Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne saboda ta janye ƙudirinta.




HILAL POV.


“Miya same ƴar ka haka ne Doc?”


Doc Zara ta tambaya cike da mamakin irin ƙunar da Ulfah ta yi. Hannayensa ya zuba aljihu yana sauke ajiyar zuciya, ita kan Teema tuni ta kusa cikin ɗakin tana hawaye kamar gaske.


“Faɗa suka yi da ƴar'uwarta shi ne wai ta watsa mata ruwan miya dake kan wuta”


“Amman gaskiya ya kamata ka sa ido sosai akan yaranka Uzair, irin wannan abun yana sa kisan kai fa”


“Ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo abu”


“Allah ya tsare gaba, Ina uwargida har yanzu bata haihu ba?”


“Har yanzu fa”


“To Allah ya raba lafiya”


“Amin”


Tun da suka jero suke maganar basu rabu ba sai da ta kawo kusa da pharmacy sannan ta ɗauki wata hanyar shi kuma ya ciro wayarsa ya kira Hajiya ya faɗa mata, ita Rashida text kawai ya aika mata, sai kuma ya kama hanyar gida dan yi ma Ezzah hukunci.
Sai da ya kama hanyar gida sannan ya kira Kalsoom ya faɗa mata halin da ake ciki, dan yasan zata tashi hankalinta sosai.


Bugu ɗaya ta ɗauka.


“Kana ina ne?”


“Ina hanyar gida, na kaita asibiti da sauƙi”


“Na je gida ban samu kowa ba sai Ezzah tana ta kuka, sai ta biyo ni gani cikin asibitin ma”


“Oooooo Kalsoom miyasa baki ragawa kan ki ne? Ba fa ke kaɗai kike ba a yanzu, da izinin wa kika fita, yanzu da wannan tulelen ciki yama zaki yi driving?”


“Napep na hau”


Ajiyar zuciya ya sauke.


“Tau gani nan juyowa”


Ya katse kiran ya juya ya koma hanyar asibitin. Yana isa aibitin su Hajiyarsa na isa yare da Mama ladi (kanwar mahaifiyarsa) da ƙanensa guda biyu. Jerowa suka yi suna tafiya yana yi ma Hajiya bayanin yadda abun ya faru.


Kalsoom na hango shi tafe tare da Hajiya ta ji babu daɗi musamman dan tana tare da Ezzah tasan dole Hajiya za tayi magana wata ƙila ma zata ce ita ce ta haddasa wannan husumar. Duk sai ta rasa yadda zata yi ga tulelen cikin nan ya mata tsaye kamar wacce zata haihu yanzu.


“Hajiya ina wuni”


“Lafiya ƙalau”


Tana amsa gaisuwar da Kalsoom ta yi mata ta wuce bata ko bi ta kanta ba. Hilal ne ya tsaya gurin matarsa.


“Miya hana ki shiga?”


“Ban san ɗakin da aka kai ta ba”


“Tau muje”


“A'a sai Hajiya ta fito, kar ta gan ni da Ezzah”


“Cemin ta yi wai tana tsoron karka dake ta”


“Ai ba duka kaɗai ba karye ta ma zanyi, ba dai ke har kin kai ki ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki ba...?”


Sai kawai Ezzah tasa kuka ta kama Hijabin Kalsoom ta riƙe gamgam tana kuka. Hilal be bi ta kanta ba ya nufi sashen da zai sadashi da ɗakin Ulfah, Kalsoom ta rufa masa baya tana faɗin Ezzah ta yi shiru ba zata bari ya daketa ba.
Ko da suka shiga Hajiya na kusa da Ulfah dake bachi, tana duba ƙonuwar cike da tausayi, can jikin ƙofa Kalsoom ta tsaya tana kallon Ulfah, Ezzah na riƙe da Hijabinta har lokacin tana kuka. Hajiya ta ɗago ta kalli Ezzah cikin tausayi da ɓacin rai ta ce


“Amman Ezzah baki da zuciyar ƙwarai, ko ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki haka?”


“Wallahi ba nice ba Wallahi Mama Teema ce...!”


Ta faɗa cikin kuka.
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *82*


Teema ta katsa mata tsawa tana zare mata ido alamar dik kika faɗa sai na ci ubanki.


“Ke karki min ƙarya, munafukar yarinya fitsararriya”


“Wallahi ba ni bace, ke kika kira ni kika ce na zo naje kitchen na duba Ulfah ta ƙone...”


Hajiya ta kalli Teema ta kalli Ezzah, ƙoƙarin ɗaukar maganar ta ke, sai kawai ta jiyo kukan Teema wai Ezzah ta mata ƙazafi.


“Wallahi ba zan taɓa yafe miki ba, makira kawai munafuka”


“Ezzah kike cewa haka? Sai kace wata babbar mace? To wai kina aikin me haka ya faru”


Cewar Hajiya tana sake da baki. Ta soma bayani tana kuka da kallon Hilal ko zai kareta ɗin nan.


“Ina cikin kitchen ina girki, na ƙare tuwo sai na ce bari na ɗora miya, sai na ce ta daga kamin daddawa ita kuma Ulfah ta gyara min tabarnuwa, ni ban san gardamar mi suke ba sai kawai naji an taɓa tukuyan miyar da ƙarfi sai ihun Ulfah na ji ina juyowa na ga ta juye mata miyar”


Izzah ta tuma ta dire ta sake tuma ta dire tana kuka da jan Hijabin Kalsoom tana faɗin ba ita ba ce, amman babu wanda ya kula ta Hilal in banda harara babu abunda yake mata, yana cike da haushinta sosai Allah ka ɗai ya san irin hukunci da zai mata idan suka koma gida. Sai kawai ta saki Kalsoom ta ruga gurin Hajiya tana kuka.


“Wallahi ba ni bace Hajiya...”


“Hilal ka saurareta mana”


Kalsoom ta faɗa cike da tausayin kukan da Izzah take yi.
Hilal ya girgiza mata kai.


“Ba wani saurare da za'a mata, ai kin san halinta”


Izzah har da faɗuwa take a gurin taɓa tashi ta kama gyalen Hajiya ta riƙe ƙam.


“Ba zaki rufewa mutane ba ki ba, Wallahi zan dake ki yanzu nan, ba sai mun je gida ba”


Hilal ya faɗa ciki fushi yana mai jin kamar ya kamata ya ɓallata gida biyu. Ihunta ne ya tashi Ulfah daman can ba wani dogon bachi ta yi ba, saboda zafin wuta ko an maka allurar ba bari yake ka yi bachi ba.


“Wayyo Allah Momie, Hajiya, Dady ka kai ni inda Momie ko Anty Kalsoom ko inda Hajiya, bana son gurin Mama Teema ta watsa min wuta, wayyo zafi dady zafi Mama Teema ta ƙona ni, Anty Kalsoom, Momie, Hajiya”


Sune ƙawai sabbatun da take tana murza jikinta sai da Hilal ya riƙe mata hannu. Suna haka sai ga Rashida ta shigo hankalinta a tashe, tana kallon Teema hawaye suka fara mata zuba.


“Ɗaya bayan ɗaya za ki bisu ki kashe, na sani Teema kaɗan daga halinki ne amman ki sani kin ci amana kuma kema amana sai ta ci ki”


Sai kuma ta juyo gurin Kalsoom tana kuka, itana Kalsoom ɗin kuka take, Hajiya ma haka, balle Teema dake ƙoƙarin kare kanta, ƙanen Hilal ma babu wanda baya hawaye.


“Kin ci amanata, sai da na ce miki ki riƙe min yara na amman kika ƙi, yanzu ga shi abunda ya faru, bana da kowa a duniyar nan sai su, su ne farinciki na”


Jakar da ke hannunta ta saki ta nufi gurin ƴarta dake sabbatu, magangun ɗazu kawai take maimaitawa. Rashida ta gadon ta riƙe tana kuka.


“Laifina ne, nice ban riƙe mutuncin aurena ba, ni na kasa zama da ku ni na cuceku Ulfah laifi na, kuma na ci amanar matar da ke riƙon ku tsakani da Allah...”


Ezza ta yi gunta da kuka.


“Momie Wallahi ba ni bace, Dady ya ce sai ya raba ni gida biyu.. Wallahi ba ni ba ce”


“Ba zan ɗauka ba, wannan ba zata kwanta jinya ba, ka kama wannan ka karya min ba, ka saurareta Hilal Wallahi ba ita ba ce, karka ɗauki alhakin yarinyar nan Hilal”


Cikin kuka Rashida take maganar gwanin ban tausayi. Hajiya ta share hawayenta tana kallon Ezzah.


“Miya faru faɗa mana”


Ras Ezzah ta zana musu abunda ya faru, duk wani tsoro na teema yau baya tare da ita, tun da ta ji zancen Hilal yace zai raba ta biyu. Duk suka cika da mamaki sai kawai Teema ta ƙara rushewa da kuka, Hajiya ta girgiza kai tana faɗin.


“Amman Fatima kin ban mamaki, kw da ake yabo da salla?”


Hilal yayi saurin ɗaga mata hannu.


“Hajiya dan Allah kar ayi maganar nan a nan, asibiti muke, kullum sai ace nine family na cikin matsala”


“Kai dalla gafara can, kai har yanzu baka san ciwon kanka ba akan ƴaƴanka, ko wace mace ka aura da irin azabar da take gwadawa ƴaƴanka, Kalsoom ta kashe Rafiq wannan kuma tana ƙoƙarin kashe Ulfah wannan wane irin masifa ce”


Rashida ta kalli Hajiya tana hawaye.


“Wallahi ba Kalsoom ba ce ta kashe shi, Wallahi nice ni na kashe ɗana da kai na...”


Sai duk kallo ya koma kan Rashida har Kalsoom ɗin kallonta take. Hajiya tasa wani dogon numfashi ta sauke ta ce


“Muje gida mu yi wannan maganar, Hilal muje gidanka a yi wannan maganar, Ke ki tsaya nan ki kula da Ulfah”


Ta faɗa tana kallon ɗaya daga cikin ƙanensa, sai kawai ta nufi ƙofar fita tare da tawagarta. Rashida ma fita tayi ta rufa musu baya dan ta shirya fasa ƙwan yau kam, bata san gidan Teema ba dan haka ta nufi tsohon gidanta kuma gidan Hilal inda Kalsoom take zaune. Hilal kan sai ya bawa ƴarsa magani tare da allura ta koma bachi sannan ya sako matansa gaba suka kama hanyar gida. Ko da suka shiga falon Hajiya na zaune falon tana jiransu, Ezza kuma na riƙe da Hijabin Kalsoom kamin ta saketa ta nufi gurin uwarta da gudu.


“Maimata abunda kika faɗa ɗazu ko kina da wata shaida”


Cewar Hajiya tana kallonta. Rashida ta girgiza kai.


“Bana da wata shaida sai Allah da kuma Teema, amman Wallahi Kalsoom bata da hannu a mutuwar Rafiq, ni naja komai”


“Kamar ya ki fito ki yi bayani mana”


Hilal ya katsa mata tsawa, Teema ta yi saurin saka baki.


“Karki ci amanata Rashida ni ban san komai akan ɗan ki ba”


Rashida bata kulata ba, ta soma koro da bayani.


“Bayan da Hilal ya sake ni, sai na riƙa zagaya makarantar su Ezzaha ina zana mata irin makirci da rashin kunyar da zata yi ma Kalsoom, ina tunani kamar idan ta yi hakan zai tausaya musu ya dawo da ni, da naga hakan be samu ba, sai na koma bin bokaye, ina neman yadda za ayi Kalsoom ta bar gidan Hilal kuma ya dawo gareni, naje wanu gurin aka mata magani aka sako mata jini, cikin dake jikinta ya kwanta ya ɓace bat, na sake komawa na yi mata wani a wannan karon be faɗa kanta ba, ya faɗa kan ɗa na Rafiq, ni kai na ban san ya faɗa kansa ba, har sai da naje na kaiwa Teema kukana ta kaini gurin wani malami shi ya faɗa min cewar na yi magani ma kishiyata ya faɗa kan ɗa na, shiyasa a asibiti aka rasa gane kan wannan matsalar sai ya nuna guba ne sai kuma ya nuna gas ne, ba komai ba ne sai sihiri. Duk wani shige-shige da nake na magani tare da Teema nake yinsa, ta kai ni gurare da dama, saboda ta fini sanin bokaye, nayi mamakin da aka ce Hilal zai aureta saboda na san an gudu ba a tsira ba ne. Sai dai na ɗauki hakan a matsayin cin amanar aure da nayi na keta haddin Allah na tozarta aure, dole nima Allah ya tozarta ni, na ci amanarki Kalsoom na yi ta miki abubuwa ko a zaman da muka yi da ke a gidan nan, ashe ma ke ƴar'uwata ce ba kishiya ba...”


Kuka take sosai ita da Kalsoom da Teema, sai dai ko wannensu da abunda yake yi ma kuka. Kalsoom babu komai a zuciyarta sai farincikin yau Allah ya wanke ta da kuma tausayin Rashida da ƴaƴanta.


“Na yafe miki Rashida, Wallahi na yafe miki har a bada, kuma na miki alƙawarin zan kula miki da ƴaƴanki fiye da yadda ke zaki kula da su, amman idan Hajiya ta yarda”


Kalsoom ta faɗa tana kallon Hajiya data soke kai tana hawaye.


“Haƙiƙa na cutar da ke Kalsoom, na miki kurkuren fahimta, na ɗauki alhakinki, na cutar da ke matuƙa, Wallahi na ji kunyar kai na sosai”


“Haba Hajiya ai ko nice a matsayin da kike kwatankwacin abunda zan aikata kenan, saboda gaskiya ba ta bayyanaba a lokacin kuma ɗan adam da zahiri yake aiki sanin baɗini kuwa sai Allah, ni dai abunda kawai na ke so ki yarda da ni kawai”


“Wallahi na yarda da ke ɗari bisa ɗari kalsoom, kuma daga yau yaranki gurinki zasu zauna. Teema baki yi ƴa ba, kin bani mamaki, ina gani kamar na ɗauko ma ɗauka mutuniyar kirki ashe ɓara gurbi ce”


Kuka sosai Teema take ta sauka daga saman kujera ta zauna ƙasa kusa da Hajiya ta kama ƙafafunta.


“Wallahi Hajiya ƙarya take min, na miki alƙawarin zan canja daga yau, ba zan sake yin wani abu marar kyau ba”


“Nasa Hilal ya aure ki ne saboda ita tunanin ke ta ƙwaraice, Fatima ko da mun zauna da ke babu aminci a tsakanin ke da mijinki da ƴaƴansa da kuma ni, mace mai shige-shigen malamai iya mata sai Allah karki je ki yi mana irin na Rashida, kin ga ƙara a rabu tun abu be yi nisa ba, kije can Allah ya haɗa ki da rabon ki, ni kan Hilal ba dan kar na zama uwar banza ba da na baka shawarar rabuwa da yarinyar nan...”


Ta ƙarasa tana kallon Hilal. Shi kan uffan be ce ba sai kallon pop yake abun duniya ya taru ya tsaya masa, idan ya shiga wannan ya shiga wannan. Miƙewa ya yi tsaye ya fice cikin rashin daɗin rai.


Bayan fitarsa Hajiya ta miƙe ta fita, ta bar Teema na kuka, Rashida kuma na hawaye. Bata yi minti talatin da fita ba Rashida ta tashi ta fice, a lokacin ne Teema ta kalli Kalsoom ta ce.


“Zan taimaka miki ki haihu, nasan hanyoyin da zan bi ki haihu, wannan cikin na ki yanzu shekarar ɗaya da wata huɗu cikin na biyar, amman idan kika taimaka min kika hana Hilal ya sake ni, ina son ki saka baki a lamarin auren mu domin a yanzu na fuskanci kina da ƙima a gurinsa da kuma mahaifiyarsa fiye da ni”


Ido kawai Kalsoom ta sakar mata tana kallon ikon Allah, ta ya zata ce ta kaita wani gurin bayan yanzu aka gama rigimar tana bin bokaye, ita bata ma tsoron wani ya ji. Kamar daga sama suka ji muryar Hilal da ke tsaye bakin ƙofa rumgume da hannayesa a ƙirji yana kallonsu, dan sam basu san da shigowarsa ba.


“Kalsoom bata iya shige-shige irin na ku ba, kuma idan lokacin haihuwarta yayi zata haihu, ke ai naga haihuwar kike nema miya hanaki bin bokayen su baki haihuwa?”


Ta miƙe tsaye yana kallonshi.


“Haihuwar da na ke so Hilal saboda kai nake son ta, ina son na haihu da kai saboda ina ƙaunar ka ne, yanzun kuma abunda nake ƙoƙarin yi ma saboda ina ƙaunarka ne Hilal, miyasa ka kasa ganin haka? Tun kana mijin Rashida na ke mafarki miji irin ka saboda kana kula da ita yadda ya dace, ashe ma Allah yayi sai na kasance ɗaya daga cikin matan ka, ka tausaya min Hilal, zan iya yi maka alƙawarin ba zan sake bin ko wane malami ba indai wannan ce kawai matsalar...”


Ta ƙarasa tare da risinawa kamar mai neman gafara.


“Ba wannan ce kawai matsalar ba, ko na zauna da ke ba zan aminta da ke ba, kuma mai hali baya fasa halinsa, ai yanzu aka gama wannan rigimar amman kika ɗaga ido kika kalli Kalsoom har kina neman ki taimaketa, dan ta saka kar na sake ke, kin manta ita da ke duka a ƙarƙashin kulawata kuke? Hajiya ma dake gindaya min sharaɗi yin abu ko hani ta bani umarnin idan na ga dama na sake ki, tun dan me zaki dawo gurin Mamata kina neman ta taimake akan abunda zan iya yanke hukuncinsa yanzu?”


Kalsoom ta girgiza masa kai.


“Saboda ta san zan iya saka ka yi ne...”


“Kalsoom karki saka bakin ki cikin wannan maganar please”


Teema ta hasala ta miƙe tsaye cikin ɓacin rai da zafin zuciya.


“Ka daɗe baka sake ni ba Hilal, ni wannan wuƙancin da Rashida take ɗauka ni bana ɗaukarsa, sai kace kai ne kaɗai na miji ana magana kana ƙara butsewa, ka sake mana ai ni tafi nono fari, zaman gidanka ko zaman wahala haka kawai za ku ɗauko ni wani kula da yara wato ga ƴar aiki kenan ko saboda an maida ni shim mai ruwa uku sha-sha-sha, da ƙurciyata na lalata kaina gurin gina rayuwar ƴaƴan wata nawa ko zuwa duniya ba su yi ba”


“Shiyasa kike cutar da su? To Allah ya toni asirin ki, kuma ki je na sake ki saki ɗaya...!”


“Ai ni da uku ka yi da ka fi burgeni”


“Ɗayan dai zan miki ƙyaji da shi”


“Tafi nono fari, ai ba kai ne autan maza ba”


“Na sani shiyasa na sake ki saboda ki samu damar auren wani”


“Aiko zaka gani dan sai kasan kayi hasarar mace irina”


Ta kaɓe masa Hijab ɗinta ta fice kamar zata tashi sama.


“Hakan be dace ba Hilal kana wasa da saki, daga wannan maganar zaka ce ka saketa kuma kana ganin yadda take ta lallaɓaka akan ka barta ɗakinta...”


“Na faɗa miki babu ruwanki da irin maganganun nan, kin cika salo da saka kanki cikin irin lamurran nan shiyasa komai aka yi sai a kin saka bakin ki shiyasa komai ake ɗora miki laifi”


“Amman....”


“Na ce ki min shiru ko?”


Uffan bata sake cewa ba sai ta cigaba da wasa da kan Ezzah shi kuma ya juya ya fice.




UZAIR POV.


Gaba ɗaya jikinsa yayi nauyi ji yake kamar idan ya motsa jikinsa zai rabu biyu, idonsa kawai yake iya zagaye ɗakin da su. Hakan ya bashi damar ganin mutanen da ke ciki a ɗakin ciki har da Abbah.


“Sannu Uzair, Sannu Allah ya baka lafiya”


Shine abunda kowa yake faɗa, sai dai shi abunda be gane ba, miya ke damunsa! Abunda zai iya tunawa kawai yaji abu ya tsikare shi sai ya faɗi, daga nan be iya tuna abunda ya faru.


Be iya amsa musu da komai ba in banda ido da yake binsu da su da kallo, har suka masa sannu suka fice cike da tausayawa. Abbah ne ya zauna kusa da shi sannan Mahaifiyarsa.


“Uzair ka ɗauki abunda ya faru da kai matsayin ƙaddara komai yana zuwa ne daga abunda Allah ya rubuta maka, kuma haƙuri shi ne zai kai ka ga har kaga ka ci riba ka samu a nan ka samu a acan”


“Wai mi yake faruwa da ni ne?”


Sai a lokacin ya samu damar tambaya.


“Uzair ka haɗu da matsala ne a ƙashinka na baya da kuma ƙashinka na ƙafarka, you wouldn't be able to walk again”


“Taya taya za a ce mun haka bayan ba haɗri na yi ba, ba wani ciwo na ji ba haka nan kawai za a ce mun na samu matsala”


“Nima abunda ya ba ni mamaki kenan, za a fitar da kai waje a duba lafiyarka”


“Abbah mi yake faruwa da ni ne?”


“Muma ba mu sani ba, likitan da ya duba ka ya tambaye ni wai ko ka taɓa haɗarin mota nace masa aa, ko ka taɓa yi baka faɗa ba?”


Hawaye suka fara masa zuba.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin bala'i ne? Miya faru da ni ne haka, Hajiya ko dai mafarki na ke yi? Allah kasa na farka Allah wayyo ni Allah na”


Haka ƴa ɗinga maganganu Abbah sai kallonsa yake cike da tausayawa, suna haka sai ga wasu friends nasa sun shigo duba shi ciki har da Dr Tahir, da wasu abokanin sha-shancinsu na Abuja. Abbah suka fara tambaya ya mai jiki ya amsa musu da sauƙi sannan suka gaishe da Hajiya dake ta sharar hawaye, suka matsa kusa da Uzair suka tsaya suna masa ya jiki.


Amsa musu kawai yake amman kana ganinsa kasan ya rikice, ba fita hanyyacinsa yayi ba, amman wannan ƙaddarar da ta faɗo masa ya gaza yarda da ita, ta ya zai zama haka mutumen da ke tafiya lafiyarsa ƙalau shi ba faɗowa yayi ba shi ba haɗari ba ace ya haɗu da wannan matsalar, ta ya haka zai faru?
Sun aje masa kuɗi mai yawa ban cin siyayyar da suka masa, Abbah na yayi musu godiya, suka kama hanya suna Allah ya sauwaƙe, sai kawai Uzair ya ƙwalawa Tahir kira, cikin sauri ya juyo ya nufo inda yake su kuma sauran abokan suka fice.


“Ina son mu yi magana da kai Abbah dan Allah ku ɗan ba mu guri”


Daga Hajiya har Abbah tashi suka yi suka fita, sai Tahir ya zauna a kujerar da Abbah ya tashi yana fuskantar Uzair ya ce.


“Na je gida na samu baka nan, matar ka ce kawai, naje na saboda na ta buga wayarka ban samu ba, kuma naje guest house ɗin ka baka nan, babu abunda matarka bata faɗa min ba, har ɗan wuta ta kira ni, daman ta san kana wannan harkar ne?”


“Shekaran jiya ta gano, lokacin da na Amira ta aiko min da saƙo, ni zargin nake ma ko ita ce ta yi min wannan asirin na koma haka ne? Da wannan daga gani lamarin iska ne aljanu ne”


“Ko kuma Amira ba saboda ta dawo na samu labarin gurin Yayanta”


“Lallai zata iya min asiri, yarinyar nan muguwace”


“Zata maka ko kuma zai dawo kan ka idan na jikinta ya kare? Kasan fa bokan nan yace maka idan be kama Namra ba, zai dawo gun ka ne, sai gashi ya kama Amira yanzu kuma Amira ta dawo ina tunanin kai zai dawoma”


“Dan Allah Tahir kaje gurin bokan nan ka faɗa nasa halin da muke ciki, idan ma wani ne yayi min ya san yadda zai yi ya kare shi, idan kuma wannan aikin ne ya kare shi dan Allah Tahir”


Tahir ya dafa shi.


“Zanje karka samu damuwa zan je har can na masa magana duk yadda aka yi zuwa yamma zan dawo na faɗa maka”


“Tahir ba sai yamma ba, kaje yanzu baka ganin halin da nake ciki...?”


Ya ƙarasa cikin kuka mai ban tausayi.


“Okay zanje yanzu Allah ya baka lafiya”


“Na gode”


Ya faɗa hawaye na zuba a idonsa. Jikin sanyin jiki Tahir ya fice yana mamakin lamarin Uzair.


ASIM POV.


Yayi rama sosai a ƴan kwanakin nan da aka yi na amsar gaisuwa, Ranar da aka kwana ɗaya da rasuwar Ƴan gidansu Mardiya suka zo har da Mardiyar gurin gaisuwa, a nan ne yake nunawa wasu ita yana cewar ita ce matar da yake son aure.


Bayan an yi addu'ah uku ya ɗaure ya ƙara kwana biyu saboda masu zuwa ƙara masa gaisuwa. A ranar ne Mama Inno ta raba yaran ta ɗauki Hajara da ƙanenta biyu wasu daga ɓangaren mahaifinsu suka raba sauran ƴaƴan, abun gwanin tausayi, ranar Asim ya ci kuka kamar zai haɗiye zuciya ya mutu dan baƙin ciki, ashe Mama bata da rabon ta shiga gidan da yake da niyar sai mata, be taɓa baƙin cikin haɗuwa da Hajiya Sadiya ba sai yau, ji yayi kamar ace tana kusa da shi ya kamata yayi mata gunduwa-gunduwa, gashi ita kuma sai damunsa take da kira, yana ce mata bashi da lafiya.
Be yarda ya labartawa Nably abunda ya faru ba, amman yana faɗa mata bashi da lafiya kuma tace zata zo ganinsa ya hana, ita kuma duk hankalinta ya tashi hakan ya hanata komawa Abuja, dan ya faɗa mata ranar da zai dawo.


Ranar da bar sokoto sai da yayi kamar zai kashe kansa, gudu ya riƙayi da motar yana kuka kamar zai tashi sama. Da wuri ya isa Katsina saboda ya tashi tun asuba ne, ɗan kawai kar Hajiya ta gane halin da yake ciki ne yasa ya sauka nasarawa, dan yin wanka ya shirya ya canja tufafi. Daga wankan har shirin be ɗauke shi minti talatin ba, yana gamawa ya fito ya nufi gurin da motarsa take. Juyowa ya yi yana kallon gidan.
Be taɓa jin yayi missing ɗin Namra ba sai yau, haka kawai yau da ya tuna ta sai ya ji babu daɗi, daya tuna mamarsa sai Namra ta faɗo masa a rai, jikin rashin daɗin rai ya nufi gidan Hajiya Sadiya.


Sai da ya kama hanyar gidan sannan ya kira ya faɗa mata gashi nan ya shigo katsina har ma ya iso gidan.


“Okay okay galni nan zuwa”


Ko minti goma sha biyar ba'ayi ba, sai gata ta iso. Yayita ƙoƙarin danne damuwarsa ya nuna mata mara rashin lafiya ne kawai matsalarsa, bayan sun zauna a falo yake labarta masa yadda rashin lafiyar ta fara da fever kwanansa biyu asibiti.


“Gaskiya ka ji jiki sosai, ka rame Allah ya ƙara lafiya”


Da Amin ya amsa yana mata wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan Manufarsa da kuma abinda yake ji a ransa a tare da shi. Ta shi tayi ta shiga ɗaki dan ɗauko masa apple ɗin, shi kuma ya fidɗo wayarsa ya aikawa Nably saƙo.


_Ki same ni a Dahir Exclusive Restaurant, yanzu ina gurin_


In few minutes ta masa reply.


_Okay on my way_


Ya aika mata da saƙon ne a yanzu dan ya samu ta fita gidan kamin Hajiya ta san wani abu kai, dan yasan ba zata bari ta fita ba.


Ta daɗe a ɗakin sannan

Please Login or Register in order to submit comment