Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Namra ya ce.


“Allah shi taimakeki ɗaga baki ki yi magana”


Namra ta ɗago hawaye na bin idonta.


“Idan har yasan ina ɗauke da cikinsa miyasa be bini ba har aka shekara be binciki inda ɗansa yake ba? Taya zan haihu ba a neme shi ba bayan kuma cikinsa ne? Tabbas Asim ya sake ni sanadiyar cikin da naƙe ɗauke da shi saboda yace na zubar na ƙi sai ya sake ni yana faɗa min shi be tashi haihuwa yanzu ba, a sanadin hakan na bar garin Katsina na koma kaduna da zama duk da yake bana da kowa a can, amman sai Allah ya haɗa ni da mutanen ƙwarai wato iyayen Lamido agidan cikina ya ɓari, kuma Lamido gashi nan zaune zai iya bada sheda”


Lamido yayi shiru har sai da idon kowa ya dawo kansa.


“Gaskiya ne wannan, a gidanmu cikinta ya zube, kuma mahaifiyarta ita ce tayi mata komai, na rantse da Allah cikin Namra ya ɓare a gidan mu, na fi tsoron Allah da kowa”


Namra ta lumshe ido tana jin wani rin sanyi a ranta. Ummi ta ce.


“Mai Martaba wannan ƙanwata ce Hajiya Sadiya kuma ka santa, itace wacce wannan yaron yayi aiki a gurinta kuma ita ma tace tasam lokacin da ya saki Namra”


Hajiya Sadiya ta kar da ido tana kallon Asim shi ma yana kallonta kallo-kallo akuya kallon kura.


“Tabbas ya sake ta saboda ya faɗa min a lokacin, har ma na nemi ya dawo da ita amman yaƙi”


“Ke macuciya karki soma samin bakinki a nan, Mai Martaba wacan Matar da ka gani ba musulmar ƙwarai bace, a cikin ƙungiyar asiri take kuma tace Maida Namra ne sabosa tana son ta bada jininta”


Subhanallah kowa ke ta faɗi ana masa kallon marar hankali. Ita kuma ta soma haukace masa.


“Saboda na faɗi gaskiya sheri zaka min? Amman Asim baka da mutunci duk hallacin da na maka?”


“Hallacin me kika min? Kika haɗani da ƴan luwani ko kuma jinin mahaifiyarta da kika shanye, Mai Martaba wannan matar da ka gani itace ta bani apple tace na bawa Namra sai gashi mahaifiyata ta ci ta mutu, kuma ta sake bani wani ni kuma na bawa ƴarta Nabila ta mutu, kuma Wallahi ba ƙarya na ke mata ba, sanadin hakan ta rasa lafiyar jikinta, kuma tiyatar da aka mata saboda maɗigon da take aikatawa ne tana shan Sperm sai ya zame mata kamar ƙanƙara sai da aka mata aiki aka cire shi, wallahi ƴar ƙungiyar Asirice duk ta cinye ƴaƴanta, dan haka ni ban yarda da ita ba”


Mai Martaba ya ɗaga masa hannu.


“Ba shi ya tara mu a nan ba, ko minene acan yake tsakaninku”


Kowa a falon ya cika da mamaki, wasu na masa kallon marar hankali, Hajiya Sadiya kam kuka kawai take tana cewa sai ta yi ƙararsa, Ummi da Mairo kuma mamaki suke, saboda akwai ƙamshin gaskiya a maganarsa. Wata muguwar harara Abdool yake watsawa Asim kamar ya tashi ya shaƙe shi.


Malamin faɗa ya gyara zama yana kallon Asim ya ce.


“Kasan idan aka samu irin wannan matsalar ana zartarda hukumcin rantsuwa ne, saboda haka zaka rantse da alƙur'ane akan kai baka saki matarka ba, saboda kai ne kake jayayya”


Ba shiri Asim ya saki baki yana kallon Malamin.
[8/3, 9:06 PM] Khadeeja Candy♥: *95*


Kallon Malamin yake kamar wanda be fahincin abunda yake faɗa ba, taya zai rantse bayan yasan rantsuwa zata iya kama shi, musamman idan da ƙur'ane ne dama ace ba da alƙur'ane ba da zai iya rantsewa da wallahi ko billahilazin saboda yana tunanin kamar su ba zasu ci shi ba.


“Ni ba zan rantse ba sai dai Namra ta rantse...”


Duk kallonsa suka yi suna mamakin kalaminsa, Abdool ya katsa masa tsawa cikin wani irin zafin rai.


“Karka rainawa mutane hankali a nan gurin, Mai Martaba zai ce ka yi abu kace sai dai wani yayi, wani irin mahaukacin mutun ne kai, idan har kana da gaskiya miya hana ka rantse, idan baka rantse a nan ba zaka rantse a kotu saboda hukuncin da aka maka a nan shi za a maka a can”


Waziri ya ɗaga masa hannu.


“Allah ya huku zuciyarka Yarima Allah ya baka haƙuri”


Ba jikin Asim ba har anta cikinsa rawa take saboda tsawar da Abdool yayi masa ga fuskarsa babu annuri. Sai a yanzu ya gano kuskuren da yayi na saka kansa cikin wannan matsalar, idan har ya ƙaryata kansa yasan dole ayi masa hukunci saboda yayi wasa da hankalin Sarki ne da kuma ɗan sarki har ma da jama'ar faɗa gaba ɗaya, sannan za a tukume shi da laifin tada husuma a gurin walimar babban mutun kamar Abdallah, bayan kuma kuma Namra zata nesance shi har a bada.
Idan kuma ya rantse yasan Allah ba zai barshi ba, sai dai yasan Allah gafurun rahimun ne zai iya yafe masa idan har yayi rantsuwar idan ya koma gida sai ya tuba, shine abunda yake ta saƙawa a zuciyarsa.


“Kai ɗan takalawa, buɗe ka yi magana ko kuma faɗa ta hukunta ka yanzu”


Cewar ɗaya daga cikin manyan faɗar a tsawace yana kallon Asim.


“Ni ba zan rantse ba, sai dai ita ta rantse saboda ita tayi jayayyar cewa na sake ta, bayan kuma ban sake ba, har taje ta yi wani aure, ni dai a iya yadda nake jin labarin faɗar nan ance min Mai Martaba mutun me mai adalci da kamanta gaskiya, shiyasa nayi iƙirarin gaskiyata saboda nasan za a ƙwatar min haƙƙina, da ace wani sarkin nin tsaɓanin wannan babu abunda zai ya fito nayi wannan maganar sai dai na barta da Allah”


Ya faɗa yana ƙoƙarin kwashe ƙafafun Mai Martaba, saboda yasa Namra ta rantse ba shi ba. Abdool ya buɗe baki yayi magana Mai martaba ya ɗaga masa hannu.


“Wannan maganar ta tsaya a haka, idan har muka cilasta wannan yaron yin abunda be tashi ba to mun shiga haƙƙinsa, dan wannan faɗa mai adalci zata bashi damar shigar da ƙara kotu domin tantance wanda yake da gaskiya tsakaninsu”


Abbah ya ɗaga hannu, sai waziri ya ce


“An baka dama farin mahaifi uba ga Gimbiya Namra”


Abbah ya kalli Namra dake kusa da Ummi zaune ya ce.


“Mamana tashi ki yi alwala ki rantse”


Babu wanda be yi mamaki furucin Abbah ga Namra ba, sai dai hakan ya karantar da kowa cewar gaskiya ce Abbah yake son ya buɗe. Namra kamar daman jiran Umarni kawai take sai ta miƙe tsaye ta nufi hanyar fita duk da bata san hanyar da zata sadata da banɗaki ba ko kuma wani gurin makamancin wannan. Hanyar da Ummi ta biyo da ita ta bi tana tafiya har ta fito part ɗin ba, sai barorin dake tsaye habarar gidan suna shanya tufafi suka rugo da gudu suka zube ƙasanta suna kwasar gaisuwa.


“Allah ya taimaki gimbiya ko da wani abun da kike buƙata ne”


Ɗaya ɗaga cikinsu ta faɗa.


“Banɗaki za a kai ni alwala zanyi”


Ta faɗa tana share hawayen da bata san sun zubo mata ba sai a wannan lokacin.


“Yana ta nan Gimbiya”


Sai suka shiga baga tana biye har suka shiga part Hajiya Shafa, a nan wasu Barorin ne suka zube suna ɗubar gaisuwa, Namra zata buɗe baki ta yi magana sai wata daga cikin barorin ta rigata.


“Allah ya taimaki Gimbiya Farida, Gimbiya Namra zata shiga banɗaki ne”


Gimbiya Farida ta miƙe tana aje wayar dake hannunta ta riƙa Namra.


“Muje ta nan”


Tare suka shiga wani ƙaton ɗaki Mai cike da kayan more rayuwa sannan ta kaita bakin ƙofar Bathroom ɗin ta buɗe mata.


“Bilmillah Amaryar mu”


Ta faɗa fuskarta da murmushi Namra tayi bismillah ta shiga, sai da ta fara tsarki sannan ta yi alwala ta fito, a bakin gadon ta samu Farida zaune tana kallon ƙofar ɗakin kamar mai nazari.
Zuwa tayi ta riƙa Namra suka fita tare, ita ta rakata har part ɗin Mai Martaba sannan ta juya ta koma, sai waiwayen Namra take.


Hasbunallahu wani'imal wakil Namra ta karanta sannan ta saka ƙafarta ta shiga falon.
Duk kallon sai ya koma kanta, ita kuma dubanta yana gurin Malamin faɗa dakw riƙe da ƙur'anen fuskarsa da ruwa da alama shi ma alwalar yayi, ƙarasawa tayi ta karɓi alƙur'ane ta riƙe tana kallon Asim ido cikin ido, kamin ta kawarda fuskarta ta kalli Malamin dake karanto mata yadda zata faɗa. Ƙur'ane ta ɗaga sama ta soma ƙaranto rantsuwar kamar yadda Malamin ya faɗa mata, sai da ta rantse sau uku sannan ana ƙarshen tace.


“Ya Allah ka nuna mai gaskiya tsakanin ni da shi”


“Allahu akbar Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Shine abunda kowa ya faɗa yana girgiza kai, Asim kan idonsa tsaya dake laƙe suka ƙara fitowa gumi ya soma keto masa ta ko ina.


“Amman Namra baki tsoron Allah da gaske baki so? Yanzu sai da kika rantse? Ni ban sake ki Amman tun da kika rantse amana zata kama ki”


Abunda Asim ya faɗa kenan muryarsa na rawa kamar wanda ya ruɗe. Sai Yayan Mahaifinsa ya soma masa faɗa tana Allah wadan da halinsa. Sai kawai ya soma rantse-rantse.


“Wallahi Baba ban sake ta, idan kuma har na sake ta kada Allah ya tayar da ni a nan gurin lafiya”


Kowa sai mamaki ya kamshi tsakanin ita da shi waye mai gaskiya, ita tayi rantsuwa da Alƙur'ane akan hakan shine gaskiyarta, shi kuma yace idan ƙaryar yake kada Allah ya tayarda shi lafiya, sai dai kowa yasan dole akwai wani abu ya faru da ɗayansu wanda baya kan gaskiya.


Tun da Namra ta soma rantsuwar Abdool ya rumtse idonsa yana saurarenta muryarta, zuciyarsa kuma cike da tsanar Asim. Maganar da Malam ya fara ne yasa shi buɗe ido.


“Tun da har Namra ta rantse akan ka saketa, ya tabbata aurenta da Yarima Abdallah yana nan, idan kuma har akan ƙarya ta rantse to Allah zai nuna mata isha dan Allah ba abun wasa ba ne, daman ana samun irin wannan matsalar idan har miji yayi jayayyar shi akan sashi rantsuwa ne, idan kuma mata tayi musun haka akan sata ra rantse ne, duk wanda yake akan gaskiya Allah ya sani kuma zai masa hukunci. Saboda haka akwai aure tsakanin Yarima Abdallah da kuma Gimbiya Namra, idan kuma har yana da ja akan hakan zai iya zuwa kotu saboda tabbatar da gaskiyarsa”


Allahu akbar suka faɗa. Asim kuma ya girgiza kai yana kallon Namra hawaye na bin idonsa ya ce.


“Da gaske ba zaki dawo gareni ba kenan! Ko da ke kika rantse, shikenan na rasa ki har a bada”


Cikin wani irin zafi rai Abdallah ya miƙe tsaye sai Mai Martaba ya ɗaga masa hannu alamar kar yace komai ko ya aiwatar da wani abu.
Mai Martaba yayi gyaran murya yana kallon Asim.


“Yaron ka gamsu da wannan hukuncin da akan yanke?”


Ya gyaɗa kai hawaye na masa zuba.


“Na gamsu ranka ya daɗe, tabbas na yi kuskure”


Ya maida dubansa gurin Namra da itama hawayen ta ke.


“Ina son ki faɗa min gaskiya tsakanin ki da Allah, zubar da cikin nan kika yi ko kuma ɓarewa yayi?”


“Babu dalilin da zai sa na zubar da ciki Asim, da ace zan zubar da na yarda na zaɓi zama da kai na zubar da cikin kamar yadda ka buƙata, cikin ya zube ne ta dalilin matsalar da nake da ita a mahaifata na rashin tsayawar ciki”


Murmushi yayi tana tuna lokacin da ya cilasta mata zaɓen cikin ko kuma aurenta, lokacin da yake iƙirarin be shirya haihuwa ba, yanzu kuma yana kan nema Allah be bashi ba, a tunaninsa idan har Namra ta rantse to za'ace ta koma ɗakinta ne, yana tunanin kamar yayi mata wayo yadda rantsuwar ba zata kama shi ba.

“Na gode Mai Martaba da ka saurareni Allah ƙara maka lafiya”


Ya faɗa kamar ba shi ba, gaba ɗaya jikinsa yayi la'asar ya saduda da lamarin dan yasan ya rasa Namra har a bada, bayan kuma yanzu ne yake jin mashin son ta na sukar zuciyarsa, yasan nan Mai Martaba yayi masa da sauƙi ne idan aka je kotu shi za a saka ya rantse, duk da yasan Abdool ba zai ƙyale shi ba.


“Baba ku tashi muje”


Ya faɗa yana fashewa da kuka. Sai duk suka miƙe tsaye jikinsu na rawa suka yi ma Mai Martaba sallama suka bi bayan Asim da ya rigasu fara tafiya. Kamar jira ake ya kai bakin ƙofar fita falon sai gashi yayi waɓi mugun faɗuwa kamar wanda aka kwashewa ƙafafu, Subhannallahi ƴan uwansa suka riƙa faɗa suka ƙarasa da sauri suka mashi suka tayar tsaye, amman sai ya kasa tsaye ƙafafunsa suka murɗe kamar an shanyesu, a nan kowa ya ƙara girmama Allah a take ishara ta bayyana iƙirarin da yayi na cewar idan ƙarya yake kada Allah ya fitar da shi lafiya ya kama shi, da ace ma shine yayi rantsuwa kamar yadda Namra ta yi da take zai faɗi ya mutu saboda bashi da gaskiya, da kama-kama suka fitar da shi.


Falon yayi tsit kamar ba kowa sai lamarin Allah suke jinjunawa, bayan kamar mintuna goma Mai Martaba ya ɗaga kai ya kalli kowa da ke cikin falon ya ce.


“Allah kenan ba a masa wasa, wani lokacin ɗan'adam muna da rauni da gazawa, da kuma isgili da gajin haƙuri, bayan ba mu wuce Allah yace mana ku mutu mu faɗi mu mutu ba, ko da beyi wannan isgilin ba dole ne yaga ba dai-dai ba saboda ƙoƙarinsa na raba auren sunna da kuma ƙoƙarinsa na saka auren cikin rikici.


Nasan hakan zai faru, dole ne a cikinsu akwai mai gaskiya, walau ita ko kuma shi yana ɗaya daga cikin dalilin da yasa na hana Abdallah yi masa komai saboda za ayi duban kamar shi Abdallah baya da gaskiya ne ko kuma an zalumce amman yanzu shi kansa ya san tsakaninsa da Allah ne ba da mu ba, ƙara Allah yayi masa sakamako da ace nan aka cutar da shi, nasan zuciyarka ta kawo Abdallah zaka iya masa komai ido a rufe, sai dai ko da yaushe ina yawan faɗa muku da ku cuci mutum ƙara ka bari shi ya cuce ka, kar ka yarda ka ɗauki haƙƙin wani ko kuma ace haƙƙin wani yana kan ka, Ubangiji yana yafiya, amman baya yafe laifin wani akan wani, kuma duk lokacin da kaci amana ko haƙƙin wani ya hau kanka zaiyi ta cinka ne a dukiyarka ko lafiyarka sannan kuma idan kunje lafiya Allah ya karɓa masa haƙƙinsa.


Ko wace rayuwa tana zuwa da jarabawa, wani lokacin aka gwada mutun dan a auna imaninsa, kuma aga iya tawakkalinsa da haƙurinsa, abunda duk haƙuri be baka ba to rashinsa ba zai baka shi ba, da ace ba ayi haƙuri ba da yanzu ba kawo nan ba, kuma daga ƙarshe ba za a ga abunda ake so ba. Ina addu'ah wannan aure Allah yasa masa albarka kuma ya kawarda duk wata fitina da zata zo nan gaba, Allah ya muku albarka, kuma yau Namra zaki kwana ɗakinki da yardar Allah”


Nasihar Mai Martaba ta ratsa zuciya da jikin duk wanda ke cikin falon, tabbas mai martaba yayi musu nasiha mai haɗe da wa'azi a lokaci ɗaya.


Hajiya Sadiya ce ta riga tashi ta fice daga falon, sannna Ummi ta tashi tare da Namra suka yi ma Mai Martaba sallama, sannan suka fito, jingine da mota suka samu Hajiya Sadiya tana hawaye, har sun buɗe motar sun shiga sai Ummi tace a ɗan jira kamar tasan Mai Martaba zai aiko kiran Namra, sai ga Waziri da kansa ya zo ya faɗa ma Ummi cewar Mai Martaba yana kiran Namra, sai Ummi tace ta buɗe mata motar ta fito ta bi bayan waziri. Falon da suka fito suka koma sai dai wannan karon babu kowa sai Anty Amarya da Abbah, da alama Mai Martaba ya basu dama su tattauna ne, waziri ma yana kawowa bakin ƙofa ya kama gabansa.


Ƙarasa Namra tayi cikin kuka ta faɗa jikin Anty Amarya da ke murmushi ta rumgume ta.


“Mamana kenan kin ga rayuwa, wannan duka sharar fage ne alamu ne na rayuwar jindaɗi da farinciki tana nan tafe, Allah ya miki albarka”


Bayan abunda Abbah ya faɗa sai Anty ta ɗora da nata nasihar akan rayuwa da kuma zaman aure kamar yadda tayi mata a can gida. Abbah ma sai da ya kara mata da wani abu, sannan suka mata sallama saboda yau zasu koma, aiko nan Namra tasa musu kuka kamar zasu yi rabuwar har abada har Anty sai da tayi kuka, sai da Ummi ta shigo.ta fita da ita sannan ta tsagaita kuka da take. Sai dai Hajiya Sadiya kan har aka koma gida kuka take, a motar Hajiya Mairo ke ce mata ta barsa da Allah ai ga amana nan ta fara kamashi, a tunaninta Hajiya Sadiya tana kuka ne saboda ƙazafin da Asim yayi mata.
Ko da suka isa gidan ana shirye-shiye fara walimar da Ummi ta shirya zata yi, wasu tufafin Ummi ta ɗauko ma Namra sanna aka kora Mai Makeup cikin ƙanƙanen lokaci da canja mata kamanin zuwa na amare, sannan ta ɗaura mata ɗankwali.


Fauza da Haleema ne suka riƙa hannun Namra suka fita da ita gurin walimar suka zaunar da ita a muhallin da aka tanada na zaman Amarya. Kowa ya fita zuwa gurin Walimar banda Hajiya Sadiya da ke ƙunshe cikin ɗakin tana aikin kuka, sai kuma Ummi dake cikin gida tana gyara wasu abubuwan, sai da Hajiya Sadiya ta tabbatar hankalin kowa yana can gurin walimar sannan ta suɗaɗa ta fita ta bar gidan gaba ɗaya.


Anyi walima lafiya, kuma an tashi kowa na sam barka da yabawa. Bayan mutane sun watse ne Ummi tasa Namra a mota ita da su Maryam da Raihanatu da kuma Gwaggo Ramatu aka maida su masaukinsu tare da sauran mutane da suka zo walima, bayan sun koma gida ne Namra take labarta musu abunda ya faru.




ASIM POV.


Babu mai mota a cikinsu kasancewar Mai Martaba shi ya aika aka ɗaukosu hara Asim ɗin, a dole tasa sai da suka fita masarautar gaba ɗaya sannan suka samu Napep suka hau, sauran kuma suka hau wata Napep ɗin ana shawarar inda za a kai shi, wasu su ce asibiti wasu kuma su ce gida ya kamata a barshi albashi sai a fidda masa konon rantsuwar da yayi. Daker aka shiga Napep ɗin da shi saboda ƙafafunsa da basa tafiya, ko da suka isa fida a wahale yake saboda shi kaɗai yasan abunda yake ji a jikinsa.


A falon Amarya aka aje shi a take ta bada kuɗi aka je aka siyo gero aka cire masa kono sai dai abunda basu gane ba ai ba shi yayi rantsuwarba, shi isgili yayi na cewar kada Allah ya tashe shi lafiya idan har ƙarya yayi. Babu irin kuka da Mardiya ba tayi ba sai nanata zancen take wai daman tasan haka zai faru tun da yace be sake ta bayan kuma ya san ya sake ta.
Ganin har rana ta faɗi babu wani sauyi, yasa suka ɗauke shi zuwa asibiti, ana kiran magariba aka bashi gado, likitoci suka shiga bashi taimakon gaggawa, sannan suka tura shi ɗakin hoto. Allura suka masa a nan ya samu bachi.




***


Ƙarfe tara dai-dai aka jera motoci ƙofar gidan da su Namra suke wato masaukinsu. Hajiya Shafa da wasu family na mai Martaba suka shiga ciki suka yi bikon amarya da kuɗi da kuma siyayya.
Ana guda aka fito da Namra tana cikin lifaya fuskarta a lulluɓe, sai ƙamshin turare take.
Barorinta suka buɗe mata mota ta shiga sai aka maida ƙofar motar aka rufe, sai sauran suka shiga sauran motocin, aka akama hanyar gidan Mai Martaba da ita, lokacin da aka shiga da ita faɗar Mai Martaba na shaƙe da mutane da kuma talakawa, sai ta yi gaisuwar ban girma Mai Martaba yayi musu addu'a sannan aka shiga ɗakin ɗayar matarsa tayi musu addu'ah sannan aka yi canji mutane da wato mutanen da suka je bikonta ba su zasu raka ta ɗakinta ba.


Ko da aka isa da ita ɗakinta shaɗaya har ta gota, babu wanda beyi mamakin ganin irin gidan da aka kaita ba duk kuwa da kasancewar dare ne, baka iya banbance shi da rana saboda hasken da gidan ke da shi, yanayin gidan zuwa fenti da kwaliyar gidan duka irin na masarautarsu ne yayi, wani abun burgewa kuma yadda aka ƙawata gidan da komai fari kamar fentin gidan, wato furnitures da aka zubawa Namra komai fari ne har labulayenta, da center carpet, kai har agogon bangonta fari ne, duk inda suka yi masu camera na biye suna ɗauka, tun farkon fitowarta har zuwa gaisuwa da kuma kawo ta gidan.


A ɗakin da yafi ko wannne haɗuwa aka kaita, kasancewar ɗakuna biyar ne a gidan kuma ko wanne sai da aka saka masa kaya, sai ta hau tsakiyar gadon ta zauna, kanta lulluɓe da mayafi.
Wasu daga dangin ango suka mata Allah sa albarka suka fice, sannan wasu daga ƴan'uwanta suka kama hanya, sai aka bar Maryam kawai sai Raihanatu da kuma wata ƴar'uwarsu Husaina.


Bayan kamar minti talatin sai suka soma jin busa da algaita da kirari irinta ta ƴaƴan sarakuna, shi ma mai nasa video yana biye da shi yana ɗauka. Har aka shigo da shi cikin ɗakin, sai ya zauna bakin gado yana ƙamshin turare, fuskarsa ta sha rawani kamar Mahaifinsa. Abokaninsa sai zolayarasa suke shi ko bakinsa har kunne.


Nasiha suka musu akan zamantakewar aure da kuma haƙuri, masu auren cikinsu sai zolayar samarin suke, wasu kuma na zolayar Abdool wai ango sai sha mai. Sai da suka ga shabiyu ta gota sannan suka musu addu'ah da fatan alheri, sannan suka saka Maryam da waɗanda suke tare gaba, har wasu na cewa suna son Maryam a zatonsu budurwa ce.
[8/5, 7:03 PM] Khadeeja Candy♥: *96*


Bayan abokansa sun wuce Abdool ya tashi ya rufe ƙofor falo ya dawo ɗakin fuskarsa da murmushi, rawanin kansa ya fara cirewa ya aje sannan cire babbar rigarsa.


“Amaryata wacce ta wacce amarya tsada”


Ya kai hannu zai yaye gyalenta, sai ta matsa baya ta ƙara jan gyalen ya sauko. Matsawa yayi kusa da ita ya sake miƙa hannun sai ta kauce hannunta mai zanen lalle ta ziro masa. Murmushi yayi yasa hannunsa aljihu ya ɗauko wani ɗan ƙaramin box ya ɗora mata saman hannu, sai ya miƙa hannun ya yaye mata mayafin. Idonta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi


“Har da idon sai na siya...?”


“Ai kace wannan amaryar ta fi ko wace Amarya tsada”


Murmushi ya sake yi sai ya cire tsadadden agogon hannunsa ya ɗora mata saman hannu, sai a lokacin ta buɗe ido ta saka su cikin nashi haƙoranta a washe.


“Kin manta ban siye murmushin ba”


“Maganar ma ai baka siya ba an yi maka nasiha ne kawai”


Hannu ya kai ya riƙa gefen fuskarta yana shafa shi da babban yatsansa.


“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar, lallai na fi ko wane Namiji sa'a a duniyar nan”


“Kana koɗa Namra da yawa, har kana sa tana jin kamar ta fi ko wace mace zama sarauniya”


“Na haɗu da mata da yawa ciki da wajen ƙasar nan amman babu wacce ta sace min zuciya sai Namra, she ko ma ƙaramar sarauniyace ba”


Lumshe ido tayi tana murmushi. Box ɗin ya amsa ya buɗe ya fiddo zobe mai kyau ya kama hannunta ya saka mata.


“I Love you so Much Abnam”


“Na gode sosai”


Matsawa yayi kusa da ita.


“Godiya kawai? Ai hausawa na cewa yaba kyauta tukuici”


Ta rufe fuskarta domin ta gano ma'anar zancensa. Shi ma dariyar ya yi, ya jata ƙirjinsa ya rumgume, a hankali ya sauke numfashi ya ɗora kansa kaman nata.


“Gani komai nake kamar a mafarki, ina tuna lokacin da na fara ganinki irin halin rayuwar da na shiga saboda ke kuma gashu yanzu komai ya zama tarihi, inshallah ni ne mijinki ke kuma matana har Aljanna”


Lafewa ta yi a ƙirjinsa kamar babu wanzuwarta a doron ƙasa, gudun zuciyarsa take sauraren tana auna yada nata zuciyar yake hawa da sauka tare da ta shi.
Sun daɗe a haka sannan ya ɗagota ya mata kiss saman ido.


“Karki min bachi saman jiki kisa na ƙarye”


Tayi dariya tana bugar masa chest.


“Ouuuuch”


Ya faɗa yana kanne mata ido ɗaya. Shi ya fara sauka saman gadon sannan ya miƙa mata hannun, ta riƙa hannunsa ta sauƙo suka shiga bathroom ɗin tare, shi ya fara alwalar sannan ya taimaka mata ita ma tayi suka fito. Sallaya biyu ya shinfiɗa ɗaya a gaba ɗayar kuma tana baya da shi kaɗan.
Mayafinta ya ɗauka ta rufe jikinta kasancewar fafaɗa ne kuma mai kauri. Yana gaba tana biye

Please Login or Register in order to submit comment