Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ledoji a gabansu amman sun riƙe baki sai mamaki suke, da alama akwai abunda ya faru.


“Lafiya?”


Maryam ta riƙo hannunta.


“Ke ƴar gidan Abbah wai Amira ta dawo”


“Amira kuma? Daman tun tafiyar da ta yi bata dawo ba sai yanzu?”


“Wallahi sai yanzu, kuma jiya ita ma ta dawo kamar ke”


“Amman kun ji wani abu game da ita?”


“A'a nima Iklima ce take faɗa min ta dawo”


Anty Amarya ta ce


“Allah ya kyauta”


Duk suka amsa da Amin.


UZAIR POV.


Yana shiga bedroom ɗinsa ya fito ya nufi na Yasmin dan yana son ya bincika ko da akwai sauran abunda ta boye, jikinsa na bashi ba saƙon wasiƙar ne kawai ba. Bincike ya fara mata cikin durowoyin ɗakinta kama ya koma gurin wasu takardu da suke gefen gadonta, be samu abunda yake so ba, sai kaiwa ya juya ya fita ya nufi wata ƴar ƙaramar durowarta da take aje takardun aikinta da littafanta duk ya bi ya watsar sai bincike yake mata. Wani abu ya ji ya tsoki tsararsa, kamar an soma masa mashi a kunkuru, tun yana juriya da riƙe kunkurun nasa har ya ji abun ya ƙara sukarsa da wani mugun zugi, wata zarananniyar ƙara ya saki yana jin abun masa ƙasa cikin ƙashin ƙafafunsa, ihu kawai yake yana mirgina, abun ba kyau maza a ƙasa😖


Da gudu mai aikinsu ta so kansa tana tambayar ba'asi. Ganin abun ba na banza ba ne ƴasa ta fita neman mai gadi ko zai iya taimakawa. Ko da Mai gadin ya shigo Uzair wani abu yake kamar mai ɗaukar rai. Da sauri Mai gadi ya kira Yasmin ya faɗa mata abinda yake gudana.


YASMIN POV.


“Zan turo maka number ka kira mahaifiyarsa ka faɗa mata”


Amsar da Yasmin ta mayar masa kenan ta katse kiran, ta aika masa number sannan ta cigaba da kuka tana zanawa mahaifiyarta abubuwan da Uzair yake mata wanda hakan kawai ya isa ya tabbatar da gaskiyar abunda ya yi ma ɗanta, bayan ta fito gidansu Namra ta nufo gidansu dan ta na jin bata buƙatar komawa gidan a yanzu.


“Ko ma minene shiru ya kamata ki yi ki rufawa mijinki asiri”


“Irin wannan rufa Asirin ne yasa mata da yawa maza suke cutar da su, idan aka muku fyaɗe ko aka yi ma ƴaƴansu, wannan abun yana cutar da mata da yawa, mu muke faɗar a daina ɓoye abu a riƙa fitowa a ana faɗa yau kuma sai a same ni da wannan aikin na ɓoyewa? Ɓoyewar nan da ake shi kw basu damar ƙara aikata abunda suke aikatawa, at least ko da ba a hukunta su ba, duniya zata kunyata su kuma asan ko su waye, ban ga dalilin rufawa Uzair asiri ba ko da kuwa ubana ne balle mijina, ina yawan faɗar cewa ni dai i would never in my life encourage anyone to live with an adulterer tun da har Allah ya ce a jifasu su mutu, they are as good as useless to be seen alive in this world, sai kuma na zama ni ce zan rufa masa asiri miye amfanin aikina?”


“Nidan indai zaki ɗauki shawarata ban ga abun burgewa ga mace ta kai mijinta kotu ba da sunan wai yayi ma ɗansa fyaɗe, kina da hujja ne?”


“Ko bana da ita dole zan samo ta”


“Ni kam ba da yawun baki na ba Yasmin wannan sam be dace ba, idan ma zama ne ba zaki iya da shi ba, sai ki nemi ya rabu da ke kawai ki hutu”


Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”




AMIRA POV.


“ji na yi gidan nan ya isheni ina ta jin kamar idan ban gudu ba wani abun zai iya faruwa da ni. Ban tsaya ɗaukar komai ba sai kuɗi, tun daga lokacin da na bar gidan nan nahau mota na kama hanya ban sake sanin inda nake ba, ban san inda direba ya sauke ni ba ban san ya nayi rayuwa ba, sai a ƴan kwanakin nan da wannan sojan ya tsince ni a bolar gidansu, shine yayi ta min addu'ah da komai har hankalina ya dawo, na faɗa masa inda nake ya saka direba ya kawo ni gida”


Duk kai suka girgiza cike da tausaya musamman Ammy da ke kuka kamar yadda Amira ta ke yi.


“Amman Namra ta ci amanar abota, ai gashi nan ta fara ganin abunta, ɗazu-ɗazu hajiya Haulat ta ƙira ta faɗa min ita ta dawo gida aure ya mutu, kuma ance can gidan auren ta ci kwakwarta”


Salman Big bro nasu ya kalli Ammy dake wannan maganar yana faɗin


“Ai ba laifinta ba ne, ita Amira ai cin amanar ta tashi yi, da yanzu da gaske ne idan an sakawa Namra wannan abun maganin zai kamata ai kim ga ita ta ci amana kenan, waya sani ma ko koma miki ne yayi, a haɗa baki da ke a sace ta har a ayi mata ƙazafi, wallahi kun ci amanar juna ke da ita”


Abban Amira ya ɗaga masa hannu cikin ɓacin rai.


“Idan kasan bakin ka ba alheri zai faɗa ba, ka tashi kawai ka bar falon nan. Allah zai saka miki Amira zura mata ido kawai daga ita har ɗan'uwan na ta”


“Wane irin a sa muku ido? Aja mata haƙƙinta dai, babu irin abunda ba'ayi ba amman yarinyar nan ita da mahaifiyarta suka tsaya kai da fata akan babu hannunsu a ɓatan Amira, aka kiɗa aka raya aka daka yarinyar ta ƙeƙashe ƙasa tace bata san gaibu ba akan ɓatan Amira sai yanzu kuma gaskiya ta bayyana za'ace a ƙyaleta”


Taɓe baki Salim yayi ya miƙe tsaye ya fice daga falon.


“Babu wani haƙƙi da za a ja mata ku zuba musu ido kawai, ko bayan rage kika zagaya kika ɗauki wani hukunci sai na ɓata miki rai Wallahi, tun da na ce a bar maganar nan barinta shine ya fi kawai”


Ya miƙe tsaye ya fice daga falon. Kuka sosai Amira take, sai dai ba kuka dawowa gida ba, kukan rabuwa da Abdool tana jin kamar zata mutu idan ta tuna baya kusa da ita a yanzu.


ABDOOL POV.


Ya ware hannayensa.


“You see Ummi na faɗa miki Mai Martaba bashi da matsala, na zauna na fahimtar da shi kuma ya fahimta”


“Hakan na da kyau ai, sauran yarinyar ko?”


“Wannan ba matsala ba ne, zan ji da shi, so na ke sai an kwana biyu sai naje na ganta ko?”


Ummi tasa dariya, the way da yake mata maganar kamar wani ƙaramin yaro.


“Allah ya baka sa'ah”


“Amin my happiness. This week zan koma aiki, hutun mu ya ƙare”


“Ai daman ai baka yi hutu ba, ina fatar da kana da number wayarta”


“Wallahi bana da ita saboda yarinyar akwai jan aji amman zan sa a nema min. Am ɗazu mun yi waya da mahaifiyar Amira ta isa gida lafiya ƙalau”


“Mashallah, yau za su kwana cikin farinciki, ita kanta zata fi sakewa”


Kafaɗunsa ya ɗaga irin ina ruwana ɗin nan. Ummi ta watsa masa harara.


“Bari yarinyar nan ta ƙi amincewa da kai, ta yi ta baka wahala”


Ya sa dariya.


“Haba Ummi karki min baki mana”


Ya miƙe tsaye ya fice yana dariya.


ASIM POV.


Da rana ya sauka sokoto, kai tsaye gidansu ya nufa, duk da be so sake dawowa garin ba tare da an canja musu gida ba, sai dai matsalar har yanzu ba a samu gidan da suke so ba. Mama ta yi mamakin ganinsa sosai tun da be kirata ya faɗa mata zai zo ba balle ta tanadar masa da wani abu.


“Wannan zuwa haka ba waya ga shi komai ba a tanadar maka ba”


“Ba komai nima zuwan ya kamani ne kawai”


“To Allah yasa dai lafiya”


“Lafiya ƙalau, na ji ance Namra tana garin nan ne, shiyasa na zo dan zan maida aurena ne”


Mama ta daki ƙirji.


“Auren ka Asim? Kai kam mi ya kai ka daga Allah ya raba da ƙaddara”


“Kin san tana da ciki fa na sake ta, ni gaskiya yanzu so na ke na maidata”


“Amman Asim kana ganin zaka iya tunkarar gidansu yanzu ka ce zaka maida aurenta, mahaifinta ai sai ya yanka namanka da wannan fitinanniyar ƙanwarta”


“Koma minene dai sai naje gidan, ai yanzu be isa ya wulaƙanta ni ba, dan na fi ƙarfinsa Wallahi”


Tattaunawa suka soma yi kan maganar aurensa da Mardiya da irin abubuwan da ya shirya, sannan ya bijiro mata da maganar samun gidan, a nan take labarta masa am samu wani a Abdullahi Fodio Road amman wai har miliyan uku, ita gani take kamar yayi tsada, waɗannan da ake samu kusa kuma duk bata son unguwar.


“Ƙar hakan ya dame ki, indai gida yayi miki za a biya kuɗi a saka komai sabo sai ku koma”


“Yanzu kana da har miliyan uku na gidanmu?”


“Akwai su, zinari fa na ke siyarwa, kin san kuɗin da mike samu kuwa?”


“Allah ya ƙara arziki ai haka nake so, sai ka samu kawon ka Na Malam ku yi magana shi ya san inda gidan ya ke”


Haka suka wuni suna fira sallah ce kawai ke tashinsa, sai da akayi magariba sannan ya shiga yayi wanka ya shirya cikin ƙananan tufafi ya saka turare ya shigo ɗakinta.


“Mama ni zanje wani guri da abokina sai gobe zamu dawo”


“To Allah ya tsare hanya”


Ya sa kai ya fice sai ƙamshin turare yake. Be daɗe da fita ba aka aiko ana yi ma Hajara sallama.


“Je kace tana nan zuwa”


Sai Hajara ta tashi ta ɗauki kayan kwaliyarta ta gyara fuskarta sannan ta saka Hijabinta ta fice. Bayan fitarta Mama ta ɗauki tabarma ta shinfiɗa a waje ta zauna tana sauraren Garkuwa Fm.
Tana haka sai ga Hajara ta dawo, ta doso inda take.


“Mama Yaya Asim ya bar makulli a ɗauko wayarsa a mota ya barta sai kiransa ake, kuma Mahmud (Saurayin da ya zo gurinta) Idan wasu suka ga wayar zasu iya fasa gilashin motar su ɗauka”


“Amman ya fita da wayarsa, sai dai idan ba ɗaya ba ce, lalaba aljihun wandon da ya cire ɗazu ko daki samu makullin ni dai be ba ni ba”


Ta faɗa tana tsakalen haƙori, da karen darbejiya bushesshe. Hajara ta nufi ɗakin Mama inda ya sarkafa wandonsa ta soma lalabawa ta ji kuɗi mai mugun yawa kamin ta yi arba da makulin.


“Ga makullin nan bari na ɗauko, amman Mama kin ji Aljihun yaya kuɗi cike”


“Ke da gaske?”


Mama ta yi sauri ta tashi ta nufi ɗakin. Hannu tasa cikin aljihunsa ta ciro rabonta saka inda take ajiyar kuɗi, sannan ta koma waje gurin tabarmarta zauna. Sai ga Hajara ta shigo da wayoyi biyu da makullin sannan kuma da Apple hannunta.


“Aje masa, wannan karki canye ki rage min”


Ta miƙa mata wayoyin da Apple ta juya, hankalinta yana gurin Mahmud kar ya ce ta bar shi.


“Ina kika samo tuffah”


“A motar Yaya”


Mama ta yi murmushin jidaɗi.


“Oh Yaro yayi kuɗi har tuffa ake ci a mota yanzu haka ya manta da ita da wayoyin nasa da ya bari, ko da yake abun ba ɗaya ba naga fa ya fita da wasu”


Ta faɗa tana gantsara apple ɗin, babu ko bismilah balle kuma ta damu da wankewa. Haka ta kama shi ta wanke tass tana cewa idan Hajara ta zo ta bata kuɗi ta siya wani wani tun da akwai shi a titi, har ta ƙaro mata ma dan wannan ma ta jidaɗinsa. Sau biyu ana kiran wayar Asim sai ta ɗauka ta ce baya kusa.




[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *Mama (Hajiya Zainab Kano) wannan shafin na ki ne, Allah kara miki lafiya*


*81*
Kaɗan-kaɗan ta fara tari alamar sarƙewa, tun tana yi a hankali har ya taso mata gadan-gadan ba sauƙi, sai faman bubbuga ƙirjinta take, daker ta unƙura ta sha ruwa, bata baro gaban firjin ɗin ba ta soma aman jini babu ƙaƙƙautawa, tun tana iya gane duniyar da take har ta daina ganin komai sai hudu, gashi yaran duk basa nan Hajara ya gurin fira, ba ita ta dawo ba sai goma har da dare, ganin Mama bata kan shinfiɗar tabarma dake waje yasa ta zargi ko ta shiga banɗaki ne, dan hankalinta be kawo ta kalli gefen da firjin ɗin yake ba, ledar turaren da ke hannunta kawai ta aje ta sake fita dan dawo da ƙannenta gida.
Moƙota ta shiga ta kira su, ta sako su a gaba tana biye har suka iso gida, sai a lokacin idonta ya kai gurin da Mama take kwance cikin jini, ihu tasa tana faɗin


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Ta nufe ta da sauri tana ihu, tana ƙarasa gurin da take nefa na yin tsiyarsu na ɗauke wuta, sai kawai ta ƙwala ma mai binta kira.


“Ɗauko Fitila Amina, ɗauko fitila yi sauri”


Da sauri Amina ta ɗauko fitila ta kunna ta nufo gurin da Hajara take. Suna yadawa duka suka saka kuka da ihu, Hajara ta shiga girgiza Mama tana kiran sunanta, amman ina idonta a ƙafe tana kallon sama. Da gudu Hajara ta fita ta shiga maƙota tana kuka, kan kace kwabo gidan ya cika da jama'a, kowa ya shiga sai ya fita yana girgiza kai wata maƙociyarsu ce da tafi kusa da su tasa hannunta tana kalmar shahada ta rufewa Mama idonta, da taimakon wasu mutane aka dawo da ita ɗaki, Maƙotan suka share gurin suka wanken jini, Amina da Hajara da ƙanensu kan sai kuka suke,ana ciki haka sai ga ƙanen Asim ya shigo nan take shi ma yasa kuka, sai kiran wayar Asim.ake baya ɗauka, unguwa har ta ɗauka wai Asim ya bada uwarsa, daman suna zargin ba kuɗin arziki ba ne.


Tun da direba ya ɗauke shi ya kai shi gurin Alhajinsa, suka ci amai kyau aka sha mai daɗi sannan suka koma sha'ani. Ba su bar juna ba sai da asuba shi ma dan zasu yi sallah ne bayan sun gama Asim ya nufi gurin da ya aje wayoyinsa ya duba dan yasan ya saka su silent ne. Missed calls ɗin da ya tarar ya ɗaga masa hankali sosai, daga ƙanensa da Number Mama a ɗayan ɓangare kuma ga na Hajiya Sadiya da na Mardiya ga kuma na Nably har sai ya rasa wanda zai fara kira. Maida wayar yayi ya aje dan yasan aduniya Alhajinsa ya tsani kiran waya ko kuma chat da wani a lokacin da suke tare da juna. Komawa ya yi suka kwanta wannan karon bachin gajiya suka yi saboda an kwana ana saɓa ma Allah. Ba su suka farka ba sai 11am, shi ma dan Alhajin nasa yana da meeting ne. Ada idan Asim ya aikata irin wannan saɓon yana jin ba daɗi, yanzu kan ba ya jin komai har daɗi abun yake masa, sai da suka yi sallama sannan Alhaji ya sa direba ya mai da shi gida, bayan ya faɗa masa zai sake aukowa a ɗauke sa za a kai shi gurin wani amininsa da yake minister of defence, Asim ya jidaɗi sosai da sallamar ƙwarai Alhajin yayi masa, ga kuma wanda ya ce zai haɗa shi da shi yasan shi ma zai samu kuɗi gareshi.


Taron da ya tarar a ƙofar gidansu na maza ya tashi hankalinsa sosai, daman tun da dreba ya sauke shi yake ji babu daɗi. Nuna shi jama'ar gurin suka riƙa yi a sannu-sannu suna tsikumin wai shi ne babban ɗanta, wasu na cewa ya bada uwarsa yayi kuɗi. Yana shiga cikin gidan ya tarar da taron mata gabansa yake sake faɗuwa, bama kamar yadda ya ga ƴan'uwan mahaifiyarsa da mahaifinsa mata duka a zaune tsakar gidan wasu har kuka suke, amman ko kaɗan be kawowa ransa mahaifiƴarsa ce ba ya fi alaƙanta abun da ɗaya daga cikin ƙanensa.


“Wai lafiya mi ya faru?”


Ya tambaya muryarsa har gargada take, dan yanzu kan ya fara tsarewa. Babu wanda ya amsa shi cikin mutanen da ke waje sai duk suka zuba masa ido kamar yau suka fara ganinsa. Hakan yasa ya nufi ɗakin Mama dan be ga ɗaya daga cikin ƙanensa waje ba.


“Hajara miya faru?”


Yana shiga cikin ɗakin ya aikawa Hajara da tambayar. Sai kawai ya ji an sauke masa mari har biyu a fuska. A gigice ya kalli wacce ta mare shi ɗin, Mama Inno ce, yayar mahaifiyarsa wato elder sister ɗin Mama.


“Baka da mutunci Ibrahim tir da kai tirr da halin ka, ace wai tun jiya ka bar gida baka san ka dawo ba, kuma ayi ta kira wayarka ka ƙi ka ɗaga, to burin ka ya cika daman ko gawarta baka son gani ko? To ba zaka ganta ba, an kaita gidanta na gaskiya sai kaje ka yi ta sharholiyarka daman ita ka sawa gaba”


Ta ƙarasa da kuka. Ji yayi kamar ana zooming ɗinsa, sam.ya manta da wayarsa na silent duk da yana da niyar idam ya fito zai kira duka wanɗanda suka kira shi dan ya ga har da new numbers, amman farincikin albishir ɗin da Alhaji yayi masa ya ɗauke masa hankali, zuciyarsa sai nuna masa take Mama ce yana kaicewa, a take idonsa ya cika da hawaye, mutumen da kukansa ma aiki ne.


“Kar dai ace min Mama ce...ce...ce
..”


Ya faɗa cikin kuka yana kallon gadon da ka agware.


“Ita ce, jiya da dare Allah ya karɓi abarsa..



Da sauri ya doshi gurin Hajira da ta amsa masa da kuka, ya ɗuka ya riƙa Hijabinta.


“Miya same ta Hajara miya faru faɗa min?”


Cikin kuka Hajara ta shiga masa bayani.


“Nima ban san abunda ya faru ba, ni dai kawai ina waje muna Fira da Mahmud bayan ya tafi na shigo cikin gida sai na samu babu kowa, naje maƙota ka kira su muka dawo gida sai kawai na hango ta can gefen firjin kwance idonta a ƙashe ta yi aman jini, ko da naje na kira maƙota kowa sai yace babu ta, maman Haruna ce ta rufe mata ido, na yita kiran wayarka baka ɗauka ba, kuma na ɗauki wayarta na kira ka baka ɗaga ba, na kira su Mama Inno da kawo Amadu na faɗa musu... Da suka zo aka kira wani likita (Maƙocinsu) ya duba ta yace ta rasu, da safe kuma aka yi ta kiranka baka ɗaga ba, har aka mata sutura aka kai ta”


Faɗuwa yayi zaune, ya dafe kansa wasu irin hawaye masu zafi suka soma masa zuba, ta ya za'ace mahaifiyarsa ta rasu daga ya bar ta kawai yaje ya dawo, sam be kawowa zuciyarsa zancen Apple ɗin nan ba.
Kuka ya dinga rerawa a gidan har sai da ya tashi kukan kowa a gidan, wani irin abu yake ji ana baƙinciki a zuciyarsa, be taɓa jin ɗacin da dafin mutuwa ba kamar wannan lokacin, daman ko da ya tashi be san mahaifinsa ba, dan haka be san zafin rabo ba sai a wannan lokacin, haka ya ɗinga rera kuka kamar mace, abun har babu kyau, tun wasu na tsine masa dan suna ganin kamar ya mafa mahaifiyarsa ne har suka fara tausayinsa.






NAMRA POV.


Duniya juyi-juyi a yayinda ake kuka mutuwar Mama, ta ɓangaren Namra murna ce ta cika gida ko ina sai guɗa kake ji ana yi, da kiɗin ƙwarya dan yau aka saka mare lalle, wato Maryam da Hindatu.


A cikin gidan aka yi sa salle ba kamar yadda wasu suke ba a ɗauka a kai wani guri inda ƴan'uwa. Yanzu ne wasu ƴan'uwan suke zuwa na garuruwa da kuma na cikin gati dan jiƙon lalle. Ƙarfe goma na safe aka saka jiƙon lalle wato ceremonial setting.
Amman ko da 9am ta yi gidan ya cika da jama'a abun da mai jama'ah, ba daga ɓangaren Abbah ba bana Anty Amarya ba, da kuma na Hajiya Barau, har mutane ƙauye sun iso. Goma dai-dai ƴan gidan angaye suka zo jiƙon lalle, yadda aka riƙa faka motoci a bakin gate ɗin gidan har aka rasa gurin aje wasu. Mutane sai mamakin ganin Namra suke da su a idonta suna mata kallon ta lalace ta yi baƙi, ita ko tana ganin har ta ɗan yi ƙuba a zaman nan na kwana biyu da ta yi a gida. Duka abubuwan da aka raba a gurin sa lallen daga ɓangaren Abbah ne aka kawo, wato gwaggwanin amare. Misalin huɗu na yamma aka yi wanki amare a gidan sama road gidan Alhaji Salisu Yayan Abbah amman wanda suke ƴan wa da ƴan ƙane (Cousin). An yi watsin kuɗi kamar ba gobe, bama kamar Hajiya Barau yadda ta zage tana watsin kuɗi sai ka rantse da Allah har a zuciyarta farincikin auren take, bayan kuwa ta ciki na ciki.


An raba abubuwa da dama a gurin bikin, bayan an raba abubuwan da al'ada ta tanada (Al'adar sokoto) wato raba kayan mata (Hakin maye) a gurin awankin amarya, sannan a ɗora ta su lalle da salatif da tsinke da ƙwarya da sauran kayanyakin aiki mata, daga bisani aka biyo da kayan ciye-ciye da na tanɗe-tanɗe.


Daman can tun kamin ka shigo gate sai an miƙa maka ledar takeaway, drinks kuwa sai wanda ranka yake so zaka ɗauka, bayan wanda zaka tarar a muhalin da zaka zauna tare da kayan tanɗe-tanɗe.






ASIM POV.


Haka ya koma kamar marar lafiya, sallah ma daker yake unƙurawa ya tashi ya yi, ya rufe wayoyinsa gaba ɗaya. Mutane sai gaisuwa suke masa. Bayan isha'i mutane sun fara laɓawa, ya koma cikin motarsa ya zauna sannan ya kunna wayarsa, yana haska cikin motar sai Apple ɗin yake nema, sai a lokacin ya tuna da wayoyinsa da suke cikin motar, da sauri ya fita motar wayarsa na ringing. Hajiya Sadiya ce take kiransa, sai ya koma can gefe inda babu mutane ya natsu ya amsa wayar.


“Asim ina ta kiran ka tun jiya baka ɗaga ba, ɗazu kuma na kira wayarka a kashe”


“Bana kusa ne”


Ya amsa mata cikin rashin daɗin rai dan zuciyarsa sak yanzu zarginta yake.


“Ina Apple ɗin da kace zaka bawa matarka? Wata ka bawa ne ko mi ya faru? Ni an kira ni sai faɗa suke min, wai an basu tsohuwa, ni kuma na san ba wannan maganar muka yi da kai ba, miya faru ne”


“Apple ɗin faɗuwa yayi a hanya ina da niyar kiranki na faɗa miki, maybe wata ta tsinceta ne”


“Amman Asim sai da na yi ta nanata maka kar a samu matsala yanzu gashi wata banzar tsohowa taje ta samu, garin yaya ma ka jefar da shi? Ko dai baka son kuɗin ne wai?”


“Ina so mana, ai yanzu akwai wani ko?”


“Eh amman sai naje na faɗa musu sai su ban wani, yaushe zaka zo?”




“Nan da kwana biyu”


“Zan je na ƙarɓo maka, amman dan Allah karka min sakakace irin wacan”


“Ba za a samu matsala ba wannan karon sai kin fi kowa farinciki”


“Haka nake so”


Ta katse kiran. Shi ko ya cige baki yana kallon wayar cike da baƙinciki. Yana son ya tambayi Ƙanwarsa yadda aka yi apple ɗin ya fito daga motarsa har Mama ta ci yana tsoron kar ta zargi wani abu.


“Kun samu sa'ar jinin Uwata... Wallahi kin yi nadamar sanina da kika yi a rayuwarki, sai na ɗanɗana miki wannan baƙincikin”


Yayi wulgi da wayar iya ƙarfinsa, yana huci.




UZAIR POV.


Tare da ƙannensa biyu suka iso gidan da kuma mahaifiyarsa, tana ganin irin halin da yake ciki suka ɗauki shi zuwa asibiti.
Emergency suka wuce da shi layin ƴan haɗari aka ware masa ɗaki daban likitoci suka hau duba shi, sai ihu yake kamar wanda be san inda yake ba, bayan sun yi ɗan bincike su aka tura shi gurin hoto, bayan an masa hoton suka sake dawowa da shi ɗakin suka masa allurar bachi, amman kamar an ƙara masa zafin ciwo yake ji gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sai ihu yake. A take suka sake rubuta masa wani hoton, aka je aka ɗauka.


Lokacin da aka fito da hoton, sai Likita ya kira Hajiya suka nufi wani ɗakin da ita sai ya ƙala hotunan a jikin computer. Yana nuna mata.


“Ɗan ki ya taɓa yin haɗari?”


“Gaskiya be taɓa ba, amman ban sani ba ko be faɗa min ba”


“Gaskiya ƙashinsa na baya na karye, kuma na cinyarsa ma ya karye, sannan....”


Kamin ya ƙarasa ta miƙe tsaye ta sauri har kujerar da take zaune samanta ta faɗi.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Ganin hakan yasa likitan dakatar da bayaninta, dan ya ga alamun zata fara masa kuka, shi kansa yasan be kamata ya yi mata wannan bayanin ba, ganin tana mace amman babu yadda ya iya tun da babu wani namiji babban da yayi kusa da mahaifiyarsa. Da sauri ta juya ta fice daga office ɗin tana kiran wayar Abbah. Dan babu wanda ya san an kai Uzair Asibiti dan basu faɗa ba, tun bayan da Yasmin ta daqo gida ba ta damu da tasan dalili ba, tana ganin kamar yayi hakan

Please Login or Register in order to submit comment