Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Hilal ko zaka yarda da ni”


“Na yarda da ke aje please”


Bata son musa masa, sai kawai ta aje ƙur'ane saman durowarsa tana kuka. Rumgume ta yayi tsantsan a ƙirjinsa ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya.




*NAMRA POV.*


Tun lokacin da Asim ya bata 500 yace tayi cefane bata dake saka shi a idonta ba, kullum idan ta kira zai ce mata aiki ne ya sashi gaba, yau kusan kwana uku kenan.
Ita kam abun duk yabi ya dame ta, musmman yanzu da take ɗan samun sakewa da shi sai kuma aiki ya ɗauke masa hankali.
Sai dai kwana biyu bata jindaɗin jikinta, yawun bakinta ya kan canja ɗanɗano, ga kasala da take fama da shi, sai yawan amai akai akai, ga ciwon kai.


Sai dai bata kawo ma kanta komai ba, sai hawan jini, duk da bata san alamominsa ba, amman tana jin kamar wannan ba zai rasa nasaba da hawan jinin ba, a iya saninta ta saka roba balle tace ko ciki ne, dan tana jin irin alamomin da ake faɗi na masu ciki. Tun jiya ta ci alwashin zuwa asibiti dan bincika matsalarta gudun kar ciwo yayi mata zurfi a rasa gane kansa, amman Allah be yi ba sai yau. Dan haka da wuri ta shirya ta nemi ƴar fulani data raka ta suje tare, dan bata son xuwa ita kaɗai musamman inda bata saba zuwa ba.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *59*


*RASHIDA POV.*


Ganin Safiya ta fita yasa ta juyo bata tsayawa karɓar maganinba, ta fito gabanta dai faɗuwa yake, saƙe-saƙe take na abinda zata cewa Safiya yau kan ta san kashinta ya bushe, bata da wata mafita sai ta Allah.
Kalle-kalle ta fara lokacin data fito harabar gurin ko zata Safiya amman bata ganta ba, da sauri ta nufi harabar asibitin gurin da tadan tayi parking motarta.
Zagawa tayi ta ɗayan ɓangaren ta buɗe motar sai taga Safiya tsaye tana kallonta, idonta cike da hawaye. Yanzu kan babu kayan ɗazu a jikinta, daman suna saka su ne idan zasu shiga ciki.
Dakewa ta yi tana ƙoƙarin ɓoye tsoro da fargabar dake ranta ta kalli Safiya tana murmushin ƙarfin hali


“Ke baki wuce ba, tun ɗazu nake neman ki fa”




“Ke na zo nema daga asibitin ku nake aka ce kun zo nan ku yi wani aiki”


“Ni...?”


Ta nuna kanta cike da mamakin yadda ƴar'uwarta take ƙoƙarin canja abunda yake a zahiri.


“Amman bayan kin gan ni kin cigaba da tafiya ciki...!”


Ajiyar zuciya Rashida ta sauke a hankali yadda Safiya ba zata ji ba, sannan ta kalleta da fargaba ta ce


“Safiya kar dai kina zargina da wani abu ne? Don't you trust your sister?”


“I trust you but... Me kike nema gare ni?”


“Akwai inda na so ki raka ni, but seems you don't trust me ba sai na je da ke ba”


Bata tsaya jiran abunda Safiya zata sake cewa ba, ta buɗe motar tana mai nuna tsananin ɓacin ranta ita ala dole abunda Safiya ta gani ba shi bane, gaskiya take son canjawa ƙiri-ƙiri.
Da kallo Safiya ta bita har ta tuƙa motarta ya bar harabar asibitin, kallo na mamaki abinda Yayarta take son canjawa, da kuma tunanin abunda ya kawo ta asibiti a hiv unit. Tana ɗa buƙatar bincike dan gano gaskiyar lamarin, dole ne ta bincike ƴar'uwarta, wata ƙila ma tana da masaniya akan Asmee tana da shi.


‘What if ita ma tana da shi fa?’


A zuci tayi furucin tana tafiya, da sauri ta girgiza kai.


“No no A'uzubillahi min shaidanin rajin”


Ƙoƙarin kawar da abin take, dan tana ganin kamar hakan ba zai faru ba, idan kuma har ya faru to sai idan Mijinta ne ya laƙa mata shi, dan bata san yayarta da ɗabi'ar banza ba, sai dai kuma abinda ya tsaya mata a rai tunanin abinda zata faɗi a gida, idan ta faɗi ta tonawa ƴar'uwarta asiri idan kuma ta rufa na su asirin ya tonu.




Tun a cikin mota Rashida ta fara kuka, ganin take kamar asirinta ya tonu, tun da Safiya ta ganta, har kuma ta soma zarginta, idan kuma har ta faɗa a gidan to tasan kowa zai gujeta ne, sunanta zai ɓace haka zai dagula lamarin komawarta gidan Hilal, sannan kowa zai dan dalilin fitar ta gidan, za'asan alaƙar dake tsakaninta da mijin Asmee taren su da Asmee zai lalace, duniya zata san ko wacece ita...!


“Anya zan iya bari wannan abun ya faru? Ya zan yi na hana Safiya faɗa? I can't let her do this, zata saka rayuwata a matsala data tsaka ni a matsala ƙara komai zai faru ya faru”

A fili ta yi furucin, bayan ta faka motarta a harabar gidan, ta ɗan ɗauki lokaci kamin ta buɗe ta fito tana farucin


“Idan Asirina ya tonu ai zaman gidan nan ma sai ya gagare ni, duniya ba zata kawo ƙarshe yanzu ba, i can't let it happen”


Jakarta ta ɗauka ta rufe motar already ta cire hijabin tun a hanya. Sannan ta nufi ciki tana ra saƙe-saƙe a ranta, da tunanin mafita.
Bata bari kowa yaga dawowar ta a gidan ba, saboda bata son a takura da magana ko wani abun na daban, nata ya isheta, har aka yi salla magariba bata leƙa falo ba, sai ana daf da salla i'sha, shima kuma dan taji muryar Safiya ne, sai ta fita ta zauna falo tana ganin kamar idan tana gurin Safiya ba zata iya faɗar komai ba.
Kallonta kawai Safiya take tana saƙe-saƙen faɗar ko a'a, ita kuma taɓa mata kallo ɗaya ta ɗauke kanta tayi kamar bata san da ita ba a zaman falon. Da zaman ya isheta ne yasa ta tashi ta nufi kitchen ta ɗubi abinci ta zo falo ta zauna tana ci ba dan taɓa son cin ba sai dai ta nunawa Safiya kamar babu komai a ranta.
Ita dai Safiya bata ce mata komai ba, bata kuma nuna mata ba sai kallon mbc 2 take, sai dai a ranta ta ƙudiri aniyar sai ta binciki ɗakin Rashida gobe da safe tun da tana rigan kowa fita a gidan saboda aikinta.


Sai da ta gama ci tsab sannan ta tashi ta maida plate ɗin ta sha ruwa, ta wuce ɗakinta, babu komai a zuciyarta sai tashin hankali. Saman gado ta zauna tana mamakin yadda duniyarta ta canja mata lokaci ɗaya, lallai duniya idan ta so ka, kai wawa ne, idan kuma ta ƙi ka, ka shiga uku, kai ne ya kamata ka ƙi ta a lokacin da take so ka, take zaurencen ka, ka so ta a lokacin da take ƙin ka, tana nuna maka kai ba kowa bane, ta haka zaka gama rayuwarka ba tare da ta yaudare ka ba.
Hawaye take, irin hawayen da baƙin cikinsu kan hana kuka fita, makomarta kawai take tunani ta san ko yau ba, wata rana zata samu kanta a irin wannan rayuwar da take gudun shiga, dan tasan asirita ba zai cigaba da rufuwa ba har abada.


“Na yi dama wallahi, duk wannan Alh Bashir ɗin ne yaja min, laifin Asmee ne ita taje ta ɗibo a wani gurin ta saka mana, wallahi duk na shiga matsala ita sai ta shiga, sai na sata a matsala”


Kaɗan-kaɗan take rera kukanta dan bata bukatar kowa ya ji, yau ma ya zame mata kamar ranar da Hilal ya sake ta, har garin Allah ya waye babu abunda take tunanin sai rayuwar da ta yi a baya, yadda take farkawa a gidan, ta wuni da Hilal sahibin ruhinta, yau kuma duka babu wannan, wacan rayuwar ta zamar mata kamar mafarki.


Wani abu taji ya tsaya mata a ƙahon zuciya ya yana numfashinta tafiya dai-dai har tayi salla asuba. Haƙiƙa wanda Halal be wadata shi ba, to Haram ba zai wadatar da shi ba, ko da kuwa ya wadatar da to ya aure shi ne na ɗan wani lokaci ya sake shi, a lokacin ne zai gane illar abinda ya aikata. Zina ya zama ruwan dare yanzu babu matan aure babu budare, an maida abun ado, wasu har gobe suna cin ribar abun saboda Allah yayi musu istijira'i na ɗan wani lokaci, kamin su haɗu da shi, wasu kuma tun a duniya Allah zai bayyana su. Da yawa sun ɗauko ƴaƴan da bana miji ba an kawo ciki gida walau ta gurin bin bokaye ko kuma ta gurin aiki ko abokan banza, shiyasa zaka ga yara suna kashe iyayensu ko kuna musguna musu ko suna wani abu da bae dace ba, wanda abu ne mai wahala ɗan halak ya aikata haka. A social media ma yanzu zina ake macen aure ta kawo wanda ba muharraminta ba gidan mijin ta,, gidanta na sunna, har ta jashi su aikata alfasha. Wasu akan yi musu lamani kaɗan, wasu kuma da yawa, sai dai babban tashin hankali gurin haɗuwa da Ubangijin ka...!


Sai a yanzu ta soma nadamar abunda ta aikata, sai dai nadamar bata yi tasirin yanke kuɗirin dake zuciyarta ba, na komawa gidan Hilal, ta yarda asirinta ya tonu amman a gidan Hilal, ta yarda ta kauce dukan hanyar da zata kauce inda har zata koma a gidan Hilal.


Bayan ta yi wanka ta shirya cikin atamfa pink color ta ɗauki mayafinta ta yafa sannan ta ɗauki handbag ɗinta, bata tsaya karyawa ba ta fice, daman ko ta tsaya ba zata iya cin komai ba. Kai tsaye gidansu Teema ta nufa ita kanta tayi mamakin sammakon data dako mata tun da safe, sai ta shirya ta karya sannan Teema ta faɗawa Iyayenta wai zata raka Rashida gidan Rasuwa, sannan suka fita.


Rashida take driving Teema na nuna mata hanya har suka isa garin ɗan-ƙane, cikin dajin suka kai kutsawa har suka isa gidan mutumen. Wannan kan ba'a kira sa da malam ba sai dai boka, dan babu komai a jikinsa sai walki da fatu, irin arnanan ne na kaduna masara imani waɗanda zasu iya aikata komai ba tare da fargaba ba.


Sun tarar mutane da dama, cikin har da ƴan siyasar da Rashida ta sansu, da kuma wasu matan manya, inda Allah ya taimake ta ta saka niƙab ba kowa ne zai gane ta ba.
Sai da mutane da ke gabasu suka gama shiga, sannan suka shiga a lokacin sun cin ma layi.


Irin kayan tsafe-tsafen da ta gani yasa gabanta faɗuwa, har da wani ƙaton madubi baƙi an masa rubutun larabci da jan jini. Cikin fargaba da tsoro ta zauna gaban bokan tana kallon walkin dake jikinsa.
Zata fara bayani ya ɗaga nata hannu.


“Bana buƙatar ki faɗa min komai, ni zan baki labarin duniyarki, sai dai idan baki son kowa ya ji zamu iya sallamar ƙawarki”


Ta jidaɗin maganarsa dan har ga Allah bata son Teema ta ji sirrinta, dan daga ganin wannan mutumen ba zai ɓoye komai ba.
Ba tare da tace ba, Teema ta tashi ta bar mata ɗakin.
Shi wannan bokan da jini yake duba a maimaikon ƙasa da wasu suke yi da ita, sai da yayi rubuce-rubucensa sannan ya dubeta ya ce


“Auren ki ya mutu, saboda mijin ya gano kina ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki, kin yi asiri wa kishiryar ki da take gidan mijinki ya faɗawa ɗan ki! Wata ƴar'uwarki na daf da shirya miki wani abu, akwai yiyuwar ki koma gidan mijinki amman idan har kin yarda ki daina salla azahar na tsawon sati ɗaya, tabbas buƙatar zata biya, idan har kika zake jefar abokiyar zaman ki to buƙatar ki zata biya zaki same ta, amman akwai yiyuwar jifar ta dawo kan ki, haƙiƙa baƙin duhu yana bibiyarki, wannan baƙin duhun baƙar rana ce...!”


Da sauri Rashida ta miƙe tsaye tayi baya-baya tana kallonsa tashin hankali ƙarara a fuskarta. Bata iya ce masa komai ba ta fice daga ɗakin kamar wacce ta ruɗe. Tana fitowa hannun Teema kawai ta kama ta jata tana hawaye suka fice daga gurin. Teema na tambayar lafiya amman Rashida bata tsaya faɗa mata komai ba, ta shiga motar tayi mata key ganin hakan yasa Teema ta shiga gidan gaba, kamar za su tashi sama haka Rashida ta riƙa tuƙin motar suna ratsa dajin, har sai da Teema ta riƙa ta tana girgizawa, sannan ta dawo hayyacinta har ta rage gudun ta faka gefen titi tana kuka.




*ABDOOL POV.*


Satinsa biyu a kaduna, kusan kullum sai Amira ta tura masa saƙon barka da safiya da dare ma haka, sai dai har yanzu be taɓa mata reply ba, shi kan ba ma ita ce gabansa ba. Kusan kullum sai yayi waya da Ummi kamar yadda ya saba, ya maida hankali akn aikinsa sosai dan aiki ne mai muhimmanci.

Yau kam be kira Ummi da safe ba har sai da ya shiga office, yana shirin kiranta sai gata ta kira shi. Da sauri ya ɗauka Cikin jindaɗin kiran na mahaifiyarsa


“Ummi na ta kai na good morning”


“How are you?”


“Im fine i miss you, na ga nawa satin nan ya zo na zo gida na ganki”


“Nima ai ina son ka zo akwai maganar da zamu yi da kai”


“Wace magana ce?”


“Idan ka zo zaka ji, akwai kayan da nayi oda daga paris za su iso Lagos jibi, zan tura maka address ɗin sai ka aika a karɓo min”


“Yes Ma'am”


Dariya tayi ta kashe wayar shima ya sauke yana murmushi cike da ƙaunar mahaifiyarsa.


Ɗayan ɓangaren kuma yana jin rashin daɗin maganar da tayi ma mai martaba na cewar yace a nema masa mata, sai dai babu yadda ya iya tun da shi kansa ya san yana buƙatar auren a yanzu, idan be yi ba a yanzu sai yaushe, lokaci tafiya yake baya jiran kowa, kuma shi har yanzu be da wacce zai iya fitarwa a matsayin matar aurensa.
Sai dai shi kuma ya sha alwashin aurar da duka ƙanensa dan ba zai yarda Ummi ta riƙa matsa masa ba bayan ga ƙanensa mata nan duk sun isa aure.




*Ummi*
Tana gama waya da shi, sai ga Amira ta shigo da sallama cikin ladabi, already ta gaishe da Ummi da safe so bata buƙatar repetitive, sai kawai tace


“Ummi me za a girka na rana?”


“Ayi mana mana miyar kuɓewa sai Shukura tayi tuwon semo”


“Tau”


Ta miƙe tsaye ta fice cikin tsantsar ladabin nan. Bata kira Shukura ba da kanta tayi tuwon semo miyar kuɓuwa sannan kuma tayi miyar agusi dan kawai ta burge su. Ko da azahar tayi har ta gama komai ta jera a dinning sannan ta shiga tayi wanka.
A lokacin ne su Amal suka dawo makaranta tare da Haleema, daman yau Meesha bata je ba, dan su da lacca. Fauza ce kawai ta tafi sai Haleema.


A ɗaki suka samu Ummi da Meesha suna duba wasu atamfofi da aka turo ta whatsapp. Jikin Ummi Amal ta faɗa tana zuba shagwaɓa wai ita ala dole ga auta.


“Ummi yunwa”


“Ai ga abinci can ana gama”


“Me aka girka”


Haleema ta tambaya tana zaunawa kusa da Meesha.


“Tuwon semu miyar kuɓewa”


“Ɓi bana so, sai dai ki girka min makaroni”


“Kai Amal kin cika son rigima wallahi, miyar tayi daɗi fa”


“Wa yayi? Wannan Amira ko”


“Eh miya har kala biyu tayi”


.“Ni bana so bata iya komai ba sai ƙazanta”


Haleema ta buge mata baki


“Data saba girkawa kina ci fa? Wai Amal miyasa baki da kunya, ke uban kowa kin raina, Amirar nan aiki da take ko da muke cikin gida albarka, tana ƙoƙari sosai wallahi”


“Ta riga ta saba wahalar ne tun gidansu, maybe talakawa ne”


Cewar Meesha, tana taba eyebrows.


“Ba wani sabo wallahi kawai dai tana da mutunci ne, kuma gani nake kamar Big bros take so, dama an haɗa su wlh dan zata kula da shi”


Meesha ta tofarda yawu


“Tuuu Allah kiyaye big Bros da wannan yarinyar amman wallahi Haleema baki da hankali zuwa makaranta be amfane ki ba, daga ganin yarinya an taimaka mata ki ce wai ta auri yayanki, ke anya kina son yaya kuwa? Ke nifa ban ma yarda da yarinyar nan ba, tsantsan ɗinta yayi ta cika shige mana jiki, waya sani ko cutar mu ta zo tayi”


Amal ta haye saman gadon Ummi tana hararar Haleema.


“Sai na gayawa Dude, mu mana son ta”


Ummi ta kama kunne Amal.


“Bana raba ki da yi ma manya rashin kunya ba?”


“Ooo Ummi it hurt”


Ta riƙe kunne, tana son kuka. Haleema yaja wani dogon tsaki


“Ke kin wuce shiga halin da ta shiga ne hala? Idan Allah ya tubuta shine mijinta ya zaki yi?”


Ummi ta kalle ta kallo da babu wasa a fuskarta.


“Ke Haleema ki daina wannan maganar, yarinya daga taimako sai kuma neman wuce gurin tana da tarbiya zata bar gaban iyayenta ana neman ta koma bata so sannan ki ce ta auri ɗan'uwanki dan baki da tunani? Kin san iya zaman da ta yi taraiya da su? Wanda yayi maka hallaci ya cancanci hallaci shiyasa take zaune tare da mu, amman nan gaba kan gurin iyayenta zan maida ta, Allah ya bata miji na gari”


“Amman Ummi ta mana hallaci wallahi, kuma idan ba a barta ta auri Yaya kamar ba a mata hallaci ba”


Meesha ta zungureta


“Ai ke sai ki mata hallaci ko? Yayan manya ma Big Bros be so ba sai ita yarinyar data ƴan fashi, ashe za'a iya haɗa kai da ke ayi ma masa wani mugun abu, haka kawai daga ganin yarinya ki ce a haɗa su amman baki da hankali Haleema”


“Ke da kika da shi ai sai ki ara min na saka, ko ita ba mutum bace? Ke idan kina so wani ya zaki ji”


“Ba zan so wanda ya fi ƙarfina ba balle har na damu, ke daga ganin ajin Yaya kin san yafi ƙarfin Amira wallahi, yarinyar data gama bada kanta ga mazan banza sai kuma ta dawo yaya ya aureta, ai abun kunya ma ne wallahi”


Cikin faɗa Meesha ta ƙarasa tana jin kamar ta kama Haleema tayi mata shegen duka. Ita Haleema ji take kamar ta daki yar'uwarta. Har sai da Ummi ta katsa musu tsawa.


“Haleema kar na sake jin irin wannan kalamin a bakin ki, Aisha ke kuma ya isa tun da ba cewa aka yi za a aura masa ita ba, ku Shafa min lafiya dan Allah ku tashi ku bani guri”


Duk miƙewa suka yi suka fita, ban da Amal data laƙe jikin Ummi ita ala dole sai an dafa maya makaroni.


“Ai kema kin iya dafawa, Amal har mota kike tuƙi fa amman ki zo kina min abu kamar jaririya, idan yanzu aka miki aure ai sai zama dan kin girma, ba kece auta ba autana tana nan zuwa”


Ummi ta faɗa da raha a fuskarta. Amal ɗin tasa dariya dan tasan abu ne mai wahala a yanzu.


“Za a ce tsohuwa ta haihu”


Ummi ta tiƙi bayanta tana dariya


“Yes Tsohuwa maman Amal, tashi ki cire uniform”


Tashi ta yi ta fice tana dariya.




*NAMRA POV*


Kamar yadda suka saba yi duk mai ciwo, bayan ta faɗa masu matsalarta sai suka bata gwajin jini da fitsari, suka sa kuma taje ta yanki sabon kati dan duba wacan matsalar nata na robar dake hannunta dan a bayanin da ta yi ma likita ya fahimci ciki ne a jikinta. Sai dai bashi da tabbacin haka tun da ta faɗa masa tana saye da roba, duk da yasan ana samun irin wannan matsalar a wani lokaci.


Awan fitsari kawai ta samu yi, a take, na jini cewa suka yi sai da yamma ta zo ta karɓa, su kuma waɗanda zasu dubata a ɓangaren robar sun tashi aiki.
Tun da karɓo results ɗin ta kasa ta buɗe dan bata son ta ga abinda yake ciki, tasan idan har ciki ne tana cikin matsala dan bata gama warkewar ciwon mahaifarta, kuma ga roba jikinta ace tayi ciki tasan duka ƙarin matsalar ne. Ko da ta koma gurin likitan yana shirin tashi, har ya haɗa kayansa, a tsai-tsaye ya duba takardar tana fuskarsa da mamaki ya ce


“Kina ɗauke da juna biyu”


Ras ras ras gabanta ya faɗi, sai ta faɗi saman kujera tana hawaye. Da sauri likitan ya aje kayan hannunsa.


“Hey wannan ba wata matsala bace ana samun irin haka daman, amman abunda yafi zan rubuta miki hoto sai kije ayi hoto a bincika lafiyar cikin, kuma ki tabbar kin je an cire miki wannan robar”


“Doc mahaifa tana da matsala shiyasa aka samun robar”


“Ba lallai ne har yanzu matsalar ki tana nan ba, shiyasa nake son ki yi hoton”


Ya ɗauki wata takardar yayi rubutu ya miƙa mata.


“Kije ayi miki hoto, zuwa gobe sai ki kawo na duba ki, ko kuma ki dawo wani likitan ya duba ki, ki kwantar da hankalin ki ba wani abu nima mai ɗaki na ta taɓa haka”


Jakarsa ya ɗauka ya rataya ya face. Sannan ita ta tashi ta fito tana hawaye, maimakon taje gurin hoton sai kawai ta yanke shawarar komawa gida dan ita har yanxu jikinta na bata ba ƙalau take ba, balle bata da kuɗin da zasu isheta hoto tun katin ganin likita na asibitin ma kusan ɗari bakwai ne.


Tun cikin Napep take ta kiran Asim amman ya ƙi ya ɗaga saboda yana gaban Hajiya, wacce ta zame masa kamar uwa a yanzu, yadda yake jinta ko Mama data haife sa baya jinta haka nan.
Hakan yasa ta yanke shawarar tura masa saƙon karta kwana.


Ƙin ɗaga wayar yayi dan akwai yana gaban Hajiya, ita ta jidaɗin hakan da yayi ko ba komai tasan ya girmamata, gashi tun da yazo gidan be taɓa fita da sunan yaje gida gurin matarsa ba.
Sai da ta gama lissafa masa abunda zai siyo mata sannan ta bashi kuɗin tana murmushi ciki ladabi ya karɓa ya tashi ya fice.


Sannan Hajiya tayi murmushi ta maida dubanta ga ƙawarta, Hajiya Ubaida.


“Gaskiya yaron nan yana da ladabi ina kika damo shi?”


“Uhmm tsuntsune daga sama gasasshe Allah ya bani daga gyaran gate”


A nan ta kwashe labarin komai ta bawa Aminiyarta yadda suka haɗu da sharaɗin data gundaya masa da kuma zaman gidan da yake, da kuma ƙudirinta a kansa.
Hannu Hajiya Ubaida ta bata suka taɓa


“Shegiya Sadiya duk abunda kika sawa gaba sai kin ga bayansa, hala yarinyar mai kyau ce?”


“Tana da kyau wallahi ta haɗu ba ƙarya, sannan kin ga na samu dama biyu, daman Alhaji Usaini ya dame ni na samo masa sabin shiga, wai duk wanda nake kai masa basa da ladabi kuma an taɓa amfani da su, kwana biyu sai su fara masa tsageranci”


“Ai kin san manyan mutanen nan sun fi son tsaida mutum ɗaya, wanda zasu riƙa amfani da shi kullum”


“Eh shi ma haka yace, wai idan yana bin irin guys ɗin nan za'a iya gane shi, yafi son tsaida mutum ɗaya, kuma kin ga irin wannan zai fi jindaɗinsa dan ga alama zai yi ladabi, sannan garin su ɗaya, idan ta kama ya koma can ma, ni sai ya barmin matar a nan, dan ba zan taɓa nuna masa ina don matarsa ba, shi wata rana zan iya buƙatarsa”


Hajiya Ubaida ta ƙalƙyale da dariya.


“Ke Allah dai ya yafe mana, ya shirya mu”


“Amin kedai ai ina son tuba amman sai nan gaba, dan bana son Zeenat ta san halin da nake ciki”


“Gaskiya kam, ai ƙara ai daina da wuri kar azo aji kunya”


Hajiya Sadiya tayi fuskar tausayi kamar mai tsoron Allah da gaske, tana kallon Hajiya Ubaida wacce sana'arsu ta zama ɗaya.




*ASIM*


Be wuce kasuwar ba, sai da ya bi ta gida dan jin abinda Namra zata faɗa masa, badan saƙonta da yaga ni babu ma abunda zai sashi bi ta gidan. Kamar baƙin haɗari haka ya doshi gidan bakinsa ƙumshe da maganganu kala-kala, dan gani yake a yanzu shi ma ya kai matsayin da zai iya faɗawa magana son ransa, balle Namra da yake gani kamar banza.


A ɗaki ya tararar da ita kwance sai hawaye take. Daker ta ɗago ta kalleshi, duk da tana cikin yanayin damuwa hakan be hanata, kallon irin shigar dake jikinsa ba. Takalmin dake ƙafarsa kaɗai zasu iya kaiwa dubu 10+ balle wando da T-shirt.
Be ji zai iya zama a ɗakinba, sai kawai ya tsaya jikin ƙofa yana mata wani kallo, azuciyaraa yake hantararta ganin yadda ta ƙara lalacewa.


“Ya aka kika samu ciki?”


Wani kallo tayi masa zafin furucinsa yana zuciyarta.


“Kamar ya? Ina da wani mijin ne bayan kai”


“Ni ya za'ayi na sani, yanzu ai ba a shedun mutum”


“Shigowarka Asim irin wannan furucin zaka min? Tun da kasa ƙafa ka bar gidan nan babu ruwanka da ni kamar ba matar ka”


“Ya kike so nayi Namra aikin zan bari na zo na tisaki

Please Login or Register in order to submit comment