Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba, kuma bata tsaya jiran abunda zai ce ba ta juya tayi tafiyarta.


Wani kallo ya bita dashi, daman duk cikin Family Abbah Maryam tafi uban kowa tsageranci. Buɗe Motarsa ya yi ya shiga zuciyarsa cike da tunane-tunane, hannu yasa ya shafa kansa, sai ya ciro wayarsa ya nemo wata number ya danna mata kira.
Ana yin picking ya ce


“Tahir kana ina?”

Ban ji me aka ce masa ba, sai kawai yace


“Ok gani nan zuwa yanzu”


Daga haka ya kashe wayar, ya ƙarama gudu. Can kaɗai ne yake jin zai iya tafiya ya fayyace sirrinsa, tun da duk akan layi ɗaya suke.
Sai da ya yi tafiya mai nisa, sannan ya isa bakin wani ƙaton gate.
Horn yayi mai gaɗin ya buɗe masa sannan ya kunna kai cikin ƙaton guesthouse ɗin. Parking ya yi, ya fito ya nufi hanyar shiga gurin. Zazzaune ya tararda su, Tahir da Najeeb. Tun daga ganin yanayin shigowarsa sun san akwai wani abu a ƙasa. Tahir ne ya fara magana


“Lafiya kake Uzair?”


Bakinsa ya cika ma iska ya busar


“Wallahi ina cikin matsala”


“Matsalar me?”


Najeeb ya tambaya, cike da son sanin abunda ke damun amininsa.
Uzair be ɓoye aminansa komai ba, tun daga ganin da Namra tayi ma friends ɗinsa na Abuja har zuwa nemanta da yayi, kuma kalaman da Abbah yayi masa yanzu, sannan ya ɗora da sace ta da yayi.
Tahir ya girgiza kai


“Uzair you Fuck up, ai yin wannan abun da kanka matsala ne, mun riga mun san junan mu toh miye na ɓoyewa kasa kanka a matsala? Yanzu ka sace yarinyar mutane kana ganin asirinka ba ze tunu ba?”


“Nayi tunanin zan iya solved ɗin matsalar ne, da nayi nufin na riƙe ta ne har kwana biyu ta yadda za a yi tunanin ta gudu da bi saurayinta ne. Ga Yasmin ta juya min baya na rasa gane kanta, kuma yanzu idan ta dawo zata iya faɗa asirina ya tonu kuma kasan komai ze iya faruwa, family ni za a zaga kuma.mahaifinta ba zai ƙyale ni ba”


Tahir ya dawo kusa da shi ya dafa shi.


“Ka kwantar da hankalinka, irin wannan yarinyar ta dabara bata musu, kuma irin wannan sirrin ba a sake da shi”


Najeeb yace


“Lallai kam, irin wannan yarinyar malamai za a shiga da ita, fiussss an gama da ita”


Tahir yace


“Shine kawai, yanzu kaje kayi abunda zaka yi da ita, kasa a maida ita gida kamin asuba, zan rubuta maka wani magani ka bata tasha zata manta abunda ya faru, idan Jafar ya dawo zamu zauna mutattauna”


Murmushi jindaɗi yayi, yajin ya samu mafita gurin abokansa.
Cikin kuzari ya tashi bayan Doctor Tahir ya rubuta masa maganin a takarda, ya yi musu sallama ya fice.








__________________________
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖😘🌺
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*

Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


NOT EDITED ⚠️




*PAGE - 8*


Yana cikin mota yana driving zuwa guesthouse ɗinsa, kiran Najeeb ta shigo wayarsa. Picking yayi ya kara a kunne sai ya mai da tuƙin da hannu ɗaya.


“Hello”


“Uzair kana ina? Ka isa gidan ne?”


“A'a gani dai kan hanyar zuwa siyen maganin”


“Karka siyo ka wuce gidan kawai, idan ka isa ka jira ni gani nan zuwa, kuma ka tabbatar bata farka ba, idan kuma ta riga ta farka, karka bari ta gan ka, ina ka aje ta?”


“A guesthouse ɗina”


Sai ya kashe wayar, ya ƙara ma Motarsa gudu. Yana isa, Najeeb na isa. Sai duk suka yi saurin fitowa Motar. Najeeb ya nufi shi yana faɗin


“Yanzu ya kamata mu mai da ita gida”


“Taya?”


Najeeb ya kalli ko ina na gurin, sannan yace


“Ni zan kaita, faɗa min inda ka ɗauke ta, zanje can na maidata, zamu saka mai gadin nan naka ya je a inda take ya riƙa ihu da neman taimako har mutane su taru su, su nuna masa gidansu, zai bamu haɗin kai dai ko?”


“Me zai hana indai an bashi kuɗi”


Uzair ya faɗa.


“Okay zan tsara masa yadda zai yi, miye sunan Saurayin nata?”


“Asim sunan shi Ibrahim, amman anfi saninsa da Asim”


“Good yanzu kira ɗaya daga cikin masu tsaronta ya duba mana idan bata farka ba”


A take Uzair ya ciro wayarsa. Najeeb kuma ya nufi gurin mai gadin.
Ɗaya daga cikin yaran ne suka shaida masa har yanzu bata farka ba. Shi kuma ya nufi Najeeb ɗin ya faɗa masa.
Sai da Najeeb ya gama tsarama mai gadi yadda zai yi, sannan ya juyo gurin Uzair.


“Good yanzu kasa su ɗauko ta, su saka ta a mota na, sai ka shiga taka motar ka nuna mana daidai inda ka ɗauke ta”


“Baba Audu zaka iya ko?”


“Ƙwarai Zan iya ranka ya daɗe ai wannan abu ne mai sauki, kuma taimako ne”


Baba Audu ya faɗa da kansa. Sai Najeeb yayi murmushi.


“Zamu baka dubu ɗari idan aiki yayi kyau, zamu baka wasu dubu ɗari na rufar sirri, ka tabbata dai ba'a samu matsala ba”


Har ƙasa Baba Audu ya risina yana godiya baki har kunne.


“Allah Ubangiji ya saka da alheri, ai ni ko baka bani komai ba, zan iya maka fiye da wannan”


Najeeb ya nuna masa Mota.


“Kaga Mota can je ka shiga gidan gaban”


Sai kuma ya kalli Uzair


“A fito da ita yanzu”


Cikin sauri Uzair ya nufi gurin, be daɗe ba ya fito, wani namiji na ɗauke da ita. Ita kuma ta langwaɓe kamar wacce ta mutu.
Najeeb da kansa ya bude Motar suka saka ta gidan baya. Sannan Najeeb ya shiga driver seat, Baba Audu ya shiga front seat, Uzair kuma ya shiga Motarsa, sai ya shiga gabansu dan nuna musu hanya.


Cikin mintuna suka isa gurin. Can nesa da gurin suka faka, sai Najeeb ya buɗe motar ya fito da ita. Uzair ya nuna dai-dai inda ya ɗauketa sai Najeeb ya ajeta a gurin, yasa car key ɗinsa ya ɓarke mata Hijabi, ya yagashi, ya barƙa rigar afamfar dake jikinta, har rabin breast ɗinta ya fito.
Sanna ya ɗago ya kalli Uzair


“Ta fito da waya?”


“Yes ga wayar ta nan hannu na”


Ya faɗa yana ƙoƙarin cirota daga aljihunsa. Najeeb ya miƙa masa hannu


“Wani wayar zan taka ta da mota, kuma ka bani layin da ka kira ta da shi”


“Why?”


Najeeb yayi masa wani kallo


“Haba Uzair ya kake abu kamar ba wayaye ba? Baka san za'a iya amfanin da wayar a gano sawon hannunka ba? Za a iya gano ka idan kana amfani da layi, kuma yanzu ai amfanin layin ya ƙare”


Kamin Uzair yayi magana, kiran Amira ya shigo wayarsa. Da sauri Najeeb ya tambaya.


“Who's calling?”


“Her Best friend”


“Did she know?”


“Yes tare da ita muka haɗa komai”


“Karka yi picking call ɗin nan it risk, let's go kar wani ya gan mu”


“Da wahala wani ya gan mu, baka ga yanayin gurin ba? Ko da rana ba a cika wucewa ba balle yanzu pass 11 fa”


Najeeb yayi murmushi, irin na har yau baka waye ba Uzair. Sai kuma ya kalli Baba Audu


“Da ka daina hango hasken Motar mu, zaka fara ihun”


“Toh ranka ya daɗe”


Cikin sauri suka nufi motocin su, Najeeb sai wage-wage yake kamar mai neman wani.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa09.html




🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*

Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


*PAGE - 9*


A lokacin da Baba Audu ya daina hango su, sai ya buɗe dukanin muryarsa ya kwarara uban ihu yana neman taimako.


“Wayyo Allah jama'ah a taimaka mana, a ceto rai, jama'ah ku kawo agaji”


A yanayin gurin, ba kowa bane zai iya saurin fita, saboda yanayi na tsoro da ake ciki, gashi ta bayan layin unguwar ne ba mutane sosai.
Cikin ƙarfi hali da bugawar zuciya, Baba Audu yake ta kwarara ihun yana wage-wagen jiran wanda zai fito.
Tsinta-tsinta aka fara fitowa ana nufar gurinsa, sai tambayarsa suke lafiya. A nan ya soma ƙirƙiro hawayen ƙarfin hali yana faɗa musu abunda Najeeb ya tsara masa.


“Wallahi wasu mutane yanzu suka jefo da wannan yarinyar daga mota, kuma suka zo suna ƙoƙarin taɓa mata mutunci”


Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Shine abunda kowa yake faɗa, dan makamacin wannan be taɓa faruwa a unguwar ba. Wani dattijo ya kai hannu ya gyara mata Hijabinta, ta yadda zai suturta mata breast ɗinta dake buɗe.
Waɗanda suka santa sun gane ta, sai dai kowa mamaki yake, yana tunanin suye ne suka mata haka? kuma a ina ta haɗu da su haka.
Wani saurayi ne ya kawo ruwa aka zuba mata, amman shiru bata farka ba, haka akayi ta zuba mata ruwan but still bata motsi. Anan mutane suka ce a ɗauke ta a kaita gidansu


*** *** *** ***
Babu irin kiran wayar da Anty Amarya bata yi ma Namra ba, tun tana ringing har aka kai ga kashe wayar.
A lokacin hankalinta ya tashi sosai, ita da Maryam har Aisha da Hindatu sai da hankalinsu ya tashi.
A take Anty Amarya ta fara kuka, tana tunanin abunda ze samu ƴarta, kuma tana tsoron kar Abbah yaji, sai duk tabi ta rikice ita da Maryam. Aisha da Hindatu suka ce zasu je bayan layi su duba ko Allah yasa zasu same ta.


Anty Amarya ta share hawayenta.


“Babu inda zaku je cikin daren nan, bayan layi da yake da duhu idan wani abun ya same ku fa, ban san abunda yasa Namra ta raina ni ba, ta ya zata saka ƙafa ta fita ba tare data faɗa min ba? Duk abunda ya same ta ita tajawa kanta”


Maryam ta ɓata fuska.


“Gaskiya Anty Namra bata kyauta ba, amman da kin bari munje mun duba ko zamu ganta”


“Babu inda za ku je, idan Abbah ku ya gani kuce masa me?”


“Abbah ba ze gani ba, tun da yana part ɗinsa, kuma ba daɗewa zamu yi ba, dubowa kawai zamu yi mu dawo”


“Babu inda za ku je yanzu goma ta wuce, inda har kuna jin magana ta, toh karku je ko ina nemanta, ai ita ta kai kanta, ina zaune falo tabi ta ƙofar kicin ta fita, ba dai-dai bane tasa ƙafa ta fita ba tare da sani ba”


Anty Amarya na gama faɗar hakan, ta tashi ta nufi falo tana hawaye. Yanzu kan babu abun ɓoyewa dole ta faɗa ma ƙannenta abunda yake faruwa, su kansu basu jidaɗi ba, sai laifin Namra suke gani, wai taya zatayi haka kamar wata ƙaramar yarinya.


Haka suka yi zaune jugum, kowa sai addu'ah yake, babu irin roƙon da Mama Zainab bata yi ma Anty Amarya ba akan ta bari suje su dubota, amman ta hana.
Har kusan shaɗaya babu wani labari, sai shabiyu saura kwata, suka soma jin hayaniya a habarar gidan, sai doko musu sallama ake da muryar maza.


Wani irin faɗuwa gaban Anty Amarya yayi, har sai da ta dafa zuciyarta ta lumshe ido. Mama Zainab da Hajiya Raliya ne suka riga fita, Aisha da Hindatu suka rufa musu baya.
Maryam kuma ta tsaya kusa da mahaifiyarta ganin halin da take ciki. Cikin ƙarfin hali Anty Amarya ta tashi, Maryam ta ɗauko mata hijabinta ta saka sannan suka nufi ƙofar fita.


Ko da suka fito har Hajiya Barau ta isa gurin, Abbah kuma ya fito daga part ɗinsa ya nufi gurin da mutane suke tsaye, riƙe da Hannun jikan Imam jikan Hajiya, da alama shi ya je ya faɗawa Abbah.
Cike da kasala Anty Amarya ta ƙasara gurin ita da Maryam. Tana ganin halin da Namra take cike gabanta ya ƙara faɗuwa, a take kasala ta sauki mata. A nan Maryam ta fara kuka ganin Namra kwance kamar matatta ga Hijabinta a yage.
Abbah ya kalli mutanen cikin tashin hankali.


“Miya faru? Ina kuka ɗauko Khadija?”


Kowa sai ya nuna Baba Audu yana faɗin shi ne san abunda ya faru, tun da yace musu a gaban idonsa akayi. Tun kamin Abbah ya tambaye shi ya shiga yi masa bayani.


“Na fito ne gidan ƙanena can baya, sai na hango wata ƙatuwar mota mai kamar ta ƴan makaranta ta tsaya, a gefen gurin sai aka jefo wannan yarinyar , sai kuma suka fito su huɗu suna ƙoƙarin cire mata tufafi, shine fa sai na fara musu ihu suka gudu suka shige motar, bayan sun wuce ne, na ƙarasa inda take ina neman taimakon jama'ah ganin halin da take ciki, da jama'ah suka fito sai suka ce sun santa a nan gidan take, dan ni ba ɗan unguwar nan ba ne ban san ta ba Wallahi”


Wani irin abu ne ya taso ma Abbah, tun daga kan ɗan yatsan ƙafarsa zuwa ƙasan zuciyarsa, a take kalar idanunsa suka canja, wata jijiyar ɓacin rai ta taso masa, ta ratsa gefen wuyansa zuwa kansa, a hankaɗe ya kalli Anty Amarya.


“Yaushe ta fita?”


“Wallahi... Ban ...san ...ta fita ..ba ...”


Anty Amarya ta amsa murya na rawa. Abbah ya katsa mata tsawa




“Baki san ta fita ba kamar ya? Taya zata fita ba tare da kin sani ba?”


Kamin Anty Amarya ta ƙara bashi amsa, sai mama Zainab ta yi ɓaranɓarama, a ƙoƙarin kare Anty Amarya.


“Wallahi duk muna falo ta fita, babu wanda ya san da ita, ta hanyar kitchen ta bi, wai zata yi sallama da saurayinta”


Anty Amarya jin tayi kamar ta matse bakin Mama Zainab amman ba dama.


“Junaidu!”


Hajiya Barau ta ƙwalawa mai gadin kira. Da sauri ya amsa dan yana kusa da ita, yana kallon Namra dake kwance cike da mamaki.


“Ya aka yi Namra ta fita? Ba dokar gidan nan bace idan anyi magariba ba wanda ze fita?”


Jikinsa ya hau ɓari, yana ƙoƙarin ƙare kansa.


“Wallahi sai da na yi mata magana, sai tace wai saƙo zata karɓo nan kusa, ni sam na manta ma da bata dawo ba sai yanzu”


Abbah ya kalli Baba Audu


“Kasan mutanen ne? Zaka iya gane su?”


Baba Audu ya yi shiru kamar mai nazari.


“Gaskiya ba zan iya gane su ba, amman dai na ji suna faɗin Aasimu ko Ƙasimu, suna ce masa ya yi sauri su tafi”


“Asim..!”


Abbah ya amsa da ƙarfi. Sai kuma ya sauke ajiyar zuciya, ya kalli mutanen.


“Na gode sosai, Allah ya saka ma kowa da alheri”


Sai da suka masa Allah ya kyauta, sannan suka fita kowa bakinsa ƙunce da magana, wasu kuma mamakin fitar da ta yi suke, ga kuma ɓarin zancen da Mama Zainab ta yi.


Maryam ta nufe ta tana faɗin


“Abbah akai ta asibiti, duba fa bata motsi”


Juyawa Abbah ya yi ya nufi part ɗinsa rai a ɓace. Hajiya Barau ta ce


“Daga ta zan ɗauko mota akai ta, ai kisan halin Abban ku sai dai ta mutu a nan”


Hajiya Barau ce taja mota, da taimakon Hindatu da Mama Zainab suka sa Namra a mota, suka nufi asibitin dake kusa da su.
Suka bar Anty Amarya da Maryam suna aikin kuka, Hajiya Raliya na bata haƙuri, sai kawai Aisha ta yanke jiki ta faɗa iskokanta suka taso.




*** *** ***


Suna shiga Uduth, aka wuce da ita emergency, da sauri Nurses suka karɓe ta, aka ɗorata akan gado, suka shiga da ita wani ɗaki, taimakon gaggawa suka shiga bata kamin Likitoci su iso.


Ba a fi minti biyar ba, Doctor Hilal ya shigo cikin manyan kaya, hannayensa zube a aljihu, tare da wani likita, hankalin kwance ya ƙarasa inda take kamar ba marar lafiya ze duba ba.
Duk natsuwa Nurses ɗin suka yi suka ja da baya suka bashi guri. Hannu ya kai ya taɓa gefen wuyanta, yana kallon agogonsa hannunsa, sannan ya kalli drip ɗin da aka ɗora mata.


“Ku cire mata drip ɗin nan sai numfashinta ya dawo, ku kira Doctor Adamu ko wani likitan, da wannan ba aikin Likita ɗaya ba ne”


Yana kaiwa nan ya juya, sai Likitan da suka shigo tare ya yi saurin cewa.


“I'm sorry Doctor, Doctor Adamu is not around, that's why i call you”


Juyowa ya yi ya kallesa


“Wannan ba aiki na ba ne, and you know it, tiyata kawai na zo yi garin nan, ba kuma zan ɓata lokaci na akan abunda ba aiki na ba, jirgi zan bi na koma kaduna a can ma ina da aiki”


Yana kai wa nan ya fice. Da sauri wasu Nurses suka fita dan kiran wani likitan, shi kuma wannan likitan ya shiga bata taimako.




KALSOOM POV.


Tana tashi daga aiki, ta wuce gidan ƙawarta Salam dan labarta mata halin da take ciki.
Bayan Salma ta kawo mata abinci ta ci tayi sallah, sai take bata labarin abunda ya faru.
A maimakon ta ga ɓacin rai a fuskar Salma na taya ta baƙinciki irin mijin da zata aura, sai ta ga Salma na murmushi da yima Allah godiya


“Alhamdullah Allah mun gode maka, haba Kalsoom ko dan daɗewar nan da kika yi ba aure, be isa yasa kiyi haƙuri ki auri wannan ɗan'uwan naki a haka ba? Kina ji fa na faɗin da babbar budurwa ƙara ƙaramar bazawara, ƙannenki biyu a ɗaki ke kina nan, haba Kalsoom ki yi tunani mana”


“Ba auren ne bana so ba Salma, halin Sadiq ɗin ne na ke tsoro, ina gudun abunda ze je ya dawo, tun kamin tafi ake shawara ba sai an dawo ba, Wallahi na tsani mutum ne neman mata”


“Dan Allah ki daina faɗar wannan maganar, kar wani ya jiki ya san sirrinki, nema mata yanzu ya zamo ruwan dare, da wahala ki samu namiji me aure ko marar aure da baya neman mata, ko wace mace da kika gani a gidan mijinta tana da nata matsalar, no married friend of yours will ever tell you her marital problems,no woman will tell you her husband's fault amma karya take tace he is perfect,because no one is, dan Allah kiyi auren ki Kalsoom ke kaɗai ce a cikin kawayen mu kika rage baki yi aure ba”


Wani kallo Kalsoom ta yi mata, tana mamakin yadda ta kasa fahimtar ta.


“I have never blame myself for being single, i know I'm pretty, i'm well behaved, i'm Godly,and yet still single. Salma thats just how nature works, that is how Allah has designed it.
Idan duk a cikin ƙawaye na ni kaɗaice ban yi aure ba so what? Ni nayi kai na? Allah who created me differently and created them differently, surely made you destinies different. Komai lokaci ne Salma i don't want to rush into marriage with just any guy just because i want to be married, babu mai son ya je ya yi aure ya fito”


Salma ta dafa ta


“Haba Kalsoom zaki yi auren ne da niyar ki fito? Your idea is inside you Kalsoom, kiyi tunani me kyau, amman aure nan shi ya fi, kawai ki bawa Allah zaɓi”


Hawayen da suka zubo mata ta share ta ɗauki jakarta ta rataya.


“Na gode Salma zan yi tunani akai”


Har bakin gate Salma ta rakota, suka yi sallama sannan ta koma. Tafiya Kalsoom take tana tunani, sai taji ana mata horn, juyowar da zata yi sai taga wata hadaɗɗiyar mota mai kyau, tana binta a baya. sayawa tayi sai mai motar ya zo dai-dai ita ya tsaya, yana sauke gilashin motar.
Dattijo ne mai yalwatacciyar fuska da cikar kamala ta mai kuɗi.


“Shigo mana”


Ya faɗa yana buɗe mata front seat. Bata kawo komai a ranta ba, sai kawai ta buɗe motar ta shiga. Driving yake kaɗan-kaɗan yana gaisawa da ita.


“Ya kike ya gida?”


“Lafiya ƙalau”


“Ina zaki je ne haka?”


“Gida”


“Kuma kike tafiya a rana haka, kar fa rana ta taɓa min ke”


Ɗan murmushi tayi ta gyara yafin gyalenta.
Ba ko kunya ya kai hannu ya yaye mata gyalen


“Haba ke kuwa ya kiƙe ƙoƙarin rufe min kyau nan naki...”


Be karasa ba ta buge masa hannu tana masa wani kallo


“Sauke ni Malam, ni ba irin waɗannan matan bane”


“Haba kyakkawa daga magan...”


“Ka sauke ni nace!”


Ta faɗa a tsawace. Ba shiri ya ya faka motar ta buɗe ta fita tana tsaki.


“Ku ba za ku ce kuna son mace da aure ba sai lalata, duk Namijin da ka haɗu da shi abunda kawai yake ƙoƙari ya kai ga jikinka, ƴan iska kawai marar mutunci”


Haka tayi ta zaginsa, shi dai be bi ta kanta ba ya ƙaɗa motarsa yayi gaba.






_______________________________


Share it please, and drop your opinion. 🙌


Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa10.html


🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺

_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*


Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated


*PAGE - 10*




UZAIR POV.


A guesthouse ɗin suka koma. Bayan Najeeb ya fito motarsa sai Uzair ya fito, suka nufi bayan motacin da suke gurin.
Ta inda suka san ba za'a gansu ba suka tsaya. Sai Najeeb ya kalle Uzair ya ce


“Uzair zaka janye maganar auren nan gobe gobe ba sai jibi ba, ka ce ka fahimcin tana da wanda take so, dan haka kai ka haƙura.
Sai idan ka yanje maganar ne sannan za mu je da kai gurin Malam gobe da nisa, dan ba za a yi mata magani kana auren ta ba”


“Amman idan mahaifinta yaƙi yarda fa?”


Najeeb ya yi masa wani kallo


“Ta ya zai ƙi yarda ? Shi ze aure ta ne? Ya kake abu Uzair kamar ba ɗan duniya ba? Sai wani ɓoye-ɓoye kake ai gashi nan ka jawa kan ka”


“Babu babbar matsala kamar ganin da tayi min, yanzu idan ta faɗa dame zan kare kaina”


“Sai kace ai ta saba maka ƙazafi, kai ma ai kasan kayi kuskure na bari ta ganka, kamata ya yi kasa a ɗauko maka ita”


Uzair ya yi shiru yana nazari, tashin hankali bayyane a fuskarsa. Kiran Amira tana ta shigo masa a waya amman yaƙi ɗagawa.
Ƙarfe ɗaya da rabi na dare kiran Baba Audu ya shigo wayar Najeeb. Cikin sauri ya ɗauka yasa hands-free.


“Hello Baba Audu ya ake ciki?”


Daga ɗayan ɓangaren Baba Audu ya amsa


“Na gama komai, na fito ina babban ti-ti, dai-dai inda kace na tsaya”


“Ina fatar anyi nasara?”


“Komai ya tafi yadda kake so”


“Toh ka jira ni, zan zo nan gurin na ɗauke ka”


Daga haka ya kashe wayar, ya kalli Uzair.


“Yanzu ka wuce gida kawai, ni zanje na ɗauko shi, idan ka taso aiki gobe mu haɗu a guesthouse ɗin Jafar, kuma ka tabbatar da ka sallami waɗannan mutane da suka ɗauko ta in case of”


Be jira abunda Uzair zai ce ba, ya nufi motarsa. Sai bayan ya fice sannan Uzair ya nufi cikin guesthouse. Be daɗe ba ya fito ya buɗe motarsa ya shiga, ya ɗauki hanyar da zata kai shi gidansa.


Tun kamin yana yin parking ya kashe wayarsa, sannan ya fito ya nufi hanyar falon.
Yasmin na zaune falo tana duba wasu takardu da system Uzair ya shigo da sallama.
Sai dai bata amsa masa sallamarba ma balle har ta ɗaga kai ta kalle. Kamar hakan be dame shi ba, sai kawai yazo ya zauna kusa da ita ya rufe system ɗin dake gabanta.
Yana ganin ta unƙurin zata tashi, sai yayi saurin riƙe ta ya zaunar, ya danneta da dukan ƙirjinsa ya ɗora mata nauyinsa, yana ƙoƙarin saka mata hannu ciki riga.


“Haba Bloody miyasa kike min haka ne? Dan kawai zan ƙara aure sai na zama maƙiyinki? Ai badan bana son ki zan ƙaro wata ba, sai dan rufin asirin mu”


A kaɗan-ƙaɗan ya raɗa mata haka, cikin wani irin siga na son tada mata hankali, sai numfashi yake sakar mata a kunne.
Ƙoƙarin ƙwatar kanta take amman ta kasa, ta ƙara haɗe rai sosai.


“Sake ni mana, Uzair bana son haka”


“Zan sake ki, amman sai kin faɗa min idan kin daina fushi da ni, idan kuma baki daina ba toh zan janye maganar auren”


“Maganar auren ka be dame ni ba, babu ruwana da lamarin auren ku, dan haka ka daina saka ni a ciki”


“Babu ruwanki da lamarin aure na kuma kike fushi da ni?”


“Amman dan zaka yi aure sai ka rasa wadda zaka aura sai Aminiyata, kuma ƴar'uwa ta”


“Nima ai

Please Login or Register in order to submit comment