Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

take labartama Namra wanda zai auri Maryam da Hindatu duk sun zo sun gaida Abbah, kuma sun turo iyayensu, dan tsayar da magana.
Namra ta kallesu tana dariya.


“Eyyyye Amare”


Hindatu ce ta ji kunya har ta rufe ido, Maryam kan dariya ta riƙayi sai ta tashi ta bar falon kasancewar tana waya da angon ne.


“Saura ke”


Namra ta faɗa tana wasa da hannun Aisha, sai Aisha tayi mata wani kallo.


“Ni Anty no da na ss2”


“Ƴar jss ma anyi ma aure balle ss”


Dariya Aisha tayi ta rufe fuskarta. Dammm gaban Namra ya yanke ya faɗi, jin ƙarar tsayawar Mota, zuciyarta na nasalta mata Abbah ne ya dawo, ji take idan ya shigo rufeta zai yi da ruwan masifa. Da sauri ta tashi ta nufi ɗakin Anty Amarya gabanta na ci gaba da faɗuwa.


Tsaye ta tararda Anty Amarya tana gyara tufafin da suke wardrobe ɗinta, kallo ɗaya tayi ma Namra ta ɗauke kai tana murmushi, kamar ta san abunda Namra ta jo ma gudu.


“Ai shine yace aje a zo da ke”


“Amman be ce komai ba?”


“Be ce ba, dan shi kansa yana san kina cikin matsala akwai abunda yake damun ki”


“Babu abunda yake damuna Anty”


Anty ta bar tufafin ta zo ta zauna kusa da Namra


“Farinciki da baƙin ciki abubuwa ne da basa iya ɓoye kan su Namra, jikin ki ma ya nuna haka, dubi kiga yadda kika lalace kika rame kamar ba ke ba, Namra karki ɓoye min damuwarki, ni Mahaifiyar ki ce babu wanda ya dace ya ji matsalar ki sai ni”


“Anty babu abunda yake damu na, kawai na zo na gan ku ne”


“Namra dubi kam ki? Kin ga yadda kika lalace?”


“Ba ni da lafiya ne”


“Me ke damun ki?”


“A nan ƙasan marana iya jin ciwo ne, sai kuma ciwon kai da nake fama da shi, ga zafin jiki”


Duk abubuwan data faɗa gaskiya ne tana jin su sai dai bata jin wata matsala ne ko kuma ciwo, yanzu kuma tayi ma Anty ƙarya ne dan ta ƙyale ta.


“To gobe za muje asibiti likita ya duba ki”


“Allah ya kai mu”


“Amin”


Ta faɗa tana janye blanket ɗin dake saman gadonta.


“Ki kwanta a nan ni part ɗin Abbah ku zan kwana, idan kuma ba zaki iya kwana nan ba ki koma ɗakin Maryam”


“A'a nan zan kwana”


Ta faɗa tana kwantawa saman gadon.
Sai da Anty ta gama gyara komai na ɗakin sannan ta ɗauki wasu abubuwa ta yi ma Namra sai da safe ta fice.






ASIM POV.


Bayan ya gama shan koko Mama ta kalleshi tace


“Yau fa kwana biyu yarinyar nan bata leƙo asibitin nan ba”


“Ai ba zata zo ba”


Ya faɗa yana goge bakinshi


“Saboda me?”


“Faɗa muka yi da ita har ma mareta kuma na faɗa mata maganganu”


“Miya haɗa ku”


“Wani na gani ya rako ta, shine wai nayi magana tace ina zarginta, har da wani wai ta ji maganar da muke ɓoyewa na kuɗin a dashe”


Mama ta riƙe baki.


“Mai kaza aljihu baya jimirin ass, daga magana sai kuma tace ana zarginta? Daman tasan abunda take kenan, ni kai na wallahi naga yarinyar da wani amman ban faɗa ba saboda kar na ɓata muku zama, daman ai na faɗa maka ba da zuciya ɗaya take zaune da kai ba”


“Ai yanzu na gane halinta, dan yi mata magana shine har ta min jawabi wai ba na da komai ta aure na lalata mata rayuwa na rabata da karatun ta”


“Amman Ibrahim ka yi wauta, ai kamata yayi ka sa mata ido ka ga iya gudun ruwanta, kuma yanzu idan ma gidan su ta tafi ai sai tace ka ci amanarta kuma ka zarge ka koreta, kuma kai yanzu ko sallamarka akayi ba itace zata yi hidima da kai ba? Ni fa gida zan koma tun da can ma akwai yara ga sana'a na baro kasan idan ba dole ba babu abunda zai zaunar da nan, tunanin hakan tasa Wallahi ban faɗa maka ba.


Yanzu zuwa kaiwai zata yi ta ɓata maka suna, sannan idan ka rabu da ita a yanzu kana da halin auren wata ne? Ai dole kayi haƙuri da ita har Allah ya nuna maka kaji sauƙi sosai ka warke kayi kuɗi, ka auro wata sannan idan ita rabuwa zaka yi da ita sai ka yi, daman sun saba yaba maka rashin mutunci, kawai ka bata haƙuri kace kayi nadama, ai Allah ma ba zai barta ba ace da aurenka kana zina haba abun ai yayi muni, daman can ba ƴar tarbiya bace shiyasa ta bi mutumen aka riƙa cewa kai ne ka ɗauke ta, har ɗan'uwanta ya fasa aurenta kai aka ƙaƙaba maka ƙaya”


Ajiyar zuciya ya sauke wani irin ɓacin rai me ke ziyartarsa.


“Amman Wallahi Yarinyar nan ta ci amanata sosai”


“Haƙuri dai za kayi, ai babu yadda ban yi ba akan karka aureta amman ka tsaya kai da fata sai ka aureta”


“Nayi tunanin aurenta zai zame min alheri ne shiyasa na yi”


“Ka kirata dai yanzu kace ta dawo, kar taje ta shafa maka kashin kaji gurin matsiyacin uban nan nata mai dukiyar likudi (Kuɗin da ba'a iya ci)”


“Bana jin tana garin nan fa”


“Shiyasa na ce ai ka kirata ba kana da number uwarta ba? Sai ka kirata ka bata haƙuri tun dai lafiya ta samu an kusa sallamar ka, idan ka kira karka nuna musu wani abun ne ya haɗa ku, idan sun ce tace kayi mata wani abu kace kai ƙarya take maka, sai idan ta gaji da auren ka ne, karka yarda ka nuna wani abun ne ya haɗa ku”


Kwantawa yayi saman gadon zuciyarsa cike da baƙinciki abunda Namra ta masa, har yana jin kamar ba zai iya kiranta ba, dan ta ci zalinsa da yawa.


“Baka da wata mafita sai wannan, idan kuma kana ganin akwai wata hanya mai fiddaka sai ka yi”


Ta faɗa tana ɗaukar ledar ƙosai da robar koko ta fice.




RASHIDA POV


Mataki uku ake bi gurin gwajin jinin dan a tabbatar da mutum yana ɗauke da cutar, idan an yi na farko ba a tsallake ba sai ayi na biyu idan shima ba a tsallake ba sai ayi na uku.
Duka an yi ma Rashida kuma results ɗaya ya bada cewar tana ɗauke da cutar, tun a cikin asibitin ta fara kuka, har ta iso gurin motarta. Nadamar taraiya da Alh. Bashir take taraiyarta da shi be haifa mata ɗa mai ido ba, be sata komai ba sai baƙinnciki da da na sani.


Tunanin yadda zata faɗawa Momy take, mutuƙar da faɗa mata gaskiya ta san ita ma gudunta za ta yi, mu'alamarta da kowa zai sauya za a fara mata wani kallo har a gurin aikinta ta san sallamarta za'ayi, duniya zata juya mata baya kowa ya tsangwame ta musamman idan aka ji silar rabuwarta da mijinta, babu kuma wanda zai sake aurenta.
Dan haka ta zaɓi zama da su a haka dan ta rufawa kanta asiri. A cikin mota ta ci kukanta ta gaji sannan ta koma gida, a lokacin yamma yayi sosai duka ƙanenta suna gida. Sai dai bata yarda sun ga fuskarta ba har ta shige ɗaki.


Ta sake ɗasa wani sabon kuka tana jin kamar ta sha wani abu ta mutu.
Sai dai wani ɓangare na zuciyarta na faɗa mata, tana da buƙatar rayuwa saboda Hilal da ƴaƴanta, idan har ta kori Kalsoom daga gidan to Hilal zai iya zama mallakinta har a bada.


A kwana biyu da tace zata yi kamin ta je gurin malamin sai ta kasa, saboda mugun ƙudirinta dan bata son ta samu wata ɗaya a gida bata koma ɗakin mijinta ba.
Hakan yasa washe gari tun da safe ya shirya ba tare da sanin kowa ba ta fita. Napep ta tara ta shiga aka kaita tasha, sai ta ɗauki shatar mota har zuwa garin da Malam yake.


Yau kan bata tsaya bin layi ba, dan tun a hanya ta kira shi ta faɗa masa gata nan zuwa, hakan yasa tana zuwa sai kawai aka mata iso cikin faɗar tasa da yake tsiface-tsifacensa.
Kamin tayi sallama wayarta tayi ringing ko da ta duba sai ta ga Hajiya Basira, wani dogon tsaki taja dan yanzu haushi Alh. Bashir take ji matuƙa.


Guri ta samu ta zauna, ta soma roko masa bayani shi kuma sai kallonta yake yana wasar haƙuransa dake cike da goro.


“Ai na faɗa miki wannan duk mai sauƙi ne, idan ma ba zaki iya ba yanzu nan zamu saka iska su ɗauko mana”


“Amman ya za'ayi su iya ɗaukowa Malam?”


“Ai ko wane ɗan 'adam yana da aljanu, sai sai sun kashi kala-kala, akwai waɗanda zaune kawai suke tare da mutum su basa magana , sune yawanci zaki ga ɗabi'unsu ɗabi'un mutum, sai idan waɗancan aljanun waɗanda ake kira iska sun shiga jikin mutum sune suke nunawa, sai kuma rauhanai su kam ƙarfinsu ma basa iya zama a jikin ɗan'adam.


Irin waɗancan da basa magana ko wane ɗan adam yana da su, duk inda mutum yayi suna tare da shi, musamman idan baya tsare addu'ah, kuma kala-kala ne akwai musulma akwai mushirikai. aljanun da zan tura zai same su ne ya tambaye su inda take aje ƙyalen haitarta ko kuma pad sai su nuna musu su kuma su ɗauko. Abu ɗaya ne zai hana su ɗaukar idan lokacin data jefar tayi bismillah to ba zasu iya ɗauka ba, ko kuma ta ƙona pad ɗin”


“To yanzun nawa zan biya?”


“Zaki bada kuɗin tulu dana jaɓa da kuma na ɗauko shi ƙyalen da za'a haɗa abun da shi”


“Dubu hansin zai isa?”


“Ba'a bori da sanyin jiki yarinya, idan kin shirya aiki kawai ki zube kuɗi ayi miki aiki, a take zaki ga aiki da cikawa”


“Zan biya dubu ɗari”


“Cikin satin nan kuwa zaki ji kyakkyawan labari, dan zamu yanka zaɓar ne mu haɗa da zagen hailarta ne, sai mu yi rubuta da wasu silkulle a saka a tulum sai a je can daji a inda babu mai zuwa a rataye tulon a ƙasan tulun za mu yi ƙaramar huduwa wanda ruwan zai riƙa fita kaɗan-kaɗan, yadda ruwan zai riƙa zuba haka jini zai mata zuba har sai ruwan ya ƙare sai mu sake yin wani. Ya sunan kishiyar taki?”




“Ummul khairi, dan Allah malam a taimaka min dan Allah na kawo kukana gareka, dan Allah a taimaka min”


“Karki samu damuwa ki komawarki gida kawai”


“Malam an bincika min ƙasar nan ? An duba lamurrana?”


“Bancika ba tukuna dan ban ƴi zaton zaki zo yau ba, kuma kin ga akwai mutane da yawa a waje, amman idan na bincika ko a waya ne zan faɗa miki”


“To na gode, dan Allah a bincika min ko zan koma gidan mijina”


“Karki samu damuwa, ƙasa zata bada bayanin komai”


Ta zube masa dubu ɗari kasa sannan ta tashi ta fito, zuciyarta cike da yaƙinin abunda Malamin zai aikata mata.


Har ta dawo gida tunanin zuwa karɓar magani take, akan shawarwarin da likitan ya bata, sai dai kuma ya faɗa mata idan har bata shan magani cutar zata bayyana kanta, kuma rayuwarta zata yanke.




NAMRA POV.


Ko da takwas da rabi tayi Maryam da Hinda har Aisha sun wuce school, da wuri Anty ta shirya ma Abbah breakfast, sannan ta zuba ma Namra nata, ita kuma ta ɗauki nata dana Abbah ta nufi part ɗinsa da shi, dan bata breakfast ita kaɗai indai har Abbah yana ɗakinta ne, sai dai tare da shi. Namra na cikin ci abinci sai ga Hajiya Barau ta shigo mata da nata breakfast, tana far'ah kamar gaske.


Wanda Anty ta zuba mata ma bata ci da yawa ba, balle na Hajiya Barau ko buɗashi ba tayi ba, sai dai tana jin ƙamshin ferfesun kayan ciki na dukan hancinta.
Tashi tayi ta wanka ta shirya cikin wasu tufafin sababin da Maryam ta ɗauko mata, tana cikin ɗaurin ɗankwali Anty Amarya ta shigo.
Ta jidaɗin ganin abincin da Hajiya Barau ta kawo ma Namra sosai, hakan ba ƙaranin faranta ranta yayi ba.


“Ai baki ma ci komai ba”


“Na riga na ƙoshi”


“Namra baki son cin abinci, wannan ma baki ci da yawa ba, gaskiya dole muje asibiti a duba lafiyarki, zan je na gyara sai kije ki gaida Abbah ki”


“Tau”


Ta amsa murya ƙasa-ƙasa tana jin kamar dai kar taje. Ɗankwalin ta aje ta ɗauki hijabin Anty ta saka ta nufi part ɗin Abbah tana wata tafiya kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.


da Sallama ta shiga sai ta tsaya can bakin ƙofa ta risina ƙasa ta gaishe shi, kanta na ƙasa tana mai jin kunyar haɗa ido da shi.


“Abbah ina kwana? An tashi lafiya?”


“Lafiya ƙalau”


Sai kuma ta rasa me zata sake ce masa.


“Mahaifiyarki ta faɗa miki sati ɗaya na yarda ki yi ko? Dan kin san na gargaɗe karki kuskura dako min gida da sunan fushi ko saki”


Idonta ya cika da hawaye, a take muryarta ta soma rawa.


“Abbah ba fushi na yi ba, na zo ganin gida ne”


“Ko minene dai na faɗa miki duk kika doso min gida da sunan saki, to sai dai mahaifiyarki ta tattara kayanta ku bar min gida, tun da kin zaɓi zama da shi sama da Mahaifin ki sai kije can ku ƙarata”


Da sauri ta ɗago kai ta kalli Abbah, sam bata yi tunanin abun nasa ya kai har haka ba.


“Inshallah haka ba zai faru ba Abbah, amman dan Allah ka yafe min kuma ka fahimce ni”


Da hannu ya yi mata alama da ta tashi ta bashi guri. Da sauri ta tashi ta fice tana kuka. Kamin ta ƙarasa part ɗin Anty Amarya ta tsaya ta share hawayenta, sannan ta shiga.
Lokacin Anty Amarya ta fito daga wanka tana cikin shiryawa, falo Namra ta koma ta zauna sai da Anty Amarya ta gama shirinta ta ɗauko jakarta ta fito suka fita tare.
Driver Abbah ne ya kai su asibiti, sun yi sa'ar ganin likita dan tun kamin su isa Anty ta kaira likitan dake duba su ta faɗa masa, sai yayi ma wata likita magana dan shi be shigo asibitin ba a lokacin.


Mutum biyu aka duba kamin ita, sannan ta shiga tare da Amarya. Bata ɓoye komai ba da taji tayi ma likitar bayani, ita kuma sai ta rubuta mata text ɗin jini da na fitsari, sannan ta tura gurin hoto, dan akwai buƙatar su ga abunda yake ƙasan mararta da take ji yayi mata tsaye gefe ɗaya.


Basu bar Asibitin ba sai da suka je aka musu hoton, aka basu sai suka wuce gurin ɗibar jini aka ɗibi jininta sannan suka bata wani roba ta shiga banɗakin gurin tayi fitsari ta kawo musu, sai suka je sai gobe ta zo ta karɓi results, daga suka koma gurin likitar suka kai mata result ɗin.


“Subhanallahi”


Ta faɗa lokacin da ta kalli hotonnan guda uku da suke guri ɗaya, sannan ta kalli Namra ta ce


“Me kika sha na zubar da ciki?”


Ba Namra har Anty Amarya sai da gabanta ya faɗi.


“Ban sha komai ba”


“Kin yi ɓari amman ko?”


Ta ɗaga mata kai


“Eh na yi”


“Amman ba kije asibiti ba?”


“Na je sai dai ban tsaya ba, saboda lokacin mijina be da lafiya”


“Kin yi kuskure gaskiya, da kin tsaya an duba ki ai, yanzu kin ga rabin cikin yana cikin mahaifarki, hakan ya haddasa miki wannan ciwon da kike ji, mahaifarki ta saki sosai har wani ɓangare na jikin mahaifar ya buɗe ya hudu, jiki be yi saurin ɗauke miki ba lokacin da kika yi ɓarin? Ke duk baki lura ba”


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Namra ta faɗa tana kallon Anty Amarya da tashin hankali ya bayyana a fuskarta.


“Yanzu likita me ye abun yi?”


“Za'ayi mata wankin mara ne, sai mu ɗorata akan magunguna, amman gaskiya akwai buƙatar tayi family planning na shekara biyu ko uku gudun karta ɗauki ciki har sai mahaifarta ta warki”


Kuka Namra ta saka tana dafe da cikin nata. Anty Amarya ta riƙa bata haƙuri, tana mamakin lamarin dan ita bata ma san lokacin da tayi ɓarin ba, kuma gani take kamar wani abu ta sha dan ta zubar da cikin.




KALSOOM POV.


Kwata-kwata yanzu bata gane lamarin Ezzah ta ɗauke ta kamar wata maƙiyiyarta, sam bata ma son zama falon idan Kalsoom na nan, abinci ma idan ba Doc ne yake gidan ba, sai ta ƙi ta koma can ɗaki ta keɓe kanta.


Bayan shi babu wata matsala da Kalsoom take fuskanta, ita kuma bata ɗauke ta matsala ba dan ba biye mata zata yi ba, zamanta da Doc lafiya ƙalau sai ƙarin so da ƙauna, ga ɗan cikinta tana raino gwanin sha'awa ɗan satin nan data samu har tayi fari sosai tayi ƙiba ta mulmule kamar ba ita ba, Doc har tsokanarta yake wai shi take tsotsewa ita tana ƙiba shi be gane ba.


Ita kuma ta san babu komai sai kwanciyar hankali da kuma kulawar mijinta da take samu a yanzu, ga Ulfah da Rafiq da suka zame mata tamkar ita ta haife su, dan ko maganar Mamansu basa yi, indai kaga wani baƙin hali to Ezzah da kicifin dan tafi kowa kishin uwarta yanzu.






500k words....




______________________________________________
Littafinan na kuɗi ne, idan kin san baki biya ba, karki karanta.
₦200 zaki turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.


Sai ki turo da shaidar biyan kudin ta wannan number 08036126660


DON'T READ IF YOU DIDN'T PAY...!




*PAGE - 45*


NOT EDITED ⚠


Sai da Yamma lis Anty da Namra suka dawo gida, bayan sun yi mata wankin mara sai da suka bata 6 hours suka ga condition ɗin ta sannan suka barta ta dawo gida.


Jikinta ya mutu sosai, ga tunanin dake zuciyarta, tana jin gajiya a tare da ita amman tunanin dake cikin zuciyarta ya hana ta tayi bachi bayan sun dawo gida.
Tana jin kamar ta labartawa wani damuwarta, sai dai kuma bata san yadda za su kalli abun ba, ace kamar Asim ya juya mata baya, sannan tana ganin idan har ta faɗa Anty ba zata barta ta cigaba da zama da shi ba, Abbah kuma ba zai yarda ta zauna a gidan ba.


Haka ta kwana ciki damuwa da tunani har garin Allah ya waye, karin safe ma sai da Anty ta tirsasa sannan ta ci.
Tana cin abinci tana kukan zuci, kukan da bata san ranar tsayawar hawayenta ba, kuka maraici amman bana rashin uwa da uba ba, kuka take kukan butulci bayan hallaci kukan nadama da bata da gani.


“Anty Namra kuka kike?”


Hindatu ta tambaya tana dafata, yanayinta duk ya canja ganim ƴar'uwarta cikin damuwa.
Hannu tasa ta taɓa fuskarta dan tabbatar da hawayen ya fito, sai kawai ta share tana murmushi.


“Ban ma san ya fito ba, baki iya sallama ba ne idan kin shigo?”


“Na yi sallama baki dai ji ba ne, me kike ma kuka?”


“Ba komai, dan Allah karki faɗawa kowa kin ji?”


“Tau, ga waya Anty tace na kawo miki Asim.ya kira”


Wayar ta sakarwa ido, kamar mai tsoron karɓa, ji take kamar ba wani abun ƙwarai bane zai faɗa mata, what if yace ya sake ta?


“Anty...”


Hindatu ta kira sunanta ganin yadda ta tsurawa wayar ido tana nazarin zuci. Sai a sannan ta kai hannu ta karɓa, ita kuma ta tashi ta bar mata ɗakin.
Wayar na fara ringing gabanta ya faɗi, ba ƙaramin ƙoƙari ta yi ba wajen picking ɗin call ɗin.


“Assalamu alaikum”


“Wa'alaikissalam Namra”


“Na'am”


“Kin je gida ba tare da kin sanar min ba, miyasa kika je? Kina son ki faɗa musu abunda ya faru ne? Na san ban kyauta miki ba, amman Wallahi sherin sheiɗan ne, ni kaina nasan ban kyauta miki ba, amman ina kishin ki ne Namra dan me zaki bar wani ya rako har cikin asibiti kin ganin hakan kyautawa?”


Hawaye ya fara bin fuskarsa.


“Kai yi min abunda wani be taɓa min ba, ko a mafarki ban za ci zaka aikata min ba, Asim ka yi taɓon da har na koma ga mahallacin na ba zai gogu ba, baka tambaye ni waye ba, baka bincike alaƙa ta da shi ba, sai kawai ka zarge ni, ka ɗaga hannunka ka mareni”


Ya fara mata kuka kamar gaske.


“Na san ban kyauta ba, kuma na cancanci ko wane irin hukumci, amman ki dubi girman Allah ki yafe min, dan Allah karki faɗawa kowa abun da ya faru tsakaninmu, Wallahi idan har ki ka bar zan iya shiga ko wane irin hali, haƙiƙa ni butulu ne kuma ajizi, Namra ki dubi girman ƙaunar dake tsakanin mu ki yafe min, ni har ganin nake kamar shiga tsakani ne”


“Ban faɗawa kowa ba, kuma ba zan faɗa ba, kuma na yafe maka”


“Na gode Allah yayi miki albarka, dan yaushe zaki dawo? Ko nasa Mama ta zo taje da ke?”


“Ba sai ta zo ba, zan dawo cikin satin nan”


“Yaushe?”


“Nan da kwana uku”


“Kwana uku yayi nisa Namra, da a'ce da hali sai ki dawo gobe ko jibi”


“Sai jibin dai”


“Na gode sosai Allah yayi miki albarka, duk suna lafiya ko?”


“Kowa ƙalau”


“Ina gaida kowa dan Allah”


“Za su ji”


“Na gode sai na ƙara kira”


Ta sauke wayar tana cigaba da hawaye.


“Na yafe maka, amman ba zan manta ba, zan zauna da kai saboda zama da kai ya zame min dole, son ka be amfana min komai ba Asim sai baƙinciki da damuwa”


Ta share hawayenta tana jin wani irin ƙuna da zuciyarta ke mata. Ɗan abincin da take ci sai ya fita ranta, ta tattara kayan abinci ta ɗauki tray ta nufi kitchen da shi, bayan ta aje ta dawo falonta zauna tana miƙawa Anty wayarta.


“Har kun gama”


“Eh wai tambaya yake yaushe zan dawo”


“Dika yaushe kika zo? Me kika ce masa”


“Nace masa sai Next week amman ya ce sai dai na dawo gobe, daker ya haƙura na kai jibi”


“Haba Anty Namra dika yaushe kika zo ma?”


Maryam ta faɗa. Anty tace


“Zan yi magana da shi ya bar ki kiyi ko wata ɗaya”


“A'a Anty kin san ba shida lafiya sosai ma, kuma bana son satin da Abbah ya bani ya cika ban koma ba”


Ɗaya bayan ɗaya Anty ta bisu da kallo, a tunaninta ko a cikinsu ne wani ya faɗa mata Abbah yace karta wuce sati ɗaya.
Maryam ce ta fara tsarguwa da kallon Anty ta yi magana.


“Wallahi ba ni na faɗa ba”


Aisha
“Ni ma dai”


Hindatu.
“Balle kuma ni”


“Waya faɗa? Ko muna da aljanu ne a gidan?”


Namra tayi murmushi, irin murmushin nan na ƙarfin hali ka danne baƙincikin ka.


“Ba suka faɗa ba, Abbah ne ya faɗa min da kan sa”


“Yaushe?”


“Jiya da naje gaishe shi, yau ma ya nanata min”


Anty tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai dai bata jidaɗin da Abbah ya faɗama Namra haka ba.


“Akwai abubuwan da kike buƙata ne? Dan a siya da wuri kar lokaci ya ƙure, ko kuma kuɗi zan baki kije can ki siya?”


“Kuɗin zai fi, dan ɗaukar kaya a nan ma ai aiki ne”


“Amman Namra ba zai yarda ku dawo nan ba?”


“Kwana ki ma yayi min maganar haka, amman nace ya haƙura har yaji sauƙi sosai sannan mu dawo”


“Gaskiya kam zama a nan zai fi, kim ga nan zai fi muku kuma kin ga nan ko ba komai kina kusa da mu”


Sallamar Doc Faruk ne yasa suka katse firar da suke suka amsa sallamar suna masa sannu da zuwa.
A kujerar da Namra take zaune ya zauna, kasancewar ta zaman mutum uku ce, sai ya soma gaiswa da Anty cikin far'ah, tun da shi ba baƙon gidan ba ne.
Maryam da Hindatu da Aisha sai duk suka tashi suka bashi guri, Anty ma tana gama gaisawa da shi, ta shige ɗakinta dan tasan abunda ya kawo shi, daman ita ta kira shi, ganin hakan kamar zai fi sauƙi tun da likitan gida ne.


“Daman akan maganar planning ne Anty tana tsoro kar ayi mai side effects, so ni abunda naƙe ganin ya fi shine ki yi na roba, saboda idan an saka mishi kin ga sai lokacin yayi sannan za'a cire, ba kamar allura bane da a za'a riƙa yi duk months, kuma kin ga shan ƙwayoyin zai iya ƙara miki matsala ma a mahaifa, za a iya tsuke miki bakin mahaifa”


“Amman robar idan an saka ba shi da wata illa ne?”


“Eh to kin san komai karɓa karɓa ne, amman gaskiya baya da matsaloli kamar sauran, kuma kin ga shi a duk lokacin da aka tashi cire miki za'a iya cirewa”


“Amman yanzu ina katsina da zama idan na saka ta nan za'a iya cire min a can?”


“Za'a iya cire miki mana, amman idan son samu ne inda aka saka miki a cire miki ita, saboda aikin wani ba shine aikin wani ba, kuma idan ma son samu ne likitan daya saka miki ita ya zama dik lokaci shine ya ke duba ki”


“Amman kana ganin ba zai

Please Login or Register in order to submit comment