Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ƙare da kyau, kar dai karka yarda ka ci amanar wani barshi shi ya ci amanar ka, ki zuba masa ido ki gani ba zai ga da kyau ba”


“Amman wani lokacin mutun yana buƙatar gargaɗi kai, da wannan haƙuri kike ta cutar da mu da kan ki, gashi nan a gida kullum mine ba mu da gata, komai na gidan nan Hajiya ce take da iko da shi, da an yi magana sai ki ce ayi hakuri, fisabilliah har na waje kuma sai a riƙa bari suna takamu”


Ta ƙarasa tare da miƙewa tsaye ta nufi bedroom ɗinta.


“Ke kan Maryam Allah ya shiryaki, da wannan rayuwar babu inda zata kai ki, ni ban san inda kika ɗauko wannan baƙin hali ba, ni dai ba haka na ke ba”


Bayan sun yi Sallah magariba, Anty ta shiga part ɗin Abbah da abinci a hannunta ta tsakura masa labarin abunda ya faru.
Washe gari Namra ta daɗe tana bachin safe saboda gajiya da kuma kwanciyar hankalin yau tana gida bata da wata matsala. Maryam ce ta shigo ita da Aisha suka tashe ta wai zasu je siyen wasu kayan kitchen, kuma ta fito da Yasmin a falo tana jiranta. Mulmula ta riƙa yi saman gadon sai da suka fice, sannan ta miƙe tsaye tana miƙa ta shiga bathroom, bakinta ta wanke, a nan take kallon kanta a madubi ita kanta ta san ta chanja kamar ba ita gaba ɗaya ta fita daga kamamninta, ta yi baƙi sosai idonta sun ƙara fitowa.


“Namra ko har yanzu baki tashi ba”


Jin muryar Yasmin yasa ta yi saurin barin gaban madubi ta nufo ƙofar fita tana zumuɗin haɗuwa da Yasmin.


“Anty”


Ta faɗa jikin Yasmin suka rumgume juna.


“Ashe kin ji na dawo”


“Eh Gwaggo ce ta faɗa min komai. Ban jidaɗin abunda ya faru ba Namra sai dai dawowarki ta min daɗi, saboda Uzair, ko da baki zo ni zan je har inda kike”


Gaban Namra ya faɗi ta mata wani kallo mai cike da mamaki.


“Uzair kuma, miya faru?”


Yasmin ta kama hannayen Namra ta riƙe.


“Ina son ki faɗa min tsakani da Allah, da gaske kin taɓa kama Uzair yana luwaɗi?”


“Dan Girman Allah Anty ki rufa in asiri na dawo yanzu cikin family na kuma saki sake tayar min da wannan maganar? Ko so kike Abbah ya sake kora ta ne?”


“Ko kaɗan, Namra kawai ina nema miki justice”


“Justice for what...?”


“For what Uzair did to you, shi ya ɗauke ki ranar da aka ce kin gudu kin je gurin Asim”


Idon Namra ya cika da ƙwalla.


“Waya faɗa miki?”


“Shi ya faɗa min da kansa, kuma yayi rape ɗinsa da kansa Namra, na rasa yadda zan yi abun yana ta ci na a rai, na kasa faɗawa kowa, amman na yi ma kai na alƙawari sai na shigar da ƙarar Uzair kotu da kai na, akan ki sai na nema miki haƙƙinki, saboda ɓacin suna da yayi miki kuma yasa duniya ta zargi kin gudu da saurayinki”


Kai Namra ta girgiza masa.


“Na yafe masa, dan Allah dan Annabi ki taimaka min ki bar wannan maganar”


“Kin tuna lokacin da Amira ta gudu? Shine sila saboda ke aka yi ma maganin sai ya koma kan Amira saboda ta ci amanar ki, Namra you deserve justice”


“Ke da kan ki zaki shiga kotu ki ƙalubalanci mijin ki?”


Cikin kuka Yasmin ta ce


“Yes Goyon bayan ki kawai na ke nema”


Namra ta yi saurin miƙewa tsaye fuskarta da hawaye.


“Zan yi tunani a kai, just go please”


Bata mata musu ba, ta share hawayenta ta mike tsaye ta fice. Tana fitowa falo ta karɓi Little Namra hannun Anty ta fice, ko sallama bata yi ma Anty ba. Anty na ganin hakan ta san ba lafiya dan haka ta tashi ta nufi ɗakinta inda Namra take.






ASIM POV.


Yana fita gidan Hajiya Sadiya, ya kira Matdiya ya faɗa mata ta faɗawa mamanta yau da dare zai zo ya gaishe ta. Haka kuwa aka yi, dare na yi yaje yayi wanka ya shirya cikin tufafi na alfarma, ya shiga motarsa da ya sa aka wanke masa, ya nufi wani boutique ya haɗu mata sabulai da mai da turaruka masu ɗan karen tsaɗa sai da ya kusa ciki bayan motarsa sannan ya shiga ɓangaren kayan ciye-ciye yayi leda uku, bayan ya biya ya kama hanyar gidansu.


Tass ya samu ƙofar gidan yau kam an share ba kamar kullum ba, zamansa yayi cikin mota ya kira ta a waya, ya shaida mata yana nan waje. Yau kan ta fi masa kyau fiye da kullum dan ta chaɓa ado da sari kamar wata amaryar india. Sama-sama suka gaisa yana mata wani kallo mai cike da alamar tambaya, ita kuma sai wani noƙe kai take ita ala dole tana jin kunya. Sannan ta yi masa iso, suka shiga cikin gidan tare. Ya raina gidansu sosai dan shi gani yake yanzu ya wuce irin wannan rayuwar. Bayan ya gama gaisawa da mahaifiyarta ya aje mata dubu hansi, sannan shiga ko wane ɗaki na gidan yana gaisawa da su sannan ya aje musu dubu goma. Su kan sai murna suke suna yabawa Mardiya kan ta yi miji, masu jin zafi suna ji, dan wasu har sun soma maganar ai yadda yayi ma Namra ita sakinta zai yi da ana kwana biyu.


Bayan sun fito yasa yara suka kashe kayan da ke bayan motarta suka shigar ma Mahaifiyar Mardiya da su cikin gida. Ita Mardiya ji tayi kamar ta ɗauke shi ta haɗe saboda ƙaunarsa dake ƙara mamaye mata zuciya, ko a mafarki bata zaci mutum mai kuɗi kamar Asim zai so ta ba, balle ma har ya ce zai aureta. Sun sha fira sosai sai kusan ƙarfe goma sha ɗayan dare sannan suka yi sallama.


A daren da farinciki suka kwana daga ita har Asim, har yana jin ba zai iya bari ta jima sosai ba. Sai dai abunda ya tsaya masa a rai miyasa bata nuna masa dangin ubanta ba? Ko lokacin da ya ce zai turo cewa ta yi bari ta faɗawa Uncle ɗinta.


“Idan ma bata da uba miye ruwana tun da ita nake so ba ubanta ba”


Ya faɗa yana fesa turare a jikinsa. Sannan ya ɗauki glass ya saka ya ɗauki makullin motarsa ya fice. Kai tsaye gidan ƙanen Babansa ya nufa, daman yasan a irin wannan lokacin yana gida kamin yaje gurin da yake aikin ƙira. Har ciki gidan ya shiga, sai qani ƙyaƙƙyami yake da ginin ƙasa, ya gaisa da matansa sannan suka fito waje suna tattauna maganar auren da Asim yake labarta masa na Mardiya akan maganar tura magaba, a nan suka kitse maganar sati mai zuwa sai nemi sauran ƴan'uwa suke je su nema masa aurenta, sannan kuma ya ɗora masa da maganar gidan da aka ce masa akwai amman milinya takwas ne.


Gidan ba shi da nisa sosai da unguwar hakan yasa suka ƙarasa da mota aka kira Mai gidan ya shiga da Asim ciki ya ga komai. Ya yaba da gidan sosai, komai na cikin gidan sabo ne ga sabo fenti ga fulawowi daman irin gidan nan ne da ake ginawa sababbin a saida. Ko tayawa Asim be yi ba, suka kutse magana akan idan ya dawo daga sokoto zai zo tare da shedu a bashi makulin gida takardu shi kuma ya bada kuɗi. Mutunen sai godiya yake ganin Asim be taya ba ya amince zai ba shi kuɗin. Bayan sun dawo ya aje Ƙanen Baban nasa ya miƙa masa dubu ashiri, sannan ya kama hanyar gidan Hajiya Sadiya yana aikawa Namra kira.....




Tsaki yaja bayan ya kashe wayar, lallai ma yarinyar nan ta raina masa hankali, shi zata yi ma ɓoyun ɗansa? Allah yasa ma da gaske ta zubar da cikin nan ta ga yadda zai yi da ita ƙut! ya yi ƙwafa.


Yayi mamakin ganin Hajiya Sadiya a gidan nata, bayan yasan a wacan take zama saboda ƴarta. Bayan sun gaisa ya zauna saman kujera yana kallonta.


“Mun yi waya da Alhaji yace na same shi sokoto, kuma na samu labarin Namra tana sokoto har ma na yi waya da ita, amman kin san ba lallai ba ne ta amince ta dawo gidana ba ko?”


“Nasan da hakan shiyasa ka ga na dawo nan gidan ai, nasan zaka zo nema na, abunda nake so da kai ka yi ta try har sai kaga ta aminci, idan kuma hakan be samu ba, to zan baka abunda zaka bata, kuma ka tabbatar ya kai ga bakinta, ma'ana ta ci”


“Mi zaki ba ni?”


“Ina zuwa”


Ta miƙw tsaye ta nufi wani bedroom. Shi kuma ya ƙurawa pop ido kamar yau ya fara ganinsa.


“Wallahi duk kika zubar min da ciki ko? Hmmm, Allah yasa ma Ubanki ne ya zubar da shi ta yadda zan fi jindaɗin shari'ah da shi...”


Fitowar Hajiya Sadiya ce tasa ya mai da dubansa gareta yana kallon farin ƙyalen da ke hannunta. Tana ƙarasowa ta warware ƙyalen ta miƙa masa apple ja.


“Ka tabbatar ta ci wannan apple ɗin ko da kaɗan ne, amman sai idan ta ƙi yarda ta koma ɗakinta”


Ya ƙurawa Apple ɗin ido


“Kar fa wani abu ya same ta, i mean kar ta mutu, akwai baby na a jikinta”


“Babu abunda zai same ta, ka yi yadda na ce kawai”


“Okay”


Ya miƙe tsaye tare da saka apple ɗin a aljihu, ya fice. Be yi nisa da barin gidan ba Nably ta kira shi, amman sai ya samu kansa da ƙin ɗauka shi kwata-kwata yanzu ta fita ransa, Mardiya ce on top.










KU YI HAƘURI DA WANNAN🙏


*Ku yi ta yaudarar kan ku da sunan wata ta siya ta ara muku ku karanta, idan mun je can inda baki be magana zamu tsaya gaban Allah ni da ku ya mana hukunci.*


HILAL POV.


SIX MONTHS LATER...
Suna jin ƙarar tsayawar Motar Dadynsu suka fita da gudu suna masa oyoyo. Zaune suka same shi cikin motar yana waya, hakan yasa Ezzah zagayawa a front seat ta zauna tana jiran ya gama wayar ta fara masa complain.


“Dady muna dawowa daga makaranta Mama Teema tasa mu wanki”


Yana sauke wayar daga kunnensa kenan, ta soma labarto masa abinda ya faru yau. Wani kallo yake mata, irin kallon nan na ɗa da ƴa, kamin ya kai hannunsa ya kama fuskarta ya riƙe.


“Ezzah kin yi ƙanƙanta da irin abubuwan nan, kullum sai kin ce Teema ta miki kaza bla bla bla, wannan sam be dace da ke ba, babu abunda Teema zata muku sai tarbiya, ƴar'uwarki bata taɓa faɗar an mata wani abu ba sai ke”


Ta turo baki zata masa magana da kuka a lokaci ɗaya.


“Dady ni bana son ta, a kawo mana Mummie mu”


“Ba za'a kawo ba, kuma kar bakin ki ya ƙara furta kalmar ƙi ga matata, ke kowa ai baki so, har Kalsoom ba haka kika mata ba? Saboda ku Hajiya tasa na auri Teema yanzu kuma ki bijiro min da wannan maganar! Kar na sake ji”


Ya fita daga motar ya kama hannun Ulfah, sannan Ezzah ta fito ita ma tana share hawaye ta rufe masa motarsa, ta rufa musu baya.


Teema na tsinkayarsu dan tana tsaye jikin window ne, sai dai ba zata iya jin me suke cewa ba. Tana ganin ya doso ƙofar falon sai ta bar gurin da sauri ta shige bedroom ɗinta ta zauna bakin gado ta soma ƙirƙiro kuka. Tun da ya saka kafarsa a falon ya ji be ji motsin Amaryarsa ba ya saki hannu Ulfah ya doshi bedroom.
Zaune ya same ta bakin gado tana rusar kuka, zama yayi kusa da ita cikin damuwa, dan yasan dalilin kukan nata baya buƙatar tambayarta.


“Sau nawa zan faɗa miki ki yi haƙuri Teema? Wasu ma sai da suka shekara ashiri a gidan miji sannan Allah ya ba su haihuwa, balle ke da baki yi shekara ɗaya ba ma?”


Ta ɗago kai ta dube shi.


“Hilal ina tsoron kar a'ce ba zan haihu ba ne gaba ɗaya, tun da na zo gidan nan ko ɓari ban taɓa yi ba”


“Idan Allah ya ga dama zai baki just be patient, wani lokacin abun mutum nesa yake, na shigo da farinciki kuma kin rusa min shi”


“Ka yi haƙuri rai na ne yake ɓaci”


Ta share hawayenta, har ga Allah wannan matsalar tana damunta, sai dai ta kan yawaita yi ma Hilal kukan hakan ne gudun kar ya zargi ta ci amanar ƴaƴansa, duk lokacin da ya tarar da ita cikin irin wannan halin ya kan kasa mata maganar yaran, ko da kuwa sun je masa sun kai masa ƙararta ne.


“Kuɗin da na faɗa miki muna jira jiya dai Allah yayi sun fito, dan haka yanzu ki shirya muje kasuwa da yara mu yi siyayya, gobe kuma zan je da Kalsoom Hajiya kuma kuɗi zan bata, sauran kuma sai mu ƙara a account, idan na samu hutu sai mu leƙa waje”


Hannayenta ta kama ta riƙe tana murzawa a hankali.


“Hilal ya kamata ka yi tunanin ma kan ka future, kai kake ta hidima da Hajiya duk da tana da waɗanda zasu iya mata beside Abbah ka yana da rai balle ace ko zata rasa wanda zai mata ne, ya kamata ace ka tanada abun ka har sai ranar da zaka nema ko kuma ita Hajiya zata nema sannan ka ɗauko ka yi amfani da shi, ƴaran ka babu abunda suka nema suka rasa, dan me za'ace a riƙa kashe musu kuɗi haka nan kawai a banza? Ka fara ginawa kan ka rayuwa Hilal, yanzu nan kuɗi ba ƙara ka gina gida da shi ba”


“Ina da gida Teema ba ɗaya ba ba biyu ba uku ba, kuma naga yanzu mi zan yi da gida?”


“Baka mafarki tara zuri'ah kamar ta Mahaifinka? Baka fatar haɗa ƴaƴan da matanka guri ɗaya yanzu? Ni abun da naga ya fi kawai ka kawo ko 150.000k ne asiya mata lace da atamfa, sauran kuɗin kuma ka ba ni nawa ita kuma Kalsoom ka bata ta siya abinda take so, Hajiya na san idan ka bata kuɗin kashewa zata yi amman idan aka siya mata kaya, ko sakawa ta yi ai ka ji daɗi, ni k8ma ina son na fara business”


Miƙewa yayi tsaye.


“Zan yi tunani akai, bari na je na duba Kalsoom ta ce min kan ta na ciwo”


“Ka gaishe min da ita, tun da ka ƙi yarda na ganta, amman ba zaka bari ka ci abinci ba”


“A'a sai na dawo kinsan matsalar mai ciki”


Ya faɗa da murmushi a fuskarsa sannan ya juya ya fice, zuciyarsa da kwankwato, ya lura duk lokacin da ya shigo da zimmar yi ma yaransa ko Hajiya abu sai Teema ta nuna masa ba haka ba, abunda Kalsoom da Rashida ba su taɓa masa ba kenan. Duk da yana tunanin wannan karon ta yi magana mai ma'ana kuma da bada dalili. Miƙewa ta yi ta rakoshi har gurin mota, ya shiga ta maida ganbun motar ta rufe tana ɗaga masa hannu har ya fice.


Ajiyar zuciya ta sauke, ta gaga mallakar mijinta har yanzu, iya shige-shigen da take tunanin zata yi ta yi amman kan Hilal ya gagara mallaka, bata da ƙudiri raba shi da mahaifiyarsa, sai dai tana ganin kamar hidimar da yake mata yayi yawa, tun da ba shi kaɗai ta haifa ba.


“Ulfah, Ezzah..!”


Sai ga su da gudun su, bama Kamar Ulfah da hanjin cikinta ke kaɗawa, dan jikinta har rawa yake kamar zata saki fitsari.


“Uban mi kuke faɗawa Baban ku ɗazu...?”


Ulfah ta yi sauri ɗaga hannunta sama.


“Wallahi ba ni ce ba, Ezzah ceta faɗawa Dady wai kin sata wanki”


Teema ta miƙa hannu ta kama kunnenta har sai da ta yi ƙara.


“Wato dan na saku wankin uniform shine abun magana? Ke komai sai kin kwashe kin faɗawa Dadynki? Sau nawa nake ja miki kunne akan faɗawa Dadynki magana idan na miki abu?”


Ta nuna mata wani ɓangare na gidan inda rana ta baje a gurin, kamar an hura wuta.


“Oya wuce can ki kama kunnenki, kuma karki taso sai na ce ki taso”


Da sauri ta ɗuka ƙasa ta riƙa kafafun Teema.


“Dan Allah ki yi haƙuri ba zan sake ba”


“Wannan tsinin bakin na ki ba, ke me baƙi hali tun da kin yi mugun gado ko? Kije ki kashe min aure! Ke ce uwar rashin kunya uwar gulma ko? Zaki ci ubanki a gidan nan ba dai duk lamanin da na ke miki baki gani ba”


Ta faɗa tana matsar bakinta. Daman ta saba yi mata irin wannan horon a duk lokacin da ta yi mata ba daidai ba. Ta buge mata hannu.


“Ba zaki wuce ba sai na yi ƙwallo da ke?”


Ulfah ta sa kuka.


“Mama Teema Wallahi ba da ni ba”


“Ai ba da ke ba ita kaɗai, ki ki wuce ki gyara min kitchen”


“Tau”


Ta wuce da gudu idonta cike da ƙwalla. Ezzah kuma ta tashi tana kuka ta nufi gurin da ta saba tsayawa kama kunne ta kama kunnenta.


Juyawa Teema ta yi ta koma cikin falon, har ta zauna sai kuma ta miƙe tsaye ta nufi bedroom ɗinta tana ta saƙe-saƙe a ranta. Wani irin ihu ta ji da muryar Ulfah ba shiri ta zaɓura ta fito daga bedroom ɗin a firgice ta nufi kitchen.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Na shiga uku uban waya aike ki taɓa miya?”


A razane ta yi furucin kamin ta ƙarasa gaban Ulfah da ke kwance ƙasa lame-lame tana murje-murje da ihu kamar bata san inda take ba, jikinta har ya sale.
Har ta ɗaga ta tasheta sai kuma ta saketa ta fita a firgice tana kiran Ezzah.
Karo suka yi ita da Ezzah duk ta haɗa uban gumi.


“Mama Teema ga ni”


“Je ki Kitchen ki kama ƴar'uwarki yi sauri”


Ita kuma ta juya da sauri ta koma ɗakinta dan kiran Hilal.


KALSOOM POV.


tana zaune falo Hilal ya shigo bakinsa ƙunshe da murmushi da kuma sallama a lokaci ɗaya. Itama da murmushin ta amsa masa tana ƙara miƙarda ƙafafunta. Kusa da ita ya zauna daman tana zaune ne saman carpet ya kai hannu ya shafa ƙananan kitson da ke kanta yana murmushi.


“A bani canji na na kitso”


“Ba wani canji mai kitson ma ta ce sai an ƙaro”


Dariya yayi ya kai hannu ya shafa cikinta.


“Sai kice mata ai ke mijinki bawan Allah ne, ba mai kuɗi ba ne”


“Ba wani nan, ni sai ka ƙaramin”


“Baki da matsala yarinya ko nawa kike so za a ba ki, ƙuɗin da na ke faɗa miki ina jirajiya sun fito”


Ta zaro ido.


“Da gaske Alhamdulillahi”


Ya lanƙaci hancinta.


“Yes”


“Allah yasa musu albarka”


“Amin mi kike so a siya miki?”


“Ka fara cirewa Hajiya nata, sannan mu sai kuma ƴaƴanka, kai ai ko baka samu ba, ba matsala”


“Sai dai na ɗauki na ki”


“Ba matsala ai daman ni bana siyen komai yanzu”


“Ko da kin haihu?”


“Hilal anya zan haihu?”


“Haba ki daina wannan maganar mana, ke da Teema maganar haihuwar nan na ku ya ishe ni”


“Ƙara ita ai bata yi cikin ba, ni kuwa shekara har da wata huɗu ban haihuwa ba, cikin nan ya ishe ji nake kamar na cire shi na aje”


“Zaki haihu inshallah, tun da an bincika babu wata matsala”


“Allah yasa”


“Amin. Zaki haifa min Baby girl mai kama da ke”


“Baby Boy dai zan haifa mai kama da kai”


Bakinshi ya kai zai yi kissing ɗinta sai wayarsa ta yi ringing, kawar da fuskarta ta yi dan ta bashi damar picking ɗin wayarsa.


“Hello...”


Ya miƙe tsaye da sauri.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, gani nan zuwa”


“Miya faru? ”


Kalsoom ta tambaya a firgice.


“Wai Ezzah ne da Ulfah suka yi faɗa shine Ezzah ta watsa mata miya”


“Subhanallah miya haɗa su haka, ko na ɗauko hijab ɗina muje tare?”


“A'a zauna duk yadda aka yi zan kira ki”


Ya fice a firgice. Daker ta unƙura ta miƙe tsaye da tulelen cikinta.


Yana isa ya ɗauke ta suka yi asibiti tare da Teema, Emergency ya wuce da ita surgical Ward, wata Dr Khadija ce ta shiga bata taimakon gaggawa, dan Dr Hilal tsaye kawai yayi yana kallo saboda jikinsa duk ya mutu ko da suka kawo ta asibitin ma ta suma.




AMIRA POV.


Tun da suka kamo hanyar sokoto take ta aikinki kuka, har suka iso sokoto idonta ya kumbura sosai. Direban na yin horn a bakin gate ɗin gidansu, ta jita cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, wani sabon kuka ne ya sake rufeta, musamman lokacin da ta ji muryar mai gadin su yana tambayar wa suke nema.


“Amira na kawo ka min magana da iyayenta zan danƙata hannun Mahaifinta ko mahaifiyarta”


“Amira...!”


Mai gadin ya daki ƙirji. Kamin Direban ya sauke gilashin motarsa ya hango Amirar ce da gaske. Jiki na rawa ya wangale musu gate sannan ya shiga cikin gida da gudu.
Sai ga Mahaifiyarta da duka ƙanenta sun fito har da Baban yayanta. Duk motar suka nufa. Ammy ce ta fara buɗe motar sai ga Amira ta fito daga ciki tana kuka, suka rumgume juna, ƙanenta kuma suka daka tsalle suka yi kanta, Big bro ɓata ne ya tsaya a gurin ya dake yana kallon ikon Allah.


“Ke ce Mahaifiyarta?”


Ammy bata iya amsawa ba sai kuka take, Babban yayansu ne ya amsa da.


“Eh ita ce, waye kai?”


Ya fiddo id cart ɗinsa ya nuna masa,sannan ya miƙa ma Ammy waya.


“Zaki yi magana da Ogan mu”


Cikin muryar kuka Ammy ta ce


“Hello”


“Ke ce Mahaifiyar Amira?”


“Eh nice”


“Kina magana da Major Abdallah Ahmad Mai-doki, da ga rumdunar bada tsoro ta Kasa wato Nigerian Army, da fatar ƴar ki ta shiga hannun ki”


“Ta shigo na goɗe muku”


Daga hakan ɗireban ya janye wayarsa ya buɗe motarsa.


“Wait...”


Big bro nata ya faɗa sannan ya ƙaraso kusa da shi.


“Ina kuka haɗu da ita?”


“Ba ni da wani abun da zan ce ita zata muku bayanin komai da bakinta”


Ya shige motarsa ba tare da ya tsaya jiran abunda zai ƙara tambayarsa ba ya juya a guje ya bar gidan. Sai da Ammy da Amira suka ci kukan su sosai a gurin sannan suka shiga cikin giɗan still suna kuka ita da ƴarta.


NAMRA POV.


“Miya haɗa ki da Yasmin?”


Anty Amarya ta tambaya.


“Ba komai saboda kawai na ƙi amincewa ta maka Uzair kotu ne”


“Kotu a wane dalili?”


A nan Namra ta labarta mata yadda suka yi da Yasmin.


“Karki yarda da ta sa sake jefa ki cikin halin da mahaifin ki zai tsane ki”


“Nima ba zan yarda ba Anty idan munje lahira Allah zai mana hukunci ai”


“Wannan shi ya fi, kin samu kin dawo gida kuma za su kawo miki wani ruɗani, qaya sani ko da mijinta aka haɗa kai ta aikata miki haka”


“Ƙoma ba da shi ba ne babu ta yadda zan yarda ta kai mijinta kotu saboda ni”


“Hakan ya yi ki karya kije ki gaishe da mahaifinki, breakfast ɗin ki na nan dinning”


“To na gode”


Tare suka fito da Anty, suka zauna dinning sai tattauna maganar suke, bayan ta gama karyawa ta koma ɗakin Anty ta ɗauki Hijab ta saka ta nufi part ɗin Abbah.


“Assalamu alaikum”


Ta faɗa yayinda ƙafafunta duka biyu suka tsunduma cikin falon Abbah. Abbah dake dinning area ya ɗago ya kalleta idonsa sanye da farin gilashi fuskarsa kuma ɗauke da murmushi.


“Mamana”


“Na'am Abbah ina kwana”
Ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi tare da Hajiya Barau dake ƙoƙarin barin dinning ɗin, kamar zata fasa ihu tace wayyo haka ta bar falon. Sai Abbah ya nunawa Namra kujerar da ke kusa da shi.


“Zo nan ki zauna Mamana”


Ta zauna cikin wani irin jindaɗi marar misaltuwa.


“Kin tashi lafiya, kin karya ko?”


“Na karya”


“Mamana ina son na tunatar da ke akan rayuwa. Ki riƙa haƙuri da abunda ya same ki, kar hakan ya saka ki sakewa ko kuma wani tunani, ko wane bawa da irin ƙaddararsa, dukan abunda ya faru ga bawa zai zamo masa darasi ne ko kuma izna ko wata hanya ta samun cigaban rayuwa, ko da kuwa abun nan mai daɗi ne ko akasin haka, dan haka bana son ki saka damuwa a ranku ni dai na yafe miki, kuma ina son idan kin ɗan hutu kin samu sawaba sai kuma ayi maganar karatu, ina tunanin idan kika koma makaranta sake fi sakewa ki manta da komai”


“Na gode sosai Abbah Allah ya saka maka da alheri, kamin abunda ban taɓa mafarkin zaka min ba, ni kuma na maka alƙawarin va zan sake tsallake zaɓinka ba har a bada ko da kuwa a tufafi ne”


“Allah ya miƙe albarka, ni zanje na shirya akwai inda zan je kwana biyu nan ban samu na fita ba”


Ya miƙe tsaye yana faɗar hakan, ita ta miƙe tsaye.


“Tau Abbah Allah ya tsare”


“Amin”


Ya nufi hanyar da zata sadashi da bedroom ɗinsa, ita kuma ta juya ta fice zuciyarta cike da farinciki.
Ko da ta dawo part ɗin Anty ta tararda su Maryam sun dawo, ga manyan

Please Login or Register in order to submit comment