Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mallake gidan daga ita sai nata ƴaƴan”


Ezzah ta.yi shiru tana tunani sai kallon ƴan makarantar su take masu kai wa da dawowa.


“Ezzah dik duniyar nan baki da kowa kamar ni, duk wacce zata so ki abaya na take, kuma ƙarya Kalsoom take tace tana son ku, tana nuna muku haka ne dan ta mallaki Daddy, yanzu kina jindaɗi zama da ita? Bata dukan ki? Lokacin da ina nan Daddy ki yana miki faɗa?”


Duk ta girgiza kai.


“Dole ne kiyi mata abunda na saki dan na samu na koma gurin Daddy ku, na yi muku alƙawari ddana koma kullum gida zan riƙa zama ba zan sake fita aiki ba”


“Da gaske?”


“Wallahi, dan haka ki cigaba da abunda kike, har abunda ban saki ba ma ki aikata indai kinsa wanda zai hassalata ne”


“Zan riƙa yi”


“I Love you”


“I Love you too”


Rashida ta rumgume ta kamar da gayya. Sannan ta ciro chocolates da Sweet Candy dake jakarta ta miƙa mata, ta kuma bata ɗari biyu na kashewa sannan ta tashi ta fita.


Daga nan Asibiti ta nufa. Yau ce rana ta farƙo da zata fara bin shawarar likita wajen ɗora kanta akan magani, dan samun tsawaita rayuwarta kamar yadda likita ya faɗa mata.





NAMRA POV.


Two months later....


A zuwa yanzu babu wata matsala da take fuskanta a gurin Asim, tun bayan da aka sallamo daga asibiti, jiki sai ƙara sauƙi yake yana mirmirjewa kamar ba shi ba.
Duk wani mugun ƙudiri dake cikin ransa, ya danne ya barwa zuciyarsa, dan yasan babu yadda zai yi da Namra a yanzu sai kallo, idan yace zai rabu da ita matsala ne a gare shi tun da baya sgi kuɗin auren wata, shi dai yanzu ba shi da wani buri sai na yayi kuɗi.


Irin yadda yake nanata maganar har tsoro abun yake ba Namra, ahi dai yayi kuɗi dai yayi kuɗi. Haka Namra zata zauna tana masa nasiha akan duniya da abunda ya ke cikinta, amman sai dai ya kalleta kawai ya nuna mata wa'azin ya ratsashi bayan a ƙasan zuciyarsa kuma mamakinta yake, wai ita zata zaunar da shi ta nuna masa illar kuɗi, bayan ga ubanta can ya tara su ita kuma da su take tinƙaho.
Sam baya ganin wahalar da take da shi, bata saba wanki ba ko a gidansu amman haka zata zauna ta wanke nata tufafin ta wanke nasa, ta kai masa ruwanka, amman kullum sai ta matsa masa yake wanke dan ganin yake kamar tana takurasa, Allah ya zuba masa ƙuiyar motsa jikinsa indai a bangaren aiki ne.


Maganganun da Namra take masa akan rayuwa da neman kuɗi da yake magana a ko yaushe sai ya ƙara riƙe ta a zuciyarsa, wai bata son sa da alheri ta fi son yayi dauwama cikin baƙin ciki da damuwa tun da ita tana da mafita.
Ga matsalar da ci masa tuwo a ƙwarya a yanzu, wacce yake ganin kamar da ganganci ne tayi masa haka dan bata son haihuwa da shi. Ita kanta tana nadamar sanar da shi da tayi robar da aka saka mata, sai dai babu yadda zatayi dole ce tasa ta faɗa masa, tun kullum sai ya tunkareta kuma jinin har yau be tsaya mata ba, daman wani lokacin haka robar yake yi mutane dan ta ji maƙonta suna firar lokacin data shiga gidan su ƴar fulani.


Ta aika tambayarta ga wani malami ya amsa mata da cewar duk jinin daya zube bana haila bane ya zama kamar jinin rashin lafiya ne dan haka ba zatayi fashin sallah ba balle azumi.


Hakan yasa robar ma sai ta fita ranta dan ita bata son abunda zai riƙa rikitar mata da addini, hakan yasa ta yanke shawawar zuwa a cire mata robar in ya so sai tasha ƴaƴan zurma, dan maƙociyarta nan ta faɗa mata indai har ta sha ƴaƴan zurma ɗaya yana matsayin shekara ɗaya ne idan kuma tasha biyu kuma yana matsayin shekara biyu ne.
Sai dai ba kowa yake yi ma aiki ba, amman ta ga wani a whatsapp wanda Khadeeja Candy take tallah shi kam idan an sha tabbas zai maka aiki, matsalar kawai ita ba a garin take ba, kuma tana buƙatar ta bincike dan ta jin yadda abun an ce mata texted and trusted ne. Ga Kuma Asim ya dame ta da maganar kullum, dan shi gani yake kamar da biyu tayi haka.


Yau wake ta dafa da shinka (rice and beans) ta saka mai da taji, daman yana cikin favorite na ta, amman Asim duk lokacin data dafa sai ya riƙa ƙin ci yana ganin kamar tana haka ne dan karta kashi kuɗi da yawa tayi musu abinci mai kyau.
Shi yanzu har ya matso jikinsa ya koma.yadda yake ya fara fita neman kuɗi, dan ya ayyana a ransa kuɗinta zai ranta ya fara sana'ar, har hango kansa yake ya zama wani Alhaji.


Kullum firar da ita kenan, yau bayan ya gama complaint ɗin baya son wake, ya ɗasa mata firar idan yayi kuɗi, ba aza a ƙara cin wake a gidansa ba.


Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda idom Asim ya bude haka.


“Asim kenan. Idan ma zaka yi roƙon baka cewa Allah ya baka halalinka, kawai dai kai kayi kuɗi”


“Wallahi sai na yi kuɗi Namra, Wallahi Wallahi sai nayi kuɗi, kawai naji sauƙi ne”


»“Ban ce ba zaka yi kuɗi ba, Amman yana da kyau ka riƙa cewa Inshallah kuma ka riƙa roƙon halak, saboda gudun sherin zuciya, idan Allah ya rubuta zaka yi kuɗi zaka yi ko da kuwa kama kwance gida ne sai sun tararda kai, saboda an riga an rubuta zaka yi kuɗin sai dai idan kayi gajin haƙuri zaka iya samun ta hanyar da be kamata ba”


“Namra kina bani mamaki, ke yanzu da ba dan kuɗi ba iyayen ki ai ba zasu wulaƙanta ni ba”


“Wulaƙanci kamar ya?”


“Wulaƙanci ne mana, saboda an mai dani talaka wanda ba shi da amfani shiyasa aka saka miki wannan robar ba tare da sanina ba”


“Ba haka bane, kawai matsala ce ta taso kuma likitan yace dole ne nayi planning”


“To Allah ya kyauta, amman ko ma minene ai nafi kowa kusanci da ke, taya za'ayi ki yi min haka”


“Asim matsala ce fa kai yanzu kana son na samu ciki ya zo ya zube ko kuma nayi ta wahala?”


“Hmm kina dai ganin kamar ba zan iya hidama dake ba ke da abunda zaki haifa shiyasa kuka ɗauki wannan matakin”


Ta aje kofin ruwan dake hannunta


“Ba zan ɗauki halin nan naka ba Asim, babu yadda zaka riƙa cin zarafina dana iyayena, kullum mune marar mutumci a idonka, duk abunda muka maka baka gani, na sadaukar da yawa Asim, har inda be kamata na sadaukar ba na sadaukar amman baka gani”


Kamar mai jira sai kawai yayi cikinta da masifa.


“Me kika min ke da iyayenki? Me kika sadaukar min? Ran ki? Ko lafiyarki? Kullum da kin tadhi magana kin sadaukar kin sadaukar tun da na aure ki me na ƙara shi in ɓa tsiya ba? Ɗan abunda na tara dik ya ƙara na zo na kwanta a asibiti jiyan babu wani ɗan'uwanki da ya ɗauki wani abu ya ba ni, an so na mutu ban mutu ba shine yanzu zaki fara buɗe min wani babin na rayuwa, kina da kuɗi a jikin ki amman saboda baƙin ciki ba zaki fitar aci ba sai dai a mutu? To Wallahi Asim ikon Allah ne, duk wani mai son ganin bayana sai dai ni naga bayansa”


“Magana kake irin wannan zancen kamar mai magana da maƙiyansa, maitarka ta kasa ɓoyuwa har sai ta fito fili? Kuɗina sana'ah zan yi da abu na, dan ba zan zauna kullum ni ce biyar dangi a bani ba, kuma Allah be ɗora min alhakin ciyar da kai ba, ni aka ce ka ciyar ka tufatar, yanzu ka fito a siffar ka sak Asim daman dan dukiyar gidan mu ka aure ni ko, amman sai ka nuna mik baka son komai sai ni, ashe zagon ƙasa kake min ka ɗauki halin samarin zamani ka ɗorawa kan ka, masu auren jari...”


Wani irin mahaukacin mari ya kifa mata ya rufe ta da duka kamar ma dukan namiji.
Shuri yake aika mata ta ko'ina tana cigaba da dukan jikinta kamar ƴarsa.


Dukanta yayi sai da yaji ya daki iya kalaman data faɗa masa sannan ya sassauta mata ya miƙe tsaye yana ɗingishi.


“Kuma Wallahi kije aci miki wannan robar ko kuma wallahi na lahira ya fiki jindaɗi”


A fusace ya juya ya bar ɗakin. Kuka tayi har ta gode Allah sannan ta tashi zaune tana cigaba da hawaye.
Sai ynz take tabbatar da tayi kuskuren aure, ta auri mutumen da be san darajarta ba, mutumen da be san kowa ba sai kansa. Daman haka halin Asim yake abu kaɗan sai duka.


Ta share hawayenta dan itama kanta tasan ba kuka bane abunda take buƙata, sam Asim be cancanci hawayenta ba, a yanxu ta san wa take aure dole ne kuma ta shirya zama da shi. Bata da buƙatar kokawa kowa damuwarta ita ya kamata ta gyara zaman aurenta da kanta.
Ta tatsu iya tatsuwa dan haka yanzu ba zata sake bari guminta ya zuba akan Asim ba.




ASIM POV.


Ta ƙarfen dake hannunsa yana dafawa ya fito gate, sai huci yake kamar wani zaki.
Yau ji yake kamar ace ya rumtse ya bude ya gansa yayi kuɗi, ta yadda zai jidaɗin rayuwarsa. Sai yanzu yake nadamar karatunsa daya bari daman can yayi tunanin ko zai samu wani abun a gurin iyayen Namra shiyasa ya baro garin su da ita ta yadda nan zai ta cin karensa ba babbaka sai yayi ta aikata tana samu matsa kuɗi, amman yanzu ya fahimci itama maƙetaciya ce kuma bata sonsa da alheri.
Gashi yanzu ko sana'ah zai yi yasan ba zai samu kuɗi a tashi ɗaya ba, amman idan yana da karatunsa zai iya samun babban aiki.


“Mtssssss aiko karatun na yi ba aiki zan samu ba tun da nigeriyar sai da gata, su kuma waɗannan iyayen nata matsiyata ne ba aiki za su samomin ba, aiko wallahi duk wahalar da zan sha tare da ƴar su zan shata, sai na yi kuɗi tana ganin zata huta kawai na aikata gidan su.
Har ni za'ayi ma mugunta, ai ko sai na yi muku baƙin ciki dan haihuwa yanzu za a fara”


Ya ƙarasa maganar yana kallon Mardiya data doso gurin tana takawa a hankali. Tun daga kan ƙafafunta yake kallonta har zuwa fuskarta.
Shi dai kam yana son farar mace ko ba komai farar mace ko kallonta kawai kayi zata burgeka kuma zakaji kana son ta.
Tsaɓanin Namra da take black beauty, wace yake ganim a yanzu she's not his type, sai dai duk da haka ya ƙudiri aniyar sai ya kai ga jikin cos he need someone near him.
Ba zai je ya kashe kanshi da desires ba, weather blood ɗin ya tsaya mata ko be tsaya ba babu ruwansa yau zai yi yadda yake so da ita.


“Ina wuni”


Mardiya ta gaisheshi cikin ƙirsa da kisinsina. Shi kuma ya amsa mata a far'ah har kunne.


“Lafiya ƙalau Mardiya ya gida”


“Lafiya ƙalau ya jikin na ka?”


“Alhamdulillah”


“Allah ƙara sauƙi”


“Amin na gode”


Da kallo ya bita har ta ɓace masa da gani sannan ya dawo hanyyacin yana yaba kyauwon surarta a zuciyarsa.




KALSOOM POV.


Ita kanta yanzu ta rasa gane kanta balle Hilal da yanzu ya saka mata ido, dan duk ta barkace masa abu kaɗan masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
Da gangan zata ƙi masa girki ko kuma tasa shi gaba tayi masa kuka, bayan be mata komai ba. Tun daga lokacin ya fahimcin akwai abunda yake cikin matarsa, daman can sha'anin ɓacewar cikin nan nata ya bashi mamaki, ga kuma jinin daya ƙi tsaya mata wajen wata huɗu kenan, babu irin maganin da be bata ba amman abun be tsaya ba, tun yana ganin abun kamar wasa har ya fara tsorota da lamarin.

Ita kanta tasan yanzu wannan jinin ya wuce haila ko zubar ciki ya zama na rashin lafiya, kuma ta san hukunci mai jinin rashin lafiya.
Shi kuma jinin rashin lafiya, jini ne da yake zuba ba a lokacin al'ada ba, daga wata jijiya da ake kira da azil. Al'amarin wanda take wannan jinin yana da rikitarwa, saboda kama da jinin haila yake. Idan mace ta zanto jini yana zuba daga gareta jo yaushe, ko kuma a mafi yawan lokaci wanenen zata ɗauka jinin haila da na rashin lafiya? Domin ita mai jinin rashin lafiya hukunce mai tsarki na gareta, kuma irin wannan hukumci shine a gurin mace mai jinin planning irin wanda yake zuba idan anyi planning dan ya zama kamar jinin rashin lafiya.


*Hali na farko* Ta zanto tana da masaniyar kwanakin hailarta, kamin jinin rashin lafiya ya same ta. Misali idan tana jinin haila a kwana biyar ko takwas a farkon wata ko tsakiyarsa, watau tasan kwanakin hailarta da lokacinta. To ita wannan zata zauna gwargwadon kwanakin hailarta ta bar sallah da azumi ta bawa kanta hukunci mai haila. Idan kwanakin sun wuce sai haila sun wuce, sai tayi wanka tayi sallah ta ɗauki jinin da ya cigaba da zubar mata da zuba a matsayin jinin rashin lafiya. Dalili shine faɗin Annabi S. A. W, ga Ummu Habiba : ki zauna gwargwadon kwanakin da hailarki take tsare ki, sannan ki yi wanka ki yi sallah. Muslim ya ruwaito shi. Da kuma faɗarsa Annabi ga Fatima Bintu Abi Hubaish: Wannan jinin jijiya ne, ba haila ba ne. Idan hailarki ta zo sai ki. Bar sallah. Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.


Idan iyakar kwanakin hailarta ya zo kamar yadda bayani ya gabata, to wajibi ne a gareta tayi wanka. Kuma wanke gabanta domin ta gusar da abinda yake zuba yayinda ta zo yin kowace salla. Kuma tayi ƙunzugu da auduga (pad) ko abu mai kama da ita wanda zai hana kwararar jinin, sannan tayi alwala daga lokacin kowace salla saboda faɗin Annabi : Ta bar salla a cikin kwanakin hailarta, sannan ta yi wanka kuma ta yi alwala ga kowace salla. Abu Dawud da Ibn Maja da tirmizi ne suka ruwaito shi.




Hakan yasa Kalsoom ta cigaba da salla da duk sauran ibadarta, sai dai har gobe halinta be canja ba a kan Hilal idan yana cikin gidan ji take babu wanda tsana a duniya sai shi. Yara kuma abu kaɗan ta dake su, tun yana haƙuri har abun ya fara isarsa dan yanzu shi da ita basa shan inuwa ɗaya, akan yaransa.
Gashi Ezzah kullum uwarta ƙara hure mata kunne take tana koya abubuwan da take ganin kamar abun ƙwarai ne, bayan ita bata san tana lalata tarbiyar ƴarta bane kawai.
Duk ranar da ba makaranta zai kwashi yaransa ya kai su gidan Hajiyarsa. Hajiya ta lura da yanayin ɗanta damuwa ta bayyana a fuskarsa ga ramar dake jikinsa, yadda ma yake yawan kawo yaran akai-akai ta san ba lau ba.


“Wai likita akwai abunda yake damun ka ne?”


Ajiyar zuciya ya sauke, yana aje plate ɗin abincin da ke hannunsa.


“Wallahi Hajiya ni ban san matsalar, daga ina take ba ma, Kalsoom ce yanzu kwata-kwata na rasa ma gane kanta, indai ina gida bana da kwanciyar hankali, sai kuka zara riƙa min tana masifa”


“Me ya haɗa ku?”


“Ba abunda na haɗa mu haka kawai zata riƙa min masifa sai kuka, kin san cikinta ya ɓace”




“Ya ɓace kamar ya?”


“Jini kawai ta ga yana mata zuba, sai aka yi hoto aka ga babu cikin kwata-kwata a cikin ta, amman jinin har yau be tsaya mata ba, yau kusan wata huɗu kenan”


“Subhanallahi, me ya same ta haka ne?”


“Wallahi nima van sani ba? Na rasa gane kanta”


“Abun kamar lamarin iska shi kesa ciki ya ɓata, ko kuma sihiri”


“Sai maganar saki ta ke min, ita dai na rabu da ita na ta huta”


“Kasan me? Ka samu ƙwarya mai tsarki da za'afaran, sai a ruɓuta suratul Yasin da surar wa'ƙia da fatiha da ƙulhuwallahu ahad da ƙula'uzai da Ayatul kursiyu da kuma amanar rasulu har zuwa ƙarshe da suratul baƙara da ayar : ƙul-a-Allahu azine lakum am alallahi taftarun (10:59) to idan an rubuta sai a karya kummallo da shi idan ta sha sai ta samu dabino ajwah sai kayi mata tawada nan da Al-zaitul muraƙƙa sai ta cinye sauran kuma rubutun kuma ta shafe jikinta, da iKon Allah indai sihiri ne ko aljanu ko wane iri ne zai rabu da ita”


“Amman Hajiya irin wannan ai sai dai kisa waki ya rubuta mata a nan sai na kai mata ta sha”


“To zan nemi wanda zai rubuta mata inshallah, amman wannan ko Rashida ai zata iya ƙulle-ƙulle ganin ta ɓata zamanku”


Yayi ƴar dariya.


“Sai dai ko iska ne, amman ai Rashida bata da irin wannan halin”


“Hmmm Hilal ba a shedun mace, yanzu kasa ran tayi maka wannan abun?”


Yayi shiru yana nazarin maganar Hajiya.








[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: »»4»»»»»»8»»»»»»»»»




ABDOOL POV.


Ɓacin rai ne shimfiɗe a fuskarsa, idanunsa sun rine zuciyarsa har wani tafarfasa take saboda faɗan d Mai Martaba yake masa.
Har Mai Martaba yayi ya gama Abdool be ce uffan ba, dan yasan akan gaskiya yake faɗansa, kamar yadda Ummi take masa a kullum.


“Ƙanen ka Babana ƙanenka ace yayi aure har ya haihu kai ba kayi ba, kullum girma ƙara tunkararka yake amman baka ganewa, shekarun tafiya suke Babana yanzu da ace kana da mata da wannan abun zai faru da kai? Sai dai ka zauna a gida ta girka maka, ko mutuwa kayi ba mu da abunda zamu kalla mu tuna da kai sai hoton ka, ai ko mutuwa kayi ka bar mai maka addu'ah ka more, rashin auren nan naka yana damuna Babana, kuma kullum faɗa ake maka amman kamar ba'ayi”


Till now be ɗaga ido ya kalli Mai Martaba balle ta ce wani abu, shi kansa yana da buƙatar auren, sai dai matsalar bayan Namra be ga mace da ta kwanta masa ba, sannan be son ya auri mace da baya so gudun karya tauye mata wasu haƙoƙa nata, dan wanda yake so baya jin zata samu enough time nasa balle wacce baya so.


Hullar uniform ɗin dake jikinsa kawai yake taɓi yana sauke ajiyar zuciya.




“Ba na son cilasta maka auten wacce baka so, shiyasa nake ta ɗaga maka ƙafa ina baka lokaci, amman ka ƙi ka gane”


“Mai Martaba ka gafarce ni, ina nan ina ta addu'ah Allah ya bani matar da nake so”


“Allah ya baka, amman karka zarge ni da abuɓda zan maka nan gaba”


Har ya miƙe tsaye be kalli Mai Martaba ba, dan baya son Mai Martaba ya ga ɓacin ransa.

“Zan tafi, Allah ya ƙara maka lafiya”


“Yau ba za'ayi min fira ba kenan ko? Tun da nayi maka faɗa?”


Ya ɗan murmusa


“Ba haka bane, kana yawan faɗa min na kula da kai na, kuma yamma tayi i want to spend time with Ummi, dan gobe zan koma”


“Ai daman na san ita take ƙara goya maka baya kana fatali da maganar auren nan”


“Ba dan wani abu ba da sai na ce tama fika damuwa da lamarin auren nan”


“Kuma ba kayi komai a kai ba?”


“Zan yi inshallah, a ƙara min lokaci”


“Allah ya kiyaye hanya”


Ya ɗan risina kamar yadda yake masa.


“Na gode Mai Martaba”


Sannan ya juya ya nufi ƙofar fita, a bakin ƙofar ya tsaya ya saka Army shoes ɗinsa dake gurin sannan ya shiga cikin gidan sashen matan sarkin yayi musu sallama ya fito.


Kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya miƙawa mutanen dake zageye da motarsa, sannan ya shiga motarsa boys ɗinsa suka shiga wata motar already wasu na cikin motar sake gaba sai kawai suka kama hanyar gida.


Sai da ya fara shiga part ɗinsa yayi wanka ya canja tufafi sannan ya nufo part ɗin Ummi.
Sisters ɗinsa ya samu falon tare da friends ɗin su, cikin murna suka tarbesa, sai ya gaisa da Friends ɗin su sannan ya nufi ɗakin Ummi.


Zaune ya tararda ita ƙasan carpet hannunta riƙe da qur'ane tana karatu. Kusa da ita ya zauna yana sauraren ƙira'ar nata har sai da ta kai ƙarshen suratul Maryam sannan tayi addu'ah ta shafa, ta aje qur'ane a gefe ta cire gilashin idonta ta kalli ɗanta tana murmushi.


“Soja wuta soja”


Yayi dariya yana shafa dogon hancinsa.


“Uwar soja ma soja ce”


“So ya hanya?”


“Alhamdulillah”


“Ka ci abinci”


“Eh na ci tare da Mai martaba”


“Can ka fara biyawa kenan?”


“Eh kuma na sha faɗa akan mganar aure, Mai Martaba be gajiya”


Ummi tayi murmushi irun nasu na manya tana kallon ɗan nata cike da so da ƙauna.


“Kai ma ai baka gajiya da faɗan shiyasa kaƙi kayi auren ka huta, amman Abdool bana son kana cin abincin mutanen”


“Ummi ki daina zargin komai, yanzu ba kamar da bane, suna sona sosai”


“Ba lallai bane ka iya gane haka, ai maƙiyin ɓoye baya taɓa nuna maka baya son ka, kuma dik wanda ya ƙi ni to kai ma zai iya ƙin ka you have to be very careful”


“Na kan yi bismillah idan zan ci, kin san ko minene idan ka yi bismillah ba zai taɓa samun ka ba, kuma ina addu'o'i sosai musamman da safe, kuma kin san irin addu'o'in da nake musamman laƙada ja'akum wace idan aka karanta mutum ma ba zai mutu ranar ba, saboda tsananin tsarinta, idan har zaka mutu a ranar yo Allah ba zai baka ikon karantawa ba, ga a'uzu bikkalimattillahi”


“Hakan yana da kyau, nayi tunanin ko baka samun time ɗin addu'ah ne saboda aikin ka”


“Komai nauyin aikin na na kanyi sai dai ba dika ba, amman dai bana tashi ba tare da nayi addu'o'in tsari ba”


“Allah ya ƙara tsare ka”


“Amin ya rabb”


“Ina labarin yarinyar nan an sallame ta?”


“Ni na hana su sallame ta da tuni sun sallame dan taji sauƙi sosai”


“Ni abunda na ga yafi karka bar yarinyar nan ta koma cikin ƙazamar rayuwa, ya kamata kayi wani abu a a kai”


“I try my best naga ta koma gidan su amman ta ƙi, ta tsaya kai da fata ita ba zata koma gida ba, wai ji take kamar idan ta koma mutuwa za ta yi, ni kuma ban san abunda zan mata ba”


“Why not ta zauna da mu kamin hankalinta ya kwanta sai mu mai da gida gurin iyayenta”


“Kawai yarinyar bata kwanta min bane, ta taɓa zubar da ciki, kuma kin ga ta zauna da mutane ƴan iska kala kala, kar tazo ta ɓata mata tarbiyar Sisters na”


“Ba zata ɓata ba, sai dai su su gyara mata tarbiyanta, she deserved everything Abdool dik wanda ya sadaukar da ransa dan kana ya rayu ya cancanci komai a gare ka, a yanzu bata da gurin zuwa kuma idan har muka bar ta ta koma cikin wacan rayuwar kamar ba mu mata adalci ba, :sannan ka bincika an tabbatar maka da gaske guduwa tayi daga gidansu, ai ya kamata ace kayi wani abu akai na ganin kaima ka maida mata farinciki a zuciyarta ”


“Amman Ummi har yanzu babu tabbacin abunda yasa ta gudu”


“Ai kasan ita da iyayenta ba zasu fito su faɗawa duniya dalilinta na guduwa ba, ya zaka ji idan aka ce ɗaya daga cikin ƙannen ka ne? Put yourself in my shoes zaka ji irin abunda ko wane uba ko uwa take ji”


Ya sosa kansa yana miƙewa tsaye.


“I will think about it, lemme go and pray”


Daga haka yasa kai ya fice ɗakin.






RASHIDA POV.


Kusan kullum sai ta yi waya da malamin nan ko kuma nace boka, amman labari ɗaya yake bata, cewar Hilal da Rashida basa zaman lafiya, kuma har gobe jini na nan yana mata zuba.
Sai da ita bata da tabbacin hakan tun da bata ji wani motsi daga garesu ba, dan har yanzu bata ji ya saki Kalsoom ba, kuma Ezza tana yawan faɗa mata ita bata ganin suna faɗa har sai idan ta dake ta sannan Daddy ta yayi faɗa.
Izzah bata da labarin komai da yake faruwa tun da Hilal baya faɗa da Kalsoom a gaba idonta, ko lokacin da Rashida take gidan idan zai yi mata faɗa ba yayi a gaban idon yaransa gudun abunda zai je ya dawo. Balle kuma.Kalsoom da baya biye mata dan ta fahimci bata cikin hankalin kanta duba da yadda abubuwan da take masa a.yanzu abunda be tsammaci zata masa ba, kuma baya tunanin kishi ne da sai dai ta nuna

Please Login or Register in order to submit comment