Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.


“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”


Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.


*** *** ***


Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.


Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.


“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”


“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”


“Ko kuma kika sani ciki ba, daman ai na daɗe ina zarginki, duk mace da zata bada kanta ga wani namiji ba mutum ɗaya zata tsaya ba, waya sani ma ko mijinki ne ya ɗauko cutar ya saka miki ke kuma kika saka mana, ni ban san ƙaddararta kai ni mu'amala da ke ba”


“Ni bance ka zame min ƙaddara ba kai zaka ce na zame maka? Na rasa abubuwa da dama sanadin mu'alama da kai, ƴan'uwana sun guje ni, mijina ya sake ni, na rasa lafiya ta, da duk wani farinciki nawa sanadinka Bashir, duk kai ka jani ga wannan halaka”


“Ko kuma kika jani ba, da baki sake jikinki ba zan gani ne har na yi sha'awa? Idan baki yarda ba fyaɗe zan miki ne? Baki kiji na faɗa miki da zarar naje aka gwada jinina aka tabbatar ina ɗauke da wannan cutar kutu ce zata raba ni da ke...!”


Yana kaiwa nan ya doshi gurin motarsa. Ita kuwa ta raka shi da maganganu tana hawaye.


“Idan ka fasa kai ni kotu baka haifu ga uwarka da ubanka ba Bashir kai ba ɗan halak ba ne, azzalumi macuci wanda be ji kunya keta dokar Allah, sakarai mai neman Matar abokinsa Allah ya isa tsakanina da kai”


Sai ta ta kunna motarsa ya bar gidan sannan ta durƙushe a gurin tana kuka.


“Kaico na ni Rashida, ina ake siyar da farinciki ne na siya! Ina zan yi musanyar damuwa da kuka na samu sanyin zuciya! Mi na ma duniya haka ne? Miyasa suka ƙaddarori zasu taru a kai na ne? Allah na tuba ka yafe idan zunubi na ne yasa ni a wannan halin”


Kuka take sosai tana ji kamar ƙasa ta haɗiyeta ta mutu ta huta gaba ɗaya da wannan rayuwar. Ra rasa dalilin daya sa rayuwa take koya mata darussan da take ganin bata cancanci koyansu ba.






NAMRA POV.


Kai tsaye direban ya nufi gidan Mai Martaba kamar yadda Yarima ya umarce shi, horn ɗaya yayi aka buɗe musu gate, ɗayan part ɗin gidan ya nufa da su, sai ya faka daidai ƙofar part ɗin ya fito da sauri ya buɗe ma Abbah ƙofa.


“Ya ce akwai komai a ciki, idan akwai abunda kuke buƙata zaku min magana”


Kai kawai Abbah ya ɗaga masa ya nufi ƙofar. Anty Amarya ce ta amsa masa da to, Namra na riƙe da hannun Anty kanta kuma kwance saman kafaɗar Anty, har suka shiga falo, sanyin ac ne ya fara musu martabun, daga bisani ƙamshi ya biyo baya. Kai tsaye Abbah ya nufi wani ɗaki dake ɗayan ɓangare da wasu ɗakunan, yana shiga ya hango manya tufafi kala biyu saman gadon, sai kuma kayan bachi da ba a cire daga leda ba kala ɗaya, an ɗora takalmi da turare da hula mai kyau saman kayan, hakan ya tabbatar masa nan ne ɗakinsa, ɗan murmushi yayi kaɗan ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom.


Mamaki ya cika Namra da Anty Amarya lokacin kowa ya samu tufafin sajawa da kayan bachi saman gadonsa, bama kamar Namra da ta tarar har da pants da pad ya aje mata, ya akayi yasan bata sallah shine abunda ya fi tsaya mata a rai. Bathroom ta shiga, ta yi wanka, sannan ta shirya cikin kayan bachi masu kama da na maza, ta fito ta nufo falo. Anty Amarya da Abbah ta samu zaune a dinning suna cin abinci. Abbah ne ya fara ɗagowa ya kalleta, murmushin da ta gani a fuskarta yasa idonta cika da ƙwalla.


“Toh Sarkin kuka zaki fara ko?”


Cewar Anty Amarya fuskarta ɗauke da annuri, tana miƙawa Abbah tea da ta haɗa masa.


“Komai ya zo min kamar mafarki, gani nake kamar ba gaske bane, ban yi zaton Abbah zai saurare ni haka da wuri ba har ya yafe min, nasan nayi muku abubuwa marar kyau da yawa, amman duk da haka suka samu fili a zuciyarku kuka yafe min”


“Kin cancanci yafiya Mamana, saboda kin gane kuskurenki, sai dai kin shiga rigar mutane masu mutunci wanda hakan yasa kika samu yafiyata a kusa, sai dai ina fatar ba zaki ƙara aikata irin wannan kuskuren ba”


“Wallahi ba zan sake ba Abbah, na maka alƙawari har na koma ga mahallici na,ba zan sake aikata kwatankwacin wannan kuskuren ba”


“Allah yayi miki albarka”


“Amin Abbah na gode, i love you so much”


Ta zo da sauri ta rumgume shi tana kuka. Anty Amarya ta share hawayen idonta tana kallon Abbah.


“Allah ya saka maka da alheri, na gode”


“Yanzu ai ta kuka da ciwon zuciya ya ƙare ko?”


Cewar Abbah fuskarsa da murmushi yana kallon Anty Amarya cike da son Amaryarsa. Daga bisani ya kalli wayarsa da ke saman dinning tana ringing. Hajiya Barau ce rubuce a screem ɗin wayar. Miƙewa yayi tsaye, sannan ya kai hannu ya ɗauki wayar yana danna picking ya nufi bedroom.


A kujerar da ke kusa da Anty Namra ta zauna, tana share hawayen da suka ƙi tsaya mata.


“Na haɗa miki tea zaki sha?”


Ta gyaɗa kai.


“To ki zuba abincin ki ci idan kin gama zan haɗa miki”


“Bana jin yunwa Anty, tea kawai ya isa”


Ajiyar zuciya Anty ta sauke, ta shiga haɗa mata tea, tana faɗin.


“Namra duk kin rame kin koma wata iri, kin yi baƙi sosai, Yarima ya faɗa mana Asim ya sake ki ne saboda kina da ciki!”


Ta gyaɗa kai tana share hawaye.


“Kuma har yanzu be neme ni ba, ina gidansu Lamido cikin ya zube”


“Kin san ciki ba zai taɓa tsayawa a mahaifarki ba Namra saboda matsalar da kika samu, na yi mamaki ma da kika samu ciki bayan an saka miki roba”


“Shi yace sai na cire, kuma da ma samu cikin yace be shirya haihuwa yanzu ba, sai dai na zaɓa tsakanin cikin da shi, ni kuma na ƙi yarda na zubar shiyasa ya sake ni”


“Kin samu ƴancin kan ki yanzu, Allah zai bi miki haƙƙin ki. Amman ina kika haɗu da wannan yaron”


A nan Namra ta kwashe labarin komai na sanin da tayi ma Abdool ta faɗa ma Anty.


“Yana da mutunci sosai, kuma ina fatar zaki masa hallacci duk ranar da ya nemi ladan alherin da yayi miki”


“Kamar ya?”


Ta tambaya dan har ga Allah ita bata gane inda zancen Anty ya dosa ba. Anty ya miƙe tsaye tana murmushi.


“Kamar haka, ki je ki kwanta dare ya yi, zan kira Maryam na ce ta shirya zan vata mamaki, daman ta fi kowa damuwa da auren nan na ki”


“Na gode sosai Anty sai da safe”


Ta daɗe a gurin zaune sai ƙarewa falon kallo take sannan ta tashi ta nufi bedroom.
Har garin Allah ya waye, dan har yanzu ta kasa yarda da abunda ya faru, ganin komai take kamar mafarki. Idonta biyu aka yi kiran sallah asuba, unƙurawa ta yi ta tashi, sai ta nufi gurin maɓallin kutar ɗakin ta kunna. Ta shiga toilet ta tsabtace kanta sannan ta yi wanka ta fito.
Bata tsaya shafa mai ba, ta ɗauki abaya ta saka, sannan ta ɗora da hijab, gefen gado ta zauna sai ta ɗauki carbi tana lazimi, ba ita ta tashi ba sai bakwai da rabi saura, shi ma dan ta ji ana buga ƙofar falon ne.
Bata damu da tambayi ko waye ba kawai ta kai hannu ta buɗe ƙofar. Suna haɗa ido gabanta yayi mugun faɗuwa, da sauri ta sadda kanta ƙasa, shi kam ƙin sauke idonsa ƴayi har ta miƙa masa gaisuwa.


“Ina kwana?”


“Nan ba ina kwana suke cewa ba”


Ɗan murmushi ta yi wanda be kai zuci ba.


“An tashi lafiya?”


“Lafiya ƙalau, i hope you sleep well?”


“I did”


“Amman idonki ya nuna kamar ba ki yi bachi ba”


“Kana da buƙatar wani abun ne?”


Ta tambaya da nufin kawar da maganar. Wani dogon numfashi yaja ya sauke


“Ban sani ba ko kuna da bukata ne, yanzu zan kama hanya, Mai martaba ya kira ni yana da buƙatar gani na, ajima direba zai ɗauke ki zai kai ki a miki passport, da ƙarfe uku jirgi zai tashi, so za a muku duk wani abun da ya kamata, around nine za a kawo muku breakfast. I think Abbah suna bachi, ki faɗa musu na tafi”


Kai ra gyaɗa masa, sai ya zuba hannyensa aljihu ya juya zai wuce.


“Ab...da...llah”


Ta kira sunansa cikin wata irin siga da ba'a taɓa kiransa sunan yayi masa daɗi kamar yadda ita ɗin ta kira shi ba, har cikin zuciyarsa ya ji kiran nata da muryarta dake kamar zata fasa masa kuka. Juyowa yayi ya kalleta da manyan idanuwansa.


“Thank you”


Gira ɗaya ya ɗaga mata, alamar for?


“For helping me out”


Murmushi yayi mata mai fidda annurin fuskarsa.


“Safe flight”


“Wish you the same”


Murmushi yayi mata as respond ya juya ya cigaba da tafiya abunsa, kamar wanda baya son taka ƙasa. Haka kawai ta samu kanta da kasa ɗauke ido a kansa har sai da ya shige part ɗinsa.




ASIM POV.


Kallo Hajiya Sadiya ta bishi da shi, zuciyarta Allah-Allah ya amince.


“Miyasa zaki min tayi mai tsada akan kawai na auri ƴarki?”


“Saboda kai ne kaɗai na yarda da tarbiyarka, kuma nasan ƴata tana son ka, saboda ta nuna min hoton ka har tace zaka zo ka gaishe ni”


“Ko baki bani komai ba zan iya aurenta saboda aurenta na yi niyar yi, amman ki faɗa min gaskiyar abuda kike ɓoyewa wata ƙila zan iya taimakon ki”


“Ko da baka aureta ba, na yarda ka yi zina da ita, idan ta samu ciki sai ka rabu da ita”


“Miyasa sai ni?”


“Saboda ba zan iya facing yata na faɗa mata ta auri wanda bata so ba, kuma nasan ba zan saka ta aikata zina ba”


“Da baki yi gaggauwa ba, da aurin ƴarƙi zan yi, miyasa baki bar ni na aureta ba, iya ka kice min na turo iyayen Sai a ɗaura mana aure. Ki faɗa min gaskiya mana Hajiya”


“Zauna zan faɗa maka komai, saboda na yarda da kai kuma ina fatar zaka taimake ni”


Ya zauna yana fuskantar ta.


“Sunana Hajiya Sadiya kamar yadda ka sani, an haife ni a garin nan, amman ko da na tashi ban san iyayena ba, mahaifina da mahaifiyata duka Allah yayi musu rasuwar tun kamin na mallaki hankalin kai na, dan haka na tashi a gidan kakana Sarkin Katsina na wacan lokacin, na samu gata iya gata a gidan, duk da bani kaɗai bace wacce ake riƙo a gidan, amman saboda ni marainiyace, be yarda ya bar mu mun yi karatu a nan ba, a lokacin govnati na ɗaukar nauyin karatun saboda ana ƙyamar bokon ne, so duk wanda ke da ilmi za a ɗauki nauyinsa zuwa ƙasar waje karatu, Zuwaira da Murja da Sadiq su aka saka a ƙarƙashin govnati ni kuma shi ya biya min a cikin aljihunsa. Dukan mu mun yi karatu, duk da ba ƙasa ɗaya aka kai mu ba, dan ni na zaɓi London ne, su kuma Egypt aka kaisu suka yi karatun lafiya.


Na fi sawa shashanci gaba, saboda farar fatar da nake tare da su, na kan rakasu gurare daban-daban hakan yasa muka shaƙu da su sosai. Su san burina saboda ina yawan faɗa cewar nafi son nafi kowa ɗaukaka a makarantar nan, ranar sai wata take ce mun zata faɗa min wani sirri, zata kai ni inda za'a taimaka min na samu ilmin da ya fi na kowa, kuma na fi kowa ɗaukaka a makarantar. Ban yi musu ba, na biyeta ta sani a cikin wata ƙungiya, ashe ƙungiyar asirice, buƙatata ta biya tabbas, saboda a wannan shekarar ni nayi ta ɗaya a duk faɗin makarantar, daga haka sai abubuwa suka buɗe, duk abunda nake da bukata zan je ne kawai na faɗa kuma sai buƙata ta biya, a lokacin muna meet duk ƙarshen wata, amman lokacin dana ƙare karatun na dawo nan sai suka haɗi ni da manyan da suke abuja, a nan naga manyan mutane, maza da mata a cikin har da manyan ƙasar nan. Duk lokacin da za'ayi meeting ɗin, na kan bar Katsina na je abuja da sunan ganin wata Sister mu ƴar sarki, sai naje meeting idan an gama da kwana biyu na sai na dawo.


Na samu babban aiki a lokacin, nama fi kowa kuɗi a gidan mu, da haka na haɗu da baban su Nabila. Bayan mun yi aure yace baya son aiki, sai na haƙura, a nan su kuma suka soma saka min ƙa'idojin da ban san da su ba a wacan lokacin.


Sun ce min dole ne na riƙa neman mata ƴan'uwana, idan ba haka ba, ba su yarda na fitar da zakka ba. A dole na ɗauki ka'idar mu'amala da mata ƴan'uwana, tun ban saba ba har abun ya zame min jiki, ya koma bana jin daɗi mu'amala da mijina sai mata. Daga baya kuma suka ce suna son a riƙa kawo musu sabbin membobi saboda tsofin ciki suna mutuwa ne, kuma ina son a riƙa yaɗa abun.
A abuja nake zaune da mijina, ɗan haka duk lokacin da naso zuwa kawai nake gurin meeting ɗin ba tare da ya sani ba, wata rana da muka yi meeting sai suka ce suna da buƙatar na Sadaukar musu wani daga cikin iyalaina, ba ni da zaɓi dole na bada mijina, sai ya samu haɗarin mota ya mutu, daga nan kuma sai babban ɗa na, sai mai binsa, sannu-sannu suka cinye min duka ƴaƴana, Nabila ce kawai ta rage min. Shekaran jiya da nace maka zanje birnin keebi ba can naje ba, Abuja na je, gurin meeting ɗin. Yanzu kuma Nabila suke so, ko ɗanta. Ni ko da na bada ita ƙara na bayarda kai na, shiyasa nake son ka taimake ni, ka ceci rayuwata da ta ƴata saboda ita kaɗai ta rage min”


Asim ya sake miƙewa tsaye a karo na biyu.


“Wallahi Allah yana so na, wato da yanzu sai dai ki bada ni? Dan nasan zasu ma iya cewa ki kawo yaron gidanki, ko kuma idan mun yi aure ace ko bada surikin ƴar ki, ai ni duk sun kuɗi na be kai na iya rayuwata ba kuma ni daga yau na barki har a bada wallahi”


“Kar kayi saurin yanke hukuncin Asim kaje ka yi tunani”


“Ba wani tunani da zan yi, salon ki sani cikin mugun hali”


“Da ina da niyar saka ka da na saka tun farkon dana saka tun farko dana fahimci kana da son kuɗi, amman ba kai nake target ba matarka, saboda nasan idan na sata cikin ƙungiyar zasu biya kuɗi mai yawa wata ƙila ma ya iya zama fansar ƴata, amman sai gashi ka saki matarka, da yanzu ace zaka iya kawo min matarka zasu iya ɗaga min ƙafa”


Tsayawa yayi kallonta.


“Indai har Namra zata iya zana fansar ƴarki to zan iya kawo miki ita, bisa sharaɗin zaki bani naira billion uku”


“Wallahi zan baka, kuɗi ba matsala ta bace idan na faɗa maka abunda na tara sai ka haukace, kuma Namra ba kasheta zamu yi ba Wallahi, cikin ƙungiyar kawai za mu sakata”


“Amman taya zan kawo miki ita?”


“Zaka maida aurenka, sannan duk abunda zai biyo baya ya biyo, kuma idan kana so zaka iya auren Nabila”


“Ƴarki kam na yafe, amman Namra zaki sameta kamar yadda kike buƙata”


Ta miƙe tsaye ta shiga ɗakinta bata jima.ba ta fito riƙe da amt ta miƙa masa.


“Akwai milion talatin a ciki kayi amfani da su”


Ya miƙa hannu ya karɓa sannan ya juya ya fice.




TEEMA POV.

Tana kwance saman jikinsa, shi kuma sai faman dannar waya yake yana murmushi. Azatonta dan tana shafa jikinsa yake murmushi, shi kam hankalinsa gaba ɗaya ya tafi kan waya sai faman chating yake da Kalsoom.
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya sannan ya kashe datarsa ya kalleta.


“Bari na leƙa office”


“Okay Allah ya tsare min kai”


“Amin dear. Amm anjima Hajiya tace zata aiko da su Ezzah”


Sam bata ji daɗi ba, duk da tasan dalilinsu aka auro ta, amman bata yarda ta nuna masa ba.


“Kai Amman ko na jidaɗi daman ina ta jiran su zo, Allah kawo su lafiya”


“Amin”


Ya faɗa yana ɗaukar hulal dake saman hannu kujera ya saka a kai.


“Okay I love you”


“Love you too”


Da kallo ta bishi sai da ya fice sannan ta miƙe tsaye.


“Sati uku da aure ace za a ɗauko yara a kawo maka, nifa ba bautarsu na zo yi ba, ko amarci ban gama ci ba za'a haɗa ni da ala ƙai ƙai, yara zaggan-zaggan da su, su riƙa sa maka ido idan ka yi ma miji wani abu, mtsssss”


Taja wani uban tsaki ta wuce bedroom ɗinta. Bata jima ba ta fito ta nufi kitchen, girki ta ɗora sai mita take ranta duk a ɓace, dan har ga Allah bata so a kawo su yanzu ba.


“Daman fa ance wasu uwayen miji ba son suruka suke ba, in banda sheri kin san ina Amarya ɗan Amarcin ma ba za'a bari na yi ba, kai kayi naka lokacin sai kace wani ba zai yi ba, nasan dan su aka auro ni amman ai a bari na ci lokacina, tun da can ba saman ƙaya suke ba, daga zuwanka da ƙurciya zaka fara aikin ƴaƴan kishiya”


Kamar mai faɗa da wani haka ta riƙa zuba surutanta har ta yi girkin ta gama mita take, sai da tasa komai a muhallinsa sannan ta shiga ciki ta yi wanka. Tana fitowa ta shirya cikin yellow atamfa, ta kashe ɗauri ta feshe jikinta da turare sannan ta fito falo ta zauna.


Tana jin tsayawar mota ta ƙara gyara ɗaurin ɗankwalinta, tana zaton ko Hilal sai kawai ta ji mota ta tashi, su Ezzah sun turo ƙofa sun shigo fuskarsu da far'ah bakinsu kuma ƙumshe da sallama.


Ciki-ciki ta amsa musu tana murmushin da be kai zuci ba.


“Maraba da ƴaƴana”


“Momi ina wuni? Momi ina wuni?”


“Lafiya ƙalau”


Sai suka zauna saman kujera. Daga nan bata sake bi ta kansu ba, sai da ta ji motar Hilal sannan ta tashi ta koma tsakiyarsu ta zauna ta jasu jikinta ta rumgume tana murmushi.


“Ku bani labarin Hajiya...”




ABDOOL POV.


Around ten ya sauka Katsina, sai da ya fara biyawa Mai Martaba ya ganshi sannan ya wuce gurin Ummi. Da murmushi ya shiga part ɗin Ummi, kamar yasan ita kaɗaice a falon, dan duk ƙannensa sun tafi makaranta.


“Ummi barka da safe”


Ya taɓe baki tana kallonsa.


“Ni ban ga amfanin wannan hutu naka ba, kullum kai ne yawo ba zama gida, yanzu da aure kake yi wace mace ce zata ɗauki wannan rayuwar”


Kusa da ita ya zauna yana dariya.


“To ai gurin matar na je, yau zan baki labarin komai saboda na samu mafitar matsala ta, amman fa nasha wuya but at the end yau tace min Thank you”


“Kana nan kana wahalar da ƴar mutane ai dole wata ta saka cin kwakwa, tun da ka tagi Amirar nan kuka take, na rasa gane kanta idan kuma na tambaye ta sai tace babu komai, yau ma ce min tayi gida zata je daker na hana ta”


“Ina take?”


“Tana ɗakinta”


Ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin Amal. Yana tura ƙofar ɗakin ta ɗago ta kalleshi sai kuma ta juya,


“Amira can we talk?”


“Maybe Later i need some space”


Ta faɗa da muryarta ta kuka.


“Okay but i just want you to know that i care for you, if you need someone to talk to, i'm downstairs”


Daga haka ya juya ya fice. Ita kuma. Ta fashe da kuka.




*78*


Kusa da Ummi ya sake zama yana kallon tv.


“Tana son ta saka kanta cikin matsala ne kawai Ummi amman tasan ba zan taɓa son ta ba”


“Nasan tana son ka har zuciyarta, amman sam ban yarda da yarinyar nan ba, mutanen da sukayi ƙoƙarin su kashe ka, waya sani ko plan ne aka yi ta yadda idan ta aure ka zata fin jindaɗin kashe ka”


Yayi murmushin gefen baki.


“Ko babu plan Ummi bana son ta, ko da kuwa tun can farko ita mai tarbiya ce, because if i love someone i mean it no matter what she did or whoever she is, and if i said i do i do, so i don't love Amira, i only fell in love once because i have never been in that kind of situation, but when it comes to Namra i take it so serious, and i love with all my heart and blood and mind and soul i love her more than you think Ummi”


Ajiyar zuciya Ummi ta sauke, ta kalli ɗanta fuskarta da alamun damuwa.


“Tell me more about her”


Miƙewa ya yi tsaye ya nufi freezer.


“She's so simple and kind, but difficult to handle. You know when we first meet, she slap me and insult me in front of my boys, but i can't slap her back”


Ya ƙarasa yana bulbula ruwan da ya fiddo a cup. Ummi ta yi murmushi.


“I know how my son is ba ya faɗa da mata”


“Yap bana faɗa da mata because we are not in the same level, strength, brain, heart, soul and lot. Ban taɓa jin ina son wata mace ba, but lokacin da na ji ina son Namra, nasan our souls mean to be, duk da a lokacin na san tana da aure, amman zuciya ta kasa haƙura, and now what! Her husband divorce her ta je wani gida ta zauna, kuma ƙaddara ta sake haɗa mu kaduna na kaɗe yaron gidan ina zuwa sai gata a gidan, hmm' mmm funny, and now ni ne silar shiryawa da iyayenta, i hope you love her too?”


“Of course i love her ai dole naso matar da ɗa na yake so, but i'm just worried about Mai Martba, ba lalle ne shi ya so ta”


“Why”


“Saboda Bazawara ce! And i hear that Mai Martaba and Hajiya Shafa sun maka mata”


“What...!”


Ya aje cup ɗin ruwa dake hannunsa saman dinning yana kallonta fuskarsa cike da tashin hankali.


“How true it's?”


“Mai Martaba ya kira ni da kan shi, yana neman shawara akan zai ɗoraka a Sarautar Katsina, da na nuna masa be dace ba sai ya nuna ɓacin ransa, the following day ya sake kira a waya ya faɗa min Hajiya Shafa tace be kamata a ɗoraka a Saurata baka tare da iyalaiba, dan haka ta maka mata, zata aura maka Zaliha ƙanwarta, idan anyi auren da watanni sai a baka Sarautar, kuma Mai Martaba yayi na'am da hakan”


“Miyasa baki faɗa musu ina da wacce nake so ba?”


“Idan na faɗa zai ga kamar ina kare ka ne, amman ina son ka min wani abu Abdallah, duk yadda Mai Martaba zai yi karka yarda ka karɓi Sarautar nan, kai ne ɗa na uku a gurin shi, be kamata ya tsallake su ba, ya ɗauki Sarauta ya baka, nasan yana son ka, amman hakan ba zai jawo maka komai ba sai ƙiyayya da ganin laifi, kai kuma ka yi ƙanƙanta da irin rayuwar nan, kuma idan har

Please Login or Register in order to submit comment