Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ƴar'uwata ce, kuma naga kamar zaku fi zaman lafiya”


Wani dogon tsaki taja, tasa guiwar hannunta ta buge masa ciki. Ba shiri ya sake ta ya dafe cikin.


“Yasmin kashe ni zaki yi?”


Tsaki ta sake masa ta wuce ɗakinta, tana cika da batsewa. Da kallo Uzair ya bita yana murmushi, sai da ta shige ɗakinta sannan ya tashi ya nufi ɗakinsa.


Tun da asubar fari Hajiya Barau ta bugo masa waya ta faɗa masa abunda ya faru. Yi yayi kamar be sam komai ba, duk ya firgice yana nuna damuwa, sai tambayoyi yake zubo mata, yana nuna mata tashin hankalinsa kamar ance masa gata nan gabansa.


“Ban san miyasa Namra ta tsane ni har haka ba, ban san abunda na tsare mata ba, na rasa gane kanta”


“Uzair, inda har ba Allah yayi auren nan naku ba, bana jin zata zauna gidanka ko da ka aureta, kuma Wallahi a yadda zuciyar Namra take ko kashe ka zata iya yi ko kuma tayi maka wata illar, tun da bata son ka”


“Daman abunda Hajiyata take ta faɗa kenan, ni ina ganin gaskiya haƙura zan yi, ƙara taje ta auri wanda take so kawai”


“Da kam yafi maka, dan wannan auren ba zai yi ƙarƙo ba, sannan bana jin wannan yaron daya ɗauke ta ze barta haka nan, kar ayi maka kwashe-kashe”


“Barin ze fi tun da har zuciyarta wani take so, kuma duk macen da zata iya bin saurayinta kinsan ta girma”


“Ashe kai ma kana da tunani, fasa auren akam zai fiye maka”


Daga haka suka yi sallama. shi kuma ya sauka saman gadon ya nufi bathroom.
Sai tara da ƴan mintuna ya shirya, be damu da breakfast ya fito ya nufi parking space. Lokacin Yasmin har ta daɗe da barin gidan. Direct gidan Mahaifiyarsa ya nufa Hajiya Binta. A can ya yi breakfast yana labarta mata abunda ya faru, sai tace masa ai Hajiya Barau ta kira ta ta faɗa mata komai. Ta ji daɗin maganar da yayi ta basa auren Namra, ita daman zuciyarta bata natsu da aurensa da Namra ba, tun lokacin da tayi masa ƙazafi.




NAMRA POV.


Cikin ikon Allah numfashinta ya dawo, sai aka ɗaura mata drip,
Sai dai bata farka ba sai kusan Asuba, a lokacin Mama Zainab ce kawai a ɗakin, dan Hajiya da Hindatu tun cikin dare suka koma gida.
Kuma har garin Allah ya waye babu wanda ya leƙosu sai Amira, ita ma sai goma har da rabi sannan ta iso.


Namra na zaune jugummm tana tunani hawaye na bin fuskarta. Amira na shiga ta je da gudu ta rumgume Namra tana kuka.


“Wallahi da ba'a ganki ba Namra, da kashe kai na zan yi”


Namra ta share hawayenta, ta kalli Amira.


“Amira ina Asim yake?”


Gabanta ya faɗi, har sai da ta haɗiye yawun bakinta ta.


“Ina Asim yake Amira? Taya Asim ya zo gidan ku har ya baki wannan number?”


Nan ma kasa amsawa ta yi sai kukan munafurci take, zuciyarta na tsara mata irin ƙaryar da zata yi Namra dan kare kanta. kamin ta amkaro har Namra ta ƙara mata wata tambayar.


“Amira ki amsa min mana, ina Asim? Amira number da kika ba ni bata Asim ba ce, lokacin dana je ba Asim na gani ba Uzair na gani, faɗa min ta ya haka ya faru?”


Har lokacin Amira shiru take, bakinta sai rawa yake ta kasa magana. Hakan ya tabbatar ma Namra abunda take zargi.


“Uzair ya haɗa kai da ke an cuce ni”


Dam! Dam!! Dam!!! Zuciyar Amira take bugawa har cikin ƙwaƙwalwarta, ja ta yi da baya tana girgiza ma Namra kai hawaye na fita a idonta.


“Ki zargi kowa da cin amanarki, amman ban da ni, har a bada Amira ba zata taɓa cin amanar Namra ba”


Namra ta ɗaga mata kai tana hawaye.


“Asim ma ba zai iya cin amana ta ba, karki yaudari kanki wajen nuna min Asim yana so ya cuce ni. Amman ke Uzair zai iya siyen ki ya biya ki dan ya cimma burinshi, babu wanda ze fahimci ni, na ɓata ran kowa, ban san hali da Mahaifana suke ciki ba, sanadin ke da Uzair”


“Namra karki yanke hukuncin abunda baki sani ba, zan iya dafa miki qur'ane Namra, ban haɗa kai da Uzair ba dan na cuce ki.
Namra ta ya zan haɗa kai da wani ya wulaƙanta ki a titi? Har sai jama'ar unguwarku sun ɗaiko ki su kawo gidanku, Kuma su bada shaidar sun ji muryar Asim kuma sun ji an kira sunansa.


Namra tun da na bar gidan ku, ban rumtsa ba saboda tunanin da kukan rashin sanin halin da kike ciki, kina fita Maryam ta shigo ni ta ɗaurawa laifi tace ni ce silar komai, na yi tunani ke zaki bada shaida akaina ashe na yi kuskure.


Namra ki faɗa min dalili ɗaya, da zai sa na cuce ki, faɗa min Namra? Kinsan a iya zamantakewar mu da ke duk wanda ya ci amanar wani Allah sai ya fitar masa da haƙƙinsa”


Da wani irin kuka ta ƙarasa maganar kamar ta sheɗe. Kalamata sun sa jikin Namra sanyi, sai zargin da take mata ya soma raguwa, sai dai har yanzu bata ji zuciyarta ta natsu da Amira ba.
Kan ta ya kulle, ita dai tasan ba mafarki tayi ba, tabbas ta yi ido huɗu da Uzair kuma ya riƙa ta, sai dai bayan nan bata san wani abunda ya faru ba.


‘Taya Uzair yazo gurin? Miye dalilin da zai sa Uzair ya yi min haka? Taya Amira zata cu ni ta’


Sune tambayoyin da suka tsaya mata a rai, kuma suke ƙoƙari riƙita mata ƙwaƙwalwa.
Jin Amira ta dafa ta ya dawo da ita daga dogon tunanin da take.


“Namra kin fi kowa sanin ni wace ce...”


Bata ƙarasa Namra ta kai hannu ta riƙa hannunta.


“Ki yi haƙuri, kaina a kulle yake, a yanzu bana iya banbance gaskiya da ƙarya, bana iya tantance komai na rasa gane abunda yake faruwa da ni...”


Da kuka ta ƙarasa maganar, sai Amira ta rumgume ta suna kukan tare.
Shigowar Mama Zainab ne yasa suka tsagaita kukan, suka share hawayensu.


“Kuka fa ba zai muku ba, abunda ya faru ya riga ya faru sai dai a tari gaba. Likitan ya rubuta miki wani magani?”


Ta tambaya dan ɗazu Likitan daya shigo ne yasa ta fita, ta basu guri. Namra ta ɗauki takardar dake gefenta ta miƙa mata.


“Bai rubuta min komai ba, ya dai bani takardar sallama, yace bayan sati biyu na dawo”


Mama Zainab ta karɓa tana faɗin


“Masha Allah, sai ki tashi muyi harama, dan yanzu Hajiya Raliya ta kira ni wai tana son ta zo Mamanki ta hanata, kuma ƙara mu koma gida kar a fara mana taro, tun da babu wanda yaji abunda ya faru sai ƴan gida”


Namra ta lumshe ido ta jin wani abu daya tsaya mata a zuciya.
Amira ce taje ta biya komai da komai sannan ta zo ta riƙa Namra suka fita tare.




HILAL POV.


A gajiye ya fito asibitin, daker yake driving saboda gajiya, dan wuni yayi yana aiki, har jin yake kamar fever na son rufe shi.
Yau kan baya iya bin gosulon nan na government house, saboda taron da ake.
Sai kawai ya hanka ta cikin estate dan samawa kansa sauƙi sai dai tafiyar zata masa nisa sosai tun da ya biyo doguwar hanya.


“Subhanallah”


Ya faɗa lokacin da idanuwansa sukayi arba da wata kyakkyawar fuska, dake takowa izuwa hanyar daya fito. Sai ya rage gudun da yake, ya mai cigaba da kallonta.
Tana da kyau sosai mai jan hakali da saka natsuwar zuci, sai dai fuskarta kawai yake iya gani, domin jikinta rufe yake da ƙaton hijabi. Hakan kuma ba ƙaramin burgeshi yayi ba, ganinta cikin kamala ga tafiyarta a natse.
Kamin ta ƙaraso kusa da shi ya faka gefen ti-ti yana ƙare mata kallo.
Tana da tsayi da dogon hanci ga idonta dara-dara, farin fuskarta fes, sai dai a iya yadda ya fahimta kamar bata da jiki sosai.
Dai-dai lokacin data kawo kusa da shi sai ya sauke gilashin motarsa yana miƙa mata sallama.


“Assalamu alaikum Malama”


“Wa'alaikassalam”


Ta amsa mishi da zazzaƙar muryarta sai dai hakan be sa ta tsaya ba, sai ta cigaba da tafiyarta kamar ba ita ta amsa masa sallamar ba.
Da sauri Doctor Hilal ya buɗe motar ya fito ya biyo ta da ƙafa.


“Dan Allah ɗan tsaya na tambaye ki wani abu”


Allah daya haɗa ta dashi yasa ta tsaya, da badan haka ba babu abunda ze sa ta tsaya dan iya yanzu ta sallama a lamarin maza.


“Dan Allah ke matar aure ce?”


“A'a”


“Dan Allah ya sunan ki, kuma ina ne gidan ku?”


Sai a lokacin ta kalleshi, wani faɗuwa gabanta yayi lokacin da idonta suka sauka cikin nasa, kyausa yayi mata kwargiji, wanda yasa tayi saurin sauke idonta ƙasa, tana sauraren bugun zuciyarta.


“Miyasa ka tambaya?”


“I ask you first”


Ba amfanin yin ƙarya, dole ta faɗa masa gaskiya.


“Sunana Ummul-Kalsoom amman ana kira da Kalsoom, gidan mu yana ta nan gaba number 5 gidan Alhaji Faruk Kafinta”


“Toh na gode”


Bata sake ce masa komai ba, ta cigaba da tafiyarta. Shi kuma ya bita da kallo har sai da yaga inda ta shiga, sannan ya shiga motar yana murmushi, a take ya ji duk gajiyar da take tare dashi ta wartsake, cikin farinciki da annashuwa ya kunna motar ya hau ti-ti.




__________________________


What do you expect next?
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa11.html


🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


NOT EDITED ⚠️




*PAGE - 11*


NAMRA POV.


Keke Napep Amira ta tare musu ta faɗa masa inda ze kai su, sannan suka shiga.
Be sauke su ko'ina ba sai Ƙofar gidan, Amira ta biya shi sannan ta riƙa hannu Namra suka shiga cikin gidan.
Kamar mai nauyin ƙafa haka Namra take tafiya tana hawaye, gaban na bugawa da ƙarfi. Da wane ido zata kalli Anty Amarya? Idan Abbah ya kalleta me zata ce masa.
Mama Zainab ce gaba da sallama sannan Namra, sai Amira ta biyo baya. Hajiya Raliya ta amsa musu sallamar, Anty Amarya kam yi tayi kamar ma bata gansu ba, ta tashi tayi ta nufi kitchin.
Saman Kujera Amira ta zaunar da Namra, sai ta zauna kusa da ita tana amsa ya jikin da Hajiya Raliya take mata.


“Da sauki har an sallamota”


“Wallahi babu yadda ba mu yi ba ni da Aisha da Hindu muje ganin ki amman Larai ta hana, sai gashi Abbanki ya zo shi yace kar wanda ya fita da sunan ganin ki a gidan nan, toh kar ma ya kuskura ya dawo”


Fashewa ta yi da kuka, ta kwantar da kanta jikin Amira dake hawaye.
Shigowar Hajiya Barau ne yasa ta noke kanta, Amira da Mama Zainab suka amsa mata. Idonta kar kan Namra sai kallon jikinta take.


“Namra kin dawo? Wallahi Alhaji ne ya hana mu zuwa ganin ki, ya jikin?”


“Alhamdulillahi”


Mama Zainab ta amsa. Zaunawa tayi kusa da Amira.


“Ince dai babu abunda ya same ki ko?”


“A'a ba komai likita ya bincika yace babu abunda yake damunta”


Cewar Amira


“To Alhamdulillahi, Allah ya tsare gaba”


Sai ta tashi sun-sun-sun ta fice. Hajiya Raliya ta kalli Namra cikin damuwa ta ce


“Haba Namra haka kike so maƙiya su yi ta miki dariya? Ansa ranar aurenki kije ki gana da wani? Haka aka kawo mana ke shame-shame mazan unguwar nan zagaye da ke, shi haka shine daɗi?”


Amira ya share hawayenta


“Dan Allah ku daina wannan maganar, zaku ɗaga mata hankali ne kawai, ita kan ta ba'a son ran ta hakan ya faru ba, kusan babu yadda Namra zata kai kanta ga halaka ko kuma inda ta san mutuncin ta ze zube”


Namra kan kuka kawai take, tana jin wani irin ƙololon baƙin ciki ya riƙe mata zuciya. Kamar daga sama sai ga Abbah ya shigo falon fuska babu annuri.


A take cikin Namra ya ɗauki ƙugi, ko Amira sai da ta razana da yanayinsa, yana katsawa Namra tsawa jikinta ya hau rawa.


“Khadija ki tashi ki koma can gurin saurayin na ki bana son ganin ki a cikin gidan nan!”


Cikin baƙar zuciya Anty Amarya ta fito daga kitchen ta nufo inda Abbah yake tsaye tana faɗin


“Babu inda Namra zata je, ko kisan kai ta aikata idan ta shigo nan gidan ta samu mafaka, dan gidan ubanta ne ciki da waje, komai Namra ta aikata sai ance ƴar Alhaji Usaman ce ko da bata duniya, duk inda aka ga sunan Namra sai anga naka kuma dole ace ƴar ka ce”


Abbah ya nuna Anty Amarya


“Ai daman ke kike goya mata baya take duk abunda take”


Anty Amarya ta nuna kanta tana hawaye.


“Ƙwarai, nina goya mata baya nace ta fita cikin dare taje taga Asim, kuma idan taje ta faɗi ta suma jama'a su ɗauko ta su kawo maka cikin gida ni nace....”


Mama Zainab ta rufe mata baki, tana ba Abbah haƙuri. Da ƙarfi Anty Amarya ta buge mata hannu ta matsa tana faɗin


“Ki ban ni ina faɗi ciwon bakin na, wannan ƙurjin ya daɗe yana min ƙaiƙayi a cikin rai, duk abunda Namra ta aikata gare ni yake dawowa, ni nake tura ta, faɗa min wace uwa ce zata so abunda ya faru da Namra ya faru da ƴarta, amman ni yake ɗorawa laifi”


Shiru Abbah yayi yana kallon Anty Amarya data cika falon da ruwan bala'i tana zazzaga masa rashin mutuncin har yata gama be sake cewa uffan ba.
Hajiya Raliya ce keta bashi haƙuri tana cewa kar ya tanka mata, shi ma daman be da niyar sake ce mata komai, dan yasan Anty Amarya bata iya faɗa ba, idan ta birkice masa babu mai iya tare ta sai Allah, haka take wani lokacin kamar mai aljannu, shiyasa Hajiya Barau ta sallama ma lamarinta.


Tsaye Anty Amarya ta yi masa ƙyam, tana jira ya ce mata kulle ta ce masa chas, dan idonta yanzu a murje yake, zuciyarta kuma ta kawo. Abbah be yarda ya sake ce mata ƙomai ba, ya juya ya fice.
Sannan Anty Amarya ta kalli Amira a tsawace tace


»“Ke Amira tashi ki je gida”


Da sauri Amira ta ɗauki jakarta ta rayata, ko sai ajima bata ce ba, ta fice jikinta na rawa.
Tasss! Tasss!! Tasss!!! Anty Amarya ta sauke ma Namra mari har sau uku, sannan ta nuna mata ƙofar ɗakinta


“Tashi ki wuce ɗakin ki, kin samu farinciki kin jidaɗi”


Zubewa Namra ta yi ƙasa daga kan kujera tana kuka, ta riƙe ƙafafun Anty Amarya.
Riƙo fuskar Namra Anty Amarya ta yi ta sake sakar mata wani marin sannan ta tureta ta fisge ƙafarta, ta wuce ɗakinta cike da ɓacin rai.
Daga Hajiya Raliya har Mama Zainab tsaye suka yi basu yi unƙurin yin wani abu ba, dan sunsan halin ƴar'uwarsu kan akwai haƙuri amman idan ta hasala bata da daɗi.


Sai daNamra tayi kukanta mai isarta sannan ta tashi ta nufi ɗakinta. Saman gadonta ta faɗa ta sake fashewa da sabon kuka.
Har La'asar bata fito daga ɗakin ba, kuma babu wanda ya shiga inda take inba Aisha ba, itama tun da ta fita tayi shirin islamiya babu wanda ya leƙo ɗakin.
Tasan dole ne Maryam tayi fushi da ita, dan Maryam tafi kowa ɗaukar zafi idan wani abu ya faru. Sai da dare Aisha ta shigo ta aje mata abinci ta fita.




UZAIR POV.


Yana tasowa daga gurin aiki kai tsaye ya wuce guesthouse ɗin Jafar, daman tun yana gurin aikin suka sha masa kai da kira, wai duk sun hallara shi kawai suke jira.
Yana shiga ruwa kawai ya sha Najeeb ya tambaye shi.


“Ya Labarin yarinyar?”


“Wai asibiti ta kwana, Kishiyar mamarta take faɗa min ɗazu da safe, sai na nuna mata kamar ban ji ba”


“Amman kaje ka ganta?”


Jafar ya tambaya. Sai ya girgiza masa kai


“A'a na dai je gurin Hajiyata na faɗa mata maganar janye auren tace zata je ta faɗawa Abbah”


Najeeb yace


“Amman ai da kaje ka ganta Uzair sai ka nuna kasan abunda ya faru, anyway muje ciki malamin yana ciki tun ɗazu ya iso”


Uzair yayi sauri haɗiye ruwan bakinsa.


“What? Na ɗauka zuwa zamu yi gurin shi”


“No Ba zamu iya shiga dajin nan ba, sai na aika direba ya ɗauko shi, kasan su kuɗi kawai suke so da sun ga ƙuɗi komai zasu iya”


Cewar Najeeb. Tahir ya aje wayar dake hannunsa saman tebur ya miƙe tsaye.


“Muje ayi abunda za'ayi akwai inda nake son naje”


Sai duk suka ɗugunzuma suka nufi wani ƙaramin falo, da ba kasafai suke zama cikin shi ba.
Dattijo ne sanye da babbar rigarsa, kansa ya sha uban rawani, haƙorasan duk goro, ga wani ƙaton faifai dake gabansa, mai cike da jar ƙasa. Idan ka kalleshi sai kayi masa ɗaukar mutumin kirki, a fuskarsa ba zakayi zaton zai iya aikata wani mugun abu ba.


Duk guri suka samu suka zauna, bayan sun gaisa, Jafar ya kora masa da bayani


“Am daman na faɗa maka tun ɗazu, abokin mu ne yake ciki wata ƴar matsala, wata ƴar'uwarsa ce take ƙoƙarin masa zagon ƙasa, saboda ta kamashi yana aikata luwaɗi, shine take son tona masa asiri, babu yadda be lallaɓata ba amman ta ƙi yanzu haka so take ta rabashi da matarsa, da kowa nasa”


Lokacin da Jafar ya kai aya sai ya zumguri kafaɗar Uzair alamar yayi magana, sai shi kuma ya ɗora.


“Yanzu haka ta ɓata min suna a cikin familyn mu kuma yanzu haka tana nan akan bakanta na cewar ta faɗawa duniya da ƙwaƙwarar hujjah”


Malamin yayi murmushi yana gyara zamansa.


“Yanzu me kake son ayi mana, shin kana son a kulle mata baki ne ko kuma ayi mata kurciya ta bar garin gaba ɗaya?”


Kallo-kallo suka riƙayi, kowa na tunanin abun cewa, can sai Najeeb yace


“A ɗaure mata bakin kawai ta yadda komai ta gani ba zata iya faɗa ba”


“Ko kuma ayi mata kuciya ta bar garin gaba ɗaya”


Cewar Jafar. Uzair ya girgiza kai


“Idan muka mata haka ba muyi mata adalci ba, why not dai ayi mata na rufar bakin”


Najeeb yaja tsaki


“Ita ba naka sunan ta ɓata ba? Idan aka mata kuciyar ta bar gari kana tunanin wani zai zargeka ne? Sai dai ace ai halinta ne, kuma wannan shine kawai mafita”


Uzair yayi shiru yana nazari. Sai Malamin yace


“Minene sunan ta? Sai mu duba muga irin aiki daya dace ayi mata, dan aikin da ke yima wani bashi ke ma wani ba”


“Sunanta Khadija, amman Namra ake kiranta”


A take Malamin ya gyara ƙasar ya shiga bincike, yana wasu tsiface-tsiface.
Ya ɗauki tsawon lokaci yana bincike amman be gano komai ba, can ya ɗago kai ya kallesu yana jinjina kai yace


“Lallai wannan aikin ze ci ƙuɗi da yawa, kuma magana ta gaskiya wannan yarinya akwai tsari tare da ita na musamman, ba lallai bane ko wane irin aiki ya kamata sai dace”


Duk sun cika da mamaki, bama kamar Tahir daya kasa haƙura har sai da ya tambaya


“Saboda me?”


“Ban san dalili ba amman lallai akwai tsari mai ƙarfi a tare da ita, kasan ni bana aiki da munafurci kuma idan har abu baya yi zan fito fili na faɗa maka gaskiya”


Uzair ya sauke ajiyar zuciya


“Yanzu ba wata mafita kenan?”


Lailaya ƙasar yayi


“Bari mu bincika mu gani”


Sai ya koma bincike yana watsa wani farin miski a jikin ƙasar.
Zuwa can ya ɗago ya kalli Uzair yace


“Ta ƙi bayyana a binciken mu, sai dai an samu mafita, za a iya samun sa'arta ne kawai da asuba ko kuma lokacin da take haila”


Lokacin asuba lokacin ne mala'ikun da suke tsare bawa idan yayi addu'ar bachi suke tashi, Idan be yi saurin tashi yayi sallah ba, a lokacin har sheɗan yake samun sa'arsa ya saka masa kasala, da ƙuiyar yin sallah har sai rana ta fito.
Lokacin Haila kuma lokaci ne da ba ko wace mace ba ce take tsare yin addu'ah a wannaɓ lokacin ba, saboda ganin tana al'ada, bayan kuma duk kan addu'o'i an yarda mai haila ta karanta sallah ce kawai aka ɗauke mata, da ɗaukar cikakken ƙur'ane, da kuma ɗawafi.
Dan haka yan'uwa mu kiyaye addu'ah a wannan lokacin, kuma mu kiyaye Sallah asuba a cikin lokaci, tana da muhimmanci sosai.


Najeeb yace


“Amman kana ganin idan har anyi aikin zai ci kuwa?”


“Zai ci dan wannan aikin ba za a yi shi ace ba a ga nasara ba, sai dai ya zamo wanda ake son ya sama ɗin be same shi ba”


“Kamar ya?”


Tahir ya tambaya da sauri.


“Zamu yanka baƙin bunsuru guda biyu, da rago, sai a samo mana tunfafiya da kurciya da su zamuyi aikin, sai a rubutu wasu abubuwan da jinin bunsurun a watsa a riga ko zane da zata ɗaura sai a bata ta saka, inda har ba wanda ya bata ɗin nan bane yayi kuskure toh lallai babu tantama aikin zai kamata, amman fa a lokacin da take Haila ko kuma kamin sallah asuba”


Jafar ya riƙe baki


“Babbar magana, dole sai ta wannan hanyar kawai?”


“Ba dole sai ita ba, amman ita ce tafi ko wace sauƙi”


Tahir ya kalli Uzair


“Toh kai kana da mak maka wannan aikin ne?”


“Akwai wata ƙawarta ina jin kamar zata iya, amman what if ba ayi nasara ba?”




Tahir ya dafa shi.


“Ka yarda kawai za'ayi nasara, karka sawa kanka wannan”


Kai ya girgiza


“Ni dai ko na haƙura kawai na ƙyaleta”


Ganin yadda Uzair ya tsorata yasa Malamin shiga kwantar masa da hankalin


“Za'ayi nasara, karka damu, ka haɗani da wadda zata kai mata rigar na san yadda zan tsara mata komai”


Shiru Uzair be ce komai ba, shi dai sai tunani yake. Ganin hakan yasa Najeeb yace da Malamin


“Shikenan a fara aikin kawai, zan turo maka dubu ɗari a account ina tunanin zasu isa? Idan ma da wani abu sai ka kira a waya”


“Zasu isa inshallah, amman za a kawo rigar da taɓa sawa, dan da ita zamuyi aiki, kuma ina son ganin yarinyar”


“Ba matsala zuwa gobe duk yadda muka yi zaka ji ni”


Daga haka suka yi sallama, Najeeb yasa direba ya maida malamin. Sannan suka ya dawo falo suka shiga tattauna maganar.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12.html




🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*

Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


NOT EDITED ⚠️


*PAGE - 12*


HILAL POV.


Wanka yayi ya shirya cikin wata gizna, maroon color, sannan ya ɗauki hulla mai kyau ya saka, ya ɗauki agogon hannu ya saka ya feshe jikinshi da turare, sannan ya buɗe wardrobe ya ɗauko sababin kuɗi ya saka a aljihu, sannan ya dawo gaban madubi ya sake kallon kansa, ya tabbatar da kwaliyarsa ta fito, sannan ya ɗauki keys ɗinsa ya saka baƙaƙen takalmi, ya fice.


Ko da ya fito falo, Rashida na gaban dinning tana shirya musu dinner, su Ulfah zagayeta suna nuna mata assignment ɗinsu.
Kusa da ita ya ƙarasa yana leƙon abincin da take zubawa.


“Pyar a zubawa yara nasu nawa sai na dawo mu ci”


“Ina zaka je?”


“Ango zamu je rakawa ba zan daɗe ba”


Juyowa tayi ta kalleshi daga sama har ƙasa, yadda kyau nan nasa ya fito ya bata tsoro. Shi kuma sai yayi kamar be ga kallon da take masa ba sai ya kalli agogon hannunsa.


“Bari naje kar nayi latti, ni kawai suke jira”


Hannu yasa ya rufe idon Ulfah sannan yayi mata kiss a baki, sannan ya nufi ƙofa sai ƙanshi turare yake.


“Allah ya tsare min kai ni dai”


Ta faɗa lokacin da zai fice. Murmushi kawai yayi ya saka kai ya fice.
Motarsa ya shiga yayi horn mai gadi ya buɗe masa, ya hau ti-ti zuciyarsa cike da nishaɗi.
Cikin ƴan mintuna ya isa estate ɗin su Kalsoom. Numbers ɗin gidaje ya riƙa dubawa har ya kai ga number.


Dai-dai gate ɗin ya tsaya yayi horn yayi mai gadin gidan ya leƙo sannan ya buɗe masa, sannan ya shiga harabar gidan yayi parking. Sai ya fito ya nufo mai gadi ya bashi hannu suka gaisa sannan yace


“Dan Allah ko nan ne gidan Alhaji Faruk Kafinta?”


“Eh nan ne”


“Dan Allah mai gidan yana ciki?”


“Eh yana ciki”


“Dan Allah kayi min sallama da shi”


“To wa za'ace masa?”


“Ce masa Doctor Hilal ne”


Da sauri mai gadin ya nufi cikin gidan. Doctor Hilal kuma ya dawo gurin motarsa ya tsaya yana ƙarema gidan kallo.
Hilal ya kusan minti goma tsaye a gurin sannan Abban Kalsoom ya fito, yana ganin Doctor Hilal ya washe baki.


“Maraba da bokan turai,

Please Login or Register in order to submit comment