Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba, mutumen daya zaɓi zubar da mutuncin iyalansa, zan iya yafe son da nake maka Uzair”


Ya girgiza mata yana ƙara damƙe hannunta cikin nasa.


“No Wallahi sherin sheɗan ne Yasmin, ba da son raina na aikata ba, kuma duk zugar su Najeeb ce, kuma nayi ne dan na kare kai na daga cin mutuncin da Namra ta yi min”


Maganarsa ta sha banban da tunaninta, ita gun data dosa daban shi kuma maganar da yake mata daban.


“Me ka aikata Uzair?”


Ya saki hannayenta.


“Ina ruwanki da abunda na aikata ne Yasmin?”


Ya faɗa a tsawace, sai kuma ya dafe kansa ya miƙe tsaye ya nufi windo.


“Ki tsaya a matsayin ki na matata Yasmin, zai fi miki”


Ta miƙe.tsaye itama cikin ɓacin rai.


“Yes zai fi min idan na rabu da Azzalumin mutun irinka, tirr da halin ka Uzair, ina kotu ina cases ashe akwai babban Case a gidana, nayi nadamar Auren ka a yau nayi nadamar daka kasance a cikin zuri'ar mu, nayi nadamar da ka zama uban ƴaƴana, ashe gaskiya Namra take faɗa, amman ka murje ido ka ƙaryatata...”


Ya juyo a fusace yana nuna saman kamta da ɗan tsayansa.


“Ke je ki faɗawa duniya nine na sace Namra, ni na haɗa kai da amiyarta aka mata asiri ya koma kan ƙawarta, amman karki manta ɗan'uwanki kika tonawa Asiri, kuma mahaifinta zai karɓe komai nasa daga hannuna, but i'm still your husband Yasmin the love of your life kuma uban ƴaƴanki biyu, asirina asirinki ne, kuma tona min asiri kamar tonawa kanki ne da ƴaƴanki”


“Ka buɗe shafin da ban san da shi ba Uzair, ashe kai ka sace ta? Sannan ka haɗa kai da amiyarta ka mata asiri? Wane irin zuciyane da kai Uzair? Wata ƙila ma ita ka aikata mata irin abunda ka aikatawa ɗan ka, you raped your very own son Uzair Allah yayi tirr da halinka”


Dariya ya soma yi ya doso inda take.


“Allah ya faɗa acikin matan ku akwai maƙiyanku, sai yanzu na gane kan ayar nan, amman ke babbar maƙiyiya tace Yasmin, ki rasa abunda zaki zarge ni da shi sai wannan? Kina da wata hujja ne? Ke daina ganin ke lawyer ce zan iya maka ki kotu, akan wannan mummunar kalma da kika jefe ni da ita, ai ko da gaske na aikata masa be kamata ki fito ki jefe ni da wannan maganar ba, idan ma na masa ina ruwanki ɗan ki ne?”


“Shiyasa bana burge ka ko? Baka da time ɗina, saboda ba mata bane a gabanka maza ne, mu kwana gado ɗaya mu tashi amman baka yarda ka bani haƙƙi na ba, da na maka magana, ka ce baka da lafiya, ko na cika desire, ashe kasan abunda kake aikatawa, kasan irin hukuncin da Allah ya tanadarwa masu irin wannan aikin kuwa? Cewa aka ƴi idan an kama su a jefosu daga saman bene su faɗo ƙasa, ko kuma a samu dutse a buga musu a kai, miye bana da shi ne Uzair? Wace hasara ce ta cin maka na neman maza ƴan'uwanka? Uzair me kake ji idan ka neme su?”


Hannayenta ya kama, ya faɗi ƙasan gwuiwoyinsa.


“Ki rufa min asiri Yasmin, ki taimaki rayuwata, kar kowa taji maganar nan, na miki alƙawarin ba zan ƙara ba, kuma zam je nasa a kare asirin dake kan Amira i promise, Yasmin ki dubi girman Allah ki yafe min, sherin zuciya ne, da zama da miyagun abokai”


Kuka da take ne ya ƙaru.


“Ka cutar da yarinyar nan Uzair, kasa mahaifinta da duniya suka zargi ta gudu taje gurin saurayinta ne, sanadinka kowa a familyn mu ya tsane ta, duk halin da ta shiga kai ne Uzair”


“Ki yi ta tunanin wasu har ki manta da ni, ki rufa asirin wasu ni ki tona nawa, idonki yayi ta rufewa akaina har maƙota suji abunda na aikata”


“Ba maƙota kaɗai zasu ji ba, duniya ce zata ji, sai duniya tasan wanene kai, sai kowa yasan abunda ka aikata”


Ya miƙe tsaye


“Wallahi duk kika bari wannan maganar ta fita, sai kin yi nadamar zuwanki duniya, sai kin gwammace kiɗa da karatu, kuma komai na zama ni mijin Yasmin ne, ai komai yana da buƙatar uzuri da bincike, kije duk abunda zaki aikata ki aikata ɗan shege ka fasa, indai kotu kike taƙama da ita sai na nuna miki baki san komai ba akan aikin ki”


“Haka ka ce?”


“Wanda duk yaƙi ji aiba zai ƙi gani ba”


“Baka bani mamaki ba, daman masu aikata irin aikinka ai basa da kunya, kuma basa tsoron Ubangijinsu balle jama'a tirr da halinka, wallahi sai na ƙwatowa Namra haƙƙinta, sai ka raina kan ka Uzair”


“Ni mijinki kike faɗawa haka?”


“Kai mijina ne zaka taka min bayan ɗa?”


“Sai ki fito fili ki faɗa mana, kice ɗana zaki min ƙazafi, ba wai ki raɓa da Namra ba, aikin banza kaiwai... Mtssssswww”


Yaja wani dogon tsaki ya wuce daga falon kamar walƙiya. Ita kamar jiran take ya fita, ta shiga ɗakinta ta zari mayafi ta, ta goyawa Mai mata reno little Namra, ta kama hannun Adnan suka fice.






NAMRA POV.


Da hawayw ta shiga cikin gidan, sai dai kasancewar dare ne, kuma babu wutar nefa a gidan shi ya hana su gane akwai hawaye a fuskar Namra, da wannan tayi nasarar shigewa ɗaki ta kife saman kafitar tana kukanta a hankalin ta yadda ita kaɗai zata iya jin sautin kukanta.


Da sallama Anty Amarya ta shiga cikin gidan, sai duk suka haɗa baki gurin amsa mata, gaisuwa ce ta biyo baya, sannan ta ɗora da tambayar Namra, duk kallon rashin sani suka mata, ko wanne abunda zuciyarsa ta bashi, wata ce ta tare da Yarima, wata ƙila taƙi ta saurareshi ne shiyasa ya turo wata.


“Eh tana nan ciki lafiya?”


Lamido ya tambaya. Cikon murya mai kamar ta kuka Anty Amarya ta ce


“Dan Allah ku yin magana da ita...”


Kamar an jefo Namra haka ta fito daga cikin ɗakin, tana ganin Anty Amarya ta rumtse idonta ta damƙe hannayenta gam, tana maimaita.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Saboda ta kasa yarda da abunda kunnuwanta da idonta suke nuna mata, ji take kamar mafarki take kuma ba mafarkin ba ne. Ta buɗe ido ta ƙarasa gaɓan Anty Amarya ta kama hannayenta, ta taɓa ta murja ta sake kallon fuskarta, sai kawai ta rumgume ta fashe da kuka.
Anty Amarya ma kuka take, ita da Namra aka rasa mai rarrashin wani, su kam su Neina sai kallon ikon Allah suke. Kuka sosai Anty Amarya da Namra ke yi kamar an muutuwa, sannan Namra ta zube ƙasan kafafunta ya kama kafafun Anty Amarya.


“Ki yafe min Anty, na tuba dan Allah ki yafe min, ki roƙi Abbah ya yafe min, haƙƙinku ma ta bina Anty, dan Allah ki roƙa min Abbah ya yafe min”


Ta ƙamƙame ƙafafun Anty amarya, tana wani irin kuka mai yaɓa zuciya. Yanzu kam Neina da Lamido sun fahimcin wacece Anty amarya. Anty ƙasa magana ta yi saboda majina data cika mata hanci. Can Namra ta ɗago kai ta kama hannayen Anty Kaamar wace ta ruɗe.


“Anty da gaske kece?”


Ta kalli Lamido da Uwani.


“Kuna ganin abinda nake gani, ko dai mafarki nake?”


Lamido ya ɗaga mai cike da ɗaurewar kai, Uwani kuma tace


“Muna gani Namra”


Anty Amarya tasa hannu biyu ta riƙo Namra ta tashe ta tsaye.


“Nice Namra, ba mafarki kike ba, Mahaifinki ma yana nan waje, tare muka zo da shi lokacin komawarki gida yayi”


“Anty waya faɗa muku nan? Na kasa yarda ba mafarki nake ba, kaina nake jin yana juyawa”


Ta miƙe tsaye ta nufi ƙofae waje. A gurin ta samu Abbah tsaye ya maida hannayensa baya kansa ƙasa kamar mai nazari.

“Abbah....”


Ta furta tana kallonsa da kyau da kyau. Ɗan murmurshi yayi kaɗan irin murmushin da be kai zuci ba. Sai kawai Namra ta faɗa jikinsa ta rumgumeshi numfashinta na rawa, kuka yazo mata a lokaci ɗaya.


Sai da tayi kukanta mai isarta taji ta samu natsuwa sannan ta sauko gurin ƙafafunsa ta riƙe.


“Dan Allah Abbah ka yafe min, ban kyauta maka ba, kwata-kwata abunda na aikata be dace ba, Abbah Asim ya sake ni, tsoron abunda zaka min ya hanani komawa gida, dan Allah ka yafe min Abbah”


Kanta ya shafa fuskarsa ba yabo ɓa fallasa.


“Idan ban yafe miki ba, ba zan zo nan ba Namra, nasan yanzu kin riga da kin gane kuskurenki, tashi tsaye kar ki tara mana mutane”


Fitar Namra yaba Anty Amarya gaisawa da ƴan gidan, wato su Neina har take faɗa musu ai tare da Abbah ta suke yana waje.


“Haba kije kice ya shigo mana ya zai tsaya daga waje”


Sannan Anty Amarya ta nufi ƙofa da jimmar faɗa masa sunce ya shigo. Sam sam sam Lamido be jidaɗin ganin iyayen Namra ba, duk wani farinciki da son da yake ta shirya da iyayenta sai yaji baya sonsa, musmaman yadda zuciyarsa take raya masa Yarima ne silar hakan,ko ba komai yasan Namra zata fi son Abdool sama da shi, shi ko yana da ƙudurora da yawa akanta, dan ya ɗaukarwa kansa alƙawarin sai ya nuna mata banbancin dake tsakaninsa da Asim na kyauwon hali, duk da suna ɗaya zasu amsa a fagen talauci,so yake Namra tasan ba duka talaka ne mai irin zuciyar Asim ba.
Wani abu yaji yazo ya tsaya masa a zuciya, tun ba aje ko ina ba, yana jin ya fara missig Namra, zata nisanta da shi yanzu, kuma ba lallai bane ya sake ganinta.


Sallama Abbah ce ta katse masa hanzari, ya dawo daga duniyar tunanin da yake ya miƙa idonsa i zuwa inda ƙofar gidan take yana kallon Namra dake riƙe da hannun Anty Amarya. Saman shimfiɗar da Neina tayi musu suka zauna, ita kuma ta zauna a saman ɗaƴar tana gaisawa da Abbah.


“Amman na jidaɗin da kuka zo gurin ƴarku, Namra bata da tunani sai naku, kullum cikin kuka take, nasan babu iyaye na gari da zasu ƙyale ƴarsu, matuƙar ƴar nan ta sunna aka haife ta, su iyaye dole sai kana kai xuciya nesa, sau da yawa ɗa zai aikata abu kai ka daurewa zuciyarka ka ƙyale gudun kar ɗan nan ya faɗawa halaka, kuma idan mutum ya gane kuskurensa babu a abunda ya cancanta da shi sai yafiya da kuma nuna masa illar abun nan da ya aikata, ƴaƴa da mata kamar kiwo ne, ko wanne za a tambaya ubngidansa akan irin kiwon da ya bawa iyalansa, yadda mu muke da haƙƙi akan ƴaƴanmu haka muma ƴaranmu suke da haƙƙi a kan mu. Wallahi kun faranta min zuciya dana ganku da ƙafafunku kun tako cikin gidan nan ku tafi da ƴarku, a halin da Namra take da ace bata haɗu da mu ba da zata iya faɗawa ko wane irin hali, saboda bata san kowa a Kaduna ba, kun ga ko a nan rayuwarta tana cikin haɗari”


“Gangar jikina ne kawai a gida, amman kullum zuciyata tunanin Namra take, ban san aurenta ya mutu ba, da wallahi ba zata zauna ko ina ba sai a gida, kowa kuwa mahaifinta zai zaɓi rabuwa da ni ne, kullum a tunani tana can yana azabbatar da ita, nasan Halin Namra idan abun duniya zai cita ya cinye ba zata faɗawa kowa ba, itace babba amman ita marar wayo da tunani a cikinsu, da wannan tunanin naƙe bachi naƙe tashi wannan tunanin ya kan hanani sukuni wani lokacin, shiyasa ƴan'uwanta suke ganin kamar itace silar ciwon nan nawa, kullum cewa suke, Namra ce ta kwantar da ni, duk da nasan gaskiya suke faɗa amman a haka zan musa musu, kudun kar suce nafi sonta sama da su, ni ko kullum tunanin kar na mutu na barta a cikin wannan halin”


Namra ta kama hannayen Anty Amarya ta riƙe.


“Ba zan sake aikata abu makamancin wannan ba Anty, ni ba zan sake aure ba balle har na tsallake wani sharaɗi na ku, hawayenki ba zai sake zuba a kan Namra ba”


Uffan Abbah be ce ba, idonsa na kan pure water da Maryam ta aje musu mai tsanyi, wadda ta siyo shago.
Maganar duk da suke tana cikin kunnensa, sai dai be jin zai iya furta wata kalma data ɗanganci labarin da suke. Ba laifi sun ɗan yi fira sosai da Neina, kamar waɗanda daman can san juna, sai duk firar da ake Namra na cikin jikin Anty hawaye sun ƙi su tsaya mata. Abbah ya kalli agogonsa tare da miƙewa tsaye yana faɗin.


“Ya kamata mu tafi yanzu, da safe Namra zata zo ta muku sallama kamin mu kama hanya”


Yana faɗar hakan ya saka takalminsa ya nufi ƙofar fita, Lamido da kallo ya bishi yana aunasa a matsayin lallai zai iya aikatawa Namra haka, da ga alamu yana ji da kansa, ko kuma be gama hucewa bane oho.


“Allah sarki Namra, ashe kuwa zamu yi marmarinki”


Uwani ta faɗa cikin rashin jidaɗi, dan har ga Allah ita tana tunanin rabuwa da Namra dan yanzu sun ɗan tsaba da juna.


“Nima ai sai na yi Marmarin ku, mutane masu karamci da sanin darajar ɗan'adam”


Namra ta furta tana mai jin kamar karta tafi ta barsu. Har bakin mota Neina da Uwani da Maryam suka rakosu, ko da suka fito har Abbah ya shiga mota, Anty Amarya ta fara shiga sannan Namra, su Neina na ɗaga musu hannu direban yaja mota.




RASHIDA POV.


Ta rame sosai ta koma kamar ba ita ba, tun ranar da taje gidansu su Teema bata sake leƙa ko ina ba, gurin aikinta sun yi kira sai ta tura musu saƙon bata da lafiya ta email, sannan ta kashe wayarta, saboda yawan kiran da ake mata akan auren Teema da tsohon mijinta. Bata iya cin komai banda tea, sai ɗan lemu wani lokacin, kullum a kwance take salla ce kawai take tashinta. Musamman jiya ta san itace ranar ɗaurin auren Teema da rabin ranta 😢. Babu wanda yasan inda take balle azo gurinta, Momi kuma ta juya mata baya da duk ƴan gidansu, lallai sai yanzu ta gane duniya ta juya mata baya, shiyasa ake cewa idan kana son duniya da yawa ka fara barinta kamin ta barka, idan har ita ta fara barinka to ba zaka ga da kyau ba. Yanzu kan ta fara gane baƙin duhun da yake bibiyarta sai dai bata san iya inda zai tsaya mata ba. knocked ɗin ƙofar falo da taji ana yi ne yasa ta unƙurin tashi taje ta buɗe. A zatonta Momi ce ko wata daga cikin ƴan gidansu, ga mamakinta sai ta ga Asmee.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Rashida haka kika koma?”


Rashida ta sakar mata ƙofar ta dawoɓsaman cushion ta zauna, Asmee ma zama tayi a kujerar dake fuskarta ta Rashida, tana yayw mayafinta.


“Haba Rashida, na san kina son Hilal kuma na san Teema bata kyauta miki ba, amman idan ta samu labarin halin da kika shiga ai daɗi zata ji, kin ware kanki ke kaɗai kina saka damuwa a aranki”


“Ya akayi kika gane gidan nan?”


“Gidanku naje aka kwatantamin nan, zulfa'u da Rafia duk sun je gida sai a ce musu kin yi tafiya, nima ban da na matsa da ba za a faɗa min inda kike ba, dan Allah Rashida ki cire damuwar Teema a ranki”


“Ba auren Teema abunda yake damuna a yanzu ba, irin rayuwar da zata shimfiɗa a cikin gidana yafi damuna, ita zata reni ƴaƴana, kuma wallahi azzalumace zata iya yi musu komai, gata ta iya neman magani zaya iya raba su da ubansu”


“Toh ya zakiyi Wallahi Teema ta ci amana”


“Teema ta ci amana kamar yadda nima na ci amana, ta auren min miji kamar yadda nima nayi taraiya da mijin aminiyata, Asmee duk halin dana shiga a yanzu mijin ki ne sila...”


Asmee ta gyara zama.


“Ban gane ba. Kamar ya mijina ne sila?”


“Kin ci amanar mijinki kin bada kanki ga wasu saboda neman mallakar miji, ahi kuma ya ci amanar ki ya bada kansa gare ni, mijinki shi ya saka min cutar hiv, saboda kin samo gurin wannan bokan kin saka masa, tun daga lokacin da naji kince ana zargin bokan da cuta, hankalina ya tashi saboda nasan bayan mijina, mijinki ne na biyu da nake mu'amala da shi, sanadin hakan naje nayi gwaji, aka tabbatar min da ina ɗauke da cutar, har Hilal ya gane gaskiya yaje yayi gwaji shi baya da shi da ƴaƴansa, da matarsa, sanadin hakan ya sake ni, shi kansa mijinki be san da hakan ba, amman ke nasan kin san kina ɗauke da cutar, saboda haka na ci amana, nima Teena ta ci amanata, sai dai ban san makomar yarana ba, ban san wane irin tarbiya zata basu ba”


Miƙewa Asmee ta yi tsaye gume na keto mata tashin hankali ya hana hawayen dake maƙale a idonta zuba.


“Duk yarda da Amincin dake tsanina da ke, ace kin rumtse ido ta auren ki kin yi zaman banza da mijina? Ina tunanin nayi abunda zan iya na hanasa aure, ashe na kashe macijina ban tsare kan ba, wallahi ko a mafarki ban za ci zaki min haka ba, ƴar iska macuciya, ai wallahi sai kin ga abun ki, dan Teema sai ta salwantar da rayuwar ƴaƴanki... Kuma Allah ya isa tsakanina da ke!”


Ta fisgi gyalenta ta fice a fusace. Rashida kan kuka kawai take, tana mai jin tsantsar damuwa da nadama a zuciyarta. Kuka tayi sosai, daman kullum cikin yinsa take, sannan ta koma ɗakinta ta ɗauki kkaton hijab ta saka ta saka niƙab ta ɗauki makullun motar ta ta fice.






ABDOOL POV.


Tun da ya baro ƙofar gidansu Lamido cikin farinciki yake, dan yasan sahibarsa ma tana can tana farinciki, kuma yasan zai samu ladar sulhunta uwa da ƴarta, horn ɗaya yayi aka buɗe masa gate, cikin nishaɗi yayi fakin motarsa ya fito da murmushi kamar wanda aka yi ma albishir.
What he saw a bakin ƙofar shiga part ɗinsa was surprise him, kurciyar daya gani a abuja itace a nan? Haske ne ta ko ina a gidan kamar rana, hakan ya bashi damar ganin layan dake wuyanta.


“Umar...”


Ya ƙwalawa Mai kula.da gidan kira, sai ga shi da gudu yana amsa kiran da yake masa. Keys ɗinsa ya miƙa masa.


“Zagaya ta baya ka buɗe ƙofar nan a hankali, kurciyarta nake son ta shiga ciki mu kamata”


“Ranka ya daɗe ai za'a iya halbeta da danƙo”


“Kana da danƙon ne? Kasan yadda zaka halbeta bata tashi ba?”


“Eh za a iya saitawa, amman ranka ya daɗe kurciya da dare baka san me take nufi ba, balle kuma ga laya a wuyanta”


“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”


“Toh”


Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.


“Namra”


Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.


“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”


Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.


“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”


Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.






KALSOOM POV.


Hannu ya kai ya shafa fuskarta.


“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”


Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.


“Zan shiga wanka”


Hannunta ya riƙe.


“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”


Ta saka mashi kuka.


“Baka min komai ba, kawai dai...”


miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.


“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”


Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.


“Ina son zogale”


“Okay”


Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.






ASIM POV.


Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.


“Hajiya na saka kuɗin”


“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”


“Okay na zo kenan?”


“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”


“Toh ya za'ayi kenan”


“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”


“Okay what time zan zo?”


“An jima da yamma”


“Okay Allah ya kai mu”


Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.


“Ta tabbata Nably ƴarki ce”


Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.


Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.


“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”


Ya ɗan sosa kansa.


“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”


“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”


“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”


Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.


“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”


Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.




________________________________


BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️


*77*


Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.


“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”


“Akan mi, mi zan miki?”


“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”


“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”


“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”


Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.


“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”


Hawaye ya cika idon Rashida.


“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”


“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”


Ta share hawayen da suka zubo mata.


“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”


Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta

Please Login or Register in order to submit comment