'a sai nan gaba, gaskiya ni tsoro nake ji”


Ta ɗanyi dariya, tana mamakin irin rakin da Asim yake da shi. Asibitin ta wuni sai da yamma ta koma da zimmar taje Mardiya ta raka ta kasuwa suyi siyayya. Bayan tafiyarta Mama ta siyo abinci a bakin asibiti ta ci, ta kawo mo Asim, dan kwata-kwata ƙwara tayi daga ɗakin har sai da Namra ta tafiyarta, sannan ta dawo, Mama irin mutanen nan ne da basu iya samun arziki ba, waɗanda idan abu ya same su a take suke canjawa mutum, ga shegen son su yi kuɗi kamar hauka, tana daga cikin mutanen da suka tsani masu arziki, suna ganin kamar Allah ya fi son su da su, ita a nata rayuwar bata ƙi Asim yayi arziki ba ta kowa ne hali, ko dan ya rama abunda iyayen Namra suka masa.




ABDOOL POV.


A hankali yake tsotsa bakinsa kamar mai shan minti, sai wasa yake da drink ɗin dake gabansa ya kasa sha.


“Saboda Mai Martaba yace yana son ganin ka shiyasa ka wani damu ko?”


Ya ɗan ɗaga kai kaɗan ya kalli Ummi da idonsa na marar gaskiya.


“Eh mana, na san ba zai wuce yayi min maganar aure ba”


“Ai dole yayi maka maganar aure, tun da kai baka san ka girma ba, ace ko wace mace baka so, kwana ki har ƙaryar ciwo kayi min sai gashi likitan ya ƙarya ta ka, wai anya ba aljana take auren ka ba?”


Yayi dariya yana kallon ƙannensa mata su huɗu da suke zaune a ɗayan ɓangaren na falo suna sha'aninsu.


“Abdool ya kamata ace kana yi ma kan ka faɗa, mahaifin ka yana son ka, kar kayi abunda zai sa kyaunka ya ɓace a gare shi, kasan ƴan da matan uban nan naka suke, basun ka suke su kuma zuga shi zasu yi ta yi har sai sun ga taren ku ya ɓace, duk kuma wanda bashi da uwa a cikin gida yana cikin matsala dole ne yayi taka tsantsan”


Ya shafa kansa, yana jingina da kujerar dinning ɗin.


“Ummi Mai Martaba na da wani buri akai na, shiyasa ya natsa nayi aure, ni kuma bana son sarautar nan, ni kwata-kwata ma ba dan shi ba Wallahi da ba zan zauna ƙasar nan ba”


“Amman ai ba kai kaɗai ya haifa Namiji ba, amman kai ne mafi soyuwa a ransa, to dan me ba zakayi masa abunda zai sa ya ƙara son ka ba? Indai baka fitar da wanda kake so ba sai ya kai ga ɗaukar wata a cikin gidan nan ya haɗa ku, idan kuma ka ƙi yarda kasan abunda zai biyo baya”


“Ummi wanda nake so ban san inda zan ganta ba, ban san yadda za'ayi na haɗu da ita ba”


“Kamar ya?”


Ta tambaya tana kai ƙwallon anabi a bakinta.


“A Funtua na ganta bakin wani pharmacy, na fita nayi mata magana, tace min matar aure ce ita”


“Ta faɗa maka ita matar aure ce kuma zaka so ta?”


“Sam bata min kama da matar aure ba mai igiya uku, sai da matar aure kalar aure, ina ganin wannan take nufi, irin ƴan matan nan ne masu aji sosai, har marina tayi fa”


Ummi ta gyara zamanta, irin na mutanen nan da naira ta zauna a jikinsu har ta nuna kanta, ga kuma milkin dake cikin jininta, na ƴaƴan sarakai.


“Wayw Uban ta a garin nan?”


“Wallahi nima ban sani ba, irin yaran nan masu mugun ji da kan su, kuma na rasa yadda zan yi na same ta, duk wata hanya da zata sadani da sake ganin ta nabi amman ba nasara, har abinci naje na raba a inda ake sa ran zan ganta amman ban ganta ba, kuma ni Wallahi ita nake so”


“To sai yaya kenan?”


“Sai na nemota duk inda na ganta zan gane ta, ba zata min marin banza ba sai na rama, kuma gaskiya ba zan haɗu da ita hakan nan ba ga dukan alamun ita ce, dukan matan da nake haɗuwa da su ban ji komai akan su ba sai ita”


Ya faɗa yana mai tashi tsaye.


“Anya ba aljana ka haɗu da ita ba Abdool?”


“Ba aljana bace Ummi”


A faɗa yana dariya, zuwa yayi ya mata side hug, ya ɗauki anabi ɗaya ya kai a bakinsa, na biyu kuma ya jefe ƙannensa da shi.


“Ummi ki tsara min yadda zan cewa Mai Martaba”


Be tsaya jiran abunda zata ce ba, ya fice daga falon yana murmushi. Da kallo Ummi ta bishi tana mamakin yadda ɗan nata yake ƙoƙarin zame mata aljani.




ANTY AMARYA POV.


Tun da Abbah yake maganar bata ce uffan ba har sai da ya kai aya. Sannan ta sauke ajiyar zuciya tace.


“Zan musu magana, ai dukan su suna da manema, daga Hindatu har Maryam ɗin”


“Ƙara ayi musu magana su fitar da wanda suke so, da ba zan sake zaɓawa kowa miji ba”


“To, Alhaji nacw har yanzu baka je ganin Mijin Namra ba, ya kamata ko a waya ne ka kira shi ku gaisa”


“Ko Namra ce bata da lafiya ba zan kira ba, balle mijinta, ki daina kawo min wani bato daya shafi Namra, baki san irin baƙin cikinta daya ke cikin zuciyata ba”


“Toh ni idan ka min izini ina son na koma naje na ganshi”


“Ba zaki koma ba, idan be gode da ganin da kika masa ba, ya bar shi, ba familyn ta ya aura ba ita ya aura, kuma na sallama masa ita har abada, babu hannuna babu ƙafata a lamarin Namra, ta zaɓi wanda take so sai taje ta zauna da shi”


Ko kaɗan kalaman Abbah basu yi ma Anty Amarya daɗi ba, nan take ta canja fuska, ɓacin rai dake zuciyarta ya bayyana.


“Haba dai, wannan wane irin magana ne? Shikenan bata da damar ta zaɓi mijin da take so? Wannan sam ba adalci ba ne, baka ƙaunar yarinyar nan kamar ba kai ka haife ta, ɗan abu ƙanƙane sai ka ɗauki karan tsana ka ɗora mata”


Ta ƙarasa maganar da kuka.


“Ke kin fi kowa sanin na yadda na nunawa Namra so, ai ke ya kamata kiyi tunani kiga rashin dacewar abunda Namra tayi min, ko da ace ba ni na haife ta, ya kamata ace tayi min biyayya tun da nina raine ta har ta kai inda take yanzu, be kamata ta zaɓi wani ta bar ni”


Kukan Anty Amarya ta cigaba da rera masa. Shi kuma ya ɗauki jaridarsa ya buɗe yana karatu, ba dan kuma yana son karatun ba, sai dan yayi avoiding kukan na Anty Amarya, tana da matsayi a zuciyarsa, ba kasafai yake son kukanta an itace mafi soyuwa a zuciyarsa, duba da yadda take masa biyayya da kuma yadda take da ƙuruciya, sama da Hajiya Barau data kwana biyu.
Idan kuma ya biye mata yasan halinta yanzu ne zata birkice masa, har ya rasa gane kanta.


Data gaji da kukan ne, ta share hawayenta, ta tashi ta bar masa ɗakin.
Tana shigowa part ɗinta duka ƴaƴanta suka lura da yanayinta, ba ma kamar Maryam data fi damuwa da ita sosai.


“Anty Lafiya?”


“Lafiya ƙalau, kawai ina tunanin Namra ne, ban san halin da take ciki ba babu waya hannunta, kuma Abban ku yaƙi ya bar ni naje na duba su”


“Inshallah tana cikin ƙoshin lafiya Anty, kwana ki ma sai da ta turo da text wai ki taimaka mata da kuɗi, ni kuma na goge text ɗin dan nasan Asim ne zai sata”


“Amman miyasa baki faɗa min ba? Baki san halin da take ciki ba, ƙaddara ce ta riga ta faɗa mata babu yadda za muyi”


“Nayi tunanin ko shine yasa ta”


“Nawa tace a bata?”


“Bata faɗa ba”


“Gobe kije ki tura mata 300.000k sai ki kira wayar Asim ki faɗa mata, kuma kice ta siye waya tasa layin ta, kwana kin nan mafarkin ta nake ta yi, ban san halin da ƴata take ciki ba”


“Inshallah zan tura mata”


“Abbah ku ba ban saƙo gare ku, amman sai gobe zan faɗa muku”


Tana kai wa nan ta tashi ta nufi ɗakinta, tana share hawayen da suka zubo mata.




RASHIDA POV.


Tana gama aikin office ɗin ta dawo gida, tasan abunda ta shirya ma kanta shiyasa ta dawo da ƙarfe shida tsaɓanin tara na dare data saba dawowa.
Ɗakinsa ta shiga tana masa bincike ko zata ga takardun results ɗin ko kuma jinin daya ɗiba tun da yace mata be kai, amman bata ga komai ba. Har ta gaji ta dawo dakinta .


Duk da tasan yau ba a ɗakinta Doc take ba, hakan be hanata chaɓa ado ba, dan ta ɗauki hankalinsa. Daman ya saba duk wacce yake ba girkinta ba yakan shiga yayi mata sai da safe, sannan ya wuce ɗakin da zai kwana.
Tun kamin ya shigo ɗakin, ta haɗa masa tea da lemun tsami dan tasan yana son haka, ta kuma saka masa zuma a maimakon sugar, sai ta ɗauko maganin dake jakarta ta buɗe ta kaɗa masa cikin tea ɗin har kusan guda biyar.
Tana mayarda jakar ta aje yana turo ƙofar ɗakin ya shigo, gabanta ya faɗi, abun ka da wanda bata saba ba, sai dai ta wayance taje ta rumgume shi.


To her surprise sai ya sauke hannayensa daga saman wuyanta, yana ɗan murmushi. Bata damu da abunda yake mata ba, dan a tunaninta fushin ɗazun ne na dress ɗin ta tayi. Cup ɗin tea biyu ne sai ta ɗauki ɗayan ta miƙa masa.


“Ga tea”


Hannu ya kai ya karɓa ya furta


“Thank you, good night”


Har ya juya, sai kuma ya juyo ya kalleta kamar zai ce wani abu, sai kawai ya sakar mata murmushin irin na fatar faki, ya juya ya fice.


Ɗakin Kalsoom ya nufa, ko da ya shiga ciki be ganta ba, ya duba bathroom bata ciki, sai kawai ya nufi ɗakin su Ezzah dan yasan ba wuce tana can ba.
A tsakiyar gado ya tsame ta tana ta tofawa yaransa addu'o'i, su kuma sai bachi suke tayi abun su. A bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yana murmushi, har ta gama ta taso ta nufo shi.


Hannu ya kai ya laƙƙamo kunkurunta, jikinta ya haɗe da nashi, ita kuma sai haɗiyar yawu take tana kallon kofin dake hannunsa, ƙamshin tea ɗin yana kai ma hancinta ziyara.
Kaɗan ya kurɓa ya kai mata kofin a baki, ɗan tsami tsamin data ji yasa ta jidaɗin tea, ta riƙe kofin da hannu biyu har sai da ta shanye tea ɗin gaba ɗaya.


Tana shanye tea ɗin ta saki kofin tayi masa kwance a jikin, wani irin bachi mai bala'in nauyi yayi gaba da ita.


“Hey...”


Ya faɗa yana girgizata, amman ina, tayi nisa har ƙoƙarin zubewa take a ƙasa, hannayensa yasa ya ɗauke ta cak, ya nufi ɗakinta da ita. Saman gado ya kwanatar da ita ya kwanta gefenta yana shafa fuskarta, zuciyarsa cike da mamakin abunda yake cikin tea ɗin.
Ya kusan minti talatin a gurin kwance, sai yaƙi yake da bachin dake son sace shi, yana unƙurin tashi yaji an turo ƙofar ɗakin, ƙin motsawa yayi sai ya lumshe ido kamar yayi bachi, sai ga Rashida ta ƙaraso har gurin tana leƙen fuskarsa, har da sa hannunta tana masa yawo da shi dan ta inda gasken yayi bachin.


Da sauri ta juya ta fita ta nufi ɗakinsa, keys ɗin motarsa ta ɗauka, ta fito waje ta buɗe motar tana masa bincike, seat ɗinsa na gaba ta buɗe ta fara bincikar takardun da suke gurin. Jikinta ne ya bata ana kallonta, da sauri ta fito daga motar, sai taga Doc tsaye ya rumgume hannayensa yana kallonta.


Kasa motsawa tayi, numfashita mai sai da yayi nisan zango sannan ya dawo, jin tayi kamar ƙasa ta buɗe ta shige ciki, a take mararta ta cika da fitsari.






___________________________________________


One free Page remained 🙌


BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

Website
www.khadeejacandy.com.ng


*PAGE - 35. Last Free Page*


NOT EDITED ⚠️


Bata taɓa sanin gume na da zafi ba, sai a wannan lokacin, wani irin nauyi ta ji kanta yayi kamar an ɗauki duniyar nan an ɗora mata, yau ganin Hilal take ya cika ko ina na duniyar idanunta.
Yau kam ba ranar kuka ba ce, tashin hankalin daya same ta ya fi ƙarfin kuka, hakan yasa hawaye ba kusanci idonta ba, ashe abu mai sauƙi ake ma kuka, ta kasa yarda yau ita ce Hilal ya kama dumu-dumu ba.


“Kin san kina da HIV kike ƙoƙarin ɓoyewa Rashida? Do you know what lokacin dana ɗibi jinin ki result ɗin ba ɓata yayi ba, nace miki haka ne saboda ban yarda da abunda idona ya gani ba, na dawo na ɗibi jininki da na yarana da na Kalsoom nawa dan na gwada, so that na tabbatar idan da gaske kina ɗauke da cutar ne, amman ke kin san kina ɗauke da cutar kika bar ni ina kusantar ki?


Da ba dan wanann cikin ba, da sai mu ɗauki dogon lokaci a tare da dake baki faɗa ba right? What if all of us mun kamu da cutar nan?”


Ƙiri-ƙiri tayi masa da ido, cikin ƙarfin hali ta cira ƙafarta da tayi mata mugun nauyi ta tako ta ƙaraso kusa da shi.


“Kana tabbacin ni ce kaɗai nake ɗauke da cutar? Kasan ta ina cutar ta shige ni? Miyasa idon ka zai rufe har haka?”


“Ke da kan ki kike zargin kan ki, dan me zakiyi ma Doc Sabo transfer 100,000k? Dan me zaki ce idan ya kawo jinin kamin ya auna ya kira ki? You late Rashida ko da kika kira shi na riga na kai jinin amman yaƙi ya faɗa miki saboda ya san ni kamin ya sanni kuma ya san aikinsa, daman nasan ziyarar da kika kawo min ɗazu a office bata banza bace cox na lura dake kwata-kwata hankalinki baya jikin,


Bincike da kika min da tambayoyin da kika

Please Login or Register in order to submit comment