Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gobe za mu haɗu, zaka gan ni a fuska nima na gan ka a fuska”


“I can't wait, me kike so a shirya miki?”


“Na yi waya da Mom nawa zata shirya min komai”


“Ya yi kyau lallai Mom tana ji da ƴar nan ta ta”


“Ai dole ta ji da ni, ni kaɗai gare ta, ko ƙawaye na ma Mom son su take balle kuma ni”


“Wow kai lallai ko zata so miji ki ma sosai”


“Sosai ma”


“Gaskiya na yi sa'ah”


“Sa'ah?”


“Eh mana, ai kin san dole Mom ta so ni sosai, to da ni mijin Nably ne right?”


“Uhnn. Yeah”


“Ko dai ban kwanta miki ba ne?”


“Idan baka kwanta min ba, ai ba zan tsaya ina baka lokaci na ba, ni fa ban ma yarda da rayuwar social media ba amman kai lokaci ɗaya ka shiga rai na sosai wallahi”


“Haka nake so kin san ni da gaske na ke yi wallahi auren ki zan yi matuƙar kika amince min”


“Wannan maganar ya kamata sai idan mun haɗu tukuna mu yi ta”


“To na bari gimbiyata”


“Zan duba abu sai na kira ka”


“Okay i love you”


“Thank you”


Daga haka ta katse kiran. Shi kuma ya mannawa wayar kiss zuciyarsa cike da farinciki dan har ga Allah yana ƙaunar Nabila, kuma ita yake fata ta maza matarsa ta biyu.
Wani tsiririn tsaki ya ja lokacin daya isa bakin gate ɗin gidansa, cox he hate one thing buɗe gate, gani yake a yanzu ya kamata ace buɗe masa ake, shi gaba ɗaya gidan ma ya ishe shi, plan ɗinsa a yanzu na samun sabon gida ne mai rai da lafiya, gidan da duk wanda ya kallesa sai yayi magana ba wannan ƙonanne ba.
Sai da ya fito ya buɗewa kansa gate ya shiga da Motar sannan ya dawo ya rufe gate ɗin. Kusa da BQ ya faka motarsa, ya faka motarsa ya buɗe ya fito, daga shigarsa cikin ɗakunan da suke BQ ɗin sai ya fara ya ƙuna fuska, like yana ƙyama, gurin duk ya yi datti kamar be taɓa zama a gurin ba. Da shigarsa ɗakin first thing da ya fara yi ɗauko murhun gawaye da ragowar gawai ɗin da Namra ta bari, ya zuba masa kanazir ɗin da Namra take kunna wuta da shi ya saka kofinta na roba na ƙyasta ashana, nan ta ke wutar ta kama, kamar an saka mata hetur.
Ƙamin tukunyarta ya ɗauka ya ɗauraye ya zuba mata ruwa, ya ɗora saman wutar sannan ya shiga ciki ya ɗauki tsintsina ya share ɗakin tsab kamar mace, ya ruba zuwa yayi mopping, sannan ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul, ya zo ya zube ruwan a roba ya sirka da ruwan sanyi, ya kai ɗaki.


Sai da ya tura kofar ɗakin, sannan ya cire tawul ɗin jikinsa ya zauna cikin robar, kamar wani ƙaramin yaro. Ƙasansa yake gasawa, dan har yanzu zafi yake masa duk da ya sha magani, kuma yana kan sha, amman gurin na masa zafi musamman idan zai duƙa ko kuma zai yi bayan gida.
Sai dai Hajiya ta faɗa masa dan yana sabon shiga ne da ya saba komai ba zai ji ba.


Ya samu kusan minti talatin a cikin ruwa, sannan ya tashi ya ɗaura tawul ɗin ya ɗauki ruwan ya zubar a can waje. Be da mu da ƙorar da tufafinsa na ɗazu suka yi ba, ya ɗauke su a haka ya saka, ya kwanta saman katifa, yana danna wayarsa.
Number Mama ya saka, duk da yana da ita a contact ɗinsa be tsaya nema ba sai kawai ya saka ya danna mata kira.
Ta daɗe tana ringing kamin ta ɗauka tana masa complain


“Ai na ɗauka na manta da ni, ka sake wata uwar”


“Hahha Mama kenan ni na isa duk duniyar nan ai bana da uwa kamar ki”


“Amman Ibrahim ace ko ɗan kiran nan na waya babu, babu aike, babu komai, daga na yi jinyarka ka warke shikenan Namratu ta karɓe min kai?”


“Wallahi Mama kina nan cikin rai na, kawai dai akwai irin da na ke ne, akwai kuɗin da nake jira ina son da na zo zan siya miki gida na nema miki mai aiki, na saka miki komai ba za ki nema ba”


“Ibrahim da gaske?”


“Wallahi Mama”


“Wane irin kuɗi ne wannan? Karka ka jefa kan ka a halaka, garin neman gira a rasa ido, zamani ya lalace tsafi ya yi yawa”


Dariya ya yi dan yasan abunda Mama take tsoro, kamar kar ace tsafi ne a bada ita.


“Ba tsafi na ke ba, kuma ko tsafi na ke ai ba zan bada ke ba, wannan matar data ɗauke ni aiki ce take ba ni kuɗi kuma kullum idan na mata ciniki a shagonta riba uku ake kasawa ita da biyu ni da ɗaya”


“Wane irin sana'ah ne haka?”


“Wayoyi ne mu ke sidawa, da zinari”


“Hahaha Mashallah, ka ga abun Allah ko? Sannu-sannu sai ka fi haka ma, ai ina nan ina maka addu'ah indai kuɗi ne suna nan zuwa”


“A cigaba da yi mana addu'ar nan ai ita cw ke bin mu. Nan da wata ɗaya zan zo gurin ki”


“To Allah ya yarda, ya dafa maka, ɗan Albarka, irin alheri”


Dariya ya yi kana ya ɗora da.


“Zan aiko miki kuɗi ta hanyar Yusufa, zai kawo miki dubu dari da hansi ki riƙe kamin na zo”


“Kai Alhamdulillah Ibrahim Allah ya biya ka yau ɗa na ne yake ba ni wannan kuɗi Allahu akbar...”


Sai kawai ta sa kuka. Shi kuma ya kashe wayar yana dariya, da ganin kuɗin a gare shi yanzu ai ba wani abun ba ne, he past that level, manyan su ma yake hange, he's feeling so high.


KALSOOM POV.


Life goes on yadda take tsammanin rayuwa ba haka ta zo mata ba,tana iya ƙoƙarinta wajen ganin ta kwamtar da hankalinta, 5ana koyar yadda zata yi rayuwa babu abokin rayuwarta, but she can't duk abunda take tunanin sauƙi ne a gareta, sai ta ga ba haka ba.
Duk lokacin da tayi unƙurin danne abunda yake zuciyarta, ta manta da komai, sai ta kasa. Sai yanzu take gane aure rahama ne dan har ta manta da ɗan zaman da tayi na budurci a gidan, sai take ganin kamar yanzu ne ta ke koyon komai, ga maganganun mutane su na ta kai kawo a kunenta, wai ta kashe aurenta ta dawo gida, some people be like daman can irin wayayun ƴan bokon nan basa zaman aure, wasu kuma wai ta kashe ɗan kishiyarta mijin ya sake ta, maganganu dai kala-kala har da na fitar hankali.


Abincin da ta ɗibo ta saka a gaba tana kallo, ta san dai ba iya ci zata yi ba, dan ba ta jin cin komai ga kuma yunwa tana ji, kusan kullum haka take wuni, ta fi son abu mai ruwa sai kuma ɗan furau-furau, wannan abincin ma Momi ce ta cilasta mata ɗibowa wai ko zata iya ci, amman ta kasa.


Ɗaukar abincin ta yi ta nufi falo da shi, da zimmar kai wa kitchen.


“Ba ki ci abincin nan ba ko?”


Cewar Momi da ke zaune saman kujera.


“Wallahi Momi ba na zan iya ci ba”


“Sai yaushe za ki cirewa kan ki damuwar nan ne Ummu?”


“Momi dole na damu, ki duba ko abunda abunda mutanen unguwar nan suke cewa, wai na kore uwar gidana na kashe ɗan ta, ni wallahi da na san haka auren mai mata yake da ban aureshi ba, ni da ma na san haka rayuwar auren ta ke tun farko da ban yi ba”


Ta ƙarasa zancen da kuka. Ajiyar zuciyar Momi ta sauke.


“Na san ba abunda mutane suke cewa ba ne ya fi damun ki, hukuncin da mahaifin ki ya yanke ne ya hana ki sakewa, ina son ki san be yi hakan dan ya cutar da ke ba, sai dan nema miki yanci, ba wai dan ya shiga tsakanin ki da Hilal ba”


Hawayen idonta ta share, ta aje plate ta zauna.


“Ba wai rai na ya ɓace ba ne da hukuncin Dady ,kawai abun yana damu na ne, duk duk yaushe na yi auren nan yanzu ace har na dawo gida, a can gidan auren ma ba wani daɗi na ji ba, matar nan ta hana ni sakewa, ta bi ta fitine ni bayan fitar ta kuma kishi ya koma tsakanin ni da ƴarta, wallahi yaron nan ban san lokacin da ƴa ci guba ba, amman sun ce ni ce na kashe shi, da wanne zan ji? Ga shi mahaifiyarsa ta sa ya sake ni na dawo gida kuma mutanen unguwa sun ɗasa na su gulmar, dole na yi damuwa”


Da kuka ta ƙarasa maganar tana rufe fuskarta. Momy taja wani dogon numfashi ta sauke tana kallon ƴarta cike da damuwa.


“Allah zai saka miki ai zalumci baya ɗorewa, gaskiya zata bayyana sakamakin ki zai fito, kawai ki cigaba da addu'ah kina faɗawa Allah buƙatar ki, zai yaye miki komai”


Kuka ta yi sosai, sannan t tashi ta nufi kitchen ta aje plate ɗin ta fito.


“Ko za ki je gidansu gidan Salma ki ɗan yi fira ko zaki rage damuwa”


Da to kawai ta amsa ma Momi ta nufi bedroom ɗin ta, fuskarta ta fara wankewa sannan ta ɗauki hijabi ta saka ta ɗauki jakarta, ta fito.


“Na tafi”


Ta faɗa murya can ciki.


“Sai kin dawo ina a gaishe ta”


A hankali ta fito daga gidan, tana.fitowa gate ta yi sa'ar samun Napep kasanceqar an sauke wata ne gidan da ke kusa d na su, tara kawai ta yi ta shiga tana faɗa masa ind zai kai ta.

“Sauke ni a nan”


Ta faɗa tun kamin ya ƙaraso kusa da gidan Salma. Naira ɗari ta miƙa mas sannan ta fita daga napep ɗin ta ƙars da ƙafa.

Tun da ta hango gate ɗin buɗe ta fahimci Salma zata fita ne.


A hankali take tafiya har ta ƙarasa harabar gidan. Lokacin da ta isa ƙofar falon si t ki hannu zta buɗe sai ga Mijin Salma ta buɗe ya fito. Ja ta yi da baya tana ƙirƙiro murmushi, tare da gaishe shi, shi kuma ya amsa mata yana gyara hular kansa.


“Lafiya ƙalau Kalsoom ce a gidan na mu!”


“Eh wallahi yau na ce bari na leƙo Salma ne”


“Ayyah gashi bata gida Wallahi ta je suna”


Juyawa ta yi tana faɗin


“Okay idan ta zo a gaishe ta”


“Wuce wa za ki yi?”


“Eh”


“Bari na sauke ki mana, nima fita zan yi”


“A'a zan hau Napep”


“Haba di Kalsoom sai ka ce baƙuwa”


Yayi saurin ƙarasawa gurin motar ya buɗr ya shiga yayi mata key, sannan ya buɗe mata front seat.


“Bismillah”


Bata kawo komai a ranta ba, ta shigaotar tare da mai da ganbun ta rufe.


Tun da suka hau titi bw ce da ita komai ba, ita kuma t tattara duka hankalint tmaid gurin titin. Can ya kai hannu ya kunn fm, sai ya ɗan kalleta kaɗan.


“Kalsoom na ji abunda ya faru kuma sam ban jidaɗi ba, amman ki bar wa Allah komai xai fito miki da haƙƙin ki, ai duk wanda ya san wacece ke ba xai yarda kin aikata ba, wallahi tun da na ji labarin kika ban tausayi sosai, inshallah zaki samu wani na ƙwarai”


“Ai be yarda na aikata ba, laifin mahaifiyarsa ne ita ta saka sai ya sake ni”


Wani guntun tsaki yaja.


“Shi ma dai da laifinsa, ai ba a bin umarnin iyaye a saɓawa Mahalicci, dan wannan saɓawa Allah ne, ni da zaki bi shawara ta da kin bar shi kin fita harkarsa ko da ya dawo, duk da n san kina son sa sosai, amman fa kin san mu maza ba a nuna mana so”


Ya ƙarasa maganar tare da parking a bakin gate ɗin gidan su. Buɗe motar ta yi ta fita tana faɗin


“Na gode”


Ba ta jira ya amsa mata ba, bata kuma waigo ba, shi kuma be bar ƙofar gidan ba sai da ya ga ta shige sannan ya kaɗa motarsa yayi gaba.




ABDOOL POV.


Lemun d ke hannunsa ya aje yana murmushi


“Amman dai Ummi idan ban kira ba ai kamata ki kirana ni kiji ko lafiya”


“Ai na san lafiya, da ba zaka yi shiru haka nan ba, kasa muka shirya maka abinci amman baka zo ba”


“Amman ban ce amin komai ba, indi ba neman a ɗora min laifi ba”


“Yayi kyau, gobe kaga mai sake maka, faɗa min me ya hana ka dawowa jiya?”


“Kawai ina son ƙara ganin garin ne, kin san na daɗe rabona da Kaduna”


“Yanzu yaushe zaka dawo?”


Ya ɗan sosa kansa


“Uhhhh Maybe laraba”


“Allah ya kai mu”


“Amin thank you Ummi”


Ta katse kiran shi kuma ya sauke wayar cike da ƙaunar mhaifiyarsa.
Juyawa yayi ya kalli Sadauki.


“Je ka shigo d shi”


Da sauri Sadauki ya tashi ya fita, Abdool kuma ya ƙarasa gurin window falon yana kallon wani ɓangare na gidan.
Tare suka shigo da Sadauki, bakinsa ƙumshe da sallama. Juyowa Abdool yayi fuskarsa ɗauke d murmushi ya nunawa Mustafa gurin zama. Ba musu Mustaf ya zauna yana miƙa masa gaisuwar girmamawa.


“Lafiya Ƙalau sannu, ya Sunan ka ma?”


“Mustafa”


“Yeah, ka san ni ne?”


“A'a Sai dai na ga fuskar sani”


“Ina son zan baka wanki ne da guga ance kana yi da kyau”


“Ƙwarai ko ai sana'a ta ce”


“A ina kake da zama?”


“Nan unguwar malamai”


Abdool yayi wani abu da kai kamar da gaske he know him.


“Yeah na tuna kai na na kusa da gidan su Lamido ko?”


Mustafa ya washe ba ki jin an ambaci sunan abokinsa.


“Ashe kasan lamido”


“Sosai ɗan'uwan mu ne, ai kwana ki ma wata ƙanwata a gidan ta sauka, yanzu haka wata ma tana nan”


Abdool ya faɗa yana kallon Saɗauki.




“Je ka haɗo masa kayan wanki”


Sai kuma ya mai da hankalinsa gurin Mustafa.


“Ance min yaji ciwo ma ko?”


“Eh Wallahi, wani neya kaɗe shi, ni da yake bana nan sai da y kira ni na ke ji ma, Ai Allah ma ya tsare abun ya zo da sauƙi”


“Idan na samu dama zan je na duba shi”


“Aiko masu kuɗi fitar ku wuya ta ke muku”


Abdool ya ɗauki remote ya canja channel yana hamma kamar gaske.


“Mu ai har zama gidan mu na yi, baka ga baƙuwar fuska ba?”


Mustafa yayi shiru dan ya gano kamar yana bincikensa ne.


“Ina kayan su ke ne?”


Abdool yayi masa wani kallo.


“Za'a kawo”


Sai ga Sadauki ya fito da tufafin da basu fi kala huɗu ba, ya miƙawa Mustafa. Shi kuma yana karɓa y miƙe tsaye. Sai Abdool ya zaro sabin kuɗi a aljuhunsa ya miƙa masa.


“Gashi ko, a wanke da wuri”


Da mamaki Mustafa ya karɓa ganin kuɗi haka da yawa.


“Na gode Allah yasa albarka, gobe zan kawo maka su”


Murmushi kawai Abdool yayi masa as respond, ya bishi da kallo ya har ya fice.


‘Duk wannan ba zai yi ba, kawai naje na samu yarinyar nan na yi magana da ita kawai shi ya fi’


‘Idan kuma ta ƙi ta saurare ni fa?’


Ya ɗaga kafaɗunsa yana cigaba da zancen zuci.


‘Sai na ƙyale ta, ta yi ma kanta’


Miƙewa yayi tsaye ya nufi bedroom ɗinsa.




RASHIDA POV.






HILAL POV.


Yana tsaye jikin motarsa, yana kallon takunta har ta ƙarasa kusa da shi.


“Assalamu alaikum”


Ya faɗa cike da tsananin kunya da tsantsandar da kai.


“Wa'alaikissalam, Teema ko?”


Ta ƙara yin ƙasa da kanta


“Haka ne ina wuni?”


“Lafiya ƙalau ya gida?”


“Lafiya ƙalau”


“Mashallah, sunana Hilal kamar yadda aka faɗa miki Hajiyata ta ce min ta miki bayanin komai, zan zo mu gaisa da ke ne”


“Haka ne, ni kuma sunana Fatima Abdullahi, a nan nake zama ina ƙarƙashin iyayena”


“Mashallah haka yayi kyau”


Ya faɗa 6ana kallom yadda ta zuba hijabi har ƙasa gwanin sha'awa.


“Ba zan tsayar da ke ba, daman na zo ne kawai mu gaisa duk wani labari kamata yayi sai idan mun sake haɗuwa ko”


Murmushin jin kunya tayi ta ƙara ƙasa da kanta.


“A gaida min Hajiya”


“Zata ji”


Ya buɗe motar ya ɗauko ƴar siyayyar da yayi mata ya miƙa mata.


“Ga wannan”


Sai a lokacin ta ɗaga kai ta kalleshi, sai ta yi saurin girgiza masa kai.


“A'a na gode”


Bata tsaya jiran abunda zai ce ba ta nufi cikin gidansu da sauri dan kar ta karɓi kayan. Shi dai da kallo ya bita fuskarsa ba yabo ba fallasa har ta shige sannan ya ƙarasa gaban ƙofar ya aje mata ya juya.
Cikin wani yanayi ya shiga motarsa ya bar gidan. Har ya isa gidan Hajiyarsa be wani sake jiki sosai ba, shi kansa be san dalili ba, yana jinsa dai kamar cikin wani sabon yanayi.


Da far'ah Hajiya ta tarbesa dan tasan inda ya fito tun da ita ta haɗa masa abunda zai kai mata ma. Bata bari sun yi maganar a falo ba, har sai da ta shiga ɗakinta shi kuma yana biye da ita, bayan ta zauna, ya zauna y soma labarta mata yadda suka yi, farinciki duk ya cika Hajiya.


“Ai yarinyar akwai kirki ga mutunci, ina fatar dai ta maka”


“Ba laifi, umarni nake bi ai”


“Hilal bana son kana abu kamar ina tirsasa ka, ni sam....”


Shigowar Dadyn Hilal ne yasa ta maƙale maganar bata fito ba.


“Amman bn taɓa sanin baki da hankali ba, sai yau, ki kashe mas aure ki sashi neman wani aure? Bayan kin san yana son matarsa? Dan me zaki shiga tsakaninsu? Idan ma aure kike so ai sai kice ya ƙara aure amman ba sai ya saki matarsa ba, ni duk abunda ake ban sani ba, ban ɗauka abun har ya kai ga saki ba sai ɗazu”


Miƙewa tayi tsaye tana kallon Alhaji da ransa ya gama.ɓaci.


“Haba Alhaji, baka ga abunda yarinyar nan ta aikata ba ne? Zata iya kashe yaran nan, shi kansa ma”


“Shi be fiki sanin zafin yaransa ba? Be fiki damuwa da kansa ba? Kar wannan maganar ta sake fitowa bakin ki, idan aure kike so ya ƙara wannan daban amman babu yadda zaki shiga tsakanin shi da matarsa”


Hilal dai be ce Uffan ba har sai da Alhaju ya kallesa ya ce


“Tashi muje gidan su”


Miƙewa yayi tsaye ya bi bayan Alhaji da ya kaɓa rigarsa ya wuce, Hajiya ta saki baki tana kallon ikon Allah.


“Wato maganin yanzu har da ubansa ta yi ma, tayi min ta ga ni be kama ni sai ta koma ga ubansa, to wallahi ni ba ki isa ba, kurwata kur kashede uku lahaula bakwai”


Cikin fushi ta yi furucin tana jin tsanar Kalsoom a ranta.




MARDIYA POV.


Fisgice ta farka tana faɗin


“Innalillahi”


Mafarkin wutar nan da ke zo mata jifa jifa yau ma ta sake yinsa, bama kamar yanzu da har bayanta zafin gaske yake mata kamar ta tsaya kusa da wuta. Sai da ta karewa ɗakin kallo sannan hankalinta ya kwanta ganin inda take.


“Allah ka min maganin wannan masifar, ko minene yake bi na Allah ka kawar mon da shi, idan ma wata jifar ce aka min Allah ka mayar da ita ga wanda yayi ta”


Har da kukanta take wannan maganar dan har ga Allah wannan mafarkin wutar da take ya isheta, kuma ya hanata sukuni.
Kasa komawa bachi ta yi daman duk ranar da ta yi irin wannan mafarkin bata iya komawa bachi, idonta biyu har aka kira sallah asuba, amaimakon ta bari sai ta yi sallah sannan ta kwanta sai kawai ta buge da bachinta, ba ita ta farka ba sai sha ɗaya na safe, ƙirƙiri ta yi sallah azuba babu ko kunya, ko da yake abun ya samo asali ne daga gurin mahaifiyarta da bata tsawata mata.


Tana sallame sallar wayar Asim ta shigo mata, da sauri ta ɗauka tana kwabar da tasbihin da take.


“Hello”


“Good morning Mardiya ya kika tashi?”


“Lafiya ƙalau na yi missing ɗin ka”


“Nima Haka har na so na ɗauke ke ki muje yawo dan akwai maganar da nake son mu yi mai muhimmanci”


“Wace magana ce?”


“A'a ba za tayi a waya ba, kamata yayi sai mun zauna”


“Okay yaushe zaka shigo?”


“Idan na samu time zan kira ki, sai na zo na ɗauke ki”


“Okay ina jiran ka”


Daga haka ya kashe wayarsa, ita kuma ta miƙe tsaye cike da jindaɗi ta nufi waje dan ɗibar neman mai siyo mata indomie.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *69*


Be ji zai iya kwana a yau ba,ba tare da yaje gurin Namra ba, daman yasan duk daɗin bakin da yake yi ma Ummi ba wani barinsa zata yi ya daɗe ba, kuma idan har ta bar shi Mai Martaba ba zai bar shi ba, and what's on his mind nowa ya ji labarin yarinyar duk da bashi da tabbacin ko zata yarda ta saurareshi ma.


Miƙewa yayi tsaye yana duba shaddar da ke jikinsa.


“I really need to do this, ko zan samu peace of mind”


Closet ɗinsa ya buɗe ya fiɗo wata kafirar shadda golden color, ya buɗe ɗayar wardrobe ya ɗauko hular ƙobe ya aje saman shaddar, sannan ya shiga Bathroom ya watsa ruwa.
Bayan ya tsane jikinsa da tawul ya shafa mai, sannan ya saka body spray, ya saka short da white singlet, sannan ya shafa wani turare, ya ɗauki shaddar ya saka.
Wani mai ya ɗauka ya shafa ma fuskarsa, sannan ɗora da turare. Ya ɗan soma jin babu daɗi lokacin daya tuna gidansu Lamido zai je, yasan he has zero reasons to hate Lamido, but he still hate him.


“Maybe he's bad person”


Ya faɗa yana murza wani turaren a wuyansa, kamin ya ɗauki hular ya saka a kansa. Agogon hannunsa ya kalla, yaga tara da kwata, hakan yasa shi ɗan hanzarin ɗaukar wayarsa ya fice.
Sadauki na ganinsa ya tashi, sai Abdool ya ɗaga masa hannu.


“Ni kaɗai zan je”


“Allah ya tsare ya kiyaye hanya, Allah ya kare ka daga dukan ni abun ƙi, Allah yaja kwanan ka”


Abdool be kula shi ba, balle ya amsa addu'ar da yake masa, sai da ya kawo gurin motocin da suke harabar gidan sannan ya ƙwalama Sadauki kira, sai ga shi ya fito da sauri.


“Key wacan motar na ke so”


Ya nuna masa wata baƙar mota mai baƙin gilashi, wanda ke aje can gefe. Da Sauri Sadauki ya koma ciki ya ɗauko masa key ɗin motar ya miƙa masa, sai da ya sake duba agogon hannunsa sannan ya nufi motar ya shiga, gabansa sai faɗuwa yake.


Sai da ya hau titi, sannan ya ciro wayarsa ya dannawa Ummi kira. Sai da yayi mata one missed call sannan a na biyu ta ɗauka.


“Assalamu alaikum”


“Wa'alaikissalam. Ummi ki min addu'ah zanje wani guri neman abu a yanzu, kuma babu tabbas zan yi nasara, idan kuma har na ƙyale abun hankali ba zai kwanta ba”


“Abdool mi zaka aikata? Thought baka aiki yanzu ka ce sun baka hutu?”


“Eh ba aikin office ba ne, wannan aikin nawa ne na sa kai”


“Abdallah karka aikata abunda zai sa rayuwarka cikin haɗari, ka dawo gida gobe”


“O my god”


Ya dafa kansa.


“Allah Ummi ba wani abun ba ne, kawai i need your prayers”


“Ka dawo gida gobe na faɗa maka, kasan dai kullum rayuwarka tana cikin haɗari ko? Karka kuskura ka wuce gobe, umarni na ke baka”


Ta kashe wayarta cike da fushi, dan ta san idan ba haka ta masa ba, ba zai ji ba, gashi duk ya tsorata ta, da wannan maganar na shi daman ita ba son take yana tafiya nesa da ita ba.
Iskar bakinsa ya busar yana cigaba da tuƙinsa a hankali.


“Daga neman sa'ah sai kuma abu ya zama ɗan zane, ban san salon da ya kai ni faɗa mata ba, Allah ka taimake ni”


Unguwar bata da kyau sosai, amman haka ya riƙa kunno kai cikinta yana kallon ƙananan gidajen da suke unguwar har ya isa bakin ƙofar gidan. Wani tunanin ne ya zo masa, sai kawai ya ƙara gaban da gida sannan ya faka motar, ya buɗe ya fito.


Ya samu minti salati tsaye a gurin sannan ya kira wani almajiri da ke bara ya nuna masa gidan su Lamido.


“Je can gidan ka ce ana sallama da baƙuwa”


Sai da almajirin ya kama hanya, sai kuma Abdool ya kira shi ya dawo.


“Ba haka zaka ce ba, ka ce Abdallahi daga Katsina ya na sallama da Namra, Namra ko? Yes Namra zaka ce”


“To”


Almajirin ya nufi gidan da sauri. Faɗuwan gabansa ya ƙaru lokacin daya fara tunanin irin amsar da almajirin zai dawo masa da ita.








NAMRA POV.


Ba laifi yau ta dan sake bisa da jiya, ko dan yau sun ɗan tausasa ta ne kuma ta wuni a tsakar gidan ansha fira da ita. Sai dai bata janye maganar tafiyarta ba, ta yarda ta bari har sai nan gaba, idan ta ƙara jin sauƙi abubuwa sun ɗan dai-dai.


Yau ba iya Maltina da madara kawai Lamido ya bada aka siyo mata ba, har da gasasshen nama, sai dai bata ci ba kasancewar komai bata jindaɗinsa a yanzu.
Sai da aka yi

Please Login or Register in order to submit comment