Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

lokacin da nasa ayi min bincike akan ka”


“Bincike kuma?”


“Eh mana ai duk wanda xaka xauna da shi kana da bikatar sanin ko waye shi, gudun abinda zai je ya dawo amman miyasa kace min baka da mata bayan kana da ita?”


Ya ɗan sosa kansa yana cire hannunsa daga abincin daya fita ransa.


“Wallahi Hajiya naga kamar ba ki son mai matar ne shiyasa, ni kuma bana son na rasa wannan aiki na ki”


Tayi murmushin ƙasaita.


“Ba mai mata ne bana so ba, yadda nake son a min spending time ne nasan mai mata ba zai iya ba”


“Zan iya wallahi dan ni na fi ƙarfin matana na, duk abinda kike so zan miki”


“Hakan yana da kyau, namijin duniya irin ka na ke so”


Ya jidaɗi sosai.


“Anything for you Hajiya”


“Gobe aikin ka xai fara, yanzu idan ka gama, sai kaje gurin mai gadi ya nuna maka wasu abubuwan”


“Hajiya ai ni na gama ma”


“Ka daina kirana da Hajiya ka kira ni Sadiya na”


“Ai da nauyi sai dai ko nace Anty Sadiya”


Wata harara ta watsa masa.


“Na yi maka kama da Antyn ka ne?”


Kallonta yayi a zahiri kam tayi yi, dan wannan yasan ba sa'arsa bace sai dai kuma bata isa haihuwarsa ba.


“A'a Sunan ne ba zan biya faɗi a fili ba”


“To ka riƙa ce min Sadiya Babe, amman idam cikin mutane ne ka riƙa kirana da Hajiya na”


“To am gama na gode”


Har ya juya tace


“Kuma bana son sa ido, kar ka damu da baƙina ko ƴaƴan 'uwan da suke zuwa gidan nan kai dai kawai ka yi aikin ka”


“Inshallah ba zaki same ni mai tsaɓa uwarnin ki ba”


“Albashin ka 100k per month”


Da sauri ya kalleta fuskarsa ƙarara da mamaki, sai gashi kurfane ƙasa yana mata godiya.


“Allah ya ƙara miki arziki Allah yayi miki yadda kika min”


“Amin kai dai ka cigaba da biyayya kawai zaka iya samun fiye da haka ma”


“Inshallah”


“You can go, sai ya nuna ma ɗakinka da kuma aikin ka”


Ya juya ya fice yana jin wani irin nishaɗi da be taɓa jin irinsa sai yau.




*ABDOOL POV*


Ko da ya isa gida duka ƙanensa sun wuce scul Ummi ce kawai a dinning sai Amira suna karƴawa. Tun daga nesa Ummi ta hango nishaɗin dake fuskar ɗanta. Har ya ƙaraso kusa da su ya zauna a kujera daya saba zama.


“Ina ka je da safen nan haka?”


Be son maganar gaban Amira, sai kawai yayi murmushi ya ɗauki kofi ya soma haɗa ma kansa tea.


“Good Morning Yaya”


“How are you dear..”


_Dear_ taji kalmar har cikin ranta, shi kuma ya amsa mata ne da murmushi kuma ba tare da wata manufa ba.

“Ummi yau zan koma fa”


“Yeah i know i just want to know the secret of your smile?”


Shi kansa be san yana murmushi sai yanzu da Ummi ta yi magana. Yayi saurin kawar da murmushin


“Nothing”


Ya miƙe tsaye yana kallon agogon hannunsa.


“Around 9: za mu tashi”


Amira ta ji babu daɗi. Sai ta tashi jiki a sanyeye ta nufi ɗakinta, sam bata son Abdool yayi nisa. Komawa Abdool yayi ya zauna ganin Amira ta shige ɗaki.


“Ummi ina wata da na taɓa baki labari nace miki na ganta a pharmacy da hospital har na ce ina son ta sai tace min ita matar aure ce?”


“Yeah yeah na tuna what happed?”


“Ita ce take haya a gidan Amal ita da mijinta, sune suka yi wuta yanzu sun koma bq da zama saboda mijin nata talaka ne sasai”


“So...?”


“Shi ne sai na siya musu gidan...”


“Saboda me?”


“Just”


“You still love her ko?”


Ya ɗan yi shiru yana tambayar kansa. Kamin ya ɗaga kai alamar eh


“Yeah and i d....”


Be ƙarasa ba Ummi ta mikr tsaye tana dakan dinning ɗin ta katsa masa tsawa


“That it, baka da lada baka yi da Allah ba, kai baka ji kunyar kanka ba ace matar wani kake so? Kai zaka so wani ya kashe maka aure ne?”


“Ummi ba auren ta zan kashe ba, i just help”


“Help? You want to use her dan kasan mijinta talaka ne, ka kashe mata aure huh? Duk ƴan matan garin na ka rasa wacce zaka so sai matar aure Abdallah mike damun ƙwaƙwalwarka, abunda kake be kamata ba, kallon ta a gareka haramun ne, kamata yayi ace kana yaƙi da sheɗen ba wai kana bari na kai zuciyarka ga halaka ba.


Dole zan yi magana da Mai Martaba dole ayi maka aure ko baka so, dan na fahimci baka da hankali”


Cikin fushi ta ƙarasa maganar tana mai ƙyamar abunda ɗan ta ya aikata. Shikam kasa cewa komai yayi dan be da bakin magana.
Duka abunda suke Amira na jikin ƙofar ɗakinta tana sauraensu duk da akwai ta zara, dan da farko bata ji abunda Abdool da Ummi suke tattaunawa ba sai da Ummi ta ɗaga murya tana masa faɗa.


‘Wace mai sa'ah ce wannan wanda Abdool yake so? Me take da shi?’


Tambayar da tayi ma kanta kenan tana mai ƙarasawa gaban modubi ta dubi kanta.




*HILAL POV*


Yana isa asibitin ya wuce ɗakin da Rafiq yake, zaune ya same shi yana kuka. Amina da wata nurse na kusa da shi tana lalaɓashi, bakinsa ya karkace sai dalalarda yawu yake kamar musaki, ko kuma irin yaran na dolaye. Yana ganin Hilal.ya riƙa ƙokarin sauka yaje inda yake, sai Hilal ya ƙaraso da sauri kusa da shi cike da tausayawa ya ɗauke shi.


“Shiiii Daddy ya zo”


“Good mornig Sir”


Nurse ɗin ta gaishe shi sannan ta fice, Amina ma ta ɗora da nata gaisuwar tana nuna masa abincin da Hajiya tace a kawo masa.


“Okay”


Ya faɗa yana ciro wayarsa dake ringing.


“Ya aka yi?”


“Wallahi nayi lallaɓa Dady yace shi sai ya saka ƙarar”


“To shikenan aje kotun ai sai Allaura ta tono garma, amman wannan abun da za ayi ba zai na ƙi tsayawa Kalsoom ba she's my wife”


Ya kashe wayar ya maida Aljihu. Amina sao kallonsa take tana mamakin furucin da yayi, a zuciyarya ta ƙumshe zance da sunan dai ta je gida ta faɗawa Hajiya.


*RASHIDA POV.*


Bayan Rashida ta ƙare waya da shi ta cigaba da aikinta, kamar yadda ta saba. Sai da lokacin tashinta yayi sannan ta shiga tayi ma Alh Bashir sallama ta fito. Kai tsaye gidan Mom Shuraim ta nufa. Ita kanta tayi mamakin ganin Kalsoom mace da zata shekara bata kira a waya ba ma balle kuma ziyara amman yau gata gidan ta.


Abinci ta kawo irin nasu na ƴan nijar ya ji albasa har ya gaji, da ruwan sanyi sannan ta zauna suka soma firar yaushe gamo. A cikin firar na Rashida take labarta mata mutuwar aurenta da kuma abinda Kalsoom tayi mata. Mom Shuraim ta cika da mamaki matuƙa. Sai Allah wadai take tana tsinewa Kalsoom.


“Ke dai bari wallahi ina cikin matsala shiyasa na zo gurin ki ko kin san wani malami inda zamu iya zuwa a kare wannan asirin dam ance min ƴan nijar kan suna da abubuwa da yawa”


Mom Shuraim tayi shiru dam ba kowa bane yake son buɗe sirrinsa.


“Ai ko nan akwai su”


“Ni dai ki taimaka min idan zaki kai ni.can nijar ɗin ko kuma ki haɗa da wanda zata kai ni amman fa idan kin san mai aiki na gwarai”


“Toh Yanzu dai sai na bincika can gida idan na yi waya da su, zan faɗa miki”


“To na gode zan kira ki inshallah”


“Amman xaki.iya xuwa har can?”


“Wallahi ko chana ne zan iya xuwa balle nijar”


Dariya Mom Shuraim tayi ta rakota har ƙofar gida tana ta tunanin maganar a zuciyarta, sai da Rashida ta miƙawa yaranta 500 kowanensu sannan ta shiga motar ta f ɗauki hanyar gida. Ba dan zuciyarta ta gamsu Mom Shuraim ɗin zata kai ta ba, ɗan bata ga alamun haka a tare da ita ba.
Tunaninta duk ya tattara ya koma gurin abokanta, har ta isa gida tunani take wacece cikin ƙawayenta take da wannan shige shigen malamai.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *58*


Cikin rashin daɗin rai ya bar katsina saboda faɗan da Ummi tayi masa, shi kansa sai yanzu ya ke jin rashin daɗi akan abinda ya aikata. Sai dai shi yasan be dan wata manufa ba, be kuma yi ba dan ya kashe mata aure, sai ya yarda da abu ɗaya, shine son ta abu ne kuma da ba zai iya cirewa kansa shi ba amman yana ta yaƙi da zuciyaraa wajen gani ya anta da Namra a duniya.


Damuwarsa bata hana shi aikinsa ba, amman duk wanda ya ganshi a ya san akwai damuwa sosai a tare da shi. Maganar Ummi ta tsaya masa a rai na auren da ta ce zata ma Mai Martaba magana ayi masa, wata ƙila shi ne fita a garesa, sai dai yana tsoron auren mace da baya so gudun kar ya cuci kansa ya cuce ta.
Har gobe babu wacce yake gani idan ya rufe idonsa sai Namra, dukan mafarkansa akan ta ne, miyasa baya da tunani sai matar wani? Dan me zai riƙa mafarkin da babu ranar farkawarsa.


“What's wrong with me? There's something inside me, this is not me it's another Abdool behind me”


A fili yayi furucin ya miƙe tsaye ya nufi window office ɗinsa ya tsaya, yana hango wasu sojoji dake farati a rabar wajen. Kallonsu yake amman hankalisa baya gurin, can kuma ya ɗauke kansa ya juyo ya jingina da gurin yana kallon office ɗinsa.


Wayarsa dakr kan dinning tayi ƙara, alamar saƙo, kallo ɗaya yayi ma wayar ya ɗauke kai, yana cigaba da tunanin abinda yake ganin kamar shine a gare shi.
Ɗan risinar da kansa yayi yana shafa dogon hancinsa, tare da jan dogon numfashi.


Ya samu minti talatin tsaye a gurin sannan ya nufi kujerar zamansa, ya koma ya zauna yana lilo. Hannu ya kai ya ɗauki wayarsa. Saƙon sama ya buɗe wanda aka aiko masa da baƙuwar number.


_If you love something, let it go. If it comes back, it was meant to be. If it does not, hunt it down and kill it. *Smile* good evening hope you had a nice day and a pleasant evening as well._


*AMIRA*


Ya ɗan taɓe baki yana maman inda Amira ta samu waya bayan yasan bata da waya a can baya.


“Maybe Ummi ta bata”


Ya faɗa a fili sannan ya kai hannu ya ɗauki telephone ɗin dake saman tebur ɗinsa tana ringing.






*AMIRA POV*


Murmushi tayi ta tana wanda yasa Haleema kallonta.


“Kin saka number?”


“Eh na saka sai ta wa kuma?”


“Sai ta Meesha”


Haka ta riƙa bata number kowa na gidan cikin har da Amal da Shukura. Ɗaya bayan ɗaya Amira ta riƙa sawa har ta gama, sannan ta kalli Haleema tana murmushin jindaɗi tace


“Na gode sosai Haleema Allah ya saka miki da alheri”


“Ba komai ai nasan zata rage miki kewa ko da game kawai”


“Sosai ma wallahi, Allah ya bar zumunci”


“Karki damu ai komai yi ma kai ne”


Ya faɗa tana murmushi sai ta tashi ta nufi ƙofar fita tana dannar wayarta. Amira kan wayar ta sakarwa ido tana kallo, farincikin saƙon data aikawa Abdool take, bata damu da rashin reply ɗin da be mata ba, daman bata sa ran zai mata ba. Rumgume wayar tayi a ƙirginta, wani kalar nishaɗi ne ya same ta, marar misaltuwa. Tunawa da faɗan da Ummi tayi masa akan wata yasa ta jin babu daɗi, that's means akwai wace take ransa kenan, bata gane dalilin faɗan na Ummi akansa ba, sai dai taji yana faɗin bashi da lada, sai kuma maganar da tace masa idan shi ne zai so wani ya kashe masa aure.


‘Wacce yake so matar aure ce ko kuma an mata engaged ne? Akwai buƙatar na san ko wacece wata ƙila tana da wasu halaye da Abdool yake da su. Sai dai taya? Taya zan nuna na san wata da yake so? Idan har na nuna hakan za su ce ina musu sa ido, bayan kuma sun yarda da ni’


A zuci take zancen a fili kuma sai ta ce


“What's the solution?”


Kanta ta ɗaga sama tana kallon pop.


‘An ya zan iya bari wannan damar ta wuce ni? Ace na shiga rayuwar Abdool kuma ba bari wata ta ƙwace min shi? Anya zan iya barin wannan daular ta wuce ni? Zuciyata a yanzu Abdool kawai take so mutumen dana saɗaukar da rayuwata akan sa’


Ajiyar zuciya ta sauki, tana ta zancen zuci, sai dai har aka kira salla bata samu wata gamsasshiyar mafita ba. Unƙurawa tayi ta tashi ta nufi ɗakinta tana auna irin abunda za tayi ma Abdool wannan karon.


“Amira...”


Daf da zata shiga ɗakinta Meesha tayi mata kiran tana nuna mata ɗakin Ummi da alama Ummi ce take kiranta. Juyowa kawai ta yi ta nufi ɗakin Ummi cikin ladabi. Kusa da Ummi ta zauna ƙasa ta matse Ummi sosai kamar zata shige cikinta.
Sai da Ummi ta gama abinda take sannan ta cire madubin idonta ta kalli Amira a natse ta ce


“Amira ina tunanin yanzu hankalin ki ya kwanta, natsuwarki kuma ta dawo jikin ki, zama haka ba shi yi, ya kamata ace izuwa yanzu kina gaban iyayenki, ba mu san halin da iyayen ki suke ciki ba, i'm mother too i know how it feel like idan ɗan ka baya kusa da kai, musamman mace”


Ɗagowa tayi ta kalli Ummi idonta cike da ƙwalla.


“Dan Allah Ummi ki min haƙuri ki bar har nan gaba, ni kaɗai nasan halin da nake shiga idan na tuna da iyaye, kuma nasan dole na koma garesu”


Ajiyar zuciya Ummi ta sauke.


“Ba komai Allag yasa haka shi ya fi alheri, Haleema ta baki waya ko?”


“Eh ta ba ni”


“Yana da kyau ki kira wani daga cikin familyn ki ku gaisa”


“Zan yi ƙoƙarin yin haka Ummi na gode”


Ta miƙe tsaye cikin rashin kuzari ta bar ɗakin. Ɗakinta ta dawo ta xauna gefen gado tana kuka, ita kanta tasan abar tausayi ce idan ta tuna da rashin iyayenta.


“Na rasa iyaye saboda kai Uzair, ka cuce ni ka yaudare ni, kai ne ka saka rayuwarta ta koma a haka, na rasa iyayena da duka family amman ba zan rasa Abdool da familyn su ba, ba zan zama loser ba”


A fili tayi furucin zuciyarta cike da yaƙinin abinda bakinta yake faɗa.


“I have to make it work, i can't lose them both, i deserve happiness too”


Saman gadon ta faɗa ta rumgume filo tana wani kuka mai taɓa zuciya.


“Kin cuce ni Namra abotarmu bata amfana min komai ba sai nadama da baƙin ciki, nayi nadamar sanin ki a rayuwata, You and Uzair have to paid for what you both did to me”


Wani kuka take Sosai tana buga ƙafafunta kamar wata ƙaramar yarinya. Turowa ƙofar ɗakin da Haleema tayi ne yasa ta saurin tashi ta goge hawayenta, gabanta sai faɗuwa yake tana ala-ala idan bata ji zancen da ta yi ba.
Kusa da ita Haleema ta zauna cike da tausayawa, dan akan kunnenta Amira ta faɗi komai.


“Kin cancanci farinciki Amira, ba kiyi ƙarya ba kin cancanci komai daga wanda kika sadaukarda ranki gare shi, mu kuma kin cancanci soyayyarmu tun da kika ceto ɗan'uwan mu”


Hannayenta Haleema ta kama, ta riƙe


“Ba zaki rasa mu ba, ba zaki rasa familyn Abdool ba har a bada”


Da mamakin Amira take kallonta kamar wacce bata fahimci inda zantukanta suka dosa ba.


“Na daɗe da fahimtar kina son Ya Abdool, tun lokacin da kika shigo gidan nan, na lƴra da ke Amira kina rasa natsuwarki idan Abdool yana cikin gidan nan, a yanzu ma bayan Number Ummi Numbersa kika tambaya a na biyu, kina son Abdool Amira i can't hide it”


Rumgume ta Amira tayi a ƙirginta gamgam, tana kuka.




*ASIM POV.*


Bayanai gadi ya gama nuna masa ko ina na gidan, sai ya dawo falon dan faɗa ma Hajiya yadda suka yi da mai gaɗin. A inda ya barta a nan ya same ta tana zaune ta ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaƴa tana kallon ƙofa kamar ta san da shigowarsa.
Saman kujera ya zauna dan shi yanzu jin gidan yake kamar nasa, yayi sallama sai dai bata amsa masa sallamar ba har ya zauna tana murmushi.


“Hajiya an nuna min komai, gida mashallah”


Sai a lokacin ta buɗe baki tana masa magana kamar mai nauyin baki.


“Amman bana son ka faɗawa kowa abinda ka sani game da ni”


“Hajiya ai ban san komai ba, balle ma na faɗa, kuma ni bana daga cikin mutane nan masu yawan surutu”


“Zaka sani ne ai shiyasa nake gargaɗin ka tun yanzu, zaka san komai a kai na, tun da har ka furta zaka iya yin komai”


“Wallahi zan iya miki komai Hajiya”


“Yayi kyau, kaga ɗakin ka?”


“Eh yayi kyau sosai”


“Anjima zan baka kaje ka siyo abubuwan da babu, sai ka sawa ɗakin, saboda ina son ya zama ɗakin ka na ainahin, so nake ka manta da cewar kana da wata mata dabam”


“Ba komai Hajiya komai kika ce shi za'ayi inshallah”


“Thank you you're very loyal”


Ta tashi ta nufi ɗakinta tana murmushi, har a zuciyarta take jin Asim dan taga alamun zai iya komai na neman kuɗi, haka take so daman.


Shi kuma sai daɗi yake ji yadda take masa, ko kaɗan be kawo komai a ransa ba, abu ɗaya yake tunanin zata nema a gunsa, wata ƙila ba zai wuce sex ba, kuma he's ever ready indai wannan nan ne, sai dai kuma shi ɗin kansa yana buƙatar sanin ko wacece ita, dan be ga alamun tana da yaya ba.
Zuciyarsa cike da nishaɗi ya fiddo ƙaramar wayarsa ya shiga duniyar facebook. Notifications ya tarar mai yawa, ga massage da friend requests. Rabon da hau duniyar facebook tun Namra tana amarya tana ɗan cikin yanayin jindaɗin nan kamin komai ya canja.
Notifications ɗin ya fara dubawa yaga na gani sannan ya shiga massage, ya samu mata da yawa daga cikin masu masa massage kansancewar hoton dake profile ɗinsa yayi kyau, sosai idan ka ganshi sai ka ɗauka wani shege ne.
Sama-sama ya amsa massages ɗin sannan ya duba friend requests yayi accepting wasu ya bar wasu.


Be wani daɗe ba ya sauka daman be cika jindaɗin hawa da ƙaramar waya ba, rabon da yayi chat da babbar waya kuma tun yana farko farkon scul ana yayin karyar nan.


Saukowar Hajiya Sadiya ne yasa shi ɗaga kai yana kallonta. Sai kuma ya sauke irin wai shi ladabi tun da ita ce boss. Keys ɗin mota ta jefa mishi tare da Atm.


“4782 shine password ɗin, ka siye duk abunda ya kamata, ɗan bana son ƙazanta”


Ya ɗauka ya miƙe tsaye har wani zumuɗi yake, zuciyaraa fes.


“Toh Na gode sosai”


Bata amsa shi ba, shi kuma be damu da sai ta amsa ɗin ba sai kawai ya fice yana auna yadda Allah ya maida shi wani a dare ɗaya.
Be sa ko wace mota bace har sai da ya danna makulin tayi ƙara sannan ya nufi motar ya buɗe ya shiga.


‘Kamata yayi na siyar da gidan nan, idan ya zo sai na riƙa juyawa ina siyen zinari ina sai dawa, ga wannan albashi walh nan da nan za ka ga na yi kuɗi, sai dai kuma ban sani ba ko bata son na haɗa da wani aikin, wata ƙila ma zata iya min kyautar mota fa, ji yadda ta yarda da ni nan take har da ba ni atm ɗinta ta faɗa min password, daman mai haƙuri mawadaci’


Shine abinda yake ta saƙawa a zuciyarsa yana tukin motar da yake hango kansa a matsayin wani ƙaramin alhaji.


*RASHIDA POV*


Ajiyar xuciya ta sauke har da hawayen ƙirƙira dan kawai Teema ta tausaya mata, haƙiƙa ciwon ƴa mace na ƴa mace ne Teema ta tausaya mata sosai har tana jin kamar tayi mata maganin matsalarta yanzu.


“Ki kwantar da hankalin ki Rashida, zan taimake ki akwai wani malami yana nan ɗan ƙauye sokoto ne, wlh malamin har ƙasa ƙasa ake ɗaukarsa yayi aiki, aikinsa kamar yankan wuƙa yake, a take komai kike so zai miki zan kai ki gurinsa idan kin shirya”


“To ai ni kullum a shirye na ke, ni ko yanzu kika ce muje zamu je wlh”


“A'a ban da yau dan ban shirya ba amman dai gobe ki zo da wuri sai mu tafi”


“To inshallah zan zo”


“Amman aikin ki fa nasan ba hutu kuke samu ba”


“Karki damu da aikina wannan ita ce muhimmiya”


Teema tayi dariyar mugunta. Tashi Rashida tayi, Teema ta raka ta har gurin motar ta ta shiga motar tana ɗagawa Teema Hannu.
Daga gidan Teema ta wuce Asibiti dan karɓar maganinta, a mota ta tsaya ta saka niƙabi da hijab sannan ta fita.
A wani gurin ta tsaya kusa da inda ake ba da maganin, tana kalle kalle mutane, daman haka take duk ta zo wai gudun kar taga wanda ta sani. Duk da wannan shine zuwanta na biyu.


Bayan ta gama dube dubaneta ta shiga ciki ta ga likita, ya ƙara mata shawarwari, sannan ta fito ta nufi gurin karɓar maganin kai tsaye. Security dake gadin ƙofar asibitin ce ta saka ta cire nikaɓ ɗinta dan haka dokar asibitin ta gada, Rashida bata damu ba ta cire niƙab ɗin daman ko wacan zuwan da tayi sai da tasa ta cire shi.


Da fargaba ta kunna kai a gurin tana ɗan kallon mutane ƙasa-ƙasa, gabanta sai faɗuwa yake kamar zai faɗo. Kamar daga sama taji an dafata ana ƙoƙarin juyowa da ita, juyowar da ta yi sai kawai suka yi ido huɗu da Safiya cikin Uniform ɗinta.
Wani irin kallo Safiya take mata kamar wacce ta rude cox she's can't believe Rashida ce ta gani a nan ƴar'uwarta jininta.


Ita kanta Rashida mamakin ganinta take, dan iya saninta wannan ba asibitun su bace, ya aka yi ta zo nan me ya kawo ta.? Yawu Safiya ta haɗe ta wuce da sauri ta fita daga gurin gudun kar wani daga cikin manyan su ya ganta, daman fitowarta kenan daga wani ɗakin ta hango mai kama da Rashida, ashe ba kama bace, ita ɗin ce amman mai zai kawo Rashida HIV/TB unit.? Shine abinda ya tsaya mata a rai.
Miƙewa Rashida tayi cikin dakewar zuciya ta cigaba da tafiya tana son ɓatarwa da Safiya da lissafi, sai dai kuma yanzu bata san liyin da zata bi, tb ko hiv?


*HILAL POV*


Asibitin ya wuni, da rana ma Hajiya ce ta kawo masa abinci. Duk wanda ya zo sai ya tauyasawa Rafiq ganin yadda ya koma musaki sai dalalar da yawu yake. Tuni Hilal ya ɗosa shi akan magani, yasa aka sake masa wasu hotunan dan ganr ainahin matsalarsa.
Ƴan'uwansa da dama sun yi ta xuwa ganin ɗan nasa, ƴan uwan Rashida ma sun zo, sai dai ba sosai ba, Dady Kalsoom ma ya zo shi da Momy, duk da suna jin nauyi ganin kamar ƴarsu ce ta aikata abun.


Sai da yayi ma Rafiq Alurra bachi sannan ya rufe ɗakin. Ya koma office ya cigaba da aikinsa, bayan ya gama, ya sake leƙa ɗakin yaga har yanzu bachi yake. Sai kawai ya nufi gurin motarsa dan yana buƙatar taje gida yayi wanka.
Yana hanyarsa ta tafiya Hajiya ta kira shi wai zata shigo da dare akwai magana mai muhimmanci da take son suyi, shi dai da to kawai amsa mata ba dan ransa yana cikin daɗi ba, ya faka a rabar gidan ya fito jiki ba ƙwari ya shiga ciki.
Tun a falo gabansa ya soma faɗuwa jin sautin kukan Kalsoom, da sauri ya karasa ɗakinta, sai dai kamin ya shiga ya ji ba acan kukan yake fitowa ba, a ɗakin su Ezzah ne. Ƙarasa yayi ɗakin ya tsaya daga jikin ƙofa yana kallonta. Juyowa tayi ta kalleshi da idonta da suka yi ja saboda kuka.


“Haƙiƙa ina son ka Hilal, dukan abunda ya dangance ka ina sonsa ko da kuwa abun nan mai cutar da ni ne, miyasa zuciyarka ta yarda na aikata bayan ban aikata ba? Ka raba ni da ƴaƴanka Hilal bayan yanzu sun zamo jinin jikina, ban aikata abinda kake zargina da shi ba Hilal Wallahi ban aikata ba”


Ya rumgume hannayensa yana mai jingina da jikin ƙofar.


“To waya aikata?”


“Ban sani ba, amman na rantse maka da Allah ban aikata ba, idan har na aikata Allah ya isar masa ya saka masa, kuma ya bayyana gaskiya”


Jikinsa yayi sanyi sosai, yasan ba zata yi ma kanta wannan mugun furucin ba. Kasa cewa kamai yayi sai kawai ya juya ya nufi ɗakinsa. Saman gado ya zauna, ya dafe kansa dake masa wani zafi.


Jin yayi ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, ɗagowa da zai ya ga hannunta rike da ƙur'ane da dukan alamu rantse masa zata yi. Da sauri ya tashi ya ƙarasa inda take.


“No need Please ki aje ƙur'anen nan Kalsoom”


“Rantse maka zan yi

Please Login or Register in order to submit comment