Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

min ya tabbatar da akwai wani abu, and now what kin sa abu a tea ki bani nasha so that kiyi iya binciken ki ko? To bari na faɗa miki if something happens to my wife hmmm you're in trouble”


Sai a yanzu hawaye suka samu damar cika idonta har suka silalo zuwa kumatunta.


“Saboda na san idan kasan ina da HIV ba zaka faɗa min ba, idan har ya tabba ina da HIV Hilal to ta hanya ɗaya na same shi, wato sex kuma wani namiji be taɓa kusantana ba sai kai, a lokacin dana bar ka ya kusance ni ban san komai ba, sai a ɗazu nasa an nemo min Doc Sabo saboda na tabbatar idan har da gaske ina cutar ne, do you know who i try to protect? You and your dirty wife, Asmee told me everything about your bride but very soon gaskiya zata yi halinta, kuma ba zan taɓa yafe mu ku ba, aje ayi gwajin”


Tana kai nan ta raɓa gefensa ta wuce cikin falon. Juyowa yayi ya bita da kallo zuciyarsa na raya masa abubuwa da dama.
Kalamanta basu kama zuciyarsa ba, amman suna ƙoƙarin zaunawa akansa, what he believe shi dai yana da protection ɗin da ba kasafai cutar zata yi saurin kama shi ba, ko baya da protection, he's Doctor ya san cutar bata saurin kama namiji kamar mace, dan namiji ɗaya mai hiv zai kwanta da mace goma to dukkan su sun zama patient living with hiv, wato sun shiga sahun masu dauke da HIV acikin al'umma.

Amman mace ɗaya mai HIV zata kwanta da namiji 10 a rana, abu ne mai sauki namiji 2 ko 3 suka mu da wannan ciwon mai karya garkuwar jiki. Namiji zai iya daukan HIV kawai idan yana da wata kafa a gabansa abunda ya shafi kurji, yanka ko tsaga.

“He's lie”


Ya furta a hankali, yana murza saman goshinsa, zuciyarsa ta kasa yarda da zancen ta, duk da yasan Kalsoom take nufi, dan ita daya auna jininta be nuna haka ba, amman yasan result ɗin zai fito kuma dole gaskiya tayi halinta.


Shigowa yayi cikin falon cikin tunani da sarƙaƙiya, a saman babbar kujera ya zauna, ya dafe kansa, ɗaurewar da kansa yayi shi ya hana shi bachi har safe.
Har yayi sallah asuba ya dawo, be ji motsin Kalsoom ba, ita daya san wani lokacin ma takan riga shi tashi, a falon ya zauna yayi addu'o'insa sannan ya shiga ɗakinta, yadda ya tararda ita kwance rigingim har sai da ya tsorata, wani irin ninshari take kamarmacijin nan mesa na bachi, yayi mata girgizar duniyar nan amman ina, in ma ban da ƙara nauyin bachi babu abunda take.


Da sauri ya fita ya shiga ɗakinsa duba keys amman be ganshi ba, sai a lokacin ya tuna da suna guri motarsa da Rashida ta saka su jiya, da sauri ya fita daga ɗakin ya nufi gurin motar, ashe ma buɗe ta kwana, shiga kawai yayi ya kunna ta ya bar gidan.


Rashida na jin tashin motarsa ta duba agogon ɗakinta, 6:55am ya nuna, bata damu da rashin warewar gari ba ta tashi ba tare data tsaya wanka ba, ta canja tufafin jikinta zuwa atamfa ta ɗauki abaya ta ɗora sama, sannan ta ɗauki handbang ɗinta ta fice daga ɗakin.


Cikin sauri ta shiga motarta tayi mata keys gudun kar Hilal ya dawo, dan yanzu kam sam bata son haɗa ido da shi.
Gidan su Asmee ta nufa, cikin ƙanƙanen lokaci ta isa, haka ta riƙa musu horn har sai da mai gadin ya buɗe mata gate, kusan da motar Alhaji Bashir ya faka motarta, daman tasan yana nan dan yanzu be isa fita ba. Ƙofar falon ta riƙa bugawa tana sallama kamar zata tashi gidan.


Alhaji Bashir ne ya buɗe mata ƙofar yana tambayar lafiya, dan tun da yaji muryarta hankalinsa ya tashi, a tunaninsa ko tazo tayi masa wani abun ne.
Tun daga samansa ta kalle shi har zuwa ƙasan shi, daga shi sai guntun wando, sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta iya ƙirƙiro murmushi ta yaɓa a fuskarta.


“Matar ka na nan?”


“Lafiya kika mana sammako haka?”


“Lafiya ƙalau, sirrin mu ne, saƙon zan bata”


Kamin ya ƙara cewa wani abu har Asmee ta ƙaraso gurin tana tambayar wanene.


“Nice na doko muku sammako, saƙon ki zan baki”


Rashida ta amsa da kanta, tana mata murmushi. Wani kallo Asmee ta watsa ma Alhaji Bashir, irin ya zaka zo daga kai sai guntun wando haka. Sai kawai ya juya ya shige ɗakinsa.
Asmee ta riƙo hannunta suka shigo falon.


“Ke lafiya kika zo haka?”


“Taimakon ki nake nema, idan har baki taimake ni ba, zamu iya rasa ran mu ni da mijina”


“Subhanallahi miya faru?”


“Mijina ya aiko ni zuwa gare ki, maganar da zan faɗa miki sirri ce bana son kowa yaji, ko da kuwa mahaifiyarki ce ko mijin ki”


“Ban taɓa sirri dake ba na faɗawa mahaifiyarta ba, balle kuma mijina taso muje ciki”


Dar ƙarshen gadonta, Asmee ta kai ta suka zauna, sannan ta kalle ta tace


“Faɗa min damuwarki, matuƙar ina da maganinta wallahi zan miki”


“Irin samarin nan nake nema kidnappers”


Asmee ta daki ƙirji.


“Aka yi da wani ko za'a miki?”


“Wani muke son a a ɓoye mana shi, saboda ta hanyar shi ne kaɗai ne, mijina zai cigaba da rayuwa da ni, dan Allah idan kin san inda irin mutanen nan suke ki faɗa min”


“Ni ɗan maye ma miye haɗina da shi balle kuma ɗan kidnapped, Wallahi ban san wani mai wannan aikin ba”


Rashida ta kama hannayenta ta riƙe ta fara kuka.


“Ko cikin ƙawayen ki ba kisan wacca tasan mai irin wannan aikin ba? Dan Allah Asmee ki ceci rai na”


“Bana da ƙawar da zata iya faɗa min sirrinta har haka sai ke, ko da suna da irin waɗannan mutanen ba zan iya sani ba, sai idan gurin wannan Malamin zaki je, sai ya haɗa ki da wani cikin masu zuwa gurinsa, dan yana basu taimako sosai”


“A ina Malamin yake? Dan Allah ba ni addireshinsa”


“Ba a cikin garin nan yake ba, a ɗan dutse yake da kin shiga garin ɗan dutse kika ce Malam mai gobe da nisa ko ƙaramin yaro yasan gidan sa, bari na baki number wayarsa, kamin ki isa zan kirashi na faɗa masa”


“Na gode Allah ya saka miki da alheri, samin number”


Ta faɗa tana miƙa mata wayarta. Sai da Asmee ta saka mata Number sannan tace


“Amman kin san garin kuwa?”


“Karki damu zan tambaya har na isa garin, ai bada motana zan je ba, gidan mu zan bina na aje motar, saboda gudun sa ido”


“Allah yasa a dace, amman ina jin tsoro Rashida”


“Babu abunda zai faru, ba mummunan abun zan aikata ba”


“Dan Allah aro min niƙab ɗin ki da Hijab”


Ba musu Asmee taje ta ɗauko mata ta saka.
A gaggauce ta fice da daga gidan, zuciyarta har wani ɗar-ɗar take, tana ayyana irin rashin mutuncin da zatayi Doc Sabo, lallai yau zata nuna masa ta fishi zama yar duniya, Zagon ƙasan da yayi mata ƙarami ne, yanzu zata masa babban.


Kamar yadda ta tsara, a gidansu ta biya ta aje motar, ko cikin gidan bata shiga ba, balle su gaisa da Momi, tana rufe motar ta fito ta tari Napep ta shiga, ya ɗauki hanyar tasha da ita.




HILAL POV.


Be daɗe ba ya dawo, daman allurai kawai yaje ya ɗauko, yana shiga ɗakin ya haɗa allurar yayi mata, sannan ya ɗauko tawul ya jiƙa shi da ruwa, ya riƙa dafa mata a goshi.
A hankali ta fara motsi tana nishi da miƙa irin ta gaji sosai ɗin nan, hankalinsa ya ɗan kwanta lokacin daya ga ta buɗe idonta, sai ya sakar mata murmushi.


Daker ta unƙura ta tashi zaune, saboda nauyin da jikinta yayi mata.


“Wane irin bachi nayi haka?”


“Magani na saka miki a tea ɗin, tashi kiyi sallah”


Ta ɗan kalli window taga yadda rana ta fara hudowa, sannan ta unƙura da zimmar tashi tsaye, sai Doc ya kai Hannu ya riƙa hannunta.


“I trust you Kalsoom dan Allah kar ki bani kunya”


Wani kallo tayi masa, irin ban gane ba. Sai kawai yayi murmushi yana ƙoƙarin ɓoye feelings ɗinsa.


“Yanzu idan aka ce ina da hiv zaki zauna da ni?”


Dawowa tayi ta zauna, ta kai hannayenta ta riƙa fuskarsa.


“Idan har kana da hiv zan zauna da kai, kuma idan har kana da shi nima nasan ina da shi, so babu dalilin ƙyamar juna”


“What if aka ce ke kike ɗauke da shi ba mu ba?”


Shiru ta ɗan yi tana nazarin tambayoyinsa, anya Doc zai mata irin wannan tambayar haka kawai.


“Idan har ni nake ɗauki da cutar zan nisanta kai na daga gare ku, gudun kar ku kamu da cutar, har sai ta zama aids, domin wannan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki, saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar kissing ko kuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi, kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, da brush.


Amman da zarar cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) zan cigaba da mu'amala da ku kamar yadda na saba, saboda ba`a kamuwa da ita ta hanyar kissing, cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su, kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci comb, tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar, amman ba zan bari ka kusance ni ba, ko da kuwa zaka na shan magani da amfanin da kororon roba, saboda it's risk.


Sai dai kuma ka sani, rayuwata zata tarwatse zan nisanta da ƴaƴanka, duniya zata ƙyamace ni, kuma dole na rabu da kai”


Ta ƙarasa maganar hawaye na bin fuskarta. Ɗan murmushi yayi ya tashi yana ƙoƙarin ɓoye hawayen da suka cika masa ido.


“Intelligent woman, je kiyi sallah zan haɗa ma yara breakfast”


Har ya fice hawaye take, zuciyarta cike da tunanin abunda yasa Doctor yayi mata wannan tambayar.




NAMRA POV.


Ko ta koma gida, ta samu duk sun tafi walimar aure, ta wata maƙociyarsu, da ake yi yau jumma'ah. Mardiya ce kawai a gidan, ta zauna cikin ɗakin ta rafka uban tagumi.
Sallamar da Namra tayi ma sai da ta firgita ta.


“Ke lafiya kike kuwa? Ke kaɗai aka bari a gidan?”


Namra ta tambaya tana zama kusa da ita. Ajiyar zuciya mardiya ta sauke.


“Kawai ina tunanin rayuwa ne”


“Rayuwa kuma kamar ya?”


Shiru tayi tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Namra, dan bata son faɗa mata asalin abunda yake damun ta.


“Inna ce duk ta bi ta dame ni akan rashin auren nan, kamar ni nayi ma kai”


“Ayyah wai wani abun ba'a kusa yake ba, komai yana da lokaci”


“Na sani matsalar iska ne yake damuna, ina ganin kamar shine ya hana ni aure, amman ita inna ta kasa ganewa”


Ta bijiro da damuwarta a fuskarta kamar da gaske abunda yake damunta ɗin kenan. Ita kuma Namra sai tausayinta take.


“Ki riƙa azkar kina faɗawa Allah damuwarki, inshallah zai miki magani”


“Ina yi Wallahi babu inda ba mu shiga akan neman taimako ko ina sai ace mana Aljani ne ya aure ni”


“Subhanallahi, amman Mardiya, ai dole aljani ya aure ki tun da kina yawo babu ɗankwali, gashi kina yawan sauraren waƙe-waƙe, da ace baƙara kike yawan karantawa nayi imani ba zai samu nasara akan ki ba”


Ajiyar zuciya Mardiya ta sake saukewa, a karo na biyu, ta ƙara gyara zamanta.
Namra ta kalleta cike da tausayawa tace


“Ki samu allo ki rubuta suratul azari, daga farkon ta har ƙarshe, idan kin yi alwala la'asar kika rage ruwa sai kiyi amfani da su ki wanke rubutun ki shanye har kwana uku, indai matsalar aljani ne mai hana aure inshallah zai rabu da ke”


“Na gode sosai Inshallahu zan gwada”


“Allah yasa a dace, da naso ki raka ni kasuwa amman naga kamar kina cikin damuwa bari mu bari har gobe”


Kamar kar Namra tayi maganar nan da nan Mardiya ta kai idonta gurin ƙaramar jakar da Namra take riƙe da ita, sai kuma ta kawar da kai.


“Mu bari har goben dai yanzu yamma yayi”


“Eh nima ai haka na gani”


Ƴar nokiyar dake hannun Mardiya ce tayi ƙara, sai ta tashi ta bar ɗakin tana amsa wayar.
Tashi Namra tayi ta cire hijabinta, ta rataye, sannan ta ɗauki jakar wanda kuɗin suke ciki ta saka a cikin akwatin Mardiya na kaya, da zimmar ta aje a cikin dan kar taje ta jefar da ita wani gurin, sannan ta fita ta kama ruwa.




RASHIDA POV.


Data isa tasha, shatar motar ta ɗauka ita kaɗai, ya kai ta ƙauyen. Bata sha wahala ba gurin gane gidan, tambaya ɗaya suka yi aka nuna musu gurin, gidan ne mai kyau kamar ba ƙauye ba. Sun tarar da layin mata sosai a gurin haka ta samu guri ta tsaya har aka kai gareta. Sannan ta shiga.


Ƙaton ɗaki ne mai cike da kayan alatu, ba dan rawanin da taga ni a kansa ba, da zata iya rantsuwa da Allah tace wani attajiri ne ba malami ba, sai dai hakan be bata mamaki ba, dan tasan duk mutumen dake aiki da manyan yan siyasa dole ne ya tara komai.
Kallo ɗaya yayi mata ya soma gyara ƙasar dake gabansa yana faɗin ta cire niƙabin ta, ba musu ta cire niƙab ɗin tana gaishe shi. Be amsa ba har sai da ya gama bugun ƙasar sa, sannan ya kalleta yace.


“Kin zo nan ne dan a haɗa ki da wani yayi miki wani aiki”


“Haka ne ni ƙawar Asmee ce, tace zata kira ka”


Sai da ta ciro dubu hansin ta aje masa a gabansa, sannan ta koro masa da bayani. Sai da ta gama sai yayi murmushi yace


“Zan haɗa ki da wani, saboda kawai Asma'u ce ta turo ki, amman ba dan haka ba, babu abunda zai sa na haɗa ki da shi, saboda shegen mutum ne, ni kaɗai zan iya sashi abu yayi nan take”


“Na gode Malam, idan har aiki yayi kyau, kai ma zaka jidaɗi inshallah”


Wayarsa ya ɗauka ya kira, yayi tsowon minti ashiri yana lalasar mutumen sannan yaba Rashida waya suka yi magana ya faɗa mata inda zata same shi.


Bayan sun gama malamin ya kalleta yace


“Idan buƙatata da biya ki dawo ina son ganin ki, dan gaskiya akwai matsala a tare da ke, kuma akwai abunda yake shirin faruwa da ke, dole ne sai kin nemi taimako”


“Inshallah, zan dawo”


Da tsoro tayi masa sallama, tana ta tunanin wane irin matsala ne, zuciyarta nata raya mata lallai wannan malamin yana aiki kam.
Tafiyar mintuna arba'in suka yi, suka dawo cikin gari, kai tsaye tace direban ya nufi American Unique Estates da ita, a dai-dai inda ya kwatanta mata ta tsaya, ta kira number da Malamin ya bata ta mutumen tace masa tana gurin, sannan ta sallami direba fiye da yadda suka yi jingar.


Tsaye kawai take a gurin amman babu natsuwa a tare da ita, ji take kamar wani zai zo ya ganta. Bayan kamar mintuna asirin da biyar wata ƙafirar mota ta faka gabanta.
Wani Namiji ne mai shigar mutunci ya fito cikin motar tare da Amira.


“Ke ce Rashida wacca Malam ya aiko?”


Namijin ya tambaya.


“Eh nice”


Amira ta buɗe mata Motar.


“Shiga muje”


Da tsoro ta shiga motar, zuciyarta duk bata natsu da su ba.




___________________________________________


Assalamu alaikum as i said yau na kai Page 35, that's means na gama free pages kenan. Dan haka duk mai son ƙarashin wannan labari zai iya turo ₦200 zuwa wannan account 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.


Sai ku turo da shaidar biyan kudin wato screenshot ta wannan number 08036126660.
Zan saka ku group inda zan riƙa updated littafi kullum inshallah.


Na yi haka ne duba da yadda wasu suke ci da gumi na, akwai wanda ya ƙirƙiri grp a whatsapp ana tura masa naira ɗari yana tura littafan marubutan online cikin har da nawa, sannan akwai wanda ya ɗauki littafina na MAIRO ya maida shi application ya ɗora a Google play store, wanda duk yayi downloading ɗin app ɗin sai google sau biya shi, idan kuma suka ɗora talla a app ɗin kuma wannan shima sai sun biya shi, ni da nayi rubutun ban ci ba shi ya ci. Bayan haka an ɗauki littafina na SALEENA an saka a okadabooks, ba tare da izini na ba, wanda idan aka siye kuɗin zasu je ga wanda ya saka littafin ne ba gare ba, idan kukayi searching duk zaku ga abunda nake faɗa muku na Application da okadabooks.


Dan haka ya sa na canja wannan littafin uzuwa na kuɗi, dan nima na ci amfanin abuna, da wani ya ci da gumminka ƙara ka san kai ka ci, ko yayane, dan baka san ta rai ba. 😀
Ina roƙon duk wanda na ɓatawa rai sanadin canjin nan ko kuma littafin nan, dan Allah ku yafe min, nima ban za ci sauyin zai zo ba, sai daga baya, da tun farko na faɗa. Ina roƙon alfarma dan Allah kar wanda ya mai da min da Littafi document.


Na gode da shawarwari da ƙauna, Allah ya sakawa kowa da Alheri. I love you all




BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘


*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

_Write by_
*Khadeeja Candy*


*PAGE - 36*


NOT EDITED ⚠


Nitsa kai suka yi tayi cikin unguwar, sun yi tafiyar mintina goma zuwa sha uku, sannan suka isa ƙarshen unguwar, a bakin wani makeken gate black color.


Tsoron dake cikin zuciyar Rashida ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a jikinta, gani take kamar wani abun zasu mata har ta buɗe baki tayi magana, sai ta tuna da abunda ya kawo ta gurin, kuma ta san bata da wata mafita sai wannan.
Sai kawai tayi shiru da bakinta ta sakar musu na mujiya har suka faka bakin wata babbar ƙofa. Amira ce ta fara fita tana faɗin


“Fito muje”


Buɗewa Rashida tayi ta fito, sai mutun ya ja motar ya nufi wani ɓangare na gidan da ita.
Amira tayi gaba, Rashida ta rufa mata baya sai kalle-kallen gidan take.


Cikin wani ƙaton falo suka shiga, wanda aka ƙawata da kayan alatu, kallon falon tayi sosai ba dan ya birge ta ba, sai dan ɗaukar rahoto ta karanci wane irin gida ne aka a kawo ta.
Kamar daga sama ta ji Amira na mata magana.


“Idan baki yarda da gidan ba, miyasa kika shigo? Ko kina tunanin za mu miki wanin abun ne?”


Kasa cewa komai, tayi har Amira ta gaji da tsayi a gurin, ta isa gaban wata babbar kujera ta zauna tana cire gyalen abayarta.


“Guy Son!”


Ta ƙwala mishi kira, tana nuna ma Rashida kujera.


“Zauna idan zaki iya”


Rashida ta zauna zuciyarta na ɗar-ɗar, wani tunanin ne ya zo mata. What if tafa mutumen data sani? Ko kuma gidan yana tare da Dr Sabo fa?


Fitowarsa yayi dai-dai da sauke ajiyar zuciyar da Rashida ta yi, a yanayin shigarsa da kamalarsa, bata zace shine Guy Son ɗin ba har sai da ya zauna kusa da Amira, jikinsa yana Gugar na Amira.


“Wa kike son ayi miki garkuwa?”


Ya tambaya, fuska babu alamar murmushi balle wasa.


“Wani mutun ne, sunan shi Doc Sabo a asibin Alex yake aiki sashen jini”


“Cire Niƙab ɗin fuskarki kiyi mana bayanin komai”


Tasa hannu ta cire Niƙabin ta gyara zamanta sannan tace


“Mijina ne ya ɗibi jinina dana yara na ya kai masa akan yayi mana gwaji, bana da tabbaci amman ina jin kamar ina ɗauke da cutar hiv kuma ina tunanin mijina da kishiyata basa da shi, na karɓi numbersa gurin abokin aikina na kira mun yi magana akan zai faɗa min idan mijina ya kawo jinin, har na tura masa dubu ɗari, sai gashi ya yaudare ya faɗawa mijina na bashi kuɗi”


Ya kai hannunshi ya riƙa hannun Amira yasa yatsunsa cikin nata.


“So kina son ayi forcing ɗinsa ya canja result ɗin ko?”


“Haka nake so, matuƙar ya faɗi gaskiya, mijina zai rabu da ni, kuma duniya zata ƙyamace ni, zan ba ku ko nawa kake so, dan Allah ku taimaki rayuwata”


Amira ta ɗan yi murmushi.


“Ba shi kike son ayi a ɗauke miki ba, ƴaƴansa za'ayi kidnapped sai asa shi dole ya faɗi abunda kike so”


“Koma yaya ne ni dai yi min zan biya ko nawa kuke so”


Ta faɗa tana karyar da murya irin tausayin nan. Wayar dake hannu ya karɓa, ya saka wata number ya kira, ana picking yace


“Zo nan ina neman ka”


Be fi mintuna uku da aje wayar ba, sai ga mutumen ya shigo cikin ƙaƙanan tufafi, yazo dai-dai shi ya tsaya, Rashida na kallonsa gabanta ya faɗi saboda jan idonsa.


“Ka bincika min addireshin Doc Sabo yana aiki a Alex hospital sashen jini”


“Okay Boss”


Sai ya juya ya fice. Guy son ya kalli Rashida ya ce


“Bani addireshin ki, kuma karki kuskura ba ni na ƙarya dan zan gano ki”


Gabanta ya faɗi sosai, kuma ta tsorata, bata son bashi na ƙarya tun da har ya gargaɗeta, sai dai kuma idan har ta ba shi adireshin na gaskiya, bata san abunda zai faru ba.


“Sunana Rashida Abdullahi Kardam ina aiki a Stanbic Ibtc Bank, mijina babban likita ne, yana aiki a Kaduna special hospital, muna nan GRA magaji road”


“You can go, zaki ga motar data kawo ki zata maida ke inda kike”


“Thank you”


Ta saka niƙabinta ta saka sannan ta ɗauki jakarta ta fice. Amira ta tashi ta nufi gurin window falon ta tsaya, tana kallon harabar gidan. Tana sinkayar motar har suka fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta jingina da gurin ta rufe ido.


Hannunshi yasa cikin jikinta yana murza fatar jikinta, ya fara shinshinar gefen wuyanta. Buɗe idon ta yi ta ture shi da dukan ƙarfinta.
Kallon da zai yi sai hawaye ya gani sun silalo daga idonta. Yarfarda hannu yayi ya cije fuska.


“So nawa zan faɗa miki bana son hawayen nan”


“Ka bar ni nayi kuka na, ai ina da dalilin kuka”


Hannu ya kai ya riƙe fuskarta iya ƙarfinsa ya matse ta.


“Ba dalili bane, idan har kina son iyayen ki dole ne ki koma gare su, amman kin kasa kuma kin ƙi ki faɗa min gaskiya, saboda kin san mugun abun da kika aikata”


Yana kaiwa nan ya wurgar mata da fuska gefe, ya wuce ciki. Da kallo kawai ta bishi idonta na hawaye, wani irin zafi zuciyarta ke mata, ita kaɗai tasan irin abunda take ji.
Bata ganin laifin kowa sai Uzair da Namra, dan sune suka rusa mafarkinta, suka gurɓata duniyarta, suka canja tunaninta, sun salwantar da farincikinta, sune sanadin barin gidan iyayenta, sune suka sa duniya ta zage ta, sun yi nasarar sauyata daga mutum zuwa mutum mutumen da kowa ke kallonta.


Lallai bata da maƙiya kamar su, bata da wani buri illa na ganin bayan su. Har yanzu zuciyarta bata lurar da ita illar abunda ta aikatawa Namra ba, bata ganin asirin ne ya koma mata, gani take kamar da haɗin bakin Namra Uzair ya cuce ta.
Tana son komawa gida amman hakan sai ya gagareta, idan ta tuna yadda ta bar kowa nata, ta watsar da karatun ta, ta dawo nan ta zauna, sai taji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu.


Rayuwarta ta zame mata kamar mafarki, yadda sauyin yazo mata, sai yayi mata kamar a shirin fim ko littafi, silar su ne take a cikin halin da take ciki. A yanzu kan bata da mafarki sai na Namra da Uzair bata da buri sai na su.
Ƙarar buɗe ƙofar gidansu da tayi ta fita ne ya dawo mata sabo, yadda ta kai kanta har tasa ta bar garin sokoto ne ya riƙa mata yawo a ƙwaƙwalwa.


Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da wani irin mahaukacin kuka, tana yagar fuskarta. Da sauri Guy son ya fito daga ɗakin daya shiga yazo ya rumgume ta yana rarrashinta.


“Shiiiiiiiiiii, I'm sorry Amira, I'm so sorry”


Ya ɗora kansa saman na ta yana girgizata, alamar lallashi, har cikin kansa yake jin kukanta, son ta na masa yawa a ko ina na gaɓoɓinsa.




RASHIDA POV.


A inda suka ɗauke ta ɗazu, mutumen ya sauke ta, sai ta tari Napep ya kai ta unguwar da iyayenta suke. A

Please Login or Register in order to submit comment