Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

for your comments... 😘
Best regards to you all... 💖


CANDY🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

Website
www.khadeejacandy.com.ng


This page is for Birthday Girl Salwees. Happy Birthday Dear 💖


*PAGE - 26*


NOT EDITED ⚠️


Hankalin Namra be kwanta ba har sai da aka fito da shi daga ɗakin da aka masa aikin.
Sai suka dawo da shi, ɗakin da yake, anyi aiki cikin nasara da taimakon Allah.


Sai da yamma Mama ta je gidan Namra ita da Hajara dan yin wanka ta kuma ɗan huta, Mardiya Namra ta bawa keys ɗin gidan dan ta taba musu abinci kuma ta taya su zama. Ita kuma ta kwana da Asim a asibitin.


Babu irin inda Mama bata shiga ba a gidan, sai baya kyau gidan take da girmansa. Mardiyace ta faɗa mata Namra ta siyar da gadon har an bata wani abu daga ciki.
Babu irin tsinuwar da Mama bata yi ma iyayen Namra ba, a zatonta sune suka turo mata da kuɗin aiki dana magani, a nan ne Mardiya ta ƙara fayyace mata matar data taimaka ta kawo Asim asibiti ba yar'uwarsu bace, nan ma Mama ta cika da mamaki, dan a zatonta ita yar'uwarsu.


“Kai tirr da wasu mutune Wallahi, wato su babu ruwansu da lamarin mijinta tun da ba ita bace ko? Hmmm ni ban taɓa ganin iyaye irin nata ba, daman ba son auren su ke”


Taja wani godon tsaki sannan ta fito daga ɗakin, ta shiga kitchen ta fito ta shiga ɗayan ɗakin. Mardiya dai na biye da ita har ta gama duba gidan. Shikafa da miya Mardiya ta dafa tare da Hajara.
Washe gari ma wani abincin Mardiya ta sake dafa musu, bayan sun ci ta zuba wanda zasu tafi dashi a asibiti, sannan suka wanka suna cikin shiri Dillaliyar ta zo Mardiya tace mata bata nan, sannan ta rufe gidan suka nufi asibitin.




Namra suka tarar zaune a kujerar dake ɗakin tana bawa Asim tea. Ba laifi alamun sauƙi ya bayyana a yanayinsa, wanda a ada ma idan ya ɗaga ido sai yayi saurin rufewa yanzu kuma gashi har yana shan tea.
Farinciki gurin Mama ba'a magana, sai ta zauna saman gadon kusa da shi, tana murmushi


“Mashallah Ibrahim, Allah ya ƙara maka lafiya”


Ɗan murmushi yayi kaɗan irin yana jin zafin ciwon nan yana ƙarfin hali. Mama ta kalli Namra


“Yaushe ya farka?”


“Tun da asuba, har likita ya duba shi ya bada wata takardar ta gani yace allura ce za a masa guda bakwai, kullum ɗaya saboda jinin daya bugu a kansa”


“Allah yasa dai babu tsada”


“ Pharmacy asibiti sun ce duk ɗaya, dubu tara ne, ga kuma maganin da suka rubuta shima sai yaci dubu biyar”


Mama ta rafka uban tagumi.


“Tau ai fa kaji matsalar babbar asibiti, yanzu ina za a samu wannan kuɗin kuma? O Allah”


Namra ta saci kallon Mardiya da idonta ke kansu, tace


“Mardiya kuje waje ke da Hajara”


Tashi tayi ta fice ita da Hajarar. Sannan Namra ta kalli Mama tace


“Akwai kuɗin da zan siya da su, amman da abinci naso mu siya dan abincin mu ya ƙare”


Kai Mama ta girgiza


“Wai Namra iyayenki haka zasu zura miki ido, babu wani taimako? Naga dai suna da shi, amman ko ɗan abincin nan ai sa taimaka muku da shi, amman ace kayi ta sai de sai de anya haka yayi?”


Wani kallo Namra tayi mata.


“Iyayena sun yi iya ƙoƙarinsu duk kan abuɓda zasu min a yanzu kyautatawa ce, amman ba dole ba, balle kuma mijina ”


“Haka ne, daman can ai ba son auren su suke ba, sun fi son ku yi ta wahala kamar ba ƴarsu ba”


“Mama ya kamata ki kina tauna magana kamin furta ta, iyayena, iyayena kuma sun min komai tun da har suka bar ni na auri Asim”


“Amman idan ga mutunci ai da ke da shi kun zama ɗaya, ki duba kiga ko dubiya har yanzu babu wanda ya sake leƙowa daga danginku, Kuma wallahi inda wani guri ne dole ne su ɗauki nauyi naganinsa tun da da motar gidan yayi haɗari, amman sun ɗauki ƙiyayyar duniya sun ɗora masa akan auren ki kamar wanda ya kashe musu wani abu”


Zuciyar Namra ta kawo sosai, a take idonta ya cika da ƙwalla.


“Asim yayi haɗari da motar gidan mu saboda an rubuto zai yi haɗarin, wai Mama mi na tare miki ne? Miyasa kike abu kamar wanda bata yarda da ƙaddara ba, miyasa zaki ɗauki laifin haɗarin motar da Asim yayi ki ɗora min?


Kin manta da ni matarsa ce wace mace ce zata so mijinta ya kasance a halin da Asim yake? Duk abunda na masa baki gani ba? Mahaifiyarsa ce ke amman sisi ban tambaye ki na siyer da kayan ɗakina na biya masa kuɗin magani, amman duk wannan be isa a goge laifina ba? Kin kira aure na da ƙaddara kina tunanin hakan yayi min daɗi? Me kike son na masa ne? Rai na kike son na cire na bashi ko kuma ciwon kike son na maida jikina?


Haba Mama ku bar ni na ɗaya mana, da matsalar iyayena zan ji ko da ta mijina, ko kuma wanda kike ƙoƙarin sani, ke uwace wata maganar be kamata tana fitowa daga bakin ki”


Mama ta cika da mamakin jin furucin da Namra tayi mata, wani dogon numfashi taja ta sauke tana taɓe baki.


“Kin goge ladarki Namra, daman kin masa duk abunda kika masa ne dan ki faɗa kin masa, ai kaji tsiyar taraiya da mai arziki, so kike ace ɗana ya cinye miki komai ko? A ƙaƙaba masa, kamar yadda aka masa na satar ki ko? Ni da zuciya ɗaya na bar ɗana ya aure ki ba da wata manufar ba”


Ta ƙarasa maganar da kuka har da hawaye. Uffan Namra bata ƙara cewa ba, sai kawai ta ɗauki jakarta ta fice.
Sai da ta biya gurin da su Mardiya suke ta karɓi keys sai Mardiya ta biyo ta suka yi gida tare. Tun a Napep Namra ta soma yi ma Mardiya faɗa.


“Dan me zaki faɗawa Mama na siyar da gado na ? Ina ruwanki da rayuwata tana mijina? Jaka zaki tallata ni a unguwa? Ko akai na farau? Abunda ya shafi mijina da mahaifiyata nawa ne babu ruwanki a ciki, dan haka ki iya bakin ki”


Ta ƙarasa dai-dai lokacin da mai Napep ɗin ya sauke su ƙofar gida, Namra ta miƙa masa kuɗinsa ta nufi gate ɗin ta buɗe ta wuce cikin gidan a fusace. Mardiya ta rufa mata bayana tana ƙoƙarin wanke kanta.




_______________________________________


Yau yayi kaɗan ko? Bana son na bar ku babu post ne. Idan Allah ya bani iko zan yi dogon page gobe.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

Website
www.khadeejacandy.com.ng


*PAGE - 27*


NOT EDITED ⚠️


Namra na saka ƙafarta cikin falon Mardiya ta saka nata, ta zauna kusa da Namra ta marairaice tana ta ƙoƙarin kare kanta.


“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, Wallahi Dillaliya ce ta shigo lokacin da zamu fita da su, nace mata baki nan shine tace ga cikon kuɗin ki kuma tana son ta ɗauki gadon, shiyasa har ta ji, idan ma baki yarda ba zan iya zuwa na kira Dillaliyar ki tambaye ta ki ji”


Namra ta sauke ajiyar zuciya tana son danne fushinta.


“Na ɗauka ke kika faɗa, da nace baki min amana ba”


“Haba Namra nikam miye ruwana da sha'aninku tsakanin ki da miji da yan'uwansa babu ruwana a ciki. Dama tazo nan babu irin maganar da bata yi ba a kan iyayenki amman uffan ban ce mata ba, ke ma kuma ban faɗa miki ba”


Wani ɗogon numfashi Namra taja ta sauke, tayi shiru kamar mai nazari.
Mardiya ta tashi tana kaɗe jiki.


“Ni kam na tafi sai wata rana kuma”


Namra ta yi saurin riƙe mata hijabi.


“Haba Mardiya ki yi haƙuri mana, rashin fahimta ne kin ga ai ko kece ba zaki jidaɗi ba”


“Haka ne amman kin ga zama da rashin aminta da mutum ba daɗi, matsalar mijinki ma kawai ta isashe ki”


“Shine abunda ya fi damu na, yanzu ma wani maganin suka rubuta min, ina ganin sarƙa na zan siyar na haɗa da kuɗin da suke hannun dillaliya na siya masa maganin abunda ya rage mu siye abincin”


Gaban Mardiya yayi dakan uku-uku jin Namra ta ambaci zancen sarƙarta, take taji natsuwar dake tare da ita ta tafi. Sai ta tashi tana karkaɗe jiki


“Bari naje gida, daga can zan yi ma dillaliya magana nace kin dawo”


“Yauwa dan Allah ki faɗa mata, ai kin san inda ake sai da zinari ko?”


“Gaskiya ban sani ba, amman zan bincika miki”


“Yauwa na gode kin ci abinci ai ko?”


“Eh na ci, sai an jima”


Kamar walƙiya haka ta fice daga falon, zuciyarta kamar zata fito daga ƙirjinta saboda tsoron kar Namra ta nemi sarƙar ta, bata gani ba, kuma tasan ita kaɗai zata zarga tun da ita ta saba shigar mata ɗaki.


Bayan fitar Mardiya Namra ta tashi a gajiye ta shiga ɗakinta, tufafin jikinta ta cire ta ɗauki tawul ta ɗaura ta shiga wanka.
Ta daɗe tana wankan sannan ta fito cike da jindaɗin jikinta, ta buɗe lalulayen ɗakin kasancewar babu nepa, ta kwanta saman godon ba tare data saka wasu tufafin ba, saboda gajiya da kuma bachin dake cikin idonta. Nan da nan bachi yayi gaba da ita.


ANTY AMARYA POV.


“Nifa na damu da rashin kiran Namra, idan an kira ba a samu ita kuma bata kira, Allah dai yasa lafiya”


“Lafiya ƙalau Inshallah, kin san halin da Asim yake maybe ta siyar da wayar”


Cewar Hindatu tana dannar wayar dake hannunta.


“Amman kin san ba mu kyauta ba? Rashin sake zuwa duba shi da kuma kira a ji ya jikinsa? Ko a kan Namra ya kamata mu yi haka”


“Toh ai matsalan ba a samun wayarta”


“Ki je gidan su Asim gobe ko anjima ki karɓo min line sa, ko shi mu kira sai muyi magana da Namra ɗin”


“Amman ba Mamarsa taje Katsina ba?”


“Eh amman ai ba a rasa mai number ba a gidan”


“Zan je anjima inshallah”


Maryam dai na jinsu amman uffan bata ce ba, sai karatun ta take.


NAMRA POV.


Da ƙarfi taji tsawar mota a harabar gidan. Da gudu ta fito daga kitchen ta nufi gurin da motar take tsaye. Ga mamakinta sai ta ga Asim ya fito daga motar jikinsa ƙam kamar be taɓa ciwo ba, wani irin tsale ta daka ta dire saboda murna, tana shirin gudu izuwa gareshi sai kawai wasu karnuka suka taso ta bayansa suka yi cikinta suna ƙoƙarin cizonta.
Hakan be hana ta gudu da isa gare shi ba, ta rumgume shi, sai kawai taji ya ƙyalƙyale da dariya ya luma mata wata ƙatuwar wuƙa dake hannunsa. Wani irin ihu ta saka ihun da bata san har a fili tana yinsa ba. Kirgigi ta farka daga bachin tana wani irin haƙi da ambatar sunan mahallincinta.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, A'uzubillahi”


Har yanzu jikinta rawa yake, kanta sai rasawa yake, saboda mummunan mafarkin da tayi. Ta daɗe a haka sannan ta yi unƙurin tashi tana kallon agogon ɗakinta. Har biyu da rabi ta gota tana bachi bata yi Sallah.
Da sauri ta nufi banɗakin dan yin alwala, kamin ta ƙarasa ta tsaya cak, saboda abunda ta ji yana zubo mata daga ƙasanta zuwa ƙafafunta, dubarwa da zata yi sai ta ga jini sare-sare yana zuba kamar an tunkuɗo shi.


“Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un”


Shi ne abunda ta furta da ƙarfi tana mai jin tsoron halin da take ciki, kamin ta ankaro ta soma jin wani irin mugun ciwon mara marar misaltuwa, a gurin ta zube tada dafe ƙasan marar nata dake mata wani irin mugun zugi.
Mulmula ta fara yi tana kuka, tawul ɗin dake jikinta ya kwance amman bata kula ba sai neman ceto take gashi gidan babu kowa.


Sai kusan biyar na yamma hankalinta ya dawo jikinta, har ta gane inda take kwance, gurin duk ya bace da jini, sai dai har yanzu mararta na mata ciwo da zuji ga wani uban nauyi da take jin cikinta yayi.
Daker ta unƙura ta shiga banɗakin, nan ma zubewa tayi ƙasa saboda rashin ƙarfin jiki, haka sare-saren jini ya riƙa fita daga cikinta tana kuka. Bata samu sassauci ba sai gaf da magariba, sannan ta samu ta tashi ta wanke jikinta ta gyara gurin cikin rashin kuzari ta dawo ɗakinta ta kwanta ƙasa idonta har wani lumshi suke.


Daker ta iya amsa sallamar da Mardiya da Dillaliya suke, sai dai bata iya tashi ba har Mardiya ta samu meta a gurin.
Yanayin yadda ta ga Namra yayi matuƙar ɗaga mata hankali, da sauri ta ƙarasa kusa da ita ta tashe ta zaune.


“Subhanallah, Namra me ya same ki?”


Cikin dauriya da ƙarfin hali Namra tayi mata magana.


“Jini ne yayi min zuba, kuma marana ciwo take sosai”


“Ko ki tashi muje asibiti?”


“Ba zan iya tafiya ba”


“Zan riƙa ki, tashi ki saka tufafin ki muje, kuma dillaliya tana falo tana jiran ki”


“Ki ce mata ta shigo”


Ta faɗa tana wani irin dantsar baki. Mardiya taje ta shigo da ita. A tsatsaye suka gaisa da ita ta miƙawa Namra kuɗin tana mata sannu.


“Allah ya sauwaƙe amman gara kuje asibiti, daman nace bari na kawo miki cikon kuɗin ne, inya so gobe sai na zo na kwashe kayan”


Kai kawai Namra ta iya ɗaga mata, ta juya ta fita tana mata Allah koro sauƙi.
Ƙyar idon Mardiya kan kuɗin da Dilalliyar ta bawa Namra. Namra ma bata kuɗin take ba ta lafiyar ta take.


“Ki tashi ki shirya bari naje na kira mai Napep”


“Amman za a same su da daren nan? Kin ga magariba tayi kar muje asibitin ba kowa”


“A'a Asibitin Malam Yakubu zamu nan kusa take kuma shi ko yaushe yana karɓar marar lafiya, musamman irin wannan”


Ta kai Hannu ta ɗauki kuɗin da suke gefen Namra ta saka cikin bed side drawer.


“Bari a aje kuɗin nan har mu dawo”


Bata tsaya jiran abunda Namra zata ƙara cewa ba, ta juya ta fita da sauri. Cikin ƙarfin hali Namra ta tashi ta saka pad ta zura doguwar riga, ta saka Hijabi ta fito falo ta zauna, yana sauraren yadda kanta ke tsarawa ga jikinta duk yayi mata babu daɗi.


Tana haka Mardiya ta dawo.


“Tashi muje gashi can ƙofar gida”


Ta riƙa suka fita tana mata sannu, a hankalin Namra take takawa kamar mai koyon tafiya har suka isa bakin gate ɗin, da taimakon Mardiya ta shiga Napep ɗin. Sannan Mardiya ta kalleta tace


“Ina Keys ɗin a rufe gidan?”


“Na manta shi yana can gefen dinning, dan Allah ki ɗauko min jaka na, ki ɗauko dubu biyar cikin kuɗin nan da Dillaliya ta kawo”


Da Tau ta amsa ta koma cikin gidan zuciyarta cike da saƙe-saƙe. Lokacin data shiga Kitchen ta fara shiga ta ɗauki ashana, sannan ta shiga ɗakin ta ɗauko jakar data san Namra na saka atm ɗinta, kuɗi da kuma wasu abubuwan a cikin sannan ta bude dorowar ta ɗauko kuɗin ta ciri kubu biyar ta saka a jakar Namra, sannan ta ɗauki sauran ta saka wata ƴar ƙaramar jaka dake jikinta mai kamar pose ɗin tsofi, sai ta warware zagenta ta ɗaga pant ɗinta sa saka jakar cikin pant ɗinta sannan ta ɗauki ɗankwalin Namra ta ƙyasta ashanar ta liƙa masa ta jefa saman gadonta.


Sai ta fito da sauri ta ɗauƙi keys ɗin ta rufe falo, sannan ta nufi gate gabanta na mugun faɗuwa ƙirjinta kamar zai fito.
Nan ma sai da ta tsaya ta rufe gate ɗin, sannan ta shiga Napep ɗin tana miƙawa Namra jakarta. Har mai Napep ɗin ta tashi Napep ya fara tafiya idon Mardiya yana kan gidan, zuciyarta cike da wasi-wasi. Namra kam idonta a lumshe yake ta jinginar da kanta jikin Mardiya tana yadda Mararta ke mata zugi.


KALSOOM POV.


Har ta isa gida tana tunanin abunda zata faɗawa iyayenta, taya zata iya faɗa musu dalilinta na dawowa gida? Bata samu mafita wata ƙarya da zata musu ba, hakan yasa taja bakinta tayi shiru duk juyin duniyar nan da Momi tayi akan Kalsoom ta faɗa mata dalilin na dawowa gida sai taƙi, bata ce shi yace ta dawo gida ba, kuma bata musu wata ƙaryar ba.


“Bari Dady kun ya dawo idan ni baki faɗa min ba, shi ai kya faɗa masa, haka kawai ki ɗauko akwati ziƙi-ziƙi ko kunya ki tafo gida, auren an samu daker anyi yanzu shine kike son ki kashe ko? Tau baki isa ba Wallahi”


Duk irin faɗan da Momi tayi Kalsoom bata yarda ta faɗa mata abunda ya faru ba, hakan yasa Momi kira Dad a waya ta labarta masa abunda yake faruwa. Cikin ƴan mintuna ya baro office ya dawo gida. Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, ya rufe Kalsoom da faɗa akan ta faɗa masa dalilinta na dawowa gida amman ta ƙi.
Da kansa ya ɗaga waya ya kira Hilal yace yana nemansa, a lokacin Hilal yana tsakar aiki ne hakan yasa ya nemi Dad yayi masa lamani har zuwa dare.
Daren na yi sai gashi ya zo gidan, a nan ma yayi sallah isha'i, sai fira yake da Dad kamar Abbansa. Har suka shigo cikin falo sannan Dad yake tambayarsa ko akwai abunda ya shiga tsakanin su da Namra. Murmushi Hilal yayi ya wayance sosai kamar ba shi ba.


“Dad ni ai nayi mamakin da kace min Kalsoom ta zo gida ɗazu, dan gaskiya ni ban san wani rashin jituwa daya shiga tsakanin mu ba, sai dai ɗan abunda ba a rasa ba na kishi tsakanin ta da abokiyar zamanta, amman kasan rai ajizine ban sani ba ko nayi mata wani abun da ba zata iya faɗa min ba shiyasa ta kawo ƙarana”


Dad yaja tsaki yana girgiza kai irin nasu na manya.


“Kai sha'anin mata sai haƙuri, ni Wallahi na ɗauka wani abun akayi ma, babu yadda ba muyi ba amman yarinyar nan taƙi tayi magana”


Dad ya tashi ya shiga ciki gurin kiran Kalsoom. Hakan yasa Hilal gyara zamansa yana mai jindaɗin da Kalsoom bata faɗi abunda ya faru ba. Dad be daɗe ba sai gashi ya dawo falon tare da Kalsoom da Momi.
A kujera ɗaya ya zauna da Momi Kalsoom kuma ta zauna ƙasa kusa da Momi.


“Tau gashi nan shi dai yace be san wani abu ya shiga tsakanin su ba, ke sai ki faɗa idan akwai abunda yayi miki wanda be sani ba, ko kuma yayi miki shi cikin kuskure”


Ɗagowa tayi ta kalleshi, shi ma sai ya tsare ta da manyan idonsa, har sai da taji ba zata iya ɗaukat kallonsa ba, ta kawair da nata idon. A hankali ta kira sunan ta.


“Kalsoom, Dan Allah kiyi haƙuri ki yafe min, idan har akwai abunda nayi miki a cikin rashin sani ko da kuskure, koma da gangan kin san ɗan'adam aziji ne”


Ji tayi kamar yasa sarƙa ya ɗaure dukanin ilahirin jikinta, sai ta kasa sake ɗaga ido ta kalleshi, kuma ta kasa furta komai. Har Dad ya gama faɗansa da yake mata akan zamantakewar aure da haƙuri. Momi ma ta ɗora da nata sannan suka tashi suka basu guri.
Tasowa yayi daga inda yake zaune ya zauna ƙasa kusa da ita jikinsa na gogar nata, yasa hannunsa ya riƙe nata, fuskarsa kuma daf da nata ta yadda suna iya shaƙar numfashin juna.


“Babe tashi muje gida, na gode sosai da baki faɗawa Dad abunda ya faru”


“Ba zan iya bin ka gida ba, saboda ka riga ka furta duk ban biya ka ba, a bakin igiyar aurena”


“Kuskure na, na san nayi amman dan Allah ki yi, ba zan sake ba”


“Ni ba zan zauna ba, ai ka riga ka nuna kuɗin sun fi rayuwar aurena daraja”


“Shiiiiiiiiiii”


Ta ɗora lips ɗinsa saman nata, yana goga mata hancinsa.


“Ba haka nake nufi ba, zuciya na ne ya kawo har nayi wannan furucin kuma yanzu ina nadama”


Kawarda fuskarta tayi ta unƙura zata tashi, sai ya danneta da dukan ƙarfinsa.


“Don't try me, ba ki da wannan karfin bana son Dad da Mom su san halin da muke ciki, dan Allah Kalsoom kiyi haƙuri idan ma zuciyarki bata natsu ba, idan mun koma zaki iya biyana”


Be sake ta ba har sai da yawun bakinsu sukayi taraiya. Sannan ta tashi ta koma ciki, shi kuma ya fito waje yayi ma Dad sallama. Ita kuma ta ɗauko akwatinta ya karɓa ya saka a mota sannan suka tafi.
Tun da suka kamo hanya ta kalli inda take yake ba, idonta na kam gefen gilashin motar gurin ti-ti. Murmushi yayi ya kai hannu ya shafi fuskarta.


“Na san abunda na yi ban kyauta ba, amman dan Allah kiyi haƙuri, i love you so much”


Uffan bata ce masa ba, bata kuma sakar masa fuska ba, har suka isa gida. Shi kuma duk ya damu, wani irin sha'awarta yake jin tana masa yawo a jiki ga shi be ga alamun sauƙi a tare da ita ba.
Suna shiga cikin falon ta wuce ɗakin. Yayi kamar ya bita sai kuma wata zuciyar ta hana shi, sai kawai ya nufi ɗakin yaransa inda yake jin ihunsu. Da gudu suka zo suka rumgune shi.


“Eyyyy Daddy welcome”


Ɗaya bayan ɗaya ta riƙa shafa kansu, daga bisani ya kai hannu ya ɗauki Rafiq ya rumgume.


“Daddy Ammyn Rafiq ta fita wai gurin aikinta suna nemanta, tace mu zauna har ka dawo”


Ezzah ta faɗa tana wasa da ribon ɗin dake hannunta.


“Kuma tace idan ka tambaya mu faɗa maka ita ce ta ɗauki kuɗin dake cikin closet na ka”


Wani irin abun ɓacin rai ya taso yayi matsa tsaye a zuciya, yana auna irin rainin da Rashida tayi masa, taya zata fara yi masa abunda bata saba ba har tasa ya zargi Kalsoom.
Rufe ido yayi saboda wani mugun ɓaci rai da yaji ya rufe shi,


“Daddy are you okay?”


Yayi murmushin ƙarfin hali yana kallon Ezzah.


“I'm fine, Kuje ɗakin Anty ku ta dawo”


Da gudu suka nufi ɗakin suna ihu da murna.
Kamar zasu ɓalla ɗakin haka suka tura ƙofar ɗakin Kalsoom suka shiga suna mata sannu da zuwa. Yanayin yadda suka ga Kalsoom tayi musu da fuska yasa suka yi tsaye cirko-cirko suna kallonta.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

Website
www.khadeejacandy.com.ng


Meaning of POV. Point of view: used especially in describing a method of shooting a scene or film that expresses the attitude of the director or writer toward the material or of a character in a scene.


*PAGE - 28*


NOT EDITED ⚠️


“Bana ce ku daina shiga ɗaki da gudu ba? Ban hana ku ban kar ƙofa ba? Sai kace ball”


Duk kama kunnensu suka yi kamar yadda ta koya musu.


“Auntie we sorry”


“Sorry for yourselves, aya kowa ya riƙe ƙafarsa ɗaya”


Duk dariya suka saka suka rumgume.


“Allah kuwa ba zamu sake ba, Auntie da baki nan Ulfah tace Dady ya siyo mata takeaway”


Ezzah ta faɗa tana zare idon, sai murƙususu take kamar ta shige jikin Kalsoom.


“Ke kuma kika yi faɗa da wata a School”


“Eyye 2+2 kowa taje ta kama ƙafarta na ce”


“A'a ai kince ba zaki sake mana horon dare ba, yau mun yi missing ɗin ki Auntie ina kika je?”


“Wani guri na je”


Ta faɗa tana jan hancin Ulfah, har ga Allah tana son yaran, haka take jin su kamar itace ta haifi su, sam basa sakewa da Mamarsu kamar yadda suke sakewa da ita, saboda ta kan basu lokacin ta.


“Aje a kwanta gobe akwai makaranta, kar a makara”


“Okay Auntie”


Duk kiss suka mata a gefen fuska sannan ta shafa kan su.


“Idan za a kwanta a yi alwalah, Ezzah ki yi addu'ah sai kiyi ma Ulfah, ke kuma Ulfah kiyi ma Rafiq, kuma zan shigo na ga wanda ya kwanta ba dai-dai gobe akwai kama ƙafa”


Ulfah ta tsuke baki ta girgiza kai


“A'a bana so yawunta be da tsarki”


Dariyar Hilal ce ta ɗago ta duka hankalinsu izuwa garesu, ashe yana tsaye jikin ƙofa yana kallon su.
Kalsoom ta ɗan sha masa mur, irin har yanzu fa fushi nake kai, ta kalli yaranta.


“Good night sweethearts”


“Good night Sweet Auntie”


“Ku saka kayan bachi, sauran ku watsar

Please Login or Register in order to submit comment