Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ita za a zarga tun da anga shigarta gidan gashi Maryam ta haɗu da ita, hakan yasa ta fashe da kuka zuciyarta na raya mata lallai asirinta na daf da tonuwa.
Haka ta wuni ta kwana da tunanin abunda ze samu Namra, gashi kukan yaƙi ya tsaya mata, ta takure kanta a ɗaki, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin inda zata samawa kanta mafita, dan ji take kamar wani zai faru da Namra, tun da batayi dai-dai ba, kuma ba makawa ita za a zarga. Ji take duk ta tsani kanta, zuciyarta na raya mata ta gudu kawai kamin asirinta ya tonu.




MARYAM POV.


Daga Makaranta ta wuce gidan iyayen Asim. Cikin ladabi tayi sallama ta shiga. Sai Mahaifiyarsa ta amsa mata dan ita kaɗaice yau a gidan. Har ƙasa Maryam ta risina ta gaishe ta. Ta ta ɗan kawarda fuskarta dan ta gane ƙanwar Namra ce tun da sun taɓa zuwa tare da ita.


“Lafiya ƙalau”


“Dan Allah ko Asim na nan?”


“Baya nan yayarki ta zo nan na faɗa mata baya nan, ni ma ban san inda yake ba”


Daga nan sai Maryam ta canja salo.


“Kin san inda yake kam, dan babu yadda za'ayi ace uwa kamar ki bata san inda ɗanta yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai bar gida yaje nesa ba tare daya faɗa miki ba”


“Au toh ko ƙarya zan miki, macuta maciya amana, bayan kun gama cin moriyar ɗana sannan zaku watsa masa ƙasa a ido, yanzu dan munafurci ne za ku wani zo nemansa kamar ya ci bashin ku?”


“Bashin mu yaci mana, yaje ya ɗaukewa ƴar'uwata hankali ta haukace tace shi take so, yace ta kawo shi a aura mata, shine kuma dan rainin hankali zaki ce baki san inda yake ba, Wallahi sai kin nemo shi duk inda yake ko kuma naje na faɗawa Abbah yasa a kulle ku dake da danginki har sai Asim ɗin ya dawo, dan ba zaku sa muna ƴar'uwa a matsala ba”


“Eh ai zamu iya, tun da ku ƴan siyasa ne ku keda gwannati, amman bari kiji na faɗa miki ni ɗana ba zai aure ƴar marasa mutucin ba”


Maryam ta matso kusa da ita tana zare ido.


“Ooo.... Uwata ce marar mutunci ko?”


“Ni ban ce ba, salon kije ki ƙulla min ƙullaliya, Toh ta Allah ba taki ba”


“Ni dai na faɗa Wallahi ko ki nemo inda ɗanki yake ko kuma duk abunda ya faru dake ke kika ja”


Mahaifiyar Asim ta nuna Maryam da yatsa.


“Ke wannan da ganin ki ba zaki gama lafiya ba”


Maryam ta tuma ta dire.


“Ƙwarai ba zan gama lafiya saboda da kika hallice ni ai baki yi dan na gama lafiya ba, ta yadda idan an je lahira zaki jidaɗin ƙoneni a wuta ko? Ai ke cw ba zaki gama lafiya ba tsohuwa dake kina ƙarya baki san inda ɗan ki yake ba ko kunya baki ji ba”


Ta daki ƙirji.


“Ke ni kike faɗawa wannan maganar?”


“An faɗa ɗin, biri ai a hannun malami ya kan yi guɗa, a hannun bamaguje sai kuka, kuma Wallahi ko ki nemo ɗanƙi ko ki shiga a matsala”


A nan Maryam ta tofar mata da yawu ta wuce, tana bankaɗar mutanen da suka fara cika gidan gurin kallon faɗa.




_____________________________________


Me kuke tunanin ze faru a shafi na gaba?


Anya Asim zai dawo? Da gaske Mahaifiyar Asim bata san inda yake ba?
Ya rayuwar Amira da Uzair akan kuskuren da sukayi? Me zai faru da Namra?


Masu ziyarta shafina, a ƙasan blog ɗin zaku ga gurin subscribe, a nan zaku saka email address ɗin ku ta yadda da nayi sabon updated zaku samu notification, na kan fara sauke post ɗina a can kamin na kawo shi whatsapp.


Ina son ku duka fisabilliah 😘
Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa-14.html


🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


*PAGE - 14*


Sai da aka kwana biyu sannan Maryam ta labarta ma Anty Amarya da Namra yadda suka yi da Maman Asim.
Ran Anty Amarya ya ɓace sosai, daga ita har Namra basu jidaɗin abunda Maryam tayi ba.


“Ke ke Maryam ba wata ba, Allah ya sauwaƙe miki bakin mutane, kullum ana miki magana amman kamar ba'a yi, rashin kunya an faɗa miki abun ƙwarai ne? Ai gashi nan baki mutane akan ki Wallahi Allah ya sauwaƙe miki wannan rayuwa”


Maryam ta ɓata rai sosai, daman tasan za'a rina dan tasan sai Anty Amarya tayi mata faɗa, tun da bata taɓa yaba ma masifar ta ba.
Anty Amarya kam sai harararta take tana jin kamar ta dake ta.


“Aure dai zakiyi kuma mace kike Wallahi ki canja rayuwa dan baki san inda zaki faɗa ba”


“Naji Anty yi haƙuri kin san ni yarinya ce har yanzu”


Namra tayi mata wani kallo


“Kece yarinyar?”


Sai kawai tasa dariya ita da Aisha. Anty Amarya ta ɗauke kai tana amsa sallamar da Ammy tayi.
Cikin tashin hankali ta doso inda Anty Amarya take gyalenta ma a bai-bai ta yafashi.


“Hajiya Amina lafiya na ganki haka?”


Ta zauna saman kujera tana kuka.


“Wallahi ba lafiya ba, Amira ce tun jiya ba mu ganta ba, ba musan inda take ba”


Gaban Namra da Anty Amarya ya faɗi. Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Shine abunda yake fitowa a bakin su. Namra tace


“Amman an bincika ko ina? Kuma bata ga inda zata ba?”


“Bata ce ba, tun ranar data fita tace min nan zata zo inda kike ban sake sata a ido ba sai da safe, ko na na shiga ta tarar tana ta kuka wai kanta ke mata ciwo, sai ce min take tana jin tsoro, na bata magani ta sha sai tayi bachi, ko da na sake leƙawa ɗakin na dubata sai naga bata ciki, na duba ban ga jakarta ba da wayarta, sai na ɗauka ko tazo nan ne, har dare shiru, sai da Abbah ta ya dawo muka yi ta nemanta ba mu ganta ba idan an kira wayarta kuma kashe, haka muka kwana cikin tashin hankali”


Da kuka sosai ta ƙarasa maganar. Sai hawaye suka silalo daga idon Namra a take ta fasa kuka. Anty Amarya tace


“Wallahi rabonta da gidan nan tun shekaran jiya ranar laraba, ban sake sata a ido ba, Allah ya a gaji wannan yarinya ko ina ta shiga?”


Namra ta share hawayen idonta


“Ammy baku mata komai ba? Ba faɗa tayi da wani ba? Kuma babu wanda yayi mata sallama ko da a waje?”


“Wallahi bamu mata komai ba, kuma ni dai ban san wani yayi mata sallama ba, amman dai Babanta ya kai ma ƴan sanda report ko Allah ze sa a gane inda take, amman ke Namra baki san inda Amira zata iya zuwa ba?”


“Wallahi ban sani ba, ranar ma data bar gidan nan naga kamar anyi mata saƙo sai tace min wai kece ba kida lafiya bari tafi gida, washen garin ranar ne ma nace Maryam taje ta duba ki, sai tace min ai sun haɗu da Amira tace mata kin ji sauki”


“Wallahi ni ban yi wani ciwo ba lafiya ta ƙalau, na shiga uku yau ina Amira ta shiga?”


Da kuka ta tashi ta nufi ƙofa. Anty Amarya na bata haƙura har gurin har gurin gate.
Lokacin data dawo ne Hajiya Barau ta tare ta tana tambayar lafiya. Itama salati tasa lokacin tada ji abunda ya faru, suna cikin maganar sai ga Namra ta fito sanye Hijab tana hawaye.
Tana ƙarasowa kusa da su Anty Amarya tace


“Namra ina zaki ?”


“Anty zama be gan ni ba, tun da Amira ta ɓata”


Hajiya Barau ta riƙota


“Wallahi babu inda zaki, kije nemanta kema a ɗauke ki, ko kin manta abunda ya faru ne? Allah dai yasa ba Asim ɗin ne ya sace ba itama”


Namra tayi saurin girgiza kai.


“Wallahi Hajiya ba shi bane, Asim ba ze haka ba, Asim ma baya garin nan gaba ɗaya”


“Uhmm Aifa sai kiyi kuma, irin abunda aka miki ne za a mata, Inshallah mutun ɗaya ne yake muku wannan abun”


“Wallahi ba wanda zuciyarki take zargi bane, Asim baya garin nan”


“Toh a ina yake?”


Hajiya ta tambaya tana mata wani makirin kallo.


“Nima ban sani ba, amman dai ba shi bane”


Anty Amarya ta kasa mata tsawa


“Ai sai ki tsaya nan kina gardama da uwarki akan abunda baki da tabbaci, wuce ki koma ciki babu inda zaki je”


Ba dan taso ba, ta juya ta koma ciki tana kuka. Anty Amarya ta rufa mata baya tana ta mata faɗa wai tana gardama da Hajiya kamar ma uwarta.


Hajiya Barau ta tsire baki ta shige part ɗinta zuciyarta na raya mata Namra ta san inda Amira take.
Bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki waya ta kira Uzair tana labarta masa abunda ya faru. Ya kaɗu matuƙa shi kansa ya kwana biyu yana kiran wayar Amira amman baya samu. Sai dai wani ɓangaren hankalinshi ya kwanta ganin kamar asirin kan Amira ya koma ba kansa ba.
Bayan ya gama waya da Hajiya ya kira Najeeb ya labarta masa ɓatan Amira.


“Kaga abunda nake faɗa maka ko? Ai daman nacw maka aikin ba akan ka ze dawo ba akan Amira ze koma”


“Ban sani ba ko nawa na nan tafe Najeeb, amman ina cikin tashin hankali”


“Ka kwantar da hankalinka babu abunda ze faru, amman kuma ka rufe wannan maganar”


“Ya za'ayi ma an faɗa, Allah dai ya sauwaƙe, Ni wallahi ba zan sake irin wannan abun ba”


Najeeb yasa dariya.


“Uzair ka cika tsoro da yawa, shiyasa ka yi sake har waɗannan abubuwan suka faru”


“Ni dai naji”


Daga haka ya kashe wayar, ya nufi ɗakin matarsa.


Hajiya na gama waya da Uzair sai ta kira wata ƙawarta wace take taubashiyar Ammy. Bugu ɗaya zuwa huɗu ta ɗauka.


“Assalamu Alaikum”


“Wa'alaikissalam Hajiya yanzu nake labarin ki, nace ko kina da labarin abun da ya faru?”


“Wallahi bani da labari sai yanzu nake jin abunda ya faru, shima fa dan Ammy tazo da kanta ne dan Wallahi sam ni Amarya bata faɗa min ba”


“Au kina nufin sai yanzu kika ji?”


“Wallahi sai yanzu shiyasa ma nakira ki, Namra ta ɗaki ƙasa ta rantse ita ba Asim bane ya sace Amira”


“Wanene Asim kuma?”


“Ina wani tsohon Saurayin Namra wanda na taɓa baki labari nace miki mahaifinta ya mata miji amman tacw bata so sai shi ko kin manta?”


“A'a na tuna ɗan makarantar su ko?”


“Allah ya bar ki, shi ne fa, toh ai kinsan shine ya sace Namra kwanakin baya har shiyasa ma mijin da zai aureta yace ya fasa”


“Ke ya sace fa kika ce?”


“Wallahi ya sace ko kuma ta bishi ba, kuma kinga ita Amira ta faɗa tace shine yazo ya tafi da Namra ɗin kuma duk nan mutane unguwa sun shedi haka dan sunce sunji lokacin da yake magana, har fa iskanci yayi da ita”


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un toh wai ko sha ya sace Amirar?”


“Nima dai shi nake zargi, kuma magana ta gaskiya Namra tasan inda Amira take saboda tasan inda shi Asim ɗin yake, saboda ɗazu take take ƙoƙarin kare shi wai baya garin nan me me magana babu kai babu gindi”


“Amman wannan magana ai bata kyalewa bace, indai har haka ne dole ne a nemi Namra ɗin kuma ita da kanta Ammy tace min Namra ce mutum na ƙarshe da Amira ta gani”


“Ai ke dai bari ƙawayen zamani ai sai a hankali, Allah dai ya bayyana ta”


“Amin bari na kira Ammy yanzu”


Hajiya Barau tayi saurin cewa.


“Dan Allah karki ce gare ni kika ji, kinsan halin Alhaji balle kuma baka kake iko da gida ba, sai ace kayi ma ɗan kishi shaeri”


“Haba dai Hajiya sai kace wata ƙaramar yarinya da zanje nace ke kika faɗa? Ai babu wannan tsakanin mu”


“Toh na gode sai na jiki”


Daga haka ta kashe wayar.




KALSOOM POV.


Kwata-kwata Hilal be yi zuwa huɗu ba Daddy yace ya turo iyayensa. Shi kuma daman haka yake son yaji, satin daya zagawo iyayen Hilal suka neman auren Kalsoom, farin ciki gurin mahaifiyar Hilal kamar ta zuba ruwa ƙasa ta sha.
Iyayen basu bar gurin ba har sai da Daddy da ƴan'uwansa suka yanka musu sadakinta dubu saba'in suka biya sai Daddy yasa musu rana dan ba so yake aja abun da nisa ba, shirin da biyar ga watan huɗu. Cikin farinciki da jindaɗi suka bar gidan.


A ranar Rashida bata yi bachi ba saboda baƙinciki, kwana tayi kuka Hilal na rarrashinta. Washen garin ranar da akayi abun Kalsoom taje aiki sai suka riƙa taya ta murna suna ce mata amarya. Tayi mamakin inda suka samu labarin tun dai ita ban da ƙawarta Salma bata san ta faɗawa kowa ba, da Momy tace mata ƙara kawai mutane suji za'a ɗaura mata aure.


Sai daga baya suka faɗa mata ai Asma'u ce ta faɗa musu. Kalsoom ta kalli Asma'u tana dariya


“Asmee ina kika ji?”


“Abun sheri ma be ɓoyu ba balle na alheri”


“Ni ina mamakin ta ina kika ji”


“Ai tuni ni na sani dan har a wayar mijin naga hoton ki, ido na sa miki dan naga indan zaki faɗa”


Sai duk suka sa dariya. Suka mata barka da Allah yasa alheri.
Bayan ta wuce office ɗin ta Asmee ta bita tana zolayarta


“Amaryar mu amarya mu”


Kalsoom ta ɗora jakarta saman tebur tana dariya.


“Wai daman Hilal ɗan'uwan ku ne?”


“A'a unkuwar mu ɗaya dai da shi, kuma mijina abokin shi ne”


“Allah sarki ke haka unguwarku daya ba”


“Amman Wallahi kin yi dacen miji, gaskiya Hilal yana da mutunci sosai, gashi bawon mata sai yadda kika yi dashi, matarsa ma ba daɗinta yake ji ba amman sai juya shi take”


“Kin san matarsa kenan?”


“Sosai ma, amman wallahi ƴar banza ce sai kin shirya zama da ita hmmm amman aje aikinki zakiyi ko?”


“Haka yace wai baya son aiki”


“Ai saboda aikin matarsa zai ƙara aure dan ya son ya hanata aiki amman ba dama”


“Saboda me?”


“Ai ma'aikaciyar banki ce ƴar gidan su Dr. Ayuba matsayi, kin san ai ƴaƴan gidan ba daga baya ba, haka ake cewa wai aba a musu kishiya, uwarsu ma duk masifar Uban sai tun da ya aure mui”


Ta ƙarasa tana shafa baki. Ganin yadda Kalsoom ke kallonta yasa ta tsargu sai ta tashi daga saman kujerar da take zaune tana dariya tace


“Bari na koma gurin zamana kar MD ya tararda ni a nan ina tsiyaya”


Nan ma Kalsoom murmushi kawai tayi. Sai ta nufi ƙofa tana faɗin


“Mu dai ayi auren nan da wuri aje ayi mana rainon ƴan ɗiyan mu, Allah ya sanya alheri”


Da Amin Kalsoom ta amsa ta bita da kallo tana nazarin maganganunta.




NAMRA POV.


Wuni Namra tayi addu'ah tana ba Allah cigiyar inda Amira take. Duk hankalinta ya tashi ji take kamar ita ce ta ɓata, abu ɗaya zuciyarta ke ayyana mata wato Uzair, sai dai ta kan tambayi kanta da kanta ma zai haɗa alaƙa tsakanin Uzair da Amira.


Kiran da taji Maryam tana mata yasa ta tashi daga saman sallayar da take ta nufi falo.
Tsatsaye ta tararda su Anty Amarya da wasu police biyu mata tsaye a falo. Gaban Namra ya faɗi, da sauri ta ƙaraso kusa da su.


“Lafiya?”


Sai ɗaya daga cikin ƴan sandar ta nuna mata id cart ɗinta.


“From Marna Police station, Muna zargin da a hannu gurin kidnapping ɗin Amira, abokan aikin mu suna waje, zamu je da ke a station”


Ba shiri Namra ta daki ƙirgi tana nuna kanta.


“Ni....?”


Da sauri Maryam ta nufi part ɗin Abbah tana kuka. Anty Amarya ma kuka take ita da Aisha. Kamar an jefo Hajiya Barau sai gata cikin ɗakin tana salati da sallami.




____________________________________


THERE WORDS FOR THIS CHAPTER...!
WHAT DO YOU EXPECT NEXT?
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 😘💖🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa12.html


🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


NOT EDITED ⚠️


*PAGE - 15*


Suna fitowa waje Abbah na kawowa. Sai ya tsayar da ƴan sanda yana tambayarsu.


“Miya faru haka?”


“Sir muna tuhumar Namra ne da sa hannu a gurin sace Amira”


Abbah yayi ma Namra wani kallo. Sannan ya kalli ƴan sanda yace


“Ɗaya daga cikin ku zata biyo ni muje cikin motana”


Ba su musa masa ba, ɗaya daga cikin police ɗin ta bi Abbah suka shiga mota ita da Namra baya, Anty Amarya a front seat.
In banda kuka babu abunda Namra take har aka isa station ɗin. Sannan Abbah ya fita suka shiga cikin station ɗin. Ammy da ƙanwarta na tsaye a gurin idonta A kumbure.
A take wani police ya karanto masa abunda ake zargin Namra da shi, sannan yayi musu jaga zuwa office ɗin dpo. Sai da ya gama da wasu cases sannan ya su Namra suka iso gurin ya gaisa da Abbah cikin mutumci yana girmama shi.


“Ranka ya daɗe Ashe kai ne”


“Nine Wallahi ya aiki ya kwana biyu”


Abbah ya faɗa ba dan ya waye shi, sai dai shi ɗin yasan Abbah kasancewarshi sanannen ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa.


Bayan Abbah ya zauna, Namra ta zauna a kujera dake kusa da Abbah, sai Ammy ta zauna a kujarar dake gefen Namra ita da ƙanwarta.
DPO ya kalli ya dubi takarda take gabansa ya kalli Namra yace


“Amm Namra Usman ana zargin ki dasa hannu gurin ɓatan ƙawarki Amira...”


Kasa magana Namra tayi sai kuka take. Abbah ya katsa mata tsawa.


“Ki buɗe baki kiyi magana mana”


Sai kawai ta ƙara rushewa da kuka kamar zata tsuƙe. Anty Amarya tace


“Taya zata iya magana? Bayan irin ƙazafin da aka mata, a rasa wanda za'a zarga sai ita, lokacin da Namra ta ɓata miyasa bamu zargi Amira ba, ko ita Namra ba ƴa bace? Ko kuma ni ban san zafin ta ba? Faɗa min ɗa ya fi ɗa ne? Wallahi Allah sai ya saka mata shikenan dan anga yarinya bata magana komai aka kwaso sai a dire a kanta, dan kin rikice akan neman ƴarki sai ki ɗauka ki ɗorawa wani, me kuke da shi da har Namra zata sa a ɗauke Amira, wallahi ke kinsan Namra ta fi ƙarfin Amira nesa ba kusa ba...”


Dpo ya miƙe tsaye yana ɗaga ma Anty Amarya hannu.


“Dan Allah Hajiya ki saurara, an zo nan dan a sasanta ba dan faɗa ba”


Bayan ya zauna ya kalli Namra yace


“Ki kwantar da hankalin ki ba wani za'a miki ba, nan guri ne na...”


Ƙwanƙwasa ƙofar da akayi ne ya hana Dpo ƙarasa maganarsa.


“Yes come in”


Wani ɗan sanda ne ya shigo ya sare masa sannan yace


“Sir Alhaji Haruna is here to see you”


“Let him in”


“Yes Sir”


Ya sake sare masa sannan ya juya ya fice. Sai ga Abbah Amira ya shigo cikin ɓacin rai, idonsa be sauka ko ina ba sai akan Ammy, nunata yayi da yatsa.


“Amman Wallahi Asiya baki jin magana, yanzu duk maganar da na miki baki ji ba, sai da kika aikata? Yanzu miye amfanin haka? Ki zubar da kanki mutuncin kawai”


Ya ƙarasa yana miƙawa dpo hannu suka gaisa.


“Wannan maganar bata ma kamata ta fito bakin ki ba, dpo ban kawo maka rahoton ɓatan yarinyar nan ba? Babu inda ban kai rahoton nan ba”


Dpo ya ɗaga masa kai yana murmushi. Abban Amira ya miƙa Abbah hannu suka gaisa


“Alhaji Usman, yau dai mun yi zumunci dole, mata sun haɗa mu”


Abbah yayi dariya.


“Kasan sha'anin mata sai haƙuri, ba tunani suke ba idan zasu yi abu”


“Wallahi basa tunani yanzu miye amfanin wannan abun? Yanzu haka sai da aka kira ni daga gwuiwa station aka ce min ance anga Amira a tashar mota amman basu san motar data shiga ba”


Ammy ta fashe da kuka.


“Wallahi babu abunda ze sa Amira ta gudu tun da ba wani abu muka mata ba”


“Toh aljana ce aka gani kenan? Ko kuma ƙarya suke, tashi ki wuce gida bana son maganganun banza”


Cewar Alhaji Haruna Abban Amira. Abbah yace


“Karka ga laifin ta duk haka muke fama dasu inda mata ne sai haƙuri”


“Magana ce da bata da toshe balle makama ban san inda ma wannan maganar ta fito ba”


Cikim kuka tace Ammy tace.


“Hajiya Barau ce ta faɗa kuma ai ba zata yi ƙarya ba”


Abban Amira ya nuna ta da hannu yana kallon Abbah.


“Kaji ko? Jita-jita ne kawai”


Abbah yayi shiru yana motsa baki alamar nazari. Alhaji Haruna ya kalli Ammy da Ƙanwarta yace


“Ku tashi muke gida”


Da kuka Ammy ta tashi ta fice, sannan ya kalli dpo ya ciro wasu ƴan kudaɗe a aljihunsa ya aje gaban teburin dpo


“Dan Allah aka kashe maganar nan dpo, matsala ta cikin gida ayi haƙuri”


“Ba matsala, muma ai mun fi son haka”


Tare da Abbah suka fito. Anty Amarya na riƙe da Namra har suka fito harabar station ɗin. Sun ɗan daɗe suna fira da Alhaji Haruna sannan sukayi sallama cikin mutunci ya wuce Abbah kuma ya nufi Motarsa.
Har Abbah ya iso gida Anty Amarya masifa take, tana kiran Hajiya Barau da munafuka.


“Ai itama ta haifi ƴaƴa mata, zata jidaɗi idan aka mata haka? Me Namra ta tare mata ne? Ai Wallahi duk mace data ɗuka ta haifi mace tace wata macen ba zata jidaɗi ba sai Allah ya gwada mata akan ƴaƴanta”


Sai da Abbah yayi parking sannan ya kalli Anty Amarya yace


“Bana son ƙananan maganganu, ki wuce part ɗin ki ki bar ni da ita kawai”


Bata sake cewa komai ba, dan tasan halin Abbah zai iya juyarda faɗan akanta. Sai kawai ta buɗe ta fita ita da Namra suka nufi part ɗinta Abbah kuma ya nufi part ɗin Hajiya Barau.


Tana ganin Abbah hankalinta yayi mugun tashin, kamar tasan asirinta ya tono, ko da yake ta karanci yanayinsa shiyasa zuciyarta ta ayyana mata lallai akwai laifin da tayi masa.


Abbah be kula jikokinta da suke falon ba ya hauta da faɗa, daman haka yake idan ya tashi matsifa babu ruwanshi da wanda yake zaune. Ta inda Hajiya barau take shiga bata nan take fita ba, tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta kai ga fasa kuka tana faɗin


“Ni Wallahi ba da wata niya nayi ba, kuma tun da daɗewa mukayi wannan maganar fa”


“Ni dai na faɗa miki, ki iya bakin ki ko kuma duk abunda ya same ki ke kika ja, Namra dai kin kusa jikanya da ita, dan haka ba dai-dai bane ki zauna kina faɗan mugaye kalamai akan ƴarki”


Kuka take sosai tana faɗar wai ƙazafi aka mata, har jikokinta suka dafata suna bata haƙuri. Sannan Abbah ya tashi ya nufi part ɗinsa.


Namra na kwance jikin Anty Amarya tana sauke ajiyar zuciya Maryam tace


“Wallahi Allah sai ya saka miki daga Ammy har tsohuwar makirar can Hajiya”


Anty Amarya ta katsa mata tsawa.


“Ke matar uwanki zaki cewa makira ko dan darajar tsufanta kya ce mata haka, balle tana auren uban? Kin gani ina ja miki kunne akan rashin kunyar nan kina ƙarawa ko? Wallahi kika kai ni ƙul sai na ɓata miki rai”


Miƙewa tayi tsaye cikin fushi ta miƙawa Namra takardar dake hannunta.


“Ke ni dai karɓi, Asim ya zo baki nan yace a baki”


Da sauri Namra ta ɗago ta kai hannu ta karɓi takardar, sai ta share hawayenta ta tashi ta nufi ɗakinta, zuciyarta cike da zazzanar son sanin abunda takardar ta ƙumsa.




__________________________


Wannan shafi na ƴan TASKAR KHADEEJA CANDY ne, da CLASSIC LADIES, tare da NAMRA FANS GROUP. I really appreciate your comments 💖💖💖
https://chat.whatsapp.com/LHd6gwdQQWZKNeHU9z4qf0


Masu tambayan grp ga link nan. Amman ban da maza ❌


🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


NOT EDITED ⚠️




*PAGE - 16*


Natsuwa tayi sosai ta tattara dukan hankalinta ta mai da gurin takardar, sannan ta buɗe ta soma karantawa.


_SALAM_
MY DEAR NAMRA.


Na zo gidan ku ance min baki nan, na kira wayarki ban samu ba, mahaifiyata kuma ta shaida min kina nema ma, ban san ta yadda zan iya ganin ki ba amman ga sabon number waya na ki kira ni dan Allah.


Urs ASIM.


Wani dogon ajiyar zuciya ta sauke, ta rumgume takardar a ƙirjinta ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta ɗauki daƙiƙa goma zuwa shabiyar kamin ta buɗe idon, ta tashi ta nufi ɗakin Maryam.
Dariya ta tararda Maryam na ƙyalƙyala kamar wata sabuwar mahaukaciya,

Please Login or Register in order to submit comment