Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Sai da ta shige sannan Maryam ta juya da motarta tana mamakin lamarin Namra.


Cikin sanyin jiki Namra ta shiga harabar gida,har ta ƙasa falon tana jin tsoro kamar wanda za'ayi ma wani abu.


“Assalamu alaikum”


Cikin sanyin muryar tayi sallamar Yasmin da Gwaggo Kulu suka amsa mata. Tun da ta shigo cikin falon Yasmin take mata wani irin kallo kamar bata gane ta ba. Kallon gulma take mata ganin yadda tayi baƙi sosai, daman can ba fara bace amman baƙin na yanzu ya ninka sosai, ga wata rama da tayi kamar wanda ta kwanta ciwo.
Ita kuma duk taji wani yanayi na daban, musamman ganin Yasmin da tayi a gidan. Bata zace zata rarar da ita ba.




AMIRA POV.

Duk wani farinciki da Amira take yi na zuwa abuja, a yanzu na zama labari, tun jiya da Guy son ya labarta mata dalilinsa na zuwa abuja da
Sam bata son aikin da Guy son yake wani lokacin ƙara kidnapped da saffara ƙwayoyi da yake da aikin kisan kai, sai dai ta san bata isa ta hana shi wannan aikin ba, dan be haɗa aikinsa da komai ba, bata wani daɗe da shi sosai ba, amman ya sake da ita ya shigar da ita jikinsa ya nuna mata so da yarda sai dai be yarda ta hana shi aikinsa ba.


“Wa zaku je yin attacking?”


Ta tambaya tana saka kayanta a jaka.


“Wani soja ne, amman ba a Abuja za muyi attaching nasa ba, daga nan sai za mu bisa za a bamu address nasa sai idan ya koma gida za mu ƙaddamar masa”


“Kashe shi zaku yi?”


“Haka ake son mu yi”


“Waya sa ku?”


“Wata mata ce amman bata son a gane ita ce, shiyasa take son mu bishi daga nan abuja ta yadda za'ayi zaton ko abokan aikinsa ne, yanzu haka ance mana yana cikin garin abuja”


“Amman Guy miyasa kake son kashe rai?”


“Saboda ban ɗauki rai a bakin komai ba, kema wata rana zaki aikata”


“Bana fatan aikata kisan kai har a bada”


Zuwa yayi ya dafata yana murmushi.


“Karki damu idan har kin kashe mutum kin lasa jininsa babu abunda zai same ki, ki shirya muje kar mu yi latti”


Cikin sanyin jiki ta rufe akwatin. Bata san wanda zasu kashe ba amman tana jin rashin kyautawa a lamarin.
Zama tayi saman gadon kamar mai jimami har sai da ya shigo ya ɗauki akwatin nata sannan ta tashi ta fita cikin sanyin jiki.




ABDOOL POV.
Jirgin safe ya bi ko da biyu na rana tayi har ya gama meeting ɗin da zasu yi, ya koma masaukinsa.
Kwantawa yayi ya ɗan runtsa na mintuna sannan ya tashi ya shiga yayi wanka, ya ɗauro alwala sannan ya fito, ƙananan kaya ya saka yayi sallah la'asar sannan ya ɗauki wayarsa ya kunna, text ɗin Ummi ya gani, hakan ya sashi jindaɗi tare da murmushi, sai ya danna numberta ya aika mata kira. A harabar gidan yana waya da Ummi, sai shafa kansa yake yana mai jin shauƙin son mahaifiyarsa cikin ransa.


“Alright Ummi i will, Thank you love you lot”


Ya kashe wayar fuskarsa da murmushi, yana kallon wata kurciya dake sha'aninta a harabar gidan nasa.


Ido ya tsura mata sosai yana son tantance abunda ya gani rataye a wuyanta. Ɗan matsawa yayi a hankali yana kallon layar dake wuyan nata, sai ya shiga ƙoƙarin kamata, be yi nasara ba ta yi firrrrr ta tashi sama, ta haye saman ginar gidan.


Tsaye yayi yana kallonta. Sai ya ƙwalama yaransa kira.


“Hey Boys”


“Sir”


Duk suka sheƙo da gudu, sai dai kamin su ƙaraso har ta ƙara fira ta bar gurin.






1869k words. Sorry for the short chapter 🙏🙏🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*




*© Khadeeja Candy*


*PAGE - 43*


NOT EDITED ⚠


Cikin rashin kuzari Namra ta zauna saman kujera tana kallon ƙasa kamar mai jin kunya.


“Namra...”


Ta ɗan ɗago kaɗan ta kalli Yasmin data kira sunanta, sai kuma ta kalli Gwaggo Kulu dakr tambayarta saukar yaushe.


“Yanzu na zo”


“Ya hanya ina mijin na ki?”


“Yana lafiya”


Kallon Namra Yasmin take zuciyarta na raya mata ba haka kawai Namra ta zo gidan ba, idan ma wani abun ne ai gidansu zata sauƙa. Murmushi tayi ta tashi ta nufi Namra ta riƙa hannunta.


“Tashi muje ciki kin wani zo nan kin zauna kamar baƙuwa”


Kallon Yasmin Namra tayi, murmushin data gani a fuskarta ne ya bata kwarin guiwar tashi ta bita. Ɗayan ɗakin Gwaggo Yasmin ta shiga da ita, daman can ɗakin ta fi zama a duk lokacin data zo gidan.


Yasmin ta buɗe bathroom ta duba ruwan dake ciki, sannan ta fito tana miƙawa Namra tawul.


“Shiga ki yi wanka, sai na kawo miki abinci”


Idonta a ƙasa take miƙawa Namra tawul ɗin irin bata son kallonta tana jin nauyin Namra sosai.
Hannu Namra tasa ta karɓa, sai Yasmin ta fice, ita kuma ta kwaɓe tufafinta ta ɗaura tawul ɗin ta shiga wanka, ko da ta fito Yasmin ta aje mata gown ɗin atamfa da abinci.


Ɗaukar rigar tayi ta saka, daman tayi alwala tun a toilet ɗin, sai kawai ta saka hijabinta, tayi sallah. Bata ci abincin ba dan bata jin cin komai, lemum kawai ta sha, sai ta ɗauki carbi tana tasbihi.


“Assalamu Alaikum”


Yasmin ta shigo bakinta ƙumshe da sallama, murya ƙasa-ƙasa Namra ta amsa mata, sai ta zauna kusa da ita tana wasa da hannayenta.


“Kin abincin dai ko?”


“A'a bana jin yunwa”


Kallon fuskar Namra tayi da kyau-kyau, tana ƙoƙarin karantar danuwarta


“Namra, kiyi haƙuri na ji ance mijin ki yayi haɗari, kuma duk a familyn nan babu wanda yaje ganinsa, ni ma naso naje na gansa Allah be nufa ba”


“Ba komai, ai yaji sauƙi”


“Allah ƙara lafiya, tare dashi kuka zo?”


“Ni kaɗai na zo”


“Amman ba kije gida ba ko?”


Ta ɗaga mata kai, kalar tausayi. Har Yasmin zata
tambaye ta ko dai faɗa suka yi da Asim, sai kuma taga rashin dacewar haka. Sai kawai ta tashi tana faɗin


“Ni kan zanje gida, ai nan zaki kwana ko?”


Ta ɗaga mata kai. Sai Yasmin tace


“Da safe zan aiko miki da breakfast”


“Na gode Anty Yasmin”


Namra ta faɗa idonta cike da hawaye. Rayuwar da suka yi a can baya ne ya riƙs dawo mata sabo, yadda Yasmin take treated ɗi kamar wata ƙanwarta da suka fito ciki ɗaya, amman yau duk babu wannan, tun da Uzair ya shiga tsakaninsu.
Ɗan murmushi Yasmin tayi ta juya ta fice.


Ɗakin Mahaifiyarta dan yi mata sallama. Ko da ta shiga Gwaggo Kulu na banɗaki, tana alwalar magariba. Gefen gado ta zauna har ta fito sannan ta miƙe tsaye.


“Gwaggo ni kam zan tafi, Uzair ya kira ni tun ɗazu wai yana gida”


“Ba zaki bari kiyi sallah magariba ba”


“A'a sai na je can zan yi”


“Toh Allah ya tsare, kin yi magana da Namra?”


“A'a ba mu yi mafanar komai ba, amman dai tace min bata je gida ba, ina ganin dai ta zo ne ba tare da sanin mijin ba”


“Toh Allah ya sauwaƙe, shiyasa ta ƙi sauka a can ta sauka nan”


“Haka nake tunani, kuma kin san halin Abbah da zuciya ƙila ma ta je ya hanata shiga gidan”


“Toh ai sai ta yi zamanta nan”


“Ni dai na tafi, da safe zan aiko mata da breakfast”


“To Allah kai mu lafiya”


Ta ɗauki jakarta da mayafinta ta yafa ta fito, zuciyarta cike da tausayin Namra.
Motarta ta shiga tayi mata keys kamin ta isa gida Uzair yayi mata kira biyu tana ce masa gata nan kan hanya amman duk be yarda ba gani yake kamar tana gidan zamanta ne, shi ta bar masa yaro sai fitina yake masa.


A harabar gidan ta faka motarta, sannan ɗauki takardun dake cikin motar da system ɗinta ta buɗe motar ta fito, ɗayan hannunta tasa ta lanƙamo jakarta sannan ta rufe motar, ta nufi ciki gidan.


“Assalamu Alaikum”


Tun a bakin ƙofa ta zubar da files ɗin dake hannunta da handbag, system ce kawai ta samu ƙarasa tsakiyar falon ta aje ta saman kujera, tana kallon Uzair daya kama hannun Adnan ya riƙe.


“Dan Allah zo ki raba ni da yaron nan, sam be jin magana wallahi, tun ɗazu yaƙi bari na huta”


Ƙyalƙyalewa Adnan yayi da dariya yana kallon Yasmin dake murmushi yace


“Mom wai ba zai ba ni wayarsa ba, tun da ba ke kika siya ba”


“Zo ka ɗauki nawa kayi game, amman ka kwashe takardun nan ka kai ɗaki”


Ta faɗa tana nuna masa bakin ƙofa inda ta jefar da jakarta da takardun. Da gudu yaron ya sance hannunsa daga riƙon da Uzair yayi masa ya nufi gurin ƙofar yana tsalle.


“Wallahi duk kin ɓata min yaro, sam yanzu baya jin magana”


“Kai dai ka ɓata abun ka karka ɗora min laifi”


“Kuma na faɗa miki ki daina wucewa gida idan kin san ki bar min Adnan”


“Bloody yau ina gida sai ga Namra”


“What!... ”


Ya gyara zamansa.


“Wallahi, duk ta rame tayi baƙi sosai kamar ba ita ba”


“Me ta zo yi?”


“Ina ganin tayi yaji ne, dan ƙin sauka tayi gida sai ta sauka gidan mu”


Ya taɓe baki, irin ko a jiki na can ta matse mata.


“Ai bama zata yi kuskuren sauka gidan Abbah ba kam, ko minene ai ita ta jawa kan ta”


“Ni wallahi tausayi take bani, da na sani tun farko dana barka ka aureta, ji duka yaushe akayi auren amman har ta koma haka”


Ya miƙe tsaye yana wata dariya.


“Na aure ta na kai ta ina? Kin ɗin ma kin fitineni kin hanani sukuni balle kuma na haɗa ku biyu, ai ni sai yanzu na ga hikimar rashin aurenta da nayi, na gode Allah wallahi”


“Haƙurin da nake da kai babu macen da zata iya yinsa da kai, baka da time ɗin na, baka bani haƙƙina kwata-kwata ma bana gabanka, in nayi kwalliyar duniyar nan bana burge ka, ai dole nayi magana tun da ni ba ice ba ce”


“Kyaji da kan ki, kin cika jaraba ne, akwai wanda yake shekara ma babu ruwansa da iyalinsa kuma suna zaune lafiya, sai ni kullum cikin complain kike, kuma tun da kika ga ban gyara ba ai kinsan haka Allah yayi ni, ni bana da sha'awa”


“Wallahi ba haka Allah yayi ka ba, ko minene dai daga baya ne ya same ka, ai da can ba haka kake ba, ko dai dan na haihu ne na daina burge ka?”


“A'a karki sawa ran ki wani abu, wallahi bana neman mata a waje, babu ruwana da mata, kawai dai sauyin yanayi ne”


Ya sa hannayensa aljihu ya nufi ƙofar fita. Da kallon ta kaici ta bishi, har ta fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya ta tashi ta nufi ɗakinta dan dauke faralin da yake kanta na sallah magariba.


A masallacin unguwar ya yi,alwalah yayi sallah magariba, shi kaɗai yayi abarsa dan su tuni suka sauke jan'i. Bayan ya fito ne ya ciro wayarsa dake aljihu ya kira number Hajiya Barau dan tsegunta mata labarin Namra, duk da yana tunanin ta san da zuwan na ta.


Two missing calls yayi mata, bata ɗauka ba, har ya mai da wayar aljihu sai gata ta kira, cikin sauri ya ɗaga kiran nata yana takowa zuwa gida.


“Hajiya ina wuni?”


“Lafiya ƙalau Uzairu ka kira ni ina sallah, ya gida ya mijina da Yasmin?”


“Suna nan ƙalau, yanzu ma Yasmin take faɗa min wai Namra ta zo, tana gida da yake ita gida ta wuni daga gurin aikin ta wuce gida”


“Namra kuma? Amman bata sauka nan?”


“Au daman bata sauka nan ba? Ai na ɗauka ta kwana biyu da zuwa ma”


“A'a Wallahi ni ban ji labari ga kowa ba, amman ita taga Namra ɗin da idonta?”


“Haka tace min, yanzu haka tana gidan Gwaggo”


“To ko fushi take da Alhaji ?shiyasa bata sauka nan ba?”


“Idan ma fushi take da Abbah ai ke ba zatayi da ke ba, kuma ga Anty”


“A'a mu a su wa? Kishiryar uwa mai ƙaurin suna? Ta dai san ba zuwan lafiya bane shiyasa ba zata sauka nan ba, dan tasan halin Alhaji shiyasa aka ce in za a yi tukka a yi mata hanci don kada ta warware, irin wannan ranar ake gudu, daman ni nasan abin da ya ci doma ba ya barin awai, yadda yarinyar nan ta ci amanarka ai dole alhakin ka ya fita”


Uzair yayi wani shegen murmushi


“Ashe baki san ta zo ba, amman ina jin Anty ba zata rasa sani ba”


“Ina jin ta sani sai ta ɓoye, waya sani ma ko ita tace mata ta sauka gidan Hajiya Kulu tun da tasan tana son Namra, ba zata bari Alhaji ya wulaƙanta ba, ji fa ko gobarar nan da tayi har yau bata taɓa maganar ba, in ban da ƴan'uwana da suka ce suka faɗa min da ban ji ba, ai ni naji daɗin da Alhaji ya juya mata ƴarta baya, dan duk abunda take da sanin uwar nan take yinsa, ita ke goya mata baya, ko auren nan naku da anyi da sai uwar nan ta kashe shi dan bata son ka”


“Allah ya kyauta, ai ga ta nan ta dawo mata sai tayi yadda take so da ita, Yasmin tace min duk ta rame ta yi baƙi”


“Lallai kam, kowa ya keta riga tasa, ya san inda zare ya ke”


“Kaɗan suka fara gani”


Ya faɗa sannan yayi sallama da ita ya kashe wayar. Hajiya Barau ya aje wayar ta cire Hijabin dake jikinta ta tashi ta nufi part ɗin Abbah.




MARYAM POV.


Da takaicin Namra ta koma gida, sai dai bata labarta ma Anty Amarya komai ba, dan bata san ta yadda zata ce mata ba, sai bayan magariba, sannan ta labarta mata abunda ake ciki.


Duk rikicewa Anty Amarya tayi murna da farinciki suka zo mata a lokaci ɗaya, murnar ƴarta ta zo da kuma baƙinciki bata sauka a gidan ba, ita kan ta tasan sai anyi yaƙi da Abbah kamin ya barta ta zauna gidan.


“Amman Maryam ita kaɗai kika ganta?”


“Eh ita kaɗai, Anty duk ta lalace ta rame Allah kaɗai yasan abunda yayi mata tun da har kika ga ta baro shi ta zo nan, bayan kuma ta san halin Abbah”


Sai duk Anty Amarya ta ji babu daɗi, a take ta ji tana buƙatar ganin ƴarta.


“Zan faɗa ma Abbanku ta zo ganin gida ne, ai dole ya barta ta zauna”


Maryam zata yi magana sai ga wayarta tayi ringing, Sweet PaPa ta gani hakan ya tabbatar mata da number Abbah ce, da sallama ta ɗauki wayar dan tasan Abbah ya tsani ya kira mutum ace masa hello.


“Maryam”


“Naam Abbah”


“Ki ce Mamanki ta zo yanzu”


“To”


Ta kashe wayar gabanta na faɗuwa, duk da bata san anyi komai ba, amman ta ji kamar ba lafiya ba, ta kalli Anty Amarya dake cikin yanayin damuwa tace


“Wai Abbah ki zo”


Shiru Anty Amarya ta ɗan yi sannan ta tashi cikin rashin ƙarfin jiki ta nufi part ɗin Abbah ba. Zuciyarta da biyu, ta faɗawa Abbah Namra zata zo ganik gida, kuma ta ji kiran da yake mata. Sai dai duk hanzarinta ya katse lokacin da Abbah ya gargaɗe ta akan kar ta bar Namra ta shigo masa gidan.


“Ki faɗawa ƴar ki karta kuskura zuwa min gida, ta tsaya can inda ta sauka”


“Ƴata ce kai ba da kai ba? Ko shegiya na haifa ne?”


“Nine ubanta, amman na riga na yafe ta, kuma tun ranar da zata je gidan mijinta na faɗa mata karta kuskura dosomin gida da sunan yaji ko saki”


“Ai ganin gida zata zo”


“Ba ganin gida ta zo ba, na dai faɗa miki karta doso min gida”


“Ƴata tana da buƙata na, kuma dole ta zo nan gidan nan tun da ina ciki, ko wane munafukin ne ya zo ya faɗa maka sai na ci masa mutunci”


Abbah yayi banza da ita yana kallon agogon hannunsa.


“Yanzu zamu je karɓo kuɗin kwangila, karki kuskura ki bari ta shigo min gida indai ba mugun wulaƙanci kike so na mata ba”


“Idan bata shigo ba, ni zan koma gidan mu na zauna da ita, dan ba galihu ne bata da shi ba, abunda kake yi baka kyautawa Alhaji, musulunci be ce haka ba, shikenan dan kawai ta auri wanda take so sai abu ya zama ɗan zane”




“Ai daman duk abunda take da goyon bayanki take yinsa, ke kika goya nata baya”


“Ni nake goya mata baya, ai daman ka saba faɗar haka, komai nice, daman na san ba ƴata ce baka so ba, ni ce baka so, ita Hajiya da take ƴar'uwarka ai baka mata haka ba balle ƴaƴanta, sai ni da ka auro bare, nice abar wulaƙantawa ni da ƴaƴana, ko kuma saboda ni ban haifi ƴaƴa maza ba shiyasa kake min haka”


Cikin faɗa da kuka Anty Amarya tayi maganar. Sai Abbah yayi mata wani kallo na mamaki.


“Subhanallahi, ai ƴaƴa maza da mata duka ɗaya ne a gurin Allah”


“Amman kai a gurin ka ba ɗaya bane, tun da gashi kana nuna min banbanci, idan baka da rai a yau babu wanda zan kallah na ji sanyi sai ƴaƴaka, haka nima idan bana da rai babu wanda zaka kalla ka tuna da ni ko kaji sanyi sai ƴaƴana, to dan me zasu zama abun wulaƙantawa a gareka, ashe wata rana idan bana da rai abunda zaka ma ƴar ciki sai yafi wannan tun da kayi mata haka ina raye, kai da ƴan'uwanka kun sa Namra a gaba, kamar ta kashe muku wani, daman ni ce ba ku so ba ita ba”


Ta juya ta fita tana wani irin kuka kamar ta faɗi ƙasa. Har cikin ransa Abbah yake jin kukan Anty Amarya, kalamanta sun ɓata masa rai, sai kuma sun fi taɓa masa zuciya sosai har sun sa ya sauko daga fushin da yake.
Ɗakinsa ya koma ya ɗan kimtsa sannan ya fito ya nufi gurin da aka saba aje masa motocinsa.




Da kuka Anty Amarya ta shiga part ɗinta, duk hankalin Maryam sai ya tashi, kasancewar ita kaɗaice ke falon, ganin mahaifiyarta na kuka, yasa ita ta fashe da kuka ba tare da tasan dalilin kukan na Anty ba.


“Anty me ya faru?”


“Wallahi yai ba zan kwanan a gidan nan ba, babu abunda zai sa na kwana gidan da za a hana ƴata shigosa, yafi son ta je can ta zauna inda za a riƙa zaginta ana tseguminta”


“Be yarda ta zauna, ban san munafukin daya faɗa masa ba”


“Anty kiyi haƙuri, zai sauko yana cikin fushi ne”


Aisha ce ta fito daga ɗakinsu ita da Hindatu suka nufo gurin da Anty Amarya take, suna tambayar ba'asi, dan basu san abunda yake faruwa ba, suna can ɗaki suna karatun exam.


“Lafiya miya faru”


Aisha ta tambaya tana dafa Anty.


“Abbah ne yace wai Namra ba zata shigo masa gida ba”


Maryam ta faɗa tana kuka. Hindatu ta kalleta da mamaki tace


“Amman yanzu Abbah ya kira wayar Aisha yace ta faɗa niki kije ki zo da Namra”


Anty Amarya tayi saurin kallon Hindatu tana share hawayenta.


“Da gaske? Yanzu ya kira ki?”


“Eh Wallahi”


Anty Amarya ta tashi da sauri ta nufi part ɗin Abbah, kamin ta ƙarasa ta hangoshi jikin mota, yana jiran direbansa ya tashi motar.
Gurin ta ƙarasa ta tsaya masa a gaba.


“Kai kace azo da Namra?”


“Amman sati ɗaya na yarda ta yi”


Haka kawai ya faɗa ba tare daya kalleta ba, ya buɗe motar ya shiga. Sai ga Anty ta dawo falon da far'ah tana cewa Maryam da Aisha su je su taho da ita.








RASHIDA POV.


Kwanan ta biyu asibiti suka sallame ta bayan anyin mata wankin ciki, sai dai duk tsawon kwana biyun da tayi Hilal be liƙe inda take ba, duk kuwa da kasancewar a gurin yake aiki.
Kuma duk tsoron kwanakin be kawo yaransa ba, sai dai ma'aikaitam gurin sun yi ta zuwa ganinta, sanin cewa ita uwargidan Doc ce.
Ranar data dawo gida ta ci kuka kamar ta mutu, babu irin rarrashin da ƴan'uwanta ba su mata ba amman sam ta ƙi ji sai da tayi kukanta har ta gaji sannan ta saurarawa kanta.
Daren ranar da aka sallame ta ne Asmee ta zo gidan, ita tayi ta bata haƙuri tana ƙara mata ƙarfin guiwa akan inda zata kai ta Hilal ya mayarda ita, sun kitse magana akan zasu tafi tare gobe idan Rashida zata fita. Sun daɗe suna tattauna lamarin kasancewar su biyu ne kawai a ɗakin, tun Rashida na kuka har ta daina.


Tun dawowarta gida bata sa komai a cikinta ba, bata komai sai tunanin Hilal da kuma makomarta, gani take idan har da gaske tana da hiv ya makomar iyayenta zai kasance tun da dole ne tayi mu'amala da mutane. Wayarta ta janyo ta kira wata ƙawarta wace ta kasance likita ce. Bugu biyu ta ɗauka, bayan sun gaisa, Rashida take ce mata


“Dr Fatima, ina son na tambaye ki ne akan hiv, wata sis nace take rubuce-rubuce shine take tambaya ni kuma na ce bari na tambaye ki tun da ni ba sashena ba ne”


Dariya Dr Fatima tayi ta ce


“Amman gaskiya bayanin yana da ɗan tsowo, why not na yi miki ta whatsapp kina online yanzu haka”


“Yauwa to haka ma yafi, bari na hau”


“Daman na san ba zaki kira ni haka nan kawai ba”


Rashida tayi dariya bata daɗin rai ba, ta kashe wayar. A take ta kunna datar ta sa hau online. A contacts list ɗinta ta shiga ta nemi Dr Fatima tayi mata sallama. Sai da ta ɗauki ƴan mintuna sannan ta amsa sallamar sai ta koro mata da bayani.


“CUTAR KANJAMAU/TSIDA (HIV-AIDS)


HIV (human immune virus) ita kwayar cuta ce da take haifar da AIDS (Acquired immunodeficiency syndrome) ma`ana karyewar garkuwar jiki wadda aka fi sani da tsida ko kanjamau. Ita wannan cuta, cuta ce da take karya garkuwar jiki (immune system) wanda ke bada daman wanda, ke dauke da ita ya kamu da wasu cu tuttuka sakamakon karyewar garkuwan jiki. rashin kiyayewa ko kula da wannan cuta kan sa mutum ya halaka a takaitaccen lokaci kamar daga shekara 9 zuwa 11 ya danganta wani yanayi.


HANYOYIN DA AKE KAMUWA DA CUTAR KANJAMAWA/TSIDA


Ana kamuwa da ita wannan cuta ta hanyar shigar kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) chikin jini. San nan hanyoyin da kwayar cutar ke shiga jiki na dewa, kan iya shiga ta hanyar haduwar jinin me dauke da cutar ga mara dauke da cutar kamar ta hanyar cizon sauro, maniyi, ruwan farji (vaginal fluid) mafi yawan cin masu dauke da wanan cuta na kamuwane ta hanyar saduwa (sex) da me dauke da cutar. Ana kuma iya kamuwa ta hanyar yin anfani da allurar da me dauke da ita yayi mfani dashi. San nan jarirai na iya kamuwa da ita kwayar cutar daga uwa ta hanyar shayar wa, da lokacin da suke a ciki (pregnancy).


Ita wanan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing) kokuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, ma gogin baka (brush).
Idan yazama cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) ba`a kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing), cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci (comb), tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar”


Tun da Dr Fatima ta fara bayaninta Rashida take karanta abunda take aiko mata, sai da ta kai nan sannan Rashida ta aika mata da wata tambayar.


“Amman Dr ya alamomin cutar yake?”


Ta samu minti biyar zuwa shida kamin tayi ma Rashida reply


“Alamomin ita wan nan cuta ta banbanta daga mutun zuwa mutum. Mutane biyu kan iya kamuwa a lokaci guda amma ba lallai sun nuna alamomin iri day aba. Anan zamu raba alamomin kamar kasha uku muyi bayani akai.


 (acute illness)
 (asymptomatic period)
 (advanced infection)


Acute illness


(acute illness) ma`ana alamomin farko na kamuwa da ita wannan cuta. Kashi tamanin cikin dari 80% dake dauke da cutar na farawa da jin kamar alamomin mura (flu-like) dake kai tsawon sati biyu zuwa hudu rukunin farko. Abubuwan dake faruwa a wannan rukuni sune:


 Kuraje kana na a jiki (body rash)
 Zazzabi (fever)
 Boshewar makokoro (sore throat)
 Jin gajiya (fatique)
 Kumburi a (lymph nodes)
 Fashewar baki da alaura (mouth and genital ulcers)
 Chiwon nama (muscles pain)
 Ciwon gabobi (join pain)
 Amai da hamami (nausea and vomiting)
 Zufa cikin dare (night sweat)


Wa yan nan alamomin na faruwa mutum ya gaggauta zuwa kuji don gane yana dauke da ita bai dauke

Please Login or Register in order to submit comment