Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Teema ta fara gabatar masa da Rashida sannan ta fara faɗa masa matsalolinta da kuma abunda ke tafe da ita. Kai ya girgiza ya sake girgizawa sannan ya shiga duba ƙasar, can ya ɗago ya kalli Rashida ya ce.


“Wato ni bana ɓoye komai, magana ta gaskiya ƙasa ta bada bayanin ba zaki taɓa komawa gidan mijin ki ba”


Rashida ta daki ƙirji.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Sai hawaye ya fara bin fuskarta. Teema ta nuna damuwa sosai.


“Malam ko dai ƙasar bata ba da bayani dai-dai ba ne? Dan Allah a sake bincikawa”


“Ai babu wani bincike, ni ba zan cuce ku ba, kun ga idan wani ne sai ya nuna muku kamar aiki zai ci ya riƙa cin kuɗin ku”


Miƙewa Rashida ta yi tsaye tana hawaye


“Teema tashi mu je”


Kamin Teema ta tashi har Rashida ta kai ƙofar gida.


“Zan kira ka Malam”


Teema ta faɗa tana aje mishi kuɗi masu ɗan dama gabansa. A tsakar gidan ma Teema ce ta yi musu sallama da godiya, ko da ta fito waje har Rashida ta yi ma motar key ita kawai take jira.
Wani mahaukacin gudu Rashida ta fara, kamar marar hankali, har sai da Teema ta riƙa ta.


“Idan har kw baki son kan ki ni ai ina son ki, be kamata kina wannan gudun ba, yawancin bokayen nan ƙarya suke faɗa fa, ki bari zamu je wani gurin”


Uffan Rashida bata ce cewa Teema ba har suka isa ƙofar gidansu Teema.


“Idan Hankalin ki ya kwanta ki kira ni zan kai ki wani gurin”


Sai ta buɗe motar ta fita. Rashida ta fi ƙarfin minti goma a gurin tana kukan sannan ta kaɗa motarta ta yi gaba.




ASIM POV.


“Nice House”


Ya faɗa yana ƙarewa gidan kallo, hannu Nably tasa taja hancinsa.


“Gida zaka yaba ba ni ba?”


“Ke ai babu kalmomin da zan iya amfani da su na ya be ki da su, amman gida ko akwai kalmomi da zan yabe shi da shi”


Ɗan murmushi ta yi, tana ƙara kallon harabar gidan.


“Momi na ta so ta gaisa da kai, sai dai tafiyar gaggauwa ta kama ta yau, amman gobe dole ne ka dawo, dan momi ta ga wanda nake yawan bata labari”


Ya kai hannunsa ya riƙo nata.


“Wato gulma na kike?”


“Ba wani gulma, ba kai ba ne ka sace mata zuciyar ƴa ba”


“Ko kuma ƴarta ta sace zuciyar wani ba”


Cikin wasa ta kai masa duka, shi kuma ya goce yana mata wani kallo, tuni idonsa har sun soma canjawa. Yar yar daya fara jin jikinsa na yi ne yasa ya saki hannunta yana faɗin


“Bari ma zo ma tafi na wuni a gidan na ku ai”


“Wato har ka gaji da gani na kenan?”


“Kai ni har na isa, kawai dai naga magariba tana gabatowa ne, ai kin ga dole jibi naje na kai ki birthday ɗin friend ɗin ta ki, kuma mu zaga gari”


“Ai gobe ne”


Ya buɗe ido.


“Tab aiko dai gobe tafiya za mu yi da oga na, ban da haka kan wallahi babu abunda zai hana ni kai ki ko ina ne a faɗin duniyar nan”


Ta wara ido.


“Kar ka damu, nima ai ban cika son kaje ba gudun kar wata ƙwace min kai”


Sai da aka soma kiran sallah, sannan ya tashi, ta rakoshi har gurin motarsa, ta buɗe masa, har zai shiga sai kuma a juyo ya kalleta ya ce


“Haka zan je ba good bye?”


Murmushi ta yi ta juya ta juyo, kamar mai nuna masa mazaunanta, daman jikinta babu mayafi, sai kawai ta kai masa kiss a baki.


“Shikenan?”


Ya ɗaga mata kai yana wani shegen murmushi. Sannan ya shiga motarsa tana ɗaga masa hannu har ya bar gidan.


“Wow wayayiyace sosai, i'm so lucky”


Abunda ya furta kenan yana ƙarawa motarsa giya. Be tsaya ko ina ba sai da isa unguwarsu, a lokacin har an sauko daga sallar magariba, sai da ya shiga gida yayi wanka sannan ya fito a masallacin unguwar yaje ya yi alwala ya yi sallah, sannan ya koma cikin gidan ya ɗauki motarsa ya ƙarasa ƙofar gidansu Mardiya.


Ko da ya kirata yace yana kofar gidansu, bata cikin gidan, dan haka sai da ya jirata har na tsawon mintuna talati sannan ya ta iso gurin da saurinta. Ta kanta ta buɗe motar ta shiga tana masa sallama.


“Ya gida ya su Mama?”


“Wallahi lafiya ƙalau, ya naka gidan?”


“Gida na babu daɗi fa”


“Subhannalla miya same ka?”


“Kin san na zama gwauro yanzu, tun da kin kore min Namra”


Mardiya ta riƙe baki kamar gaske.


“Wai da gaske ne da ake cewa Namra ta fita?”


“Ba ki sani ba? Kuma saboda ke ta bar gidan?”


“Saboda ni kuma?”


“Eh dan ta gano ina son ki, shine ta so na sake ta ni kuma na ƙi na sake ta, shine sai ta tafiyarta”


“Kai amman ban jidaɗi ba, kaje ka dawo da ita dan Allah”


“Ni yanzu ba ta ita nake ba ta ki na ke”


“Ni kuma?”


“Eh mana, ni fa tsakani da Allah na ke son ki, kuma auren ki zan yi, shine abunda ya kawo ni yanzu, na baki kwana biyu ki je ki yi shawara”


“Amman Namra ba zata ce komai ba?”


“Ke kike ta kanta, ga wannan ni zan wuce, dan gobe zan yi tafiya yau nake son na fara shiri na”


Ya miƙa mata dubu goma, ƴan ɗari biyar-biyar. Ƙin karɓa ta yi har sai da ya matsa mata sannan ta karɓa tana masa godiya, ta buɗe mota ta fita.




KALSOOM POV.


Be barta ta yi aikin komai ba, shi ya haɗa musu abun kari, kuma ya haɗa musu ruwan wanka. Daman ita ta gaji sosai, tun da ta yi sallah asuba ta koma bachi, shi kuma ganin hakan yasa be tashe ba, ya barta ta yi bachinta, har ta gaji ta tashi dan kanta, sannan ya shigo ɗakin fuskarsa da Annuri.


“Tun ɗazu breakfast yake jiran ki”


Ya faɗa yana zama kusa da ita. Agogon ɗakin ta kalla ta ga sha ɗaya har da kwata.


“Kai ya aka yi nayi bachi haka?”


“Kin gaji ne, shiyasa ban tashe ki ba”


“Amman kai ka karya ko?”


A maimakon ya amsa mata sai kawai ya sakar mata ido yana kallonta, fuskarsa da mirmushi. Ɗan sunkuyar da kai ta yi itama tana maida masa da saƙon murmushin.


“Amarya ta”


Ya faɗa, tana mai cigaba da kallonta.


“Amaryar ka tana nan zuwa, ni kuma na zama uwargida a yanzu”


Murmushi yayi mai sauti, dan yaga kishinsa a cikin idonta.


“Ai ba gida ɗaya zaku zauna ba, kuma ita zata zauna da yara ne, that's means ke ce Amaryar”


Kai ta girgiza tana dariya, kamin ta mike tsaye.


“Bari na je na wanki bakina”


“Lemme help you”


Ya miƙe tsaye shi ma suka shiga banɗakin tare.




NAMRA POV.


Tun da ta shige ɗakin, bata fitowa sai idan fitsari zata yi ko shan ruwa, duk ta bi ta damu kanta, ta takura kanta. Duk yadda Neina ta so ta fito waje su yi fira sai ta ƙi, haka ta wuni da yunwarta daman can ba abinci take ci ba, sai Maltinar da Lamido yake badawa ana siyo mata, yau kuma ko maltinar ta ƙi ta sha.


Bayan sallame sallar isha'i yaro ya shigo, da sallama yana riƙe da kwanonsa ya bara yace


“Sallamu alaikum wai ance ana sallama da Namra, wai Abdullahi ne daga Katsina”


Tana cikin ɗaki ne, amman hakan be hanata jin abunda almajirin ya faɗa ba, sai kawai ta lumshe ido tana sauraren tsaran da kanta ke mata.


‘Wannan wane irin mutum ne?’


Ta tambaye kanta, tambayar da bata da amsa.


“Je ka ce bata nan”


Cewar Lamido zuciyarsa har wani kawowa take.


“A'a kai je ka ce gata nan zuwa”


Yaron na ficewa Neina ta kalli Lamido ta ɗora da


“Saboda girman Allah ka rufa mana asiri, muna neman abunda za mu ci ka jefa mu cikin wani halin kuma”


“Amman Neina tun da bata so ai ba ci aka ana cilasta ba”


Cikin yaren fulatancin ta mayar masa da amsa.


“Lamido babu ruwanka baka san yadda abun nan yake ba, kai dai ka cinto gefen tiri baka san tsakanin su ba, ka kama kan ka, ɗan Sarki ne fa”


Tana gama faɗar hakan ta nufi ɗakin da Namra take.


“Namra tashi kije yana kiran ki”


“Ni babu inda zan je”


Ɗukawa Neina tayi kamar zata zauna ta haɗe hannayenta.


“Ki yi ma girman Allah ki rufa mana asiri kije, haba Namra kar ki ba ni kunya mana na faɗa masa ga ki nan zuwa, dan Allah ki tashi ki je”


“Neina ko naje mi zan ce masa? Ni na riga na faɗa masa karya sake dawowa ƙofar gidan mu”


“Wallahi ban ce ki faɗa masa komai ba, saurarasa zaki yi, ki rufa mana asiri Namra”


Magiya Neina ta riƙa yi ma Namra kamar zata fasa mata kuka, sannan Namra ta tashi cikin ɓacin rai da zafin zuciyata ta fita.
Gurin da ya tsaya ɗazun a nan ya sake tsayuwa, duk da dare ne hakan be hana farin wata haskar fatar jikinsa ba, ga manyan idonsa da ya tsare ta da su har take ƙoƙarin faɗuwa kamin ta ƙaraso kusa da shi. Kasa furta masa komai ta yi, duk wasu kalamai da take da unƙurin faɗa masa sai ta kasa, suka tsaya mata iya cikin cikinta zuwa maƙogaronta, dan bakinta ƙin bata haɗin kai ya yi, ga ƙamshin turarensa da ke ta kaiwa hancinta hari.
Hannayensa dake rumgume aƙirjinsa ya cire ya maida cikin aljihu.


“Bude ba ki kiyi magana, faɗa min duk kalmar da kike tunanin ta cancanta a da ni, ki yi duk abunda kike ganin idan kin min saki samu salama.
Ayau na tsayu gabanki ne saboda kawai na ji tarihin rayuwarki, ban je neman auren ki, amman nasa a min bincike akan ki, tsakanin jiya zuwa yau labarin ki da hawayen ki sun nuna min akwai abunda kike boyewa”


Hawaye ta fara, tana ƙoƙarin ture kalamansa dake son su yi tasiri a zuciyarta.


“Ba lallai ne na cimma burina akan ki ba, mman lallai ne na faranta miki rai, kuma na taimaka miki ki cimma na ki burin, ina roƙon ki ki bani kaɗan daga tarihin rayuwarki ko zan samu sukunin rayuwa, Namra ni ba ƙaramin mutun ba ne, kuma ba wasa ya kawo ni nan ba, ki taimaka min wata ƙila ni ne silal farin cikin ki”


Ɗaga kai ta yi ta kalleshi.


“Ta ya farinciki zai dawo ga yarinyar da ta butulcewa iyayenta? Taya farinciki zai dawo ga macen data zaɓi saurayinta sama da iyayenta? Faɗa min ta ya?”


Yayi shiru yana karantar kalamanta. Yawun bakinta ta haɗiye.


“Ba kowa ba ce ni, fa ce wacce ta butulcewa iyayenta, da zabi saurayinta sama da su, wanda shi ne ya kai ni ga hakala.......”


Ƙoƙarin tsagaita kukanta take, dan ta samu damar labarta masa tarihin rayuwarta ko zai samu salamar rabuwa da ita. Zagayawa yayi ya buɗe bayan motarsa ya ɗauko carpet ya shimfiɗa mata. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna nesa da ita zuciyarsa cike da tsumayin jin labarin nata.
Sai da ta share hawayenta, sannan ta soma bashi tarihin rayuwarta...




[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *73*


Idonsa sun kaɗe sosai sun yi ja, duk ɗigar hawayenta ɗaya sai ya ji kamar an watsa masa ruwan zafi, ya kasa ɗauke kansa daga barin kallonta, har cikin ransa yake jin kukanta da kuma zubar hawayenta, samun kansa yayi da mugun tausayinta.
Ita kuma ta rumgume ƙafafunta sai kuka take, ba ƙaƙƙautawa.


Handkerchief ya riƙo daga aljihunsa ya aje mata, ba tare da ya ce da ita komai ba. Hannu ta kai ta ɗauka ta share hawayenta sannan ta fyace majina.


“Kin yi kuskuren zabar saurayinki sama da iyayen ki. Shiyasa Allah ya jarrabe ki, bayan Ubangiji babu wanda ya cancanci girmamawa sama da iyayenki”


Ɗagowa tayi ta kalleshi idonta taf da hawaye.


“Amman wanda mahaifina yake son na aura ba cancance ni ba...”


Ya tari numfashinta.


“Amman ai ya baki damar fitar da wanda kika so, sai kika nace sai shi saboda kar ya ce kin yaudareshi, ko ba haka kika faɗa min ba yanzu?”


Ta yi shiru tana sauraren hawayen dake bin fuskarta.


“Daga ƙarshe sai kuma ya yaudare ki, ya ci amanar ki, da ace kin aure wanda mahaifin ki yake so, babu yadda za a ayi ya guje ki, wata ƙila sanadiyar hakan sai ya shiryu, kuma duk abunda yayi miki dole su ne da laifi ba ke ba, baki san fushin Ubanguji yana tare da fushin iyaye ba? Idan iyayen ki sun yarda da ke, to haka shi ma Allah ya yarda da ke, kin yi aure mahaifinki yana fushi da ke taya za ki ga ribar auren?


Kin yi kuskuren rashin komawa gida Namra, ko yanka namanki za su yi su dafa su ci, bai kamata ki dawo nan ki tare ba”


“Idan kuma suka ƙi karɓa ta fa? Mahaifina ya ce karna kuskura na dawo gidansa da sunan saki ko yaji”


“Komai ya ce miki haka ne, saboda yana cikin fushi ne, da kin koma ai ba zai iya korar ki ba, idan kuma har idonsa ya rufe ya kore ki, to duniya zata miki masauki, su kuma ta juya musu baya, jama'ar gari kuma su zage su, har sai shi da kansa ya koma neman ki”


Ta bikita ɗaƴan ɓangaren na handkerchief ya share majiyar data cika mata hanci.


“Na yi nadama yanzu, na gane gaskiya”


“Kin yi nadama a lokacin da bata da amfani, kin sake tafka kuskure a cikin kuskure. Namra ba mutum kika aura ba, mutum mutume ne mai kama da mutum, siffarsa da kamarsa tasa kika ɗauka mutum ne, har kika masa inuwa, shi kuma ya saka ki a rana, mutumen da bai shirya haɗa zuri'ah da ke ba, amman Namra da yanzu a ace m cikin ki yana nan, a nan za ki zauna ki haihu kenan? Ba tare da kin koma gurin iyayen ko ba?”


Miƙewa ta yi tsaye ta yi tsaye ya saka takalminta, da zimmar komawa cikin gidan. Sai shi ma ya miƙe tsaye.


“Can i have my handkerchief!”


Juyowa ta yi ta kalli handkerchief ɗin, sannan ta kalleshi.


“Yayi ƙazanta”


Ya faɗa cikin muryarta mai gaf da yin kuka.


“Please...”


Ya ɗaga mata gira ɗaya, like he's serious. Ta ɗan ɗauki mintuna kamar mai shawarar miƙa masa abunda yake mallakinsa na ne.


“Please stop cry..”


Ya faɗa cikin muryarsa mai rawa kamar mai shirin yin kuka. Sai kawai ta miƙa masa handkerchief ɗin cike da ƙyama. Shi kuma ya miƙa hannu ya karɓa idonsa na kan fuskarta. Bata tsaya komai ba ta shigerwa tana ƙirƙirar wani sabon kuka.
Damƙe handkerchief ɗin yayi da dukan no ƙarfinsa, kamar abunda za a ƙwace masa, ya kai fuskarsa ya lumshe ido.


Har cikin zuciyarsa yake jin sanyin hawayenta, ya samu mintuna biyu zuwa uku a haka kamin ya buɗe motarsa ya shiga. Still da handkerchief ɗin a hannunsa yake driving.


“Da kin auri wanda Mahaifin ki yake so wata ƙila da ba mu haɗu ba, da ba zan iya kawowa rayuwarki ɗauki ba”


Ya faɗa yana mai sa ɗayan hannunsa ya fiddo wayarsa, sai da ya hau babban titi sannan ya rage gudun da yake ya danna ma Mai Martaba kira.
Ta ɗan jima tana ringing kamin a ɗauka.


“Assalamu alaikum”


“Wa'alaikassalam, Allah ya taimaki Mai Martaba”


“Babana kana lafiya?”


“Lafiya ƙalau Mai Martaba, Mai Mairtaba yanzu idan Madina (Sister sa wance suke uba ɗaya) ta zaɓi saurayinta sama da kai ya zaka ji? Bayan kuma kai ka yi mata zaɓi?”


“Ba zan ji daɗi ba, sai dai kuma ba zan hana ta aurensa ba, amman kuma ba zata ga da kyau ba, ba kuma dan ina mata fata ba, no saboda ba kasafai auren da iyaye basa so yake zama alheri ba”


“Idan kuma bayan ta yi auren mijin ya sake ta fa? Bayan ya gana mata azaba, sai ta dawo gare ka, ya za kayi?”


“Zan karɓe ta da hannu biyu na mata masauki ta yadda zan shimfiɗa mata sabuwar rayuwar, ita da kanta zata yi nadama ta gane lallai Uba, Uba ne, ta yadda wata rana idan ta ga wanda zai aikata hakan ita da kanta zata hane shi”


“Lallai Mai Martaba kai ne za ka taimaka min wajen dawo da martabar Namra”


“Wacece Namra?”


“Gobe da safe zan dira Katsina zan tabarta maka komai Mai Martaba”


“Allah ya kai mu”


“Amin mu kwana lafiya, Allah ya ƙara mana nisan kwana da lafiya”


Ya aje wayar yana murmushin da shi kaɗai ya san manufarsa.



AMIRA POV.


Tana gama rubuta wasiƙar ta naɗe cikin wata paper, sannan ta ɗauki salati ta saka, ta ta saka ta cikin wani madaidaicin kwali ta yi rolling da wani jan gayenta sai ya fito kamar gift.
Sai da ta gama abunda ta ke sannan ta kwashe komai ta gyara gurin. Saman gado ta koma ta kwanta tana kallon sili kamar mai tunanin wani abu. Haleema ce ta turo kofar ɗakin ta shigo fuskarta ɗauke da damuwa dan ita har ga Allah tausayin Amira take.
Kusa da ita ta zauna tana kallon kwalin dake gefenta.


“Yau duk baki leƙo mu ba? Ko abinci ba ki ci ba”


Sai a lokacin Amira ta tuna rabonta da abincin tun jiya da rana. Sai dai kuma har yanzu bata jin yunwa. Duk ta wani zurma kamar marar lafiya.
Unƙurawa ta yi ta tashi.


“Bana jin yunwa, Dan Allah Haleema ki taimaka min ki kai ni tasha na bada wannan saƙon”


“Saƙon minene Amira?”


“Wasiƙa ce na rubutawa mutumen da ya fara cuta na, wata ƙila idan ya karanta zai gane ina raye har ya wanke, na koma gurin iyayena ko Allah zai sa Yayan ki ya so ni”


Bata damu da sanin abunda yake cikin wasiƙar ba, ta miƙe tsaye


“Okay, bari na ɗauko mayafi na”


Tana ficewa Amira ta tashi cikin rashin kuzari ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta da hawaye ya ɓata ta fito. Wannan karon Hijabi ta ɗauka ta saka, sai ta zauna gefen gado tana kallon kwalin zuciyarta sai bugawa take.


“Mu tafi”


Haleema ta baɗa yayinda ta turo ƙofar ɗakin makulin motarta na hannunta. Da sauri Amira ta ɗauki kwalin suka fice. Maganganu masu daɗi da tausasa zuciya Haleema ta riƙa mata har suka isa tashar. Suna shiga aka riƙa tambayar inda zasu sai Amira ta amsa da


“Motar Sokoto muke nema”


Aka nuna musu, almajira suna haɗawa da gudu ganin haɗaɗiyar mota a zatonsu ko da kayan dako ne. A gafen motoci Haleema ta faka motar suka fito tare, da ƙafa suka ƙarasa kusa da inda ake lodin motar sokoto suka samu direban yana daga gefe zaune yana jiran a gama haɗa masa passengers. Sallama suka fara masa sai ya amsa tare da mutanen da suke gurin.


“Dan Allah saƙo za a kai mu a sokoto”


Cewar Haleema.


“Ok na minene?”


Amira ta dire musu kwalin, kana ta ɗora da.


“Wannan abun za a kai ga addireshin”


Ta ƙarasa tana miƙa masa wata ƴar ƙaramar takardar. Hannu ya kai ya karɓa.


“Okay to zaki bada kuɗin mota, da kuma number wayarki da wanda za a kaiwa saƙon”


“Zan dai baka number na, amman ban da number wanda za'a kaiwa saƙon, shiyasa na rubuta maka addireshin sa, dan Allah ka taimaka min ka kai masa har gida”


“Okay ba matsala, amman gaskiya ko baki yo ba sai kin bada dubu uku, dan za a kai masa har gida ne, kuma kin ga yanayin da ake ciki ba mu cika son karɓar saƙo ba ma”


“Ina zuwa”


Haleema ta faɗa, sai ta juya ta nufi gurin motarta, bata ɗauki lokaci ba ta dawo ta miƙa masa dubu uku ƴan ɗari biyar biyar.


“Gashi amman dan Allah ka tabbatar saƙon ya isa, ki bashi number wayarki so that idan ya kai sai ya kira ya faɗa miki”


Ta ƙarasa tana kallon Amira. Ba musu Amira ta karɓi number wayarsa ta saka a wayarta, sai ta masa flashing number ta ta fito, sai da ta tabbatar yayi saving sannan ta juyo ita da Haleema suka nufi gurin da suka faka motar su.
Haleema ce ta fara shiga sannan Amira, har suka isa gida babu wanda yace da wani uffan, Haleema na wani tunanin na dabam, Amira ma haka har suka isa gida.
Tun kamin su faka motarsu Haleema ta gane yayanta ya dawo, ganin yadda sojojin suka koma cikin natsuwarsu sosai.


“Big bro ya dawo kenan!”


Ta faɗa tana zare key ɗin motar, Amira dai bata ce komai ba, har suka fita motar suka nufi ƙofar shiga falon.
Gabanta ya faɗi sosai lokacin data saka ƙafarta cikin falo, ta yi ido biyu da Abdool.
Abinci yake aunawa a cikinsa yana zubawa Ummi satti, yanayin fuskarsa kawai zaka kalla ka fahimci baya cikin damuwa, dan annuri ne shimfiɗe a fuskarsa.


Cikin sanyin jiki Haleema ta ƙarasa kusa da Ummi dana wasar haƙura, dan tasan laifinta na fita bata faɗawa Ummi ba.


“Daga ina kike?”


Ummi ta tambaya fuskarta babu alamun dariya. Ta ɗan sosa kai tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Ummi dan bata jin zata iya faɗa mata gaskiya.


“Ya Abdool an sauka lafiya”


Amira da ke can gefe Haleema ta miƙawa Abdool gaisuwa. Ba tare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa.


“Lafiya ƙalau”


Sai ya miƙe tsaye yana yi ma Haleema wani kallo.


“Daga Ina kuke?”


“Pizza na ce ta raka ni na siyo kuma ban samu ba”


Ta faɗa tana pretending like she's serious.


“Amman idan zaku je siyen Pizza sai kawai ki kama hanya ku fita without permission?”


“I'm sorry Ummi i promise ba zan sake ba”


“You're very stupid, haka kawai zaki saka kafa ki fita ba tare da kin faɗa ba? Baki san rayuwarku tana cikin haɗari ba? Ba ni kaɗai za a riƙa farauta ba har da ku”


Abdool ya faɗa yana kallonta har handkercheif ɗin dake hannunsa ya faɗi.


“Haba Big Bros Wallahi ba zan ƙara ba, dan Allah ku yi haƙuri”


Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Amira kan idonta na kan Abdool, annurin fuskarsa kawai take kallo, a ɗayan ɓangaren kuma tana Allah-Allah ya manta da handkercheif ɗinsa ta ɗauke, ta yadda zata fi jin daɗin tuna sa idan tana tare da shi.


“Miya hana ki zuwa makaranta?”


Ya tambaya yayinda ya risina ɗaukar handkercheif ɗin.


“Yau ba mu da lacca sai four”


Be sake ce mata komai ba, ya kalli Ummi.


“Zan je gurin Mai Martaba”


“Mu zaka ku? Tun da ka sauka naga ka kira shi fa, akwai abunda kuke shiryawa ko?”


“Kedai Ummi kawai ki sa ido ki yi kallo, wannan tsakanin ɗa da uba ne”


“Idan tayi tsami ma ji, miye sunan in-law ɗin tawa?”


“Da saura Ummi, bata kama hanyar zama in-law ba tukuna, sai mun yi settling abubuwa. Her name is NAMRA...!”


Wani irin faɗuwa gaban Amira yayi har sai da kanta ya tsara.


‘Namra’


Ta maimaita sunan a ranta tana, tuna wacan Namra wacce take ganin ita ce silar shiga ta wannan halin rayuwar. Kamin ta kalli Abdool da ya kai hannu ya ɗauki apple ya fice yana wasa da shi. Ummi kuma ta tashi ta nufi Kitchen, sai ya rage daga Amira sai Haleema ne a falon. Amira ta matsa kusa da Haleema ta dafa kaɗatar.


“Haleema zan shiga ciki, idan Ummi fa faɗi abunda za a girka da ranar nan kya sanar da ni please”


“Okay Sleep well”


Cikin sanyin jiki ta juya ta nufi ɗakin Amal da ya zame mata kamar ɗakinta.




ABDOOL POV.


Cike da zumuɗi ya isa faɗar Mai Martaba, kai tsaye ya wuce part ɗinsa da yake zama. A babban falonsa ya same shi, Hajiya Shafa na haɗa masa abun karyawa, yana ganin ɗansa ya washe haƙura, wanda hakan sam be yi ma uwaegidan Mai Martaba daɗi ba.


Cikin girmamawa Abdool ya gaishe ta, ta amsa masa kamar babu komai sannan ya gaishe da Mai Martaba yana masa kirari.


“Ba wani daɗin baki da zaka min sai da ka fara gaishe ta sannan zaka miƙa min gaisuwa”


Dariya yayi shi da Hajiya Shafa, sannan ya ce


“Ayi haƙuri Mai Martaba, zafi zafina na zo dan labarta maka komai”


“Muma nan ai mun aje maka labari har da ɗuminsa”


Hajiya Shafa ta faɗa. Abdool ya ce


“Tau a fara bani na sha”


“Wannan albishir kuma Mahaifinka zai maka shi”


Ta tashi ta fice tana dariya. Mar Martaba ya miƙa ma Abdool tea da aka haɗa masa shi kuma Abdool ya aje tea a gefe ya shiga haɗa ma Mai Martaba wani yana labarta masa labarin Namra.


Sai kusan Sha ɗaya da rabi suka gama karyawa tare da Mai Martaba yadda Abdool ya zage yana cin abincin ba zaka ce ya ci abinci gurin Ummi ba.
Mai Martaba ya jinjina lamarin Namra sosai kuma ya tausaya mata duk da be ganta, bama abunda ya fi taɓa shi kamar yadda ya ji tana raɓe a gidan wasu bayan kuma uwarta da ubanta suna raye.


“Amman Ina

Please Login or Register in order to submit comment