Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har suka yi raka'ah biyu, sannan suka sallame. Hannunsa ya ɗaga masa ya riƙa kwaroro musu addu'ah tana amsawa da amin sanna suka shafa, sai ya juyo ya kalleta.


“Hajiya Akwai wata sunnar bayan wannan?”


Ta zare masa ido. Sai ta gurgiza masa kai alamar a'a. Dariya yayi ya tashi ya ɗauko ledojin da gefen gadon ya kawo gabanta ya aje, sannan ya fita daga ɗaga ɗakin gaba ɗaya. Be ɗauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo da plate da cup ta aje a gabanta sannan ya zauna yaja ledar ya buɗe ya fido ƙatuwar kaza ta ɗora saman plate ɗin sai ya mayardar ragowar gajin a gefe ɗaya, ya buɗe madara ya zuba musu a cup ɗaya sannan yasa hannu ɓare kazar ya soma kai mata a baki. Kawar da fuska ta yi tana murmushi.


“Ki taimaki bawan Allah nan ki bar shi ya ciyarda dake a wannan daren da yafi ko wane dare muhimmanci da daraja a gareshi”


“Na hutar da kai, zan iya wannan aikin”


“Ai bana son hutun ne, idan dare ya lula ke da kanki zaki min kukan gajiya ki neman na hutar da ni, amman ba yanzu ba yanzu ai ai ba aiki na ke ba”


Ta ɗan fiddo ido tana kallonsa, sai ya kanne mata ido ɗaya, ba shiri ta buɗe baki tana mamakin yadda yake ƙoƙarin faɗar maganganu kai tsaye. Hakan ya bashi damar saka mata naman a bakin.
Cikin so da ƙauna yayi feeding ɗinta, sai da ya tabbatar ta ƙoshi sannan ya cilasta mata ita ma ta yi feeding ɗinsa a dole ba dan ranta ya so ba, bayan sun ƙare ya kwashe plate ɗin ya buɗe wardrobe ya fiddo kayan bachi kala ɗaya amman na maza da mata, na matan ya miƙa mata shi kuma ya shiga ƙoƙarin zame kayan jikinsa ya canja zuwa na bachin sai ta zaro ido.


“Wai nan zaka canja su?”


“To miye? Naga an zama ɗaya”


“A'a da saura, bari na baka guri ka canja”


Wani shu'umin murmushi yayi har da cije baki.


“No ba sai kin fita ba, bari na baki guri ki canja nima kuma sai na canja a wani ɗakin ko, ƙina da gaskiya ai ba mu zama ɗaya ba amman mun kusa raba gari”


Ya fice yana dariya kamar ba shi ba. Yana fita ya ɗauki kayan bachi da zimmar canjawa sai ta ga ɗan ƙaramin wando sai wata fikicar riga iya cibiya sai kuma babbar mai kamar rariya wacce zata rufe jikin gaba ɗaya. Mayardar kayan ta yi ta aje taja gyalenta ta ƙara rufe jiki.


Shima irin kayan bachinta ne jikinsa bancanci shi baya da wannan ficikar rigar ƙirjinsa a sake yake. Tana kallonsa gabanta yayi mugun faɗuwa, ta razana sosai kamar bata taɓa ganin ƙirjin namiji a waje ba, yana doso inda take ƙanshin turaren da ya saka ya riƙa dukan hancinta, ko da ya ƙaraso kusa da ita ta rufe idonta gan numfashinta har rawa yake.


“Baki canja kayan ba?”


“Da wannan zan kwanta”


Ta faɗa ba tare da ta buɗe idon ba.


“To tashi ki hau gadon ki kwanta”


“Na fi jindaɗi a ƙasan”


“Ƙasa zamu kwanta kenan”


“A'a kai ka kwanta saman gadon, ni na kwanta a ƙasa”


Duk maganar da sukw bata yarda ta buɗe idonta ba. Shi kuma ya lura da hakan.


“Look Abnam karki tauye kan ki, ni ba baƙon tsanani ba ne, ma zan zo na takurawa masu gida ba, idan kina son kwantawa saman gadon kawai ki kwanta”


Ta yi saurin kwantawa a gurin.


“Ni ko gida ƙasa na ke bachi”


Ya ɗaga gira ɗaya like serious. Ya sauko da bedsheet ɗin ƙasa.


“Tashi a shimfiɗa”


“Dan Allah Abdallah ka bar ni nan”


Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Sai kawai yayi murmushi ya mayardar bedsheet ɗin ɗale saman gadon ya jefo mata matashin kai.


“Gashi nan kar na matso kuma ki ce wani abun zan miki, amman kin san shure-shire baya hana mutuwa ko?”


Sai a lokacin ta buɗe ido ta ɗauki filon ta tare kanta ta yi rufa da gyalenta. Hannu ya kai gurin kan bed ɗin ya kashe wutar ɗakin. Wani tsoro ne ya ƙara baibayeta, kwatakwata ta manta da irin rayuwar da ta yi a gidan Asim, ta fi jin sakewa da shi fiye da Abdool wata ƙila saboda yanayin hallitarsu ba ɗaya ba.


“Ka kunna wutar man...”


Bata ƙarasa rufe baki ba taji mutun a bayanta yasa duka hannayensa yajata jikinsa ya rumgume ta. Sai ya kawo bakinsa dai-dai kunnenta.


“Shiiiiiiii ba wani abun zan miki ba, kawai dai ba zai yayu nakwana da mace ɗaki ɗaya ba kuma ace mu kwana a rabe ba, kawai ina son jinki ne a jikina that's all”


A dole ya gunɗe bakinta ta rumtse ido, tana jin yana ɗan taɓa ta amman ta haƙura har bachi yayi gaba da ita. Washe gari ta rigashi tashi saboda bachin rabi da rabi tayi ko da aka kira assalati idonta huɗu ba ma biyu ba. Tana unƙurin tashi sai shi ma ya tashi saboda tana a ƙirjinsa ne duk wani numfashinta yana ji balle kuma motsinta.


Sai da ya fara shiga bathroom ɗin yayi wanka da alwala sannan ita ma ta shiga ta yi alwalah, tare suka yi sallah sannan ta koma bachi, shi kuma ya buɗe ƙur'ane dake cikin wayarsa ya soma karatu, ba shi ya tashi daga gurin da yake ba sai da aka buga masa waya aka sanar masa an aiko musu da abinci. Wannan karon Ummi bata aiko masa ba saboda ta san za'a aiko masa daga gidan Mai Martaba.


Sai da ya zuba abinci sannan ya shiga ɗakinta. Zaune ya sameta a gurin da ta yi bachin tana kallon ƙofa.


“Acici daga jin motsin ƙuloli har kin tashi”


Dariya ta yi


“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma”


“Ai ba kai aka kawo ma abincin ba ni aka aiko ma, yanzu ai kin kina da baki ko?”


Ya kai kayeta yana wani girgiza kai da kashe murya. Ya miƙa mata hannunsa


“Zo nan muje ki wanke bakin ki”


Kamar wata ƙaramar yarinya haka ta miƙa masa hannun ya tasota, da kanshi ya wanke mata bakin bayaɓ sun gama ya ɗauke ta ya kaita dinning.


“Kai a she nauyi ne da ke, na ji kamar jijiyoyina zasu katse”


Ya faɗa yana dariya. Shi yayi feeding ɗinta sannan yayi feeding kansa. Ko da aha biyu ta yi daga ita har shi duk sun shirya cikin fari yadi mai kamar shadda sky blue. Tana gaban madubi tana kwaliya ya ƙaraso kusa da ita ya ɗauki sarƙa ya saka mata sannan ya juyo da ita ya kalleta.


“Kin yu kyau Abnam”


“Faɗa min ma'anar sunan nan”


Bakinsa ya kai dai-dai nata ya haɗe ya tsotse jan bakin da ta sha sannan ya ɗauke bakinsa ya mayar gurin hancinta idonsa kamar mai jin bachi. Ita kan nata a lumshe.


“A-B Abdallah N-A-M Namra = ABNAM”


Murmushi ta yi ta buɗe ido tana jin yadda danshin yawunta ke zaga ko ina na bakinta, shi ma murmushin ya mayar mata yasa yatsunsa ya riƙa lips ɗinta yana murzawa a hankali, cikin hikima ya zura mata manuninsa cikin bakinta ya riƙa wasa da halshenta.


“Zan je na gaishe da su Mai Martaba da Ummi”


Ya faɗa yana kallonta, sannan ya zare hannun daga bakinta ya miƙe tsaye yana saka yatsan cikin bakinsa ya tsotse yawun.


“Allah ya tsare”


Ta faɗa tana tsotsa halshen nata. Sai kawai yasa mata dariya ya zuba hannayensa aljihu ya fice zuciyarsa cike da farincikin.


Bayan fitar da ƴan mintuna su Maryam suka dawo saboda yi mata sallama,ragowar kajin da suka tarar suka cinye suna zolayar Namra da ke ta aikin kuka wai zasu je su barta.


Sai da ya fara biyawa gurin Ummi ya gaisheta sannan ya wuce gurin Mai Martaba, Wannan karon har da Mai Martaba gurin jansa.


“Ango ango”


Wata kunya ce ta kamashi sai ya zauna ya kasa haɗa ido da Mai Martaba. Cikin girmamawa suka gaisa, sannan Mai Martaba ya ce


“Ɓan sani ba ko matarka bata da buƙatar barori shiyasa ban aika mata da su ba, idan ka yi shawara da ita tace maka tana buƙata sai ya faɗa min”


“Godiya muke Mai Martaba Allah ya ƙara lafiya, amman ina tunanin ba sai an kawo mana su ba, saboda ba nan zamu zauna ba, hutun da suka ba ni ma na sati biyu, dole Abuja zan koma da ita, kuma ga karatun da take a sokoto sauran wata bakwai ta ƙare diploma”


“Hakan na da kyau, amman kasa ido kan rayuwa, Babana kana da maƙiya da yawa matarka ma sai ta yi taka tsantsan, ni kaina a yanzu hankalina zai fi kwanciya idan kana abujar fiye da ace kana kusa da ƴan uwanka, saboda za a iya amfanin da su a cutar da kai ko kuma a cutar da matarka, duk da bana jin akwai wanda zai sake wani unƙurin sake aikata abunda Hajiya ta yi Unƙurin aikata maka”


“Wace Hajiya Mai Martaba?”


“Hajiya Karima, (Matar ƙanensa) itace tasa waɗanda ƴan bindigar unƙurin hallaka ka, saboda ita da mijinta suna tunanin idan bana raye babu wanda ya dace ya hau sarautar Katsina sai mijinta, ni kuma ina tutuyar kai ne zaka yi milkin garin Katsina ko da bana raye”


“Mai Martaba ina ka samu wannan labarin?”


“Abdallah kenan, ai ko babu komai na kan aa ido akan ƴaƴa balle kuma kai da mahaifiyarka bata cikin gidan nan, tun daga lokacin da aka maka wannan aika aikar tunani ya bani ba daga waje ba ne, sai dai ko daga nan cikin gida ne, saboda bana tunanin ina da wasu maƙiya bayan na cikin familynmu kuma akan sarautar mu, hakan yasa na zurfafa bincike ta ƙarƙarshin ƙasa sai gashi wanda aka aika gurin yin abun ya same nan a cikin faɗar nan ya faɗa min komai, wannan yasa ya tara su ita da mijin nata da duka family mu na gargasu a lokacin hankalinka yana gurin Amaryarka shiyasa ban taɓa labarta maka wannan ba”


Abdallah yayi murmushi yana auna irin son da Mai Martaba yake masa.


“Babana idan na kalleka na kan jidaɗi nasan ko bana raye kai mutum ne zaka iya riƙe gidan nan kuma ka riƙe ƴan'uwanka, iyakar soyayyar da zan nuna maka na tarbiyantar da kai na baka ilimi kuma na baka duka, yanzu addu'a ce kawai zan binka da ita, Allah ya maka albarka”


“Amin Mar Martaba na gode, Allah ƙara maka imani da lafiya”


“Amin”




Daga haka suka ɗauko wata fira, na familynsu da kuma sarautar Katsina, be bar gidan ba sai la'asar.




***


Bayan sun yi sallah azahar suka yi shirin tafiya aiko Namra ta ƙara tsaresu da kuka tun suna juriyar sai da ta saka Maryam ma ta yi kukan, isowar familynsu Abdool waɗanda suka zo ganin Amarya ne tasa ta tsagaita kukan har suka samu suka tafi. Mota mota suka riƙa zuwa ganinta kasancewar wasu yau zasu tafi wasu kuma gobe har na ɓangaren Ummi wasu ma nan suka yi sallah magariba ana kiran isha'i sannan suka fice.


Ko da Abdool ya dawo ya tarar bata cikin daɗin rai, shi ma kamar jira take yana taɓa fuskarta ta faɗa jikinsa ta fashe masa da kuka, daman yasan za a rina, saboda ya samu labari a faɗar mai Martaba cikin mutanen da suka kawo kara suna cewa tare zasu koma gaba ɗaya.


“Ooo an tafi an bar ƴar Mamarta”


Ya faɗa yana zama saman kujera riƙe da ita.


“Bari na kira miki mamanki”


Ya fiddo wayarsa ya kira Ummi ya miƙa mata ba ko kunya har da faɗa nata wai kuka take masa su Maryam sun tafi su barta. Ummi ta yi dariya


“Aure ai haka ya gada yi haƙuri kinji ƴata, duk abunda yayi miki ki faɗa min”


“Toh Ummi, na gode”


Abdool ya karɓe wayar.


“Mai Martaba ma haka ya faɗa mata wai idan na mata abu ta zo ta faɗa masa, ni idan ta min wa zan faɗawa”


“Ai mata basa laifi kuma su ƴan gata ne shiyasa, kai duk abunda ta yi maka sai ka yi haƙuri ka haɗiye”


Namra ta masa gwalo, shi kuma ya kama kunenta ɗaya ya mirɗe.


“Ummi sai da safe tun da ƴarki kika shigarwa”


“Ato da kai zan shigarwa? Dan baka da kunya ƙato da kai, Allah ya shirya ka”


Ta katse kiran. Shi kuma yasa ɗayan hannunsa ya riƙe kunnen nata ya ƙara mirɗewa.


“Wallahi da zafi”


Ta faɗa cikin shagwaɓa, sai ya saki kunnen yana dariya.


“Gobe ma bakinki ya sake min gwalo”


Dariya tayi ta unƙura zata tashi sai ya jata ta faɗa jikinsa. Hannunsa yasa cikin ɗigarta tana ƙoƙarin taɓa ƙirjinta da ke tada mishi hankali tun jiya.


“Ina zaki je?”


Tayi shiru bata amsa shi ba, shi kuma be fasa abunda yake ba, natsuwa tayi tana karɓar saƙon da yake aika mata, har ga Allah tana jin daɗin yadda hannunsa ke zagaye rigarta, kamin ya ɗago fuskarta ya haɗe bakinsu.
Yadda ya riƙa tsotsa mata halshe yasa ta sake jikinta gaba ɗaya, tana sauke numfashi a hankali, kamar wacce ta tuna wani abu sai ta zabura ta miƙe tsaye. Wani kallo yayi mata idonsa sun kaɗe kamar ba shi ba, jikinsa har rawa yake, yana mikewa tsaye ta matsa baya.


“Ba a taɓa min irin wannan wasan ba karki soma yanzu Abnam please”


Ya faɗa a wahale, sai ya ƙara matsawa ta matsa, baya tana murmushi.


“Ban yi sallah isha'i ba kuma wanka zanyi”


Rumtse ido yyi ya faɗa saman kujerar yana cizar baki. Da dariyar ƙeta ta wuce ɗakinta ta yi wanka sannan ta yi sallah.


Wasu kayan bachi ta fiddo masu abun arziki ta saka sannan ta ƙarasa gaban madubi ta soma shafa mai. Tana cikin shafa man ya shigo sanye da nasa kayan bachin, kamar na jiya sai da waɗannan fararene. Kallo ɗaya tayi masa a madubi ta ɗauke kai, maida ƙofar ɗakin yayi ya rufe, sai ya karaso gabanta ya durƙusa har ƙasa ya kama ƙafarta yayi mata kiss, tun daga kan ɗan yatsanta taji abu ya tsikareta har cikin gashin kanta, a take gashin jikinta ya tashi ba shiri ta rumtse ido. Hakan ya bashi damar luma babban farcen ƙafarta cikin bakinta ya tsotsa kamar mai shan sweet candy, ji tayi kamar ba zata iya bashi abunda yake buƙata a yanzu ba, kuma ba zata iya hanashi ba. Sai kawai ta miƙe tsayw da sauri duk da idonta a rufe yake, sai kawai taji ya rumgumeta yana ɗaukar numfashi. Zafin jikinsa ne ya rika ratsa nata jikin, a hankali ya ɗauketa ya kwantar saman gadon ya saka bakinsa cikin nata yana shafa fatar jikinta, tana ji tana gani ya tabata da kayan jikinta yana arba da chest ya sauke wani irin ajiyar zuciya sai ya kai hannu ya kai ya kashe wutar ɗakin, sannan zame nasa kayan bachin.






Sun makara gurin sallah asuba kasancewar basu yi bachi da wuri ba, more especially ma Namra da bachi be mata daɗi ba gaba ɗaya, da asubar ma sai da taimakonsa ta tashi azabar da taji a gurin Abdallah yafi wanda ta ji a darenta na farko da Asim, cikin ruwan zafi ya zaunar da ita ya riƙa gasa mata jiki sannan ya ciƙa mata buta ya riƙa mata tayi wankan tsarki, sannan ya naɗata cikin tawul suka fito, ba tare da shi ya ɗaura tawul ɗin ba kasancewar ɗaya ne na bathroom ɗinta, sai da ya aje ta saman gado sannan ya ɗauki rigar bachinsa ya ɗaura ya nufi ɗakinsa.


Da Hasbunallahu da Innalillahi ta unƙura ta sauka saman gadon ta buɗe wardrobe ta ɗauko doguwar riga ta koma ta zauna tana dantsar baki.
Sai ga Abdallah ya shigo ya ƙaraso kusa da ita da sauri ya riƙa rigar ya saka mata.


Bayan sun yi sallah ta koma saman gado ta kwanta, shi kuma ya buɗe ƙur'ane cikin wayarsa ya soma karatu, wannan karon be daɗe yana karatun ba, ya aje wayar ya koma bayan Namra ya kwanta ya rumgumeta. Wani irin daɗi yake ji for the first time in history ya kusanci halalinsa ciwon cikin da yake fama da shi yau ya kau, yana jin daɗi sosai Namra ta kai shi duniyar da be taɓa mafarkin zuwa ba, yaji daɗin ɗa be taɓa ji ba a rayuwarsa.


Basu farka ba sai da aka kawo musu abincin safe kamar jiya, sai dai yau kam basu karya ba sai sha biyu na rana bachi wahala Namra ta riƙa yi, tana farkawa ta fara zuba masa shagwaɓa tana narke masa a jiki, shi ko duk yabi ya susuce sai tarairaiyarta yake.






*** *** ***


Bayan an kwana biyu abubuwa sun ɗan laɓa Ummi ta shirya ta je gidan Hajiya Sadiya, tun lokacin da abun ya faru ta kasa natsuwa zuciyarta na nuna mata kamar akwai ƙamshin gaskiya a abunda Asim ya faɗa.


Ta yi sa'ar tararda ita gida, sai dai ba cikin yanayin jindaɗi da walwala ba. Sama-sama suka gaisa da Ummi tana wani noce kanta kamar mai jin kunya, Ummi na lura da ita amman sai tayi kamar ba ta kula ba ta ɗora da zancen da ya kawo ta.


“Na kasa natsuwa da maganar nan ne da yaron nan ya faɗa a faɗar Mai Martaba miye gaskiya a ciki?”


“Babu komai Zuwaira ƙarya ce yake min kinsan halin mutanen yau ka saka musu da alheri su maka sheri”


“Ɓana son ki ɓoye min komai Hajiya ni ƴar'uwarki ce, ko zaki ɓoyewa wani ba zaki ɓoye min ba, ba ni kaɗai naji wannan maganar ba amman nafi kowa damuwa, na san ko zai miki kazafi ba zai miki na wannan ba”


Jikin Hajiya Shafa ya mutu sosai tabbas wanda ke son ka ne kawai zai damu da kai, sai dai mi bata tunanin zata buɗe sirrinta a gurin da ake ganin ƙimarta.


“Gaskiya ne, amman bana son labarta miki komai daga abunda baki sani ba, rufe wannan sirrin zai fi buɗe sh alheri”


“Kina tunanin kamar zan labartawa wani abunda kika aikata ne?”


“Idan na labarta miki zaki daina ganina a mutun ne, kuma kwana kaɗan ya rage min a duniyar nan saboda sun faɗa min lokacin da zan mutu”


Hawaye sun soma zirya a kumatunta.


“Mu kaɗai muka rage, iyaye duka sun tafi idan ba mu kula da junan mu ba wa zai kula mana, zumuncin da kullawa daga kan mu zai fara sannan ƴaƴanmu su ɗauka”


“Ba zan iya labarta miki komai ba, saboda babu amfanin faɗa miki komai, nasan Allah ba zai yafe min ba”


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, shirka kika aikata Hajiya?”


“Ina ma shirka ce da zan iya tuba na gyara imani na kuma Allah ya yafe min, wannan fa? Allah baya yafe wani kan wani, na lalata da yawa na salwantar da rayuwar mutane da yawa cikin har da na ƴaƴana da miji na wallahi bata yi ba wallahi cul...”


Sai ta ƙasa ƙarasawa ta fashe da kuka. Ummu ta fashe komai duk da bata fili ta faɗa komai ba, jikin Ummi yayi sanyi sosai har ta rasa abunda zata ce mata jiki ba gwari ta tashi ta ɗauki jarka zata fice.


“Ai na faɗa miki faɗin bashi da fa'ida, zaki daina ganina a mutun ne ki riƙa ganina kamar wata dabba ko aljana”


“Ban daina ganinki a mutun ba Sadiya, kowa baya wuce kaddararsa, rayuwa tana zuwa mutun ne ta yadda Allah ya tsara masa da kuma yadda sheɗan ya kawata masa, zan kasance mai miki addu'ah da kuma rike sirrinki, sai dai ina baki shawara ki gyara tsakanin ki da Ubangijinki domin shi mai yawan gafara ne mai rahama”


Daga haka Ummi tasa kai ta fice zuciyarta cike da tausayin ƴar'uwarta. Fashewa Hajiya Sadiya tayi da kuka, tabbas ratuwa tana tafiya ne ta yadda Allah ya tsara da kuma son zuciya, da ace tayi haƙuri da bata shiga wannan rayuwar ba, saboda Allah ya kaddara zata samu abunda zata samu, sai dai ya danganta da imaninta da kuma gajin haƙurinta, abunda duk Allah ya rubuta ka same shi sai ka sameshi sai dai ya danganta da yadda mutun yayi haƙuri idan ka yi gajun haƙuri ya zo maka ta haram idan kuma ka yi haƙuri ya zo maka ta halal amman tabbas abunda Allah ya rubuta naka ne, naka ne no matter what...!
[8/7, 2:47 PM] Khadeeja Candy♥: UZAIR POV.


Be yarda an shiga kotun ba kamar yadda ita Yaamin ɗin ta so ganin ya ƙi ya bata takardar sakinta, tun da Ummu ta ga takardar tasa ya rubuta mata takardar sakin yana kuka ta aika mata, Uzair yana son Yasmin amman babu yadda ya iya tun da ta zaɓi rabuwa da shi, shi kanshi yanzu yasan babu wanda zai zauna da shi sai mahaifiyarsa, wata biyar da faruwar hakan wata lalurar ta sake samunshi, ta yoyon kashi a dubura, daman tun last year ya fara wannan abun maganin da yake sha'ane yasa abun tsaya masa, yanzu kan babu magani kuma ga zaman keke wanda ya zame mata jiki tun da kullum a nan yake zaune. A yanzu ne kowa ya ƙara tabbatar da gaskiyar abunda Namra ta faɗa.


Ranar da labarin ɗaurin auren Namra ya same shi yayi kuka har sai da idonshi suka canja kala, tabbas yasan ya cuci yarinyar sai dai ba haƙƙinta ne kaɗai ya ke binshi ba har saɓawa Allah da yayi, saboda ya tsallake iyakarsa, ya aikata laifin da Ubangiji ya hana bayinsa tsarkaka su aikata, yasan baya cikin bayin Allah na gari.
Kaito! Da wata rayuwa dai ƙara babu, yau gashi baya amfanarda kanshi da komai, ga kuma kunyar duniya ta isheshi, ƙanensa ma basa da lokacinshi, mahaifiyarshi ce kawai take kula da shi, ita kanta da taga abun yayi yawa sai ta nemo mai kula da shi ana biyanta duk ƙarshen wata, saboda ragewa kanta wahalar ita kaɗai.


Sai a yanzu ya gane ashe babu riba a cikin tsaɓawa Allah da cin amana, yayi nadanar da babu amfanin tun da yasan Abbah ba zai taɓa yafe masa ba, abunda Matarsa ta yi masa ma ishara ne idan yaronsa idan ya girma ba zai samu labari mai daɗi ba, ji yake kamar ya mutu ya huta, kunyar duniya ta ishashi a family da abokai babu wanda be ji abunda ya aikata ba, yana ji yana gani jindaɗi da kwanciyar hankali ya gagareshi lafiyarsa jikinsa ma ta tafi ta barsa, komai ya zo masa kamar mafarki, haka wani lokacin zai zauna yayi ta kuka idan ya tuna irin rayuwar jindaɗin da yayi yau ga shi ya koma wani kalar mutun da a gidansu ma uwarsa ce kawai ta damu da shi, sai a yanzu ya gane yayi kuskuren aikata abunda ya aikata sai dai lokaci ya ƙura masa babu ta yadda zai gyara komai ko da kuwa zai so haka, duk ya bi ya rame kamar ba shi ba gaba ɗaya halittarsa ta canja a Wheelchair ma idan ya zauna sai yayi kamar zai koma gefe, sai a ayanzu ya gane ashe cin amana da tsaɓawa Allah babu riba a ciki duk romon da yasha yana ganin kamar ya more ashe sakayyah na biye.


KALSOOM POV.


Tana jin kamar ta fi ko wace mace sa'ar miji a duniya, bata da mtsala ta ko'ina, mijinta na nuna mata so da kulawa ƴan'uwanshi ma haka, ga su Ezzah da suka zame mata kamar ita ce ta haifi yaran.


Wani lokacin ta kan zauna ta auna irin rayuwar da tayi a gida zuwa aurenta irin rigingimun da gwargwarmayar da tasha a lokacin da tayi kishi da Rashida amman yanzu komai ya zama tarihi, babu komai a cikin duniyarta sai farinciki jindaɗi komai ya zo kamar a mafarki, addu'ah da ta daɗe tana yi aje an amsa mata tuni jindaɗin na ne yake nesa, tabbas wani jinkiri alheri ne, kuma bayan wuya sai daɗi, rayuwa bata tabbata a guri ɗaya dole akwai canji ɗan adam baya taɓa zama a cikin wahala kullum maruƙar ka riƙe gaskiyarka kuma ka ji tsoron Allah ka yi haƙuri wallahi sai kaga canja domin dukan tsanani yana tare da sauƙi haka Allah ya faɗa.


Ta zama uwar ɗiya bayan ƴaƴanta uku da ta haifa ga ƴaran Rashida da su a yanzu sun tasa sosai. Shi kansa Hilal sai a yanzu ya fahimci irin tasirin da Kalsoom ta keda shi a zuciyarsa da kuma rayuwarsa, domin gudumawwa take bashi ta ko ina, sai a yanzu ya gane mai haƙuri mawadaci lalla yayi dacen mata, a cikin ɗari yayi nasara zarar ɗaya, komai jindaɗi suke yinsa da kwanciyar hankali ga soyayyar da suke

Please Login or Register in order to submit comment