Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

masa ya juya a fuce ya kama hanya.


“Asim!Asim!! Asim!!!”


Haka ta bishi da kira tana kuka, amman ko waigowa bai yi ba balle ya amsa mata. Zubewa ta yi a gurin tana kuka, kukan tausayawa kanta da zuciyarta, dan ita ma kanta ta san tana son Asim, zata yaudari zuciyarta ne kawai idan har ta ce zata iya rayuwa da wani namijin da ba Asim ba.
Ta kusan minti goma shabiyar a gurin tana kuka, sannan ta buɗe Motarta ta shiga. Hanyar da zata sadata da gidansu ƙawarta Amira ta ɗauka tana wani irin gudu na fitar hankali.


Cikin ƴan mintuna ta isa gidansu Amira, daga wajen gidan ta faka motar ta dan ba zata iya jira mai gadi ya buɗe mata ba, sai ta fito ta taka da ƙafa ta shiga cikin gidan still tana kuka.
Mahaifiyar Amira ta yi mamakin ganin ta haka, sai tambayarta take lafiya, ita dai bata yarda ta faɗa mata komai ba, ta wuce ɗakin Amira kasancewar gidan ba baƙonta bane.


“Ke lafiya miya same ki?”


Amira ta tambaya cike da tashin hankali tana girgiza Namra. Bata ɓoye mata komai ba, tun daga yadda suka yi da Abbah, har abunda ya faru tsakaninta da Asim a yau.
Wani dogon tsaki Amira taja ta ɗauke hannunta daga jikinta


“Ke dan Allah duk kin tayar min da hankali, ni na ɗauka ma wani abun ne”


Kallon rashin fahimta Namra ta yi mata da idanunta da suka rine saboda kuka.


“Ban gane ba, Amira ko baki fahimci abunda na faɗa miki bane?”


“Na fahimta sarai, ai da hausa kike magana, naga dai babu wani abun tada hankali a ciki, tunda kina da mafita”


Namra ta ƙara kallonta


“Wace irin mafita? Ai nima mafitar nake nema”


“Kawai ki bishi ku gudu kuje can wani guri a ɗaura muku aure, daga baya iyayenki zasu yafe min idan suka fahimci irin son da ke tsakanin ku”


“Wannan ba mafita bace Amira, ni ba zan iya wannan ba, duk son da nakewa Asim bai kai wanda nake yi ma iyayena ba, ko wanne muhallinsa daban”


Amira ta taɓe baki


“Ashe ko ba son ƙwarai kike masa ba, tun da har ba zaki iya sadaukar da kan ki a gare shi ba”


Shiru Namra ta yi kamar mai tunani, sai kawai ta share hawayenta ta ɗauki jakarta ta rataya tana faɗin


“Bari na wuce akwai inda zanje, sai mun yi waya”


“Toh, Allah ya kiyaye hanya”


Lokuta da dama haka Amira take nata yaɓen maganar duk data zo bakinta, ta kan bata shawara tsaɓanin tunaninta, sai dai babu wanda zata faɗawa damuwarta kamar ita da Anty Yasmin.
Da wani mugun kallo Amira ta bita tana harararta, can kuma ta taɓe baki.


“Wahalalliya, ashe ƙaryar so kike tun da ba zaki iya barin iyayenki ba”


Wayarta ta jawo ta soma danne-danne, kamin ta tashi ta nufi ɗakin mahaifiyarta dan labarta mata abunda ya faru.




Har Namra ta fito daga gidan nazarin kalaman Amira take, sam bata ganin dacewa akanta guje iyayenta, saboda saurayin da zai iya barinta ya ɗauki wata, taya zata iya gudu mutanen da suka shekara ashirin da biyu suna bata gudummawa, akan saurayin da haɗuwarsu bata wuce shekara uku ba, idan har ta yi hakan ta yi babban butulci wanda ta cancanci ko wane irin sakamako. Sai dai wani ɓangare na zuciyarta, yana karantar da ita akan abunda Amira ta faɗa mata shine mafita, dan idan ba haka ba mahaifinta ba zai taɓa bari ta auri Asim ba.


Har ta isa gidan Barrister Yasmin wannan tunanin take, tana hangowa kanta illa da kuma alfanun da ke tare da ita idan har ta zaɓi guduwa ta bar iyayenta.
Ta daɗe a cikin motar tana kiran wayar Asim, amman yaƙi picking at the end ma sai ya kashe wayar gaba ɗaya, cikin rashin kuzari ta buɗe motar ta fito tana kallon balcony ɗin ƙofar Yasmin, sai a lokacin ta lura da Motoci uku da aka faka a gurin.


‘Waɗannan ba Motocin Ya Uzair bane, kar dai ace baƙin har sun iso, ko da yake abuja ba nesa bace idan sun shigo jirgi’


Shine abunda take rayawa a zuciyarta tana ƙoƙarin duba agogon hannunta, 11:23am ya bata hakan yasa ta saki jiki ta nufi ƙofar, tana isa ta kai hannu ta murɗa ƙofar. Abunda ta yi arba da shi yasa ta mutuwar tsaye, zaro ido ta yi ta rufe bakinta da sauri taja baya.


Cikin sauri Uzair ya ture Mutumen da ke samansa ya tashi ya nufi inda take, har ya iso kusa da ita jikinta rawa yake, gashi be da riga daga shi sai gudun wando. Shima hankalinsa ya tashi sosai bai tsammaci a buɗe ya bar ƙofar ba, mamakin kansa yake ma yadda bai ji buɗe gate ɗin gidan ba da fakawar Motar ta.


Da hannu ta nuna shi, sai kuma ta kasa magana. Cikin zafin hannu ya kai hannu ya cafko hannunta ya jefa ta cikin parlor.
Baya-baya tayi tana neman mafita sai kawai ta shige kitchen da samawa kanta makami, tana shiga ta nufi inda wuƙa take ta kai hannu ta ɗauka. Shi kuma ya kunno kai cikin Kitchen ɗin zuciyarsa na bugawa da ƙarfi.


“Ba zan miki komai ba Namra, matukar kika rufa min asiri, wallahi kuskure ne ba a son raina bane cilas ta ni suka yi”


Nuna shi ta yi da wuƙar da ke hannunta tana girgiza kai


“Ba zan rufa maka asiri ba Ya Uzair, tun da ba rufin asirin kake so ba, tun ba yau ba na taɓa ganin wani video a wayarka, Namiji na kissing ɗin Namiji ɗan'uwansa sai kace min sabon Memori ne ka siye baka san da video ba, yanzu kuma na kama ka da ido na.


Kai wane irin Namiji ne dan Allah? Matarka ta yarda da kai ta baka amana amman kana cutar, cutar ma bata tsaya akan ka har sai ka neme ni! Kuma miye abun son ga Namiji ɗan'uwanka? Tirrr da kai Ya Uzair, na yi baƙinciki da ka kasance mijin Anty Yasmi, sam bata cancanci zama matarka ba”


Murmushi ya yi ya jawo ƙofar Kitchen ɗin ya rufe.


“Na nemeki ne saboda naga abunda nake so a jikinki, lokacin da nace na aureki ai cewa kikayi kina da wanda kike so, daman nima ban shirya zama da mata biyu ba, shiyasa na nemi yin sex da ke.


Amman yanzu bari kiji na faɗa miki, duk kika kuskura kika bari maganar nan ta fita, kika faɗawa duniya cewar ni ɗan homo ne sai na tarwatsa rayuwarki, ki rubuta ki aje”


Ya faɗa mata haka fuska a ɗauri babu alamar wasa a lamarinsa, sannan ya buɗe ƙofar kitchen ɗin


“Zo ki fice, amman ki rubuta ki aje duk kika kuskura fitar da wannan maganar sai na salwanta rayuwarki”


Daga haka ya fita ya bar mata kitchen ɗin.
Ita kam bata yarda ta fito ta nan ba, sai ta buɗe ƙofar baya ta kitchen ɗin ta fita gabanta na mugun faɗuwa, har ta shiga Motarta jikinta rawa yake, zuciyarta na raya mata karta ɓoyewa ƴar'uwarta kuma aminiyarta abunda mijinta keyi, gani take idan har tayi haka bata yi mata adalci ba.
Tana fita daga gidan ta faka gefen ti-ti ta dannawa Yasmin kira, three miss call tayi mata amman bata ɗaga ba, ta san ba zai wuce tana cikin kotu ba, sai kawai ta yanke shawarar tura mata saƙo.


Ko da ta isa gida Anty Amarya bata nan, part ɗin kuma babu kowa, ƙannenta duk suna makaranta, hakan ya bata damar shiga ɗakinta ta baja kolin hajar tunaninta.


UZAIR POV.


Lokacin da Uzair ya ga Namra ta fita sai ya gargada ƴan iskan friends ɗinsa, ya gyara gidan tas kamar komai bai faru ba. Ba ayi minti Arba'in ba, sai ga Yasmin ta dawo gidan, cikin sauri ta shigo parlor tana dube-dube.
Uzair na zaune saman kujera yana kallonta, hankalinsa kwance kamar ba komai, sam be yarda ya nuna akwai wani abun a fuskarsa ba, tashi yayi ya tare ta, tare da rumgumeta yana kissing


“Lafiya wife?”


Ta sakar masa jikinta sosai


“Wallahi miss call ɗin Namra na gani da text ɗin ta, wai na yi sauri na zo gidana, shine duk hankalina ya tashi”


Dariya yayi sosai a zuciyarsa yana jinjina ƙarfin hali irin na Namra.


“Haba dai sai kace baki san Namra ba? Zata iya disgaki fa ai ba yau ta saba ba, karki tashi hankalinki”


Juyowa tayi sukayi kissing ɗin junansu sannan ta ce


“Ta katse min aiki na, ina fatar dai tayi maka kosan kazar?”


Hancinta ya laƙata


“Namra bata ma zo nan gidan ba, friends ɗina kuma har son kama hanyar Abuja daman ɗaurin aure suka zo”


Da haka ya shammace ta ya cigaba da kissing ɗinta.


NAMRA POV.


Duk yadda ta so ta labartawa Anty Amarya abunda ke cikin ranta na game da Uzair sai ta kasa, haka ta wuni tana tunanin abunda ya faru tsakaninsu da Asim, da kuma shawarar da Amira ta bata, a ɗayan ɓangaren kuma ƙwaƙwalwarta na ɗauke da hoton abunda taga Ya Uzair yayi.
Har bayan Sallah Isha'i tana kiran wayar Asim amman ya ƙi ya ɗaga, ta tura masa massage no reply, abun duniya duk ya bi ya dame ta.


Shigowar Anty Amarya ne yasa ta tsaita natsuwarta, har tana ƙoƙarin gyara zamanta.


“Abbanki yace na faɗa miki baƙonki ba zai samu zuwa ba”


Anty Amarya ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zaunawa saman gadon kusa da ita. Namra ta ɗan kalleta kaɗan


“Miyasa?”


“Nima ban sani ba, amman na naji a waya yana cewa wai kin masa ƙarama, kuma yana jin nauyinki”


Namra ta ɗan yi murmushi ƙaɗan ta kwanta jikin Anty Amarya.


“Shima dai yasan ni ba sa'arsa bace”


Anty Amarya ta shafa kan ƴarta.


“Allah dai yayi miki zaɓin da yafi alheri, ya yaye miki damuwarki”


“Amin Mamana”




KALSOOM POV.


Around eight thirty Kalsoom ta fito ɗakinta, a lokacin Saleena har ta wuce makaranta. Ita ta haɗa musu breakfast bayan ta gama, ta zuba ma Dad da Momy nasu ta ɗauka ta nufi part ɗinsu.
Bayan ta gaishe su, ta aje musu abincin tana ƙoƙarin rasowa Momy tayi mata tuni da zuwa gidan ƙanwarta Zainab.


“Ban manta ba Momy, yanzu idan na shirya can zan fara zuwa na aje kayana sannan na wuce aiki”


“Hakan yayi Allah ya kawo miki naki mijin”


Sai da ta amsa sannan ta tashi ta fice. Kala biyar ta ɗauka a maimakon uku, dan tasan sai ta fi kwana uku a can, cikin ƙaramin akwati ta saka su, sannan ta shirya kanta ta fice.
Kamar yadda ta tsara sai da ta fara biyawa gidan ta aje kayanta sannan ta wuce gurin aiki. Biyu da rabi ta tashi daga aikin direct gidansu ƙawarta Salma ta wuce.


Ta taki sa'ah, tana shiga mijinta na fita. Sai da tayi Sallah Salma ta ɗebo mata abinci ta ƙoshi sannan ta ɗauko mata zance.


“Kalsoom wani gari ne nake son muje tare da Ruƙayyah ita zata kai mu, ance malamin yana aiki sosai dan mutane da dama suna dacewa”


Kalsoom ta sauke ajiyar zuciya


“Ni wallahi har na gaji da irin wannan shige-shigen, kullum ana abu kamar ba'ayi, wani gurin ace aljanu ne wani su kuma su ce sihiri ne, na rasa gane kan matsalar nan, Wani lokacin har ji nake kamar na kashe kai na”


Salma ta dafata


“Subhanallahi, haba Kalsoom ki daina wannan maganar mana, Allah ya baki aikin da zaki iya taimakon kanki, Allah ya rufa miki asiri aure ne kawai Allah bai kawo miki ba, shine kuma kike ƙoƙarin butulce masa, kina wannan maganar sai kace ba musulma ba?”


Kalsoom ta lumshe ido ta buɗe ta kalli Salma cike da damuwa ta ce


“Salma duk abunda Allah ya ban da wanda zai ban bai kai kamar aure ba, aure shine cikar mutuncin ko wace ƴa mace, ni fa ba dotse bace Salma ina da sha'awa ina tsoron abunda zai kai ni ga halaka”


Salma ta riƙata tana ƙoƙarin kwantar mata da hankali.


“Roƙon Allah baya faɗuwa ƙasa Kalsoom, komai zai zo ya wuce kamar ba'ayi ba, kuma ba asan inda rabo take ba wata ƙila mu dace”


“Ni dai ba zan sake zuwa ko ina ba, na haƙura ballantana kinsan Ruƙayya ba a sirri da ita, kuma ko munje ba wani dacewa za muyi ba, tun da babu wanda zai iya matso maka da nesa kusa, babu wanda zai iya goge abunda Allah ya rubuta maka, sai dai kawai su ci kuɗinka, na fawwalawa Allah komai daman da shi na dogara”


Duk yadda Salma ta so ta lallaɓa Kalsoom su je, sai taƙi dan ita yanzu ta riga ta sadaƙar. Sai da Yamma Kalsoom ta bar gidan Salma.






__________________________________


How about dis journey?


#threefamily
# Vote
#Comment
#TeamNamra
#TeamKalsoom
#TeamHilal
#Candy
#Blog


Always check my website for more.


BEST REGARDS💖
Khadeeja Candy 🌺


www.khadeejacandy.com.ng
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*

Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated




*PAGE - 3*


DOCTOR HILAL POV.


Bayan ya gama abunda yake ya shiga ya yi wanka, sannan ya fito falo ya yayi breakfast, sai kuma ya sake dawowa ya tashi Rafiq ya shiya sannan ya fice.


Kamar yadda ya saba gidan Hajiya ya nufa dan kai Rafiq ɗin, kasancewar Hajiya na da ƴan aiki da yawa masu kula da shi, wani lokacin ya kan aje shi a falo yace a shiga dashi gudun kwankwamin Hajiya, ko kuma ya aje mata shi ya yayi saurin barin gidan.
Sai dai yau bai yi sa'ah dan yana shiga ya ci karo da ita cikin falon tana karyawa, sun-sun-sun yayi ya gaisheta.


“Hajiya Barka da tashi”


“Barka dai mijin Hajiya, har ta tafi aikin ko? Bari dai kaji na faɗa maka na kusa barin rainon ɗan ku”


Maganar tayi masa zafi, sai dai babu yadda ya iya tun da mahaifiyarsa ce, kuma idan sabo ya saba da irin waɗannan kalaman daga bakin Hajiya da Alhaji, Murmushi yayi ya shafa kan sa.


“Hajiya haƙuri dai za'ayi, kisan ƴan rainon nan ba tsoron Allah suke ba”


“Kai ai kana tsoron Allah, tun da har kakr barin Matarka tana shiga cikin maza tana gogaiya, ace mace idan ta fita takwas na safe ba zata dawo ba sai cikin dare? Bata da lokacin mijinta balle na ƴaƴanta”


“Hajiya kin san aikin banki ne, kuma ita ce Manager ta banki dole ne ta riƙa bada lokacin can”


“Toh ta bar aiki mana dole ne? Amman ace mace ta bar Yaro ƙarami mai shan nono dan kawai ta je aiki”


Murmushi kawai yayi ya tashi yana shafa kai yana faɗin


“Bari na wuce”


Har ya kai ƙofa bai ji tace masa komai ba, sai ya juyo yana murmushi yace


“Hajiya ni fa bana son fushin nan da kike da ni”


Wani kallo ta watsa masa


“Yaushe na ce ina fushi da kai?”


“Toh ai ban ji kince Allah ya tsare ba”


“Ko ban ce ba ai Allah tsare ka zai yi”


Wata irin dariya yayi, ya dawo yayi mata side hug


“Allah ya bar mana ke Hajiya, i love you”


Dariya tayi tana faɗin


“Jeka ka aikinka kamin Alhaji ya fito, kasan nashi faɗan babba ne”


Ficewa yayi yana dariya, zuciyarsa cike da shauƙin son mahaifiyarsa.
Uku da ƴan mintuna ya tashi aiki, sai da ya biya ya ɗauko Yaransa daga makaranta sannan ya dawo gida, sai da suka yi sallah sannan ya zuba musu abinci suka ci, wani lokacin lokacin ta kan tashi da wuri ta dafa musu abinci, wani lokacin kuma sai dai yayi musu takeaway. Bayan sun gama ci suka shirya suka tafi Islamiya.


Haka Doctor Hilal yake fama da irin wannan kaɗaicin kamar marar mata, gashi shi ba mutun ba ne mai son yawa fita, indai ba gurin aiki ba kullum zaka tararda shi a gida.
Matarsa kuma ota da gidan sai dare, babu yadda ya iya tunda babanta ya tsaya kai da fata akan lallai sai tayi aikin banki kasancewarta babbar ƴarsa, tana da ƙanne maza amman ya tsaya akanta dan kawai yaga ya kashe mata aure, tun asali ba Doctor Hilal ya so ta aura ba, shiyasa baya ƙaunar surikin nasa ko kaɗan, shi kuma baya jin zai iya rabuwa da ita saboda yana son matarsa ita kuma tana sonsa.


Ulfah da Ezzah na dawowa daga makarantar islamiya, suka ɗauko Homework ɗin su Doctor Hilal ya yi musu.
Gimbiyar tasa kan bata dawo gida ba sai bayan Isha'i. Da sallama ta shigo amman ko inda take bai kalla ba balle har ya amsa mata sallamar, sai ta kwanto jikinta tana masa shagwaɓa


“Yanzu zan yi sallah ka kasa amsa min haba Dear”


“Yaran ki har sun gaji sun yi bachi, yau kwatakwata Rafiq bai sha nono ba, idan ni ina iya haƙuri na su kuma ba? Rashin ba su lokacin ki da kike shi zai sa ki kasa karantar wane hali ƴaranki suke ciki”


Bata yi mamakin kalamansa ba, daman yakan yi fushi da ita wani lokacin, kuma ta lura da hakan tun daga lokacin da samu promotion. Yana tashi tayi saurin sakin handbag ɗinta ta riƙo shi, sai ya ture hannunta


“Zaki iya fushi da ni?”


“A'a ni Wallahi ba zan iya”


Ta faɗa a marairaice


“Toh ki koya daga yanzu, ta yadda za mu iya yin sati ba muyi magana da junan mu ba”


Rumgume shi tayi tana kukan shagwaɓa.




KALSOOM POV.


Ko da ta isa, Zainab na kwance falo tana bachi. Mayafinta ta aje ta ɗauki hijabi ta saka, ta bi gidan gyara tass, sannan ta ɗora musu girki.
Haka ta kwana huɗu tana musu aiki, cikin rashin sakewa dan gani take kamar Zainab ɗin da Mijinta zasu raina ta, ta kan abuɓda bai dace ba amman bata magana, sai dai kwallafawa zuciyarta idan har ta je gidan sai ta faɗawa Mony irin zaman auren da Zainab keyi. A kwananta na huɗun ne Momy tayi ma Mijin Zainab magana ya kawo ƙanwarsa dan ta taya Zainab zama, Ranar da zata dawo ranar ce Zainab ta fara awo cikin, dan haka dole ita ce ta rakata bata je aiki ba a ranar, asibitin ta je aka yi ma Zainab komai, sannan suka dawo gida tare, da zimmar ita Zainab ɗin zata koma gidanta da yamma.
Bayan sun gama cin abinci rana ne, Kalsoom ta ɗauko labarin dan Momy ta ja mata kunne.


“Gaskiya Momy ayi ma Zainab faɗa, ya kamata ace ta canja rayuwa ta riƙa lurar da mijinta abunda ya dace da wanda bai dace ba, kinsan mijinki fa kece makarantarsa ta farko, gareki zai fara ɗaukar darasi”


Momy tace


“Mi akayi?”


“Sam sam sam mijinta baya son alheri kuma baya son yan'uwansa suna zuwa gidan, sannan idan za ayi girki sai dai komai yaje ya siyo ƙire-ƙire kamar ba mai kuɗi ba, idan fa kika saba masa da wannan rayuwar ita zai riƙa miki ko can gaba”


Zainab ɗin ta haɗe rai sosai irin bata ji daɗin maganar ba.


“Nifa gaskiya bana son haka, daga zuwa jinya sai kuma kizo kina faɗar sirrin gida na”


“Ba ina faɗar sirrin gidanki bane, gaskiya nake faɗa miki”


“Toh ya kike son nayi masa? Ai halinsa ne idan yaga dama zai canja, Anty Kalsoom kefa ba auren nan kikayi ba balle kice kinsan yadda abun yake, ki bari har kiyi auren sannan ki faɗa min abunda da zan yi da wanda ba zan yi ba”


Saleena tayi farat tace


“Haba Anty Zainab daga an faɗa miki gaskiya”

Zainab ɗin ta yatsene fuska.


“Wane irin gaskiya, so take na masa bala'i ne ya sake ni nazo na zauna tare da ku”


Momy ta kalli Kalsoom tace


“Ki daina irin haka ba kyau, koma minene ki kyale ta can ita ta sani, ba kyau kana faɗin sirrin ɗan'uwanka, ita fa rayuwar aure sai da haƙuri kuma ke baki yi ba balle ki gane haka, ku daina wannan maganar bana so”


Duk maganar nan da Momy take kan Kalsoom na ƙasa saboda idonta daya cika da ƙwalla, daga bisani ta tashi ta nufi ɗakinta tana hawaye. Saleena ma ta tashi ta bar musu gurin tana harar Anty Zainab.




NAMRA POV.


Ranar Assabar aka yi walimar kamar yadda aka tsara, Namra na cikin ɗalibai talatin da uku da suka haddace wani ɓangare na Alƙur'ane, da ban aka ware su aka karramasu, aka kira manyan mutane suka yi musu kyauta.
Maryam na cikin Ɗaliban da suka sauka bana, bayan walimar makaranta sai da Anty Amarya ta shirya nata walimar a gidan dan karrama ƴarta.
Ƴan'uwa da abokan arziki da dama sun samu halarta, cikin har da Anty Yasmin da Ya Uzair. Anci ansha nama kam kamar mayankansa, ga uban takeaway da Anty Amarya ta
shurya gwanin ban sha'awa.
Ana sallah la'asar Ya Uzair ya tashi zai wuce dan Yasmin tace ita kam sai dare. Anty Amarya ta ɗauko masa takeaway, ƙin karɓa yayi sai yace a bawa Namra ta kai masa. Ba dan ta so ba ta karɓa ta nufi gurin Motarta fuskarta babu annuri. Shi ko yana cikin motar ya hakince yana kallonta.


“Ba nace karki faɗa Yasmin ba? Shine har da buga mata waya ko?”


Ya faɗa bayan ya kai hannu ya karɓa.


“An faɗa mata ba, amman zan faɗa mata very soon dan ba zan bar ta ta cutu da kai ba, ba zai yiyu ka laƙa mata cutar HIV ba ina zaune ina kallo”


“Wai miyasa idonki ya buɗe haka? Alaƙar dake tsakanin ki da Yasmin ita ce tsakani ɓa da ke, kuma Yasmin matata ce babu ruwanki da lamarin mu”


“Idona ya buɗe ne tun daga lokacin dana fahimci kai fasiƙi ne, kuma wallahi sai na tona maka asiri, har nema da kayi sai na faɗa”


Wani dogon tsaki taja, ta juya ta nufi hanyar falo.
Da wani irin kallo ya bita yana jin kamar ya kamo ta ya shaƙure, ƙwafa yayi ya rufe motarsa.


Sai bayan sallah isha'i kowa ya watse, a lokacin ne Maryam da Namra suka samu damar duba kyaututukan da suka samu, Ba wanda suka fi murna kamar na Abbah da yayi musu kyautar Zinari, ihu suka riƙa yi kamar zasu tashi gidan dan murna, ba ma kamar Marya data daɗe tana roƙon Abbah ya sai mata zinari.
A tare suka nufi part ɗinsa dan yi masa godiya, sai suka tararda shi zaune tare da Hajiya barau fuskokinsu shimfiɗe da murmushi.
Guri suka samu suka zauna suna masa godiya, sai ya amsa da far'ah kamar ba shine yake fushi da Namra ba, ita kanta abun ya bata mamaki sai dai kuma ta jidaɗin hakan.
Daf da zasu tashi ne Abbah ya kira sunan Namra


“Khadija”


“Na'am”


Da faɗuwar gaba ta amsa, ta dawo ta zauna tana jiran ta ji abunda zai ce. Sai da yayi gyaran murya sannan ya ce


“Kisan yadda nake da Uzair ko?”


“Na sani Abbah”


“Toh ya aiko Hajiya gata nan zaune ne yace yana son ƙara aure kuma ke yake so ya aura idan na amince masa”


Dakan shida-shida gabanta yayi saɓanin uku-uku dana kowa ke yi, da sauri ta kalli Abbah sai kuma ta sadda kanta ƙasa kamar wanda bata gane abunda suke faɗa ba.
Can ƙasa-ƙasa ta tsinkayo muryar Hajiya tana cewa


“Uzair kam ko wani gurin yaje neman aure ai mu zamu shige masa gaba, balle yace yana son ƴar mu”


Abbah yayi murmushin jindaɗi yace


“Sosai kan, wallahi yaron nan yana da tarbiya, ga hankali”


“Kuma ina fatar Khadija ba zaki bamu kunya ba, zamu yi matuƙar farinciki idan har kika amince da wannan auren”


Cewar Hajiya Barau. Abbah ya kalli Namra fuskarsa babu alamun wasa yace


“Zan baki kwana uku kije kiyi shawara, but lemme remind and warning you for the last time, kar damar dana baki na shawar ki zo ki ce min ba ki amince da Uzair ba”


Bata iya cewa komai ba har na tsawon lokaci, sai kawai ta tashi tayi baya-baya ta ƙara baya baya tana dafa kai kamar wanda zata faɗi, har sai da Maryam ta riƙa ta suka fita.






____________________________________


Yauwan Comments din ku yawan typing dina, comments din ku gwarin guiwa ne a gare ni.




#DOCTOR HILAL TEAM
#NAMRA TEAM
#KALSOOM TEAM
#UZAIR TEAM

#Comment
#Share
#Vote
#Blog
#Threefamily




BEST REGARDS 💖
Khadeeja Candy 🌺
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa04.html




🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*

Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated




*PAGE - 4*


NAMRA POV.


Da kuka Namra ta shiga part ɗin Anty Amarya, sai ta zube

Please Login or Register in order to submit comment