Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗakinsu.


“Daddy ƙyale ta Mama tace ta ji sauƙi fa”


Ulfah ta faɗa tana lanƙwamo wuyan Kalsoom da Hilal. Ɗan murmushi Kalsoom tayi tana riƙa hannunta.


“Na sani ta ji haushi ne ba a kai ta ta ga Mama ba”


Hilal ya miƙe tsaye zuciyarsa na raya masa akwai abunda Rashida tacewa ƴarsa.


“Bari naje gurin Hajiya tace tana nema na”


“Okay Allah ya kiyaye bari nayi magana da Ezzah”


“No karki yi magana da ita yanzu, bari sai da safe”


“Okay Allah ya tsare”


“Daddy Allah ya tsare”


Ulfah ta faɗa tana tsalle.


“Amin Sweetheart sai na dawo”


Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya fice. Cikin ƴan mintuna ya isa gidan Hajiyarsa, ba tare da fargabar komai ba ya fito mota ya shiga cikin gidan.
Yana shiga falon ƙannensa da ƴaƴan ƴan'uwansa da suke gidan suka soma gaidashi suna masa sannu da zuwa, sai da ya gama gaisawa da su sannan ya nufi ɗakin Hajiya.


Da sallama ya shiga, ta amsa masa ba tare da ta kalleshi ba, sai sarƙoƙin dake gabanta take gyarawa, har ya zauna ƙasan Carpet yana ɗan kallon yanayinta.


“Hajiya ga ni Allah yasa ba laifi na yi ba”


“Au ashe ka san kayi laifi? Yanzu abun da kayi ma yarinyar nan dai-dai ne? Ban samu naje ganinta ba sai da yamman nan ina zuwa suka ce min wai ka sake ta, duk kunya ya kamani”


Ya ɗan shafa kansa.


“Ayyah Hajiya sorry ban nemi shawarar ki ba, nima a kai tsaye sakin ya zo min, kuma bana da wata mafita sai ta sakin ne”


“Amman fisabillillahi baka tashi sakinta ba sai da tayi ɓari? Kai baka ma tsoron ace Kalsoom ce? Na san kana haƙuri da ita, dan kai ne kaɗai zaka iya ɗaukar abunda Rashida take maka, amman ai tuni ya kamata ka yi haka ba yanzu ba”


“Hajiya idan na sake ta a lokacin da Kalsoom bata nan wa zai kula da yaran? Kuma lokacin ba zan iya sakin ta ba saboda bata min komai ba”


“To me ta maka yanzu? Tun tun tun baka gano illarta ba sai yanzu? Hilal bana son ka zama cikin irin mutanen fa”


Yayi ƙasa da muryarsa yana son faɗa mata gaskiyar lamari.


“Hajiya ba zan iya ɓoye miki ba, Rashida tana da Hiv kuma ni da Kalsoom da ƴaƴana duka ba mu da shi sai ita, kuma ta hanyar sex ta samr shi”


Wani abu Hajiya tayi da hannu irin na ƙyama da tsoro idan sun zo ma mutum a lokaci ɗaya.


“Kana nufin Rashida tana bin maza a waje kenan?”


“Ba wai ina nufi bane, haka ɗin ne, tun da ga alamu ya nuna kuma ta tura ma likitan da na ba jininta ya auna kuɗi dan ya ɓoye yace ba haka ba ne”


“Idan ko har haka ne, ba kayi laifi ba Hilal dan irin wannan matar babu mai son ta zamo uwar ƴaƴansa, ni dama can yarinyar nan bata min, ai ƙara ma daka sake ta taje can ta ƙarata ita da uban nata daya tsaya mata”


“Amman Hajiya dan Allah karki faɗawa kowa saboda rayuwar ƴarana, zasu iya shiga wani hali kuma duk wanda ya ji zai riƙa mana wani kallo ne”


“Haba Hilal ai wannan sirri ne tsakanin ɗa da uwa, babu wanda zai ji har abada, amman me zaka faɗawa iyayenta ne?”


“Zam ce ta zubar min da ciki ne shiyasa na sake ta, ai nasan ba zata taɓa faɗa musu gaskiya ba”


“Allah ya kyauta, Mahaifin ka ma be sani ba, dan ban faɗa masa ba, nima haka zance masa. Ai Allah ba azzalumin kowa bane shiyasa asirinta ya tono tun wuri da sai duk ta laƙa muku shi sannan a gano”


“Kwata-kwata matar nan ta fita rai na wallahi, babu abunda bana mata, babu irin haƙurin da bana yi da ita akan zamantakewar mu, akan me zata je ta bi wani a waje? Idan akwai abunda nake mata wanda bata so ko kuma be gamsar da ita ba ai sai ta faɗa min ai tattauna aƙe so zamantakewar aure da fahimtar juna, dan me zata watsar da yaranta taje ta aikata wannan mummunan abu? Allah kaɗai ya san iya tsawon lokacin data ɗauka tana aikatawa, nayi nadamar zama da ita Hajiya.


Da nasan haka zata zama da tun farko ban aureta ba, kuma ban sa laifin kowa ba kamar na mahaifinta dan shine ya tsaya kai da fata akan dole sai ta yi aiki, saboda kawai baya son aurna da ita, yanzu ai sai ya aura mata wanda yake so ”


“Ƙaddarori ne idan Allah ya kawo sai haƙuri, Allah dai ya ƙara tsarewa”


“Amin ni zan wuce”


“To Allah ya tashe mu lafiya, akwai waina a kula idan zaka ci”


“A'a bana son komai yau sai da safe”


Daga haka ya fice, Hajiya na kallonsa cike da tausayawa.
Koda ya koma gida Ulfah da Rafiq sun yi bachi, Kalsoom ce kawai a falo, ta ƙurawa tv ido, duk da hankalinta ba nan yake ba.
Shigowarsa yasa ta ɗago kai ta kalleshi fuskarta da yanayin damuwa.


“Har ka dawo?”


“Eh ke kaɗai ce a falon?”


“Eh me Hajiya tace maka?”


“Tace idan na zo na cire miki kunne guda na kai mata”


Ya faɗa yana jan kunnenta har sai da tayi ƴar ƙara


“Ouuchhh nima tace na kai mata hancin ka”


Taja masa hanci ta tashi da sauri daga gurin. Ƙyalƙyalewa yayi da dariya, yana kallon kunkurunta.


“Kalsoom zo nan”


“No no no”


“Please?”


“No no”


Ta nufi ɗakinta da sauri, sai ya bita yana dariya.


******
Washe gari da wuri Kalsoom ta tashi kamar yada ta saba, sai da ta ciro musu uniform ta ɗora musu saman kujera sannan ta nufi kitchen ta haɗa musu breakfast, har ta gama haɗa breakfast ɗin tunanin Rashida take, tana ganin kamar Hilal be kyauta ba idan be barta taje ta ganta ba.


Sai da ta zuba musu abincin a kula sannan ta shiga ɗakinsu ta tashe su, Ulfah ta fara tayarwa t miƙar da ita tsaye tana girgizata, sannan ta shiga tashin Ezzah


“Ezzah tashi ku yi shirin makaranta na gama muku abinci”


“Ki ƙyale ni ni ba zan je ba!”


Ta faɗa a tsawace tana jan bargota ta ƙara rufa, Kalsoom bata sake taɓa ta sai kawai ta shiga da Ulfah ta haɗa mata ruwan wanka ta fito ta nufi ɗakin Doc.
Zaune ta tararda shi yana karanta saƙon da Rashida ta aiko masa. Daga bakin ƙofa Kalsoom ta tsaya tace


“Doc Ezzah tana ta fushi har yanzu”


Ya ɗago ya kalleta


“Kamar ya me tace?”


“Wai ba zata je makaranta ba”


“What! Ba zata je makaranta ba as how? I hate nonsense”


Ya aje wayar dake hannunsa ya nufi ɗakin nasu, Kalsoom na biye da su a baya, sai dai bata ƙarasa shiga ɗakin ba, ta tsaya daga bakin ƙofa.


Yana shiga ya shiga tashinta, tana jin muryarsa sai ta buɗe bargo ta buɗe ido, fuska a takure tana kallonsa.


“Tashi ki yi shirin makaranta, kika ce ba zaki makaranta ba?”


“Zan je ni bana son tana tashi na ne”


“Saboda?”


“Ni bana son ta Ammyn ta faɗa min itace ta koreta baka son Ammyn Anty kake so kuma ba zaka sake kai mu inda take ba sai dai mu zauna da Anty kuma ba zata sake zuwa nan gidan ba, ni bana son ta Daddy i hate her”


Buge mata baki Hilal yayi, ya katsa nata tsawa.


“Kar na sake jin bakin ki ya furta irin wannan kalamin, tashi kije ki shirya zuwa makaranta ko na zane ki yanzu nan”


Da sauri ta tashi ta shige bathroom tana kuka. Kalsoom dake tsaye jikin ƙofa tayi saurin barin gurin, ta nufi ɗakinta.
A gaban madubi ta tsaya tana hawaye, zuciyarta sai bugawa take,motsin shigowar Doc ne yasa ta saurin juyo ta kalleshi


“Doc ka rabu da Rashida ne?”


Ya saka hannyensa aljihu yana ɗaga mata kai alamar eh.


“Me yasa?”


“Hakan shi yafi dacewa”


“Dan Allah ka dawo da ita ƴaranta suna da buƙatar ta”


Ta faɗa da muryar kuka hawaye na mata zuba. Matsowa yayi kusa da ita ya ɗafa kafaɗunta yana magana a hankali.


“Basa buƙatar ta matuƙar suna tare da ke, i trust you zaki basu tarbiyan daya kamata, kuma zaki kula min da su, ba zan taɓa maida Rashida ba ko da hakan yana nufin ƙarshen rayuwar ƴarana ne”


“Me ta aikata maka ne?”


Ya rumgume ta ƙam-ƙam a ƙirjinsa yana shirin mantar da ita zancen da suke. Sai gurin Takwas saura ya bar ɗakin. Ko da ya fito duk suna falo suna jirana, Ezzah idonta yayi ja sosai daga ganin alamu kuka tayi sosai, amman sai yayi kamar be kula ba har ya kai su makarantar be yi Ezzah magana ba balle ya rarrasheta.


Daga makarantar ya wuce asibiti dan jin kiran da Rashida take masa, sam be ji wani abu a ransa ba, na tsoro ko kuma na tunanin irin abunda ƴan'uwanta zasu masa.
Mahaifiyarta ya tarar a ɗakin dare da Babanta sun sata gaba, ita kuma sai rusar kuka take. Daddyn ta na ganin Hilal yayi kansa kamar zai dake shi.


“Me ka zo yi cikin asibitin nan me ya kawo ka? Marar mutunci marar tarbiya, wanda be san hallaci ba, sai yanzu data gama zazzage maka mahaifarta dan ka auro wata zaka sake ta? Daman can ne bana son auren ku da ita dan ban yarda da tarbiyarka ba”


“To ai yanzu sai aka aura mata wanda ka yarda da tarbiyarsa, idan ta cika idda zata iya auren wanda kake so”


Momy ce tayi saurin riƙe hannun mijinta ganin yadda ya ware zai zabgawa Hilal mari.


“Karka so ma faɗa min maganar banza, ko ba daɗe ko ba jima sai Allah ya jarrabe ka da son Rashida kuma wallahi ba zan bari ta koma maka ba, tun da ka ci amanar ta”


“Nima ba zan koma ba Daddy nice na nemi ya sake ni, kuma yanzu nice na kira shi akwai abunda zan faɗa masa, dan Allah ka bar ni nayi magana da shi”


Rashida ta faɗa cikin kuka. Wata muguwar harara Mahaifinta ya watsa mata kamin ya fice shi da Momy da idonta ke cike da hawaye.



Cikin shesshekar kuka Rashida ta kalli Hilla ta soma magana dashi tana jin zuciyarta kamar zara narke.


“Hilal ka san ina son ka, shiyasa ka yi min haka ko? Duk irin zamantakewar da muka yi da kai haka zaka saka min? Taya kake tunanin zan rayu babu kai”


“Ta yadda kike rayu da wani na a lokacin da nake tare da ke, haka zaki rayu da wani a lokacin da ba ni, ƙaryar so kike min Rashida tun da har kika iya aikata zina da wani namiji bayan ni ban rage ki da komai ba”


“Ni ba dutse bace Hilal, dole akwai lokacin da zan buƙace wani a kusa da ni, a lokacin bana gida, idan nayi kwalliya sai dai mutanen office su yaba min, su za su gani ba kai ba, kuma dole ce tasa na fara aikatawa kamin abun ya zame min jiki”


“Faɗa min dawa kike tarayya?”


“Ba zan faɗa maka ba, amman ina son ka san da wani abu ɗaya, har a bada ba zan daina son ka ba, kuma ina roƙon alfarmar karka faɗawa kowa sirrina”


“Ba zan faɗawa kowa ba, kuma ba saboda ke ba, sai dan saboda Ƴaƴana”


“Ba zaka sake jindaɗin rayuwar aure ba Hilal, iya rayuwar da muka yi itace ta jindaɗin aure, wallahi Kalsoom ba zata mallake min ƴaƴa ba, idan har ban zauna da kai ba babu wata mace da zata zauna da kai a duniya da sunan rayuwar aure, baka isa ka raba ni da ƴaƴana ba, wata mace kuma bata isa ta maye gurbina ba”


Matsowa yayi kusa da ita cikin zafin rai zai mata magana. Sai ga Asmee ta shigo ɗakin. Sai kawai ya juya ya fice ba tare daya faɗa mata abunda yayi niya ba.
Da sauri Asmee ta ƙaraso kusa da ita ta dafa ta.


“Ke lafiya Hilal yake kuwa? Wai jiya bayan na bar nan asibitin na ji mummunan labari da gaske ne kuwa?”


Kwantowa tayi kikin Asmee tana kuka


“Da gaske ne Asmee ya sake ni”


“Me kika masa?”


“Ban masa komai ba haka kawai ya sake ni”


“Hmmm sherin kishiya ne, ai kinsan yadda mijinki yake son ki ba zai sake ki haka nan kawai ba, wani asiri ne aka masa”


“Ba zai mai da ni ba, shikenan ƙarshen aurena da shi”


“Wallahi ƙarya ne, ƙarya ne wallahi Allah ya sa kiji sauƙi da wuri, kin ga malamin nan da na kai ki gurinsa? Wallahi ki koma yayi miki aiki a gigice Hilal zai maida ke”


“Zan koma yayi min aiki, amman bana Hilal ya mayarda ni ba, sai dai na wani abun daban, na riga na yafe Hilal har a bada”


“Kar kice haka Allah dai ya baki lafiya”


Ƙara fashewa tayi da kuka ta ƙamƙame Asmee tana jin wani irin zugi da zuciyarta ke mata.




AMIRA POV.


Daga ita sai tawul ta fito daga banɗaki, ta zo ta zauna gaban mirrow tana taje kanta. Sai da ta gama ta shafa mai tayi kwalliya sannan ta kalli Guy son dake kwance saman gado yana kallonta tace


“Amman kasan matar nan ta raina mana hankali? Sai da tasa muka bincika ko waye likitan sannan zata ce mana wani ta fasa”


“Manta da ita kawai, akwai wani aiki da zamu je yi Abuja jibi, akwai wanda ya kira ni kuma na san zamu samu kuɗi da yawa”


Ta baro inda take zaune, ta nufo inda yake tana wara ido


“Da gaske?”


“Na taɓa miki ƙarya?”


“No I'm just asking, you know how a like Abuja”


“Yeah shiyasa zan je da ke ai”


Rumgume shi tayi cike da jindaɗi, shi kuma ya shiga shafa jikinta.




NAMRA POV.


Cikin wani irin kuka ta isa gida. Yau duk wani tsoro da take na gidan be ziyarce ba, dan baƙinciki dake tare da ita tafi tsoro, yadda ta ga dare haka taga dare, sai ta tashi tayi sallah, tayi addu'ah samun mafita da sauƙi a zuciyarta. Tana gurin bata tashi ba har aka kira sallah asuba, kasa cin komai tayi da safe, ji take kamar ta kashe kanta ta huta, kalaman Asim sun tsaya mata a rai, sai yanzu ta fara gasgata kalaman Anty Amarya, ayau Asim ya nuna mata ko waye shi, ya buɗe mata sirrin dake ransa, sannan ya zarge ta da abunda wani be taɓa mata ba.
A tau ta tabbatar da tayi zaɓen tumun dare, sai a yanzu tana ganin laifin zuciyarta.


“Miyasa kika bar ni na kamu da son wanda ba dan Allah yake so na ba? Dan me baki bar ni na so waninsa ba? Duka yaushe muka yi aure da shi amman yau ya sauya min ya nuna min abunda ban taɓa mafarki ba? Yanzu ya zanyi da rai na? Na bar karatuna saboda shi na zo garin da ban san kowa ba saboda shi amman duk ban masa ba?”


Ita ƙaɗai take magana da kanta, tana wani irin kuka mai taba zuciya. Bata ji a yau zata iya kwana a katsina, dan a yau bata buƙatar kowa a kusa da ita sai yan'uwanta, da mahaifiyarta, tasan ko hira kawai tayi da su zai rage mata damuwa, sama da zaman kaɗaici da take yanzu.
Tashi tayi ta matsa kusa da inda ta aje ƴan komatsanta.
Jakarta ta buɗe taga kuɗin da yayi mata saura, sai ta shiga BQ ɗin ta ɗauko Sarƙa da wayarta ta saka a jakarta ta sauya hijabinta ta jawo BQ ɗin ta fito tana kuka.


Sai da ta tari Napep ta shiga sannan wani tunanin ya zo mata. Idan ta koma gida da wane ido zata kalli Anty Amarya? Me zata cewa Abbah? Masu jiran su yi musu dariya tasan zasu yi. Har ya kai ta tasha bata samawa kanta wata mafita ba, sai dai hakan be hana ta shiga motar sokoto ba, tun da bata da wani gurin zuwa sai can.




ABDOOL POV.


Yana zaune ƙasan Carpet yana cin abinci, Ummi dake zaune saman kujera ta tsare sa da ido tana kallon ɗan nata cike da tausayawa.
Sai da ya gama cin abincin sannan ya kalleta yana murmushi.


“Ummi wannan kallo ai sai ki tsorata ni, gani zanje Abuja gobe ai sai kisa nayi tunanin ko mutuwa zan yi”


Ɗan murmushi tayi ta kawar da kai.


“Kawai ina tausayin ka ne, jiya da zafin jiki ka kwana saboda tunanin nan yarinyar how i wish ina da wani abu da zan yi akai”


“Karki damu, ni ai haka jiki na yake, mutane suna cewa ba komai bane dan kaji mutum da zafin jiki”


“Ba irin naka zafin ba, wacan ɗan ɗumi ake nufi kuma shi ma a mace ne ba namiji ba”


Dariya yayi ya tashi tare da plate ɗin


“Ummi kenan, ni fa bana da wata damuwa yanzu sai ta Mai Martaba”


“Zan yi magana da shi ai na faɗa maka, kawai kai dai ka samu natsuwa kuma ka kwantar da hankalin ka”


“I will try inshallah”


“Ni Allah yasa ma Abujar nan da zaka je ka haɗu da wata wanda zaka so fiye da wannan ma”


“Ai gurin aiki zamuje ba gurin hutawa ba, idan kuma kina son na ɗauko miki soja shikenan, sai na auro soja”


Wani tsaki taja ta ɗauke kai ta mayar gurin tv. Shi kuma yayi dariya ya shige kitchen.




[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*




*© Khadeeja Candy*


*PAGE - 42*


NOT EDITED ⚠


Da yamma lis Namra ta sauka babbar tashar sokoto, sai da kowa ya gama fita motar kasancewar ita ce a can baya sannan ta fito jiki a sanyaye, tana kalle-kalle kamar mai tunanin inda zata je.


A hankali ta cira ƙafarta da tayi mata nauyi saboda zaman mota ta fara takawa, ta doshi ƙofar fita tashar gabanta sai faɗuwa yake kamar zai fito, wani abu ta ji ya zo ya tsaya mata a zuciya, yana ƙoƙarin danne mata numfashi.

Ta daɗe a tsaye bakin ti-ti sannan ta tari Napep ta shiga, sai da ya fara tafiya da ita suka yi nisa sannan ta ɗan karkato ya tambayeta inda za a kai ta ganin bata ce masa komai ba tun da ta shiga Napep ɗin.


“Hajiya ina za mu?”

Shiru tayi kamar mai tunani, ta ɗauki tsowon lokaci bata amsa shi ba, har sai da ya ƙara tambayarta.


“Clapperto....road, gurin....gawon nama”


“Dari biyu zaki biya Hajiya”


“Ok..ay.. Allah Kai... Mu lafiya”


“Amin”


Ya kai hannu ya kunna waƙar Umar M Shariff ta duniya makaranta. Sauraren waƙar take tana hawaye, hankalinta da tunaninta gaba ɗaya ya tattara ya koma gidan su da take tunkara yanzu. Abunda zata faɗa musu take ta saƙawa amman har ta saka samun mafita.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Ta furta a hankali lokacin da Mai Napep ɗin ya kunna kai cikin unguwar. Jin tayi kamar tace ya juya da ita, sai dai idan ya juya da ita ɗin ina zata ce ya kai ta?

“Ya isa...”


Ya faɗa a lokacin daya kawo bakin ƙofar gidan su. Sai da ta share hawayen idonta sannan ta ciro kuɗinsa ta miƙa amsa, sannan ta fita jikinta har rawa yake irin na tsoro da rashin gaskiya yana tare da ita.


Sai da Mai Napep ɗin ya wuce, sannan ta doshi ƙofar gidansu, cikin wani irin mugun faɗuwar gaba. Har ta kai hannu zata tura ƙofar gate ɗin sai kuma ta tsaya tana jan numfashi.
Tafi kowa sanin waye mahaifinta, ta kuma san halinsa ba zata manta furucin da yayi mata ba, bata san iya furucin da zai ƙara mata ba.
Babu wacce ta faɗo mata a rai, sai Gwaggo Kulu, ƙanwar Abbah, mahaifiyar Anty Yasmin.
Tasan ƙanwar Abbah ce amman Abbah yana jin maganar ta sosai kuma tasan yadda Gwaggo Kulu take son ta cikin ƴaƴan Abbah.


Juyawa tayi da saurin ta nufi farƙon unguwar dan ta can ne zata fi saurin samun abun hawa. Sai da ta kusa ƙarasawa babban ti-ti sai ta ga Motar Maryam ta kunno kai cikin unguwar. Da sauri Namra ta kawar da fuskarta dan kar Maryam ta ganta, ashe tayi a banza dan baya-baya Maryam tayi da mota ta fara leƙen fuskarta, hakan be gamsarda ita ba har sai da ta faka motar gefe ta fito ta fara bin Namra da ƙafa tana kiran sunan ta.


“Anty Namra ke ce?”


Juyowa Namra tayi ta kalleta idonta da hawaye ta ɗaga mata kai.


Wani irin tsalle Maryam ta daka ta rumgumeta tana ihu.


“Wallahi ban ɗauka ke bace nayi zaton wata ce mai kama da ke, Anty Namra ina za ki?”


“Gidan Gwaggo Kulu zan je”


Ta faɗa cikin kuka tana rumgume da ƙafaɗar Maryam. Maryam ta ɗago ta kalleta


“Miyasa ba gida kika zo ba?”


“Amman nasan Abbah ba zai bari na zauna ba, korata zai yi”


Maryam ta dafa kafaɗunta.


“Fushi kika yi?”


Tayi shiru bata amsa ta ba, hakan ya tabbatar ma Maryam amsar tambayar.


“Wani abun Asim yayi miki ne? Karki ɓoye komai Anty Namra ki faɗi abunda yayi miki, dan ba zai yiyu ya taɓa mana ƴar'uwa ba mu ƙyale shi”


“Be min komai ba, ni dai kawai na gaji da zaman can ne”


“To ki zo muje gida”


“A'a ni ba zan je ba, Abbah zai kore ni kuma Anty ba zata ji daɗi ba”


“To ya zaki yi? Kina da inda ya fi miki gidan uban ki ne? Ko yanka namanki zai yi yayi gunduwa-gunduwa da shi dole ne ki shiga tun da baki da inda ya fi miki nan”


“Ni dai ba zan je ba, gidan Gwaggo Kulu zan je”


“To muje na kai ki”


Maryam ta faɗa tana nuna mata motarta. Kamar ba zata shiga ba, sai kuma ta nufi motar ta buɗe ta shiga. Sannan Maryam ta shiga driver seat ta tashi motar, ribas tayi ta juya ta inda ta fito, sai da suka hau babban ti-ti sannan Maryam ta kalleta tana takaicin halinta tace


“Wani lokacin Anty Namra kina ban haushi da mamaki wallahi, kina abu kamar ba kece yayata ba, abunda kike yi ko Aisha da take ƙaramar mu ba zatayi ba. Kin san abunda yake cutar da ke? Tsoro da gudun zuciya, da ganin ke ba zaki iya ba, sune suke cutar da ke.


A duk kuma lokacin da kike ganin ke ba zaki iya ba, to ba zaki taɓa iyawa ba har a bada, lokacin da zaki hankalto kice zaki yi a lokacin ba ki da time, shiyasa yan karon magana suka ce if you say yes to others make sure you didn't say no to yourself, saboda zaki cutar da kan ki ne kawai, ba zaki taɓa burge kowa ba a duniyar duk abunda za kiyi wani sai yace kin masa ba dai-dai, ya kamata ace kin canja haka nan accept responsibility for your life, ya kamata ki san it is you who will get you where you want to go, no one else, duk wanda kika gani yana kusa da ke wallahi da zaki waiwaya wata rana zaki ga duk babu so, sai mai miki so na haƙiƙa, wasu duk dariyar fuska ne bda xaki san abunda yake zuciyarsa da ba zaki sake kallonsa ba.


A maimakon ki ƙara hankali da tunani amman kullum sai wata iri kike zama, kamar wanda ake cirewa ƙwaƙwalwa ana zubarwa, tsoron nan da yake ran ki dan Allah ki cire shi Namra, you have to your fears, kuma ya kamata ace kisan cewa kema kina da right and freedom...”


Tun da Maryam ta soma maganar in banda kuka babu abunda Namra take, ta san gaskiya ƴar'uwarta ke faɗa mata, tabbas akwai tsoro a a tare da ita, tsoron abunda mutane za su ce, tsoron ɓacin rai, tsoron ganin ita ba zata iya ba, da kuma gudun zuciyar wanda duk take tare shi. A rayuwar Namra bata iya so ba, irin son nan take yi na sadaukar da komai nata saboda wanda take so ko kuma ta yarda da shi. Indai Namra ta aminta da kai to kai je ka kwanta kawai kayi kwana, ita zata maka komai idonta ya kan makance ga duk wanda take so, bata ji bata gani.


“Mtsssssss”


Maryam taja tsaki.


“Aikin kenan sai kuka, da anyi miki abu kuka dai kuka, da kuka zai miki magani ai da tuni yayi miki, haka kika zo kika sakarwa yarinyar Amira jiki ta yi ta cin amanarki, Allah kaɗai yasan dalilin guduwarta daga gida, amman kullum uwarta ke take cewa ke ce sanadi”


Unguwar Bafarawa estates Maryam ta kai Namra, gidan Gwaggo Kulu.
A bakin gate ɗin gidan tayi farkin ta kalli Namra


“Yanzu idan kin shiga sai kice mata me?”


“Zan ce nan na fara sauka ne”


“Toh nidai ba zan shiga ciki ba, kuma idan na koma gida zan faɗawa Anty duk yadda muka yi da ita zan dawo na faɗa miki”


“Amman dan Allah karki faɗawa Abbah”


“Tau ina gaida Gwaggo”


Namra ta fita motar cikin yanayin damuwa ta shiga gidan Gwaggo.

Please Login or Register in order to submit comment