Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kalaman da Teema tayi masa sun ƙatse mata duk wani hanzari da take da shi, har ta samu kanta da nauyin baki kasa furta mata komai, abun ka da mai sauri karaya nan da nan sai ta fara hawaye.


“Kin fi kowa sanin yadda na ke son mijina Teema, amman kika min zagon ƙasa har kika ja hankalinsa akan ki, waya sani ko asiri kika masa?”


Teema ta yi ƴar dariya.


“Wallahi ban masa magani ba, uwarsa cw da haɗa mu, kuma yaga yana so na, nima ina sonsa shikenan fa, amman ki kwantar da hankalinki zan ƙwatar miki ƴancin ki, kuma zan miki hanyar da zaki dawo gurin mijinki”


“Allah ya isa tsakanina da ke, kin ci amana ta kin min zagon ƙasa Teema wallahi ba zan taɓa yafe miki ba”


Tana kaiwa nan ta juya ta fice fuskarta da hawaye.
Wani banzan tsaki Teema taja.


“Aikin banza ai daman Allah ishenshe ne, kinji na roƙe ki ki yafe min ne, ni wallahi ko ubanki yayi min aurensa zan balle wani mijin ki ex-husband mtssssssss”


Rashida ya fito ɗakin idon kowa yana kanta, wasu na Teema rashin gaskiya wasu kuma suna ganin bata yi laifi ba, daman yanzu ko mijin ƙawarki ne aure shi za'ayi balle ita da har ta fita gidan miji. Bama kamar hawayen da suka gani a fuskarta. Ita kam ba ta nasu take ba, haka ta fito abunda yake ranta ya isheta, damuwarta tayi mata yawa.


Har ta shiga motarta ta fara driving bata da wani kuzari, hawayen da take kuma sun ƙi su tsaya mata. Wayarta da ke front seat ta yi ƙara alamar kira, kallo ɗaya ta yi ma wayar ta ɗauke kanta tana cigaba da rera kukan da bata san ranar tsayawar hawayenta ba, Alh Bashir ne, tasan shi ma ba zai wuce ya labarta mata Hilal zai auri ƙawarta ba, ita mamakinta ma ko Hilal ya manta Teema ƙawarta ce? Tsayawa tayi tunanin duk da tasan bata da ƙawaye barka tai hakan amman ba zai rasa sanin Teema ba, wata ƙila yayi mata haka ne dan ya rama abunda ta yi masa. Haka zuciyarta take nuna mata, cikin sauri ta ɗauki wayar ta faka gefen ti-ti, tana tunanin abunda zata faɗawa Hilal, da kiransa zata yi, sai kuma wata zuciyar ta bafa shawarar aika mata da saƙo. Sannan ta jefar da wayar ta cigaba da tuƙinta tana kuka har ta iso gida.
Ga wayar sai ringing take, friends har da waƴanda suka daɗe basu kira ta ba, yau kiranta suke dan su ji ƙwan. Bata samu gurin faka motarta ba, saboda Motar Ummu Faisak da ke waje ta tare nata hanyar gareji, daman can gidan ba wani yarwantaccen gida ne ba, gida ne na zaman mutun ɗaya.


Ba ta damu da share hawayen fuskarta ba ta shiga falon a haka. Ganin Momi da Ummu Faisak yasa ta ƙara narkewa ta fashe da kuka har da faɗuwa saman kujera. Nan take Ummu Faisak tasa kuka ganin yar'uwarta cikin damuwa. Momi kan tsawa ta katsa musu daga ita har Ummu Faisak ɗin.


“Miye abun kuka ga hukuncin Ubangiji? Ba ke kika jawa kan ki ba? Ai kin yi arziki da sai da kika fita gidan miji ita zata shiga, kuma ba ƴar'uwarki ce ta ci amanar ki ba! Ai ke kika fara yi ma kan ki zagon ƙasa da kan ki, kika taka mutumcin aurenki kika je kika bada kan ki ga wanda ba muharramin ki ba, ke wannan ma be isheki ishara ba? Cutar da take jikin ki bata isa ta nuna miki Allah ɗaya ne ba? Ai cin amanar miji Rashida ba ƙaramin haƙƙi ba ne, mijina yana can yana fafutar neman abunda zai kawo miki ke da ƴaƴansa, amman ke kina can kina cin amanarsa? Aiki hauka ne? Nasan 95% mahaifinki ne ya ja miki shi da ya tsaya kai da fata akan sai kin yi aiki, amman be ce kije can ki yi lalata ba, ai ba ke kaɗai ce mace ma'aikaciya ba, akwai da yawa waɗanda suke kare mutuncin mazan su da kuma na ƴaƴansu da na su da na iyayensu, ba ga ƴar'uwarki nan ba? Ummu Faisak aiki take, ita bata lalace ba saboda ta san mutuncin kanta, ki ba abun baƙin cikin ki ba ne ace wani namiji wanda ba mijin ki ba ya san surar jikin ki? Kin ɗauki rayuwar turawa kin sawa kan ki, baki da lokacin tarbiyantar da ƴaƴanki, tufafi ko sai waƴanda kika ga dama kike sakawa, nan aka auro miki Kalsoom na zo ina yaba shigar da take irin tarbiyar da ta samu a gidansu, kika ce min na fi son ta, da ke, kika ce ina miki abu kamar ba ni na haife ki ba, a lokacin ruɗin duniya na ke guje miki amman idon ki ya rufe.


Dan baki da hankali zaki wanke ƙafafu kije gidansu Teema to ki ce mata me? Ki zauna ki yi wa kan ki karantun ta natsu, ki nemi yafiyar ubangijinki, kuma ki nemi yafiyar mijinki tun haƙƙinsa be cigaba da binki ba, dan duk abunda kika aikata da aurensa haƙƙinsa yana saman kan ki, kin yi sa'ah da Allah ya rufa miki asiri tun wuri, dan duk mai cin amanar mijinta sai taga ishara wallahi ko ba daɗe ko ba jima, kiyi taka tsantsan da duniya Rashida dan ta fara barinki tun kamin ke ki barta, karki yarda ki ci amanar wani, ƙara ke a ci amanar ki, balle kuma miji. Tashi muje”


Momi ta ƙarasa tare da kallon Ummu dake gefenta, kana ta miƙe tsaye idonta cike da ƙwallah, ranta kuma a ɓace ta fice, Ummu Faisak ta rufa mata baya tana cigaba da hawaye.


Hannu Rashida ta ɗora saman kai, tana kallon ɗakin kamar sabuwar mahaukaciya.


“Innalillahi Allah kasa mafarki na ke yi, Allah ka farkar da ni daga wannan mummunan bachi, Allah ka farkar da ni Allah, Allah ka tashe ni...”


Ta rushe da wani irin kuka tana dafe da kanta da take jin yana jujjuya mata.


HILAL POV.


_Hilal ka san wacece Teema kuwa, wallahi wallahi bokaye ta ke bi, kuma ta fi karfin iyayenta, karka aure ta Hilal dan Allah, ban yardar ta tarbiyantar min da ƴaƴaba, ka auri ko cece amman ban da Teema_


Yana gama karanta saƙon ya saki tsaki, ya aje wayar saman teburinsa, ya miƙe tsaye ya fice daga office ɗin.
Duk inda ya wuce ango ake ce masa daman wasu tun jiya ya basu iv wasu kuma sun samu labari, yana isa gurin karɓar results ya buɗe ciki ya shiga. Daya bayan ɗaya ya gaisa da su, sai tsokanarsa suke, wai ango ka sha mai.


“A'a ban sha fa da saura”


Sai duk suka sa dariya har shi Hilal ɗin da yayi magana, ɗaya daga cikin likitocin dake tsaye ward ɗin ya ce


“Doc baka da kunya”


“To kunyar me zan ji kowa ai yasan komai, kai bani results ɗin Amarya ta na gani”


“Amarya ko uwargida?”


“Amarya dai, to duka yaushe na yi auren ?ba ƙaddarori bane dai idan Allah ya kawo babu yadda za'ayi”


“Aiko yanzu na ke shirin kai naka result ɗin, dan kana tafiya Doc Ahmad ya wanka hoton ya ce ina kake nace ya kawo wannan albishir ɗin ni zan yi ma madam shi da kaina”


“Ai ana ɗaukarta Hoton ta sha mun kai na maidata gida, ita dai ciwo take ji, shiyasa kaga na masu na ƙarɓi results ɗin so that na san abunda yake damunta kar mu yi cuta daban magani daban, tun jiya kuka take min wai tana jin abu a mararta kamar dutse sai amai take”


Kamin ya miƙa masa results ɗin sai da ya miƙa masa hannu.


“Congratulations ba dutse ba ne alheri ne, sai dai idan ka duba zaka gani”


Ya karɓa zuciyarsa fari ƙal.


“Wow ka ce na yi aiki Alhaji...”


Sai duk suka kwashe da dariya. Shi kam be ma kula su ba hankalinsa ya tafi gurin Hoton.


“Six months i'm surprise, kwata kwata ban kawo wa rayuwata ciki ba ne, dan tace ƙasan mararta kuma ita pain her, ko tsayin kirki bata iya yi, jiya gaba ɗaya a rikice muka kwana”


“Yeah yayi mata kwance ne, baka ganin yadda yake, sai kun kula da shi sosai gaskiya, Allah ya raba lafiya”


“Amin”


Ya fice da sauri, ɗaukar wayarsa ce ta zame masa dole, ba dan haka ba , ko office ɗin ba zai koma ba, a gaggauce ya ɗauki wayar ya fice. @360 ya bar asibitin tsabar zumuɗi ji yake kamar ma ya rumtse ido ya gansa gida. Cikin ƙanƙanen lokaci ya isa, daman be sa ran zai tarar da ita falo ba, dan haka ya wuce bedroom ɗinta kai tsaye, kwance ya same ta ƙasa ta duƙunƙune da bargo sai rawar sanyi take. Wani irin tausayinta ne ya kama shi, sai ya aje keys da takardar dake hannunsa saman mirror, ya kwanta bayanta ya yaye bargon dake jikinta ya ɗora fuskarta saman nata, jikinta yayi zafi aosai amman hakan be hana shi rumgumarta ba.


Ta buɗe ido da ker ta ɗan taɗo kai ta kalleshi.


“Gadon baya min daɗi”


Ta faɗa da muryar ta nan ta marar lafiya. Lumshe ido yayi yana murmushi.


“i'm sorry dear it's all my fault”


“Dan Allah ka min allura ko zan samu sauƙi”


“Ke da samun sauƙi sai nan da five months”


Ta yi dauriyar sake kallonsa cikin idonta na marar lafiya.


“Whats do you mean?”


“Sweetheart ƴou're pregnant”


Ƙarfin halin tashi ta yi, sai ya riƙa ta tashi zaune da kyau, ya kwantar da ita jikinsa.


“Da gaske?”


“Yes Dear six months”


Ta yi saurin kai hannu ta taɓa cikin, yo hwr surprise cikinta be yi girma ba, impact babu wani alama na ciki na jikinta idan ba wannan ciwon da ta yi ba.


“Amman ko dai one months...?”


“No wata shida dai, kin ga hoton da aka miki ɗazu can”


“Amman na yi menstruation last months fa”


“Nima abunda ya bani mamaki kenan, but kin tuna wacan lokacin da kika samu ciki ya ɓata? Ina tunanin shi ne ya kwanta miki, sai yanzu ya tashi, daman ana samun hakan nan wani lokacin, that's why we need to take good care of it, saboda mu samu ya dawo dai-dai”


Ɗagowa ta yi ta kalleshi, hawaye suka zubo mata.


“Congratulations”


Sai ya aika mata da kiss a goshi.


“Thank you Dear”


Ta ɗora kansa saman wuyanta, hannayensa zube saman cikinta.




ASIM POV.


A can ya kwana gurin Alhajinsa, da safe yasa aka kawo musu abun karyawa, sannan suka yi wanka, yadda Alhaji Nasir ya shirya cikin manyan tufafi ba zaka kalleshi kace yana aikata wani mugun abu ba.


Asim ma ya fito cikin ƙananan kayana kamar wani mutumen arziki, hankalinsa kwance zuciyarsa cike da natsuwar abunda ya aikata. Ba laifi yanzu be ji zafin da yaji da farko ba, sai dai har yanzu be fara jin daɗin da Alhaji Nasir da Hajiya Sadiya suke labarta masa zai ji ba, wata sai ya ƙara gwarewa akan harkar.


Alhaji Nasir ya saka turare ya kalli Asim ya ce.


“Har yanzu baka ƙarasa ƙwarewa ba a kan harkar nan, ya kama a sama maka kasuwan turawa nan ka kalla,dan ina son haɗa ka da manyan mutane ta yadda zaka ƙara gwarewa, ka ci moriyar ƙurciyarka”


Wani daɗi ne ya lumluɓe Asim, dan yasan kuɗi zai samu, daman burinsa kenan ya yi kuɗi.


“Zan ƙoƙarta Inshallah, ina godiya sosai”


“Idan kana da buƙatae wani abu ka riƙa min magana, dan yanzu nauyinka ya dawo kai na, shiyasa na tura maka wannan kuɗin dan ka samu na ƴi ma kan ka hidima, amman fa a riƙe sirri, kuma ni ina da kishi gaskiya ɓana son ka yi mu'amala da wani idan har ba ni na haɗa ku ba”


“Zaka same kamar yadda ka tsammace ni inshallah”


Daga haka Alhaji Nasir ya miƙe tsaye.


“Ni zanje Abuja ajima kaɗan, yanzu zan leƙa gida ne”


“Ba matsala Alhaji Allah ya kiyaye hanya”


Sai da ya fita da kusan mintuna latatin sannan Asim ya fito daga gidan ya nufo gida. Ko da ya shiga Mama har ta soya nasa dankali da ƙwai ymta haɗa masa tea mai kyau dan tasan shine favorite ɗinsa, shi kam ko kallon su be yi ba, dan yanzu ya wuce gurin kwaɗayin irin waɗannan, beside yama riga da ya ƙarya gurin Alhaji Nasir.


“Nayi tunanin zaka dawo jiya muka ta jira baka dawo ba, na kira wayarka kashe”


“Eh masallaci na kwana, bayan gama sallah isha'i daman na kan yi haka ko a gida yanzu saboda ina nafila dare”


Yayi mata ƙaryar ne saboda bashi da hujjar cewa ya kwana a wani guri bayan kuma ga gidansu. Ita kam daɗi ya mamaye ta.


“Ai haka na da kyau, ƙara a riƙa godiyar Ubangiji, sai kaga yana ƙara maka, kuma ya kamata ka samu lokaci muje gurin Malam na Allah ya baka ƙaiƙayi koma kan masheƙiya saboda maƙiya”


Miƙewa yayi tsaye.


“Kai Mama ni duk bana da lokacin wannan, yanzu dai ga kuɗi nan ki rabawa maƙota, idan na samu gidan sai a faɗa min”


“Toh ya yi Allah ya tsare min kai, amman har zaka koma yanzu? Jiya jiya fa ka zo garin nan ”


“Wallahi aikwai aiki a can, kuma ki ciri kuɗi ki buɗe account a bank zan turo miki kuɗi ki bawa su Baba sani, kuma ki faɗa musu anytime zasu iya jin kirana akan maganar auren nan”


Yadda yake mata magana kamar yana bada umarni ne. Wani jin kansa yake yanzu kamar minister. Ta so ya tsaya su yi fira amman bata samu dama ba dan ya nuna yafi son tafiya kamar wanda ake tsakala. Har bakin mota ta rako shi tana faɗar masa


“Yanzu sai iyayen Namra sun samu labari ka yi kuɗi, amman basu san ka sake ta ba, tun da bata zo gida ba”


“Dole ne ai su samu labari, ni nafi son haka ma”


Ya buɗe motarsa ya shiga. Tana ɗaga masa hannu har ya kama hanya.


Be tashi da wuri ba, dan ko da ya baro sokoto shabiyu har da kusan rabi. Ko da iya isa Katsina yamma ta yi sosai, sai dai Nably ta yi masa kira ya fi biyar dan jin lafiyarsa, Mardiya ma ta kira ta faɗa masa tana son ganinsa.
Yana isa katsina ya kira wayar Hajiya ya fara gaisheta, still ta faɗa masa tana birnin keebi, dan ya so ya fara zuwa ya gaishe da uwar ɗakin tasa ko zai goge laifinsa. Gidansu ya sauka yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sannan ya wucce gurin ƙanen dad ɗinsa wanda ya manta rabonsa da yaje can sun suna aikin ƙira kamin su haɗu da Hajiya Sadiya.


Su kansu sun yi mamakin ganinsa, daman suna jin labarin yayi kuɗi sama-sama a gurin jama'ah, bama abunda yafi basu mamaki kamar yadda kuɗin suka taso masa lokaci ɗaya. Sun yaba da motarsa da kuma shigarsa har suka masa fatan Allah ya tsare, a nan ya ɗauki kuɗi mai yawa ya bashi, abkan da suka yi aiki tare ya raba musu wani abu. Sai da Ƙanen Baban nasa ya rakosa zuwa gurin motar yake labarta masa dalilin zuwan nasa.


“Gida nake so a sama min kamar na miliyan biyar, mai kyau sosai”


Shin kam riƙe baki yayi jin Asim ya ambaci miliyan har biyar, yana mamakin ace yana da wannan kuɗi haka da yawa, a take zuciyarsa ta raya masa ba kuɗin halal ba ne, sai dai babu damar faɗa masa gaskiya dan yana tsoro, daman idan kana da abun hannu ana tsoron faɗa maka gaskiya balle Asim da yasan zai iya yin cikinsa da masifa.
Da zimnar idan an samu za a kira shi a sanar da shi suka aje, sannan ya yi masa sallama ya kama hanyar gidansu Mardiya.


YASMEEN POV.


Tana shiga ta aje kwalin, ta koma kan Adnan daya sauka ƙasa yana zare zaren shoes ɗinsa, da hannu ɗaya but still hannunsa ɗaya yana gurin sai susa yake. Yana ganin Yasmee yayi saurin dainawa, yana wara idonsa na marasa gaskiya.


Hannu biyu tasa ta ɗauke shi sai ta zauna ta ɗora saman jikinta tana murmushi.


“Aya tell me mi Dadee yake ma ka?”


Rufe ido ya yi yana dariya, ita kuma ta maida kunnenta gurin bakinsa.


“Faɗa min mana ko mu ɓata”


“Ba zaki faɗa ba?”


“Ba zan faɗa ba”


“Wannan abun ƴake sa min a nan”


Ya nuna mata gurin fitsarinsa, sai ta sauke shi ƙasa.


“Nuna min mi yake sa maka”


“Wannan abu yake samin a baya, sai yacw na kwanta, kuma da zafi sosai yace idan na faɗa sai ya yanka ni da wuƙa ƙamar yadda ake yiwa rago”


Ya cire wandonsa ya nuna mata. Wani irin faɗuwa gabanta ya yi, a take ta samu kanta cikin wani irin tashin hankali, wanda bata taɓa sa masa rana ba, a take zuba ta fara karyo mata, numfashinta yayi mata mugun nauyi, sai tayi saurin rumgume Adnan dan kar ya ga hawayen dake ƙoƙarin zubo mata.


“Your Dadee did a great thing”


Ta soma shafa bayansa cike da tausayinsa kanta da kuma nata, sai dai ko kaɗan bata son ya ga hawayenta. Sai ta sauke shi ta mike tsaye.


“Bari na zuba maka abinci ka ji”


Ta yi saurin juya ta bar ɗakin. Kitchen ta shiga sai ta samu mai aikinta tana yanka salat da tumatur.


“Jeka kawai zan ƙarasa”


“Toh”


Aje ragowar da ke hannunta ta fice. Hannu biyu Yasmin tasa ta riƙe kitchen cabinets sai ta fashe da wani kuka marar sauti. Ƙafafunta kasa ɗaukarta suka yi, sai gata ƙasa jikinta har karkarwa yake.


“Innalillahi wa'inna ilaihi”


Shine abunda take ta maimaitawa, gudun kar kukan ya ci ƙarfinta. Kulolin ta buɗe ta ɗauki plate ta zuba masa white rice and pepper soup, ya saka nasa spoon, sannan ta ɗauki ruwa ta wanke fuskarta ta fito tare da abincin.


Ɗakinta ta nufa riƙe da abincin, hawaye sun ƙi tsaya mata. Aikin baban giwa ta samu yana yi, dan har ya buɗe kwalin data aje, azatonsa wani abun ci ne a ciki ko chocolate ganin. Ita bata ma bi ta kan kwalin da ya fasa ba, shi kawai take kallo har ta aje abinci, tausayinsa duk ya kama ta, sai ta riƙo hannunsa ta karɓi takardar dake hannunsa ta aje gefe. Taja shi jikinta, ta rumgume.


“Momee babu komai a ciki”


Cikin kuka ta amsa shi.


“Ba na ka ba ne, na Dadee ka ne”


Kuka take sosai tana ta ƙoƙarin ƙaryata abunda zuciyarta take son yarda da dashi, can kuma ta sake shi ta janyo abinci ta aje masa a gabansa. Ta zauna ta tsare shi da ido hawaye na cigaba da mata zuba.
Kamar kuma an tsikare ta share hawayen idonta, ta miƙe tsaye ta ɗauki wasiƙar da jimmar maidawa cikin kwalin, babu abunda ya bata mamaki kamar ganin da tayi babu komai a kwalin sai wasiƙa, babban kwali kamar wannan a'ce babu komai a ciki sai wasiƙa, to me wasiƙar ta ƙumsa ne haka?
Zaunawa ta yi a kusa da kwalin ta warware wasiƙar, gabanta sai faɗuwa yake ta soma karantawa.


_Zuwa ga Azzalumin mutun, macuci mayaudari, nasan kana nan raye kamar ƴadda nima na ke raye, ko kuma na ce ka so ka halaka ni Allah be baka dama ba, ka yaudare ni Uzair kace Namra zamu ma Asiri ashe ka haɗa kai da ita ne ni kuka yi ma wannan asirin na bar gida, ban taɓa gane haka ba, sai a yanzu da nake da buƙatar da dawo na kasa, Wallahi Wallahi kaje ka karya wannan asirin ko kuma na sa a kashe ka, dan kasan na san ka, kuma na san inda kake, ni ko baka san inda na ke ba a yanzu, kuma ina tabbacin baka san ko wacece ni ba_


Sai number wayarta daga ƙarshe. Abunda ya tsayawa Yasmin a rai, wacece wannan yarinyar? Sannan mi suka ƙulla da Namra? Mi mijinta ya aikata ne?
Ta miƙe tsaye cike da rashin kuzari, abubuwa biyu sun tsaya mata a lokaci ɗaya kuma akan mutun ɗaya. Wani tunanin ne ya zo mata, da sauri ta ɗauke kwalin ta fita da shi ta saka cikin shara, sai ta dawo ɗakin ta ɗauki wasiƙar ta mayar da ita a yadda take, sai ta je cikin littatafanta na aiki ta samu wata silver paper, ta yi wrapping ta naɗe wasiƙar ciki da kyau ta saka salatif, ta kai masa ɗakinsa ta aje masa.
Tana shigowa ɗakinta jiri ya kwasheta, ta faɗi dafe da kai.






ANTY AMARYA POV.


Cikin ƙarfin hali ta unƙura ta nufi part ɗin Abbah, dan yau bata jin daɗin jikinta sosai, wata ƙila fever ɗin ne zai sake dawo mata. Yadda ta tararda Hajiya Barau da Abbah a falon ya ɗan tashi hankalinta, dan a zatonta ya aika kiranta ne dan su tattauna maganar auren da ake na su Hindatu da Maryam. Zaunawa tayi tana kallon yanayin Hajiya Barau da ta riƙe baki tana kallon Abbah, sam bata lura da takardar dake hannun Abbah ba sai da ya mika mata takardar.


“Wai wasiƙa ce daga Faɗar Mai Martaba sarkin Katsina, wai ana bukatar gani na gobe”


“Subhanallahi miya faru?”


Anty Amarya ta tambaya zuciyarta na rawa fat fat fat.


“Wallahi ban sani ba, ni abun ya ban mamaki mi na aikata da Sarki Katsina zai aiko kirana? Ina ma na san shi?”


Hajiya Barau ta mere baki, har da wani ƙis take.


“Allah yasa ba Namra ta yi maka janye janye ba”


Kallo ɗaya Anty Amarya ta yi mata ta ɗauke kai, maganar na sukarka, ta miƙe tsaye ta bar musu falo.

“Zan sa ana ma min jirgin da zai je Katsina gobe da wuri zan sauka dan jin ko minene”


“To Allah yasa mu ji alheri, Amman da ka kira Abdulraman (Baban ɗansa) kun je tare, kar ka je kai kaɗai”


Ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman ɗaya, Yana sosa gemunsa da hannunsa.


“A'a da Larai zan je (Anty Amarya)”


Uffan Hajiya Barau bata ce ba, dan maganar bata mata daɗi ba, sai kawai ta miƙe tsaye ta fice daga falon.




___________________________________________


There are no words to explain how sorry I am. Nasan duk abunda zan faɗa muku ba zaku yarda ba, wallahi i'm kind of busy those days, ku yi Hakuri dan Allah ku gafarta min Love you all Fisabilliah 🌹




I dedicate this chapter to Hajiya Ramatu, Mrs tijjani, My Asmee, Ahmad Ismael. I really did not know how will to write in words! But your gesture is such 😘 Thank you very much Allah ya ƙara arziki, ya bar zumunci.♥️
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *76*


“Me kike a nan?”


Ya tambaya yana haɗe fuska. Bayanta ta nuna ba tare data juya ba, sai dai bata san abunda zata faɗa masa ba. Ya nunata da phone ɗinsa.


“ I know kin karanta wasiƙar nan Yasmin”


Still wata kalma bata fito daga bakinta, wani kallo take masa kamar mai nazari. Raɓawa yayi gefenta zai wuce sai kuma tsaya yana kallonta ido cikin ido.


“Ba sai mun yi playing wannan game ɗin, nasan ke lauyer ce”


Da kallon mamaki ta bishi, ta kasa gasgata abunda kunnuwanta da idanunta suka ji mata. Me yake nufi da Namra bata zame masa matsala ba ita ba zata zame masa ba? Wacece ita? Da waya yake waya?


Da sauri ta rufa masa, sai ta same shi sitting room ya haɗa kansa da guiwa ya dafe. Tsaye tayi masa aka.


“Me waɗannan abubuwan suke nufi Uzair? Wacece wannan ? Mi kuka aikata kai da Namra? Da wa kake waya?”


Ɗagowa yayi ya kalleta, idonsa sun kaɗe alamar damuwa da ɓacin rai na tare da shi lokaci ɗaya.


“Miyasa kike son saka kanki ga abunda idan kika ji zai iya zame miki matsala? Miya kike son saka kanki ga abunda be kamata ya dame ki ba?”


Ya tambaya muryar ƙasa ƙasa kar ba komai. Zama tayi kusa da shi tana masa kallon mamaki.


“Ni matarka ce Uzair, damuwarka damuwata ce, Namra kuma ƴar'uwata ce, be kamata ka ɓoye min komai ba, please tell me maybe i can help”


ya shafa fuskarsa yana cikama bakinsa iska.


“Is about some business da zamu yi da yayanta, shine take min sheri, shine nace Namra bata zame min matsala ba ita zata zame min yarinyar da ta yi min ƙazafin Luwaɗi”


Wani ɗan murmushi tayi mai cike da rainin hankali, shi kansa ya fuskanci hakan.


“To be frank i read the message, Uzair you can't hide the truth jus...”


Yayi saurin riƙa hannayenta jikinsa a mace.


“Yasmin trust me please, kin san ina son ki”


“Ba maganar so ko ƙi muke a nan ba”


“Just promise me ba zaki bar ni ba”


Hawaye sun zubo mata.


“Idan har zargina ya tabbata a kan ka dole ne zan rabu da kai, ba zan iya zama da mutuemn daya zaɓi saɓon Allah sama da tsoronsa

Please Login or Register in order to submit comment