Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba, shi dai ya mai da hankalinsa gurin tuƙinsa, ita kuma hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma gida da tunanin inda zata kwana yau a garin kaduna. Ganin sun shiga GRA har suna ƙoƙarin wucewa bata ce ga inda za a sauke ta ba yasa yayi mata magana.


“Malama mun shiga GRA ɗin fa”


Sai kawai tayi shiru ba dan kuma bata ji shi ba, sai dai bata san abunda zata ce masa ba. Hakan yasa ya ƙara maimatawa yana mai rage gudun da yake.


“Gaskiya ni ban san inda zanje ba”


Juyowa yayi ya kalleta.


“Baki san sunan mai gidan ba ne? Kuma baki da number waya?”


“Ban sani ba, kuma bana da number, sau ɗaya na taɓa zuwa”


“Amman irin wannan tafiya ai it risk, ace baka da number wanda zaka sauka gunsa kuma ba kan guri ba?”


Tayi shiru bata ce komai ba. Sai a yazu take nadamar zuwan da tayi a kaduna ita kanta ta san tayi wauta.
Jin bata ce komai ba yasa ya ce


“Ina zan sauke ki dan ni akan aiki na ke”


“Wallahi idan ka sauke ni ban san inda zanje ba, dan bana da kowa a kadunar nan sai Allah, tun da ban san gurin wanda zan sauka ba”


Cikin muryar kuka tayi maganar, juyowar da zai ya kalleta sai kawai yaji shesshekar kukanta. Baya iya ganin hawayen idonta dan Napep ɗinsa bata da wutar ciki wance wasu suke sakawa, hasken dake gefen titin be iya ya haska fuskarta har yaga hawayenta ba,amman a yadda ya karanta kamar tana cikin wani hali ne.


“Bawai Allah ke mutum ce?”


“Ni mutum ce wallahi kuma ba cutar da kai zan yi ba”


A nan ta saka ƙafarta ta sauka daga cikin Napep ɗin ta saka hannunta a jaka ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa.


“Ba ni canji”


Ta faɗa tana ta ƙoƙarin tare kukanta dake son fitowa. Kasa karɓar kuɗin yayi kuma ya kasa tafiya, kallon fuskarta yake dan yanxu hasken gurin ya haska fuskarta, bata yi masa kama da mugayen mutane ba, jikinsa be bashi zata cutar da shi ba, hakan yasa shi idan har ya barta a nan gurin be kyauta masa ta, kuma besan abunda zai same ta ba tun da tace masa bata da kowa sai Allah.


“Shiga mu je”


“Na gode”


Ta faɗa tana share hawayenta, sai ta shiga Napep ɗin da sauri. Tun da ya soma tuƙin be tsaya ko ina ba sai malali, a mararraba ya tsaya ya miƙa ɗari da hansi aka bashi canji sannan ya ƙarasa ƙofar gidan na su mai cike da rufin asibiti, dan a kira su da talakawa ba kasancewar suna da rufin asiri da wadatar zuci. Sai dai a zahiri kan talakawa ne sosai masu ginin bulu wanda ba ayi ma filistaba.


“Fito muje”


Ya faɗa bayan ya kashe Napep ɗin. Cikin sanyin jiki ta fito tana dansar bakumi saboda mugun murɗa da mararta take mata. Yana gaba tana biye har suka shiga cikin gidan mai ɗauke da ɗakuna uku, duk da dare ne hakan be hanata ganin yalwantaccen tsakar gidansu ba mai ɗauke da bishiyar mangoro guda biyu ɗaya a jikin ɗaki ɗaya kuma a tsakiyar gidan.


“Neine (Inna da yaren fulatancin) ga baƙuwa”


Wacce saurayin ya kira da neiner ta miƙe daga saman tabarmar da take ta nufo Namra tana murmushi.


“Maraba maraba laƙe marhabun baƙonƙa annabin ka, siter ƴata sita (Zauna zauna)”


Ya faɗa lokacin da take ƙoƙarin zaunar da Namra saman tabarmar da take zaune. Namra ta zauna tana kallon yaran gidan da suka kewaye waya suna kallon india hausa a wata ƙaramar wayar hannu. Gaba ɗaya hankalinsu ya tattara ya tafi can sam basu ma san da zuwanta ba.
Neine da kanta ta shiga ɗaki ta ɗauki ma Namra tuwon masara ta aje mata gabanta, sai ta nufi wani ɗan madaidaicin tulu ya bulbulo mata ruwa a kofi ta kawo mata tana mai sakar mata fuska kamar ta santa.


Shi dai yana daga can gefe yana bawa cat ɗinsa kifi, amman hankalinsa yana gurin Namra yana kallon yanayinta.






-----------------------------------------------------------------
I PITY RASHIDA 😢
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *64*


Suna ta gaba-gaba suna tare Abdool kamar wanda wani abu zai same shi, sai kirari suke masa wasu na ture mutane dake gefen gurin dan Abdool ya samu hanya. Mutane sai kallo a ke wasu ma har sun wuce sai suka dawo ganin duka numbobin motar an saka YARIMA ABDOOL, duk wanda kuma yaga jajaye kaya yasan sarki ne ko kuma ɗan sarki.


Abdool be nuna tausayi a fuskarsa ba, na ganin irin raunin da aka yi ma Lamido, sai dai a can zuciyarsa ne yake tausayinsa ganin yadda jini yake masa zuba a kai kuma ya riƙe ƙafarsa sai cizar baki yake alamar yana jin zafi sosai, kowa yaga yadda Napep ɗin tasa ta yi sai ya tausaya masa duk ta lalace kai baka ce ma wanda yake ciki zai yi rai ba, saboda buguwa da tayi da transformer garin ya kauce musu har ya transformer ta faɗo kan Napep ɗin tasa, shi da be yi hanzarin fita ba da Allah kaɗai yasan irin ciwon da zai ji.


Lamido ya kalli Sadauki ya soma magana da shi kaɗan-kaɗan, yana gama maganar ya juya da sauri suka soma take masa baya, suka buɗe masa motar ya koma. Sannan Sadauki ya kalli sauran dogara ya ce


“Yarima ya yi umarnin a kai shi asibiti”


Da sauri Dogaran suka nufi gurin Lamido suka riƙa shi suka saka shi motar su. Sai suka sauya hanya daga masaukin Abdool zuwa Asibiti mafi kusa da su.
Anyi masa kyakkyawar karɓa, a asibitin, duk da kasancewar basu san Yarima Abdool ba amman suna ganin motoci ya dogarai sun san babban mutum ne.
Duk abinda aka yi aka maga Abdool na ciki mota zaunensa har aka gama dubasa aka saka masa baldeji a kai suka rubuta masa magani, a cikin asibitin dogaren yaje ya siya masa magani sannan suka dawo da shi gurin motar. Da gudu Sadauki ya nufi Motar Yarima Abdool ya ƙwanƙwasa gilashin motar sai ɗayan dogaren dake ciki ya sauke gilashin motar.


“Ran Yarima ya daɗe, an kammala masa komai, sun ce yaji ciwo kai sai kafarsa da ɗan targaɗe kaɗan”


Da Abdool yake magana amman yayi kamar be jisa ba, idonsa na kan Lamido dake tsaye jikin wacan motar yana kallon titi. Kallonsa sosai Abdool yake a zahiri yana da kyaun natsuwa da kuma kyaun fuska, gashi dogo ga fari ga dogon hanci gashin kansa kawai idan ka kalla zaka gane bafulatani, sai dai hakan be hana Yarima Abdool jin wani iri akansa ba, wata ƙila akwai wani giɓi a tare da shi, ko kuma akwai wani abu a tare da shi wanda Yarima Abdool baya so, dan ya tsanar mutum haka nan kawai.


Haka Abdool ya kwashe daƙiƙu talatin da wani abu be ce da Sadauki komai ba, wata ƙila yau jinin sarautar ni ya motsa har yayi abunda be saba ba, kuma abunda yake ganin kamar be dace ace mutum yana yi ba.


“Za mu bi ta gidan su mu aje shi sai mu wuce”


Ba dan sun saba ba, da ba zaka zaci da su Yarima yake ba, yanayin yadda yayi maganar muryarsa na ƙasa sosai, ko kaɗan idonsa ba su kalli Sadauki ba, har yanzu idonsa suka kan Lamido yana masa kallon rashin dalili.


“Allah yaja zamanin Yarima, an gama”


Ya bar jikin motar da sauri ya nufi gurin wacan motar da Lamido yake tsaye.


“Kai ɗan talakawa shiga mota muje, Yarima mai jiran gado ya ce aje a kai ka gida”


Maganar ta daki zuciyar Lamido har sai da ya kalli Sadauki sai kuma ya kalli Motar yarima duk da baka iya hango wanda yake ciki sai dai na ciki ya ganga. Har zai yi magana sai kuma wata zuciyar ta hana shi, sai kaeai ya rage tsawonsa ya shiga motar, still ransa ya sosu da furucin da Sadauki ya yi masa. Sai da ya shiga motar sannan Sadauki ya dawo a motar ya Yarima ya shiga suka kama hanyar Tudun wada.


Lamido ne yake ta nuna hanyar da za abi har aka isa gidansu. Ganin masu jajayen kaya sun fito tare da Lamido yasa mutane suka fara taruwa ana kallonsu, dan kowa yasan daga gidan sarki ne. Masu boko suka karantar number motar, yara kuma suka shiga cikin gidan da sauri suka sanar da Neine cewar ga wasu nan sun zo da Lamido ciki motar sarki an ji masa ciwo. Ba shiri suka fito daga gidan gaba ɗayasu suka nufo Lamido. Bugun gabansa ne ya ƙaru ganin Namra a cikin mutanen dake fitowa daga cikin gidan, ita ma hankalinta a tashe yake kamar wani nata ne aka jima ciwon. Sai da suka saka shi cikin gidan, sannan ɗaya daga cikin dogaran ya zo ya buɗewa Yarima mota ya fito.


Ƙarƙashin itacen mangoro suka shimfiɗe Lamido, uwani ta ɗauko matashin kai a ka aza masa. Kusa da shi Namra ta zauna tana ta kallon kansa tare da yi masa sannu, idonta cike da ƙwalla, har cikin jikinta take jin ciwon Lamido.
Shigowar Yarima Abdool yasa Namra ta ɗago kai ta kalli ƙofa, karam idonta ciki cikin nasa, sai yayi saurin kawar da nasa idon, ya cigaba da takawa kamar wani ɗawuisu, ya tunkaro tsakar gidan, dogarai na take masa baya. Ita kam kallonsa take da kyau dan tantance wanda ta gani ɗin, da gaske shi ɗin ne ko kuma waninsa mai kama da shi? Daman Ɗan sarki ne? Anya shi ke wacan kuwa na Katsina wanda yayi mata kyautar gida ko dai twins ne?


Har ya ƙaraso gurin idonta na kansa, shi kuma ya ƙi ya kalleta sai kallon ƙyakkyami yake ma gidan abunda ba halinsa ba. Da sauri Uwani ta ɗauko wani Babban tabarma ta shimfiɗa masa, jikinta har rawa yake. Baya cikin kayan sarauta hasalima farar shaddace jikinsa, wanda ta haska kyaunsa. amman hakan be hana ƙwarjinsa fita ba, dan du Ƴaƴan sarakuna da ban suke a duk inda suke.


Be zauna ba, kuma be cewa kowa ko ƙala ba har sai da Neina da sauran matan unguwar suka miƙa masa gaisuwa, nan ma hannu ya ɗaga musu sai dogaran suke amsa musu da sunan Yarima ya amsa, kuma ya gaishe ku.

“Allah ya sauwaƙe”


Shine kawai abunda ya furta, shi kuma iyakar laɓɓansa Sadauki ne ya maimaita dan suji. Sannan ya ciro cak ya miƙawa Sadauki shi kuma ya karɓa ya miƙa wa Neina dan ita yake zaton ma mahaifiyarsa ce.


“Godiya take Yarima”


Hannu biyu tasa ta karɓa jikinta na rawa, badan tasan ko takardar me ne ba. Kuma tsoro ya hana ta tambayar ko minenen.


Juyawa yayi ya sai dogoran suka take masa baya. Tunani biyu ne a zuciyarsa miya kawo Namra gidan ita da take Katsina? Mine alaƙarta da ƴan gidan? Ko kuma ƴar'uwarta ce? Mijin ta ne wacan to wannan fa? Ko dai yayanta ne? To ai ba suyi kama ba. Shine abunda yake ta tunani har ya doshi motar.


_Miyasa ba zaka iya yaƙin zuciyarka ba? Dan me zaka nace abunda ba halalinka ba? Idan ita ce sai me miye ruwanka da ita?_


Iskar bakinsa ya furzar yana sauraren bugun zuciyarsa, da kuma tunanin yadda ƙaddara take kawo masa mai kamaninta.


“Ya Rahman”


Ya furta yayinda yake ƙoƙarin zama cikin motar. Wannan karon hankalinsa ba akan jarida yake ba, gaba ɗaya ya tattara ya koma can gurin Namra daya gani, idanuwansa suna kan titi ruhinsa kuma yana can gurin motar da ba tasa ba.


Daga nan basu tsaya ko ina ba sai masaukinsa, kamin ya fita motar sai da ya duba agogon hannunsa ɗaya saura ya gani, hakan ya sashi ɗan hanzarin fita yana magana da sadauki.


“A kira Mai Martaba a sanar masa mun iso, wayana a kashe yake zan ɗan kwanta na huta”


“Allah ya taimaki Yarima yadda ka ce haka za'ayi”


Gaba ya wuce suka buɗe masa ƙofa, duk jin yake rayuwarsa babu daɗi, kuma be san dalili ba.


HILAL POV.


Jikin ƙofar ɗakin ya jingina yana kallonta da sauraren kukan da take rerawa. Rumgume hannayensa yayi yana tunanin ta ina zai fara. Ita kam bata ma san da shigowarsa ba, ta maida gaba gabas sai rusar kuka take.
Sauke hannayensa yayi ya nufi inta take zaune ya zauna gabanta yana kallon idonta.


“Yanzu abinda kike min adalci ne? Ki zauna kina kuka kin san yadda nake ji kuwa? Na rasa ɗa na ke kuma kin zauna a nan ki na kuka”


Ɗagowa tayi ta kalleshi


“Kai ɗa ka rasa, kuma kana da wasu, ni kuma miji na rasa”


“Ba ki rasa ni, kin san abinda na ke so da ke?”


Ta girgiza nasa kai.


“Zaki zauna nan for a while as zaman idda kamar yadda addini ya ce, ni zan je gida na faɗawa su Momi komai, wannan fushi na Hajiya na kwana biyu ne na nasan nan gaba kaɗan zata sauka, dole ne Hajiya tayi fushi Kalsoom saboda bata fahimce kamar yadda ni na fahimta ba”


“Ta yarda na zauna ne?”


“Bana jin zata hana, abunda na ke so dake ki yi mata uzuri kuma ki bata lokaci. Zan ɗauke ki muje gida anjima a can zan maida aure na”


Kai kawai ta ɗaga masa ta share hawayenta. Har ya mike tsaye sai kuma ya juyo ya kalleta ya ce


“Hajiya ta ce za a maida zaman makoki a can”


Nan ma kai ta ɗaga masa. Sai ya juya ya fice zuciyarsa babu daɗi. Zaune ya hango Hajiya a falon tana kallon ƙofar ɗakin Kalsoom daya fito fuskarta babu annuri. Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa ya ƙaraso kusa da ita ya dafa kujera yana kallonta.


“Hajiya karki zama cikin iri surukan nan”


“Ba ƙoƙarin zama nake ba Hilal amman duk abunda yake gaskiya dole a faɗe shi, idan kai ta maka magani ni bata min ba, kuma Wallahi tallahi sai ka ƙara aure ko da kuwa bana numfashi, dole ka auri wacce zata riƙa maka ƴaƴanka mace ƙwarai ba mai ƙoƙarin kashesu ba, ni zan nema maka mata da kai na”


Tana kaiwa nan ta miƙe tsaye ta nufi ƙofar fita ranta na ƙololuwa a ɓaci. Shi dai da kallo ya bita har ta fice sannan ya saka hannyensa aljihu ya nufi ƙofar ransa a jagule.


RASHIDA POV.


A nasu gidan suke nasu amsar gaisuwar daban, duk da kasancewar waɗanda badu san aurenta ya mutu ba suka je can gidan gidan har sai idan sun tambaya ne sai ace musu gata nan. A harabar gidan suka shimfiɗa tabarma duk da kasancewar yaro ne hakan be hana ayi masu taro ba, sai dai ba irin zuwan nan ake na wuni ɗaya ba sai dai su zo su zauna na ƴan mintu su yi mata gaisuwar su wuce.
Tabarmarta daban tana zaune gefe ɗaya, ƴan gidan suna zaune gefe ɗaya. Idonta kumbura sosai duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata wasu har da Allah ya isa suke mata duk a tunaninsu tana kuka ne saboda rashin ɗanta, sai dai a gurin Rashida abun ba haka yake ba, ita tana kuka ne saboda tunanin makomarta ganin asirinta ya tonu tun yanzu, tasan dole zamantakewar ta da ƴan gidan dole zai canja dan taga alamun hakan tun yanzu.


Misalin biyu da rabi Teema ta zo gidan gurin gaisuwa, sosai take son magana da Rashida amman babu dama saboda mutanen dake ta kai da kawo. Tana gurin kuma sai ga Asmee bayan ta fito gidan Hilal ta nufo nan.
Duk abunda ya faru a gidan sai da ta bawa Rashida labari. A nan Rashida take labarta musu maganar sakin da Hajiya tasa aka yi ma Kalsoom, dan su ba susan da maganar ba. Duk daɗi suka ji har mutenan dake gurin da kuma Asmee da basu san kan abun ba, amman ban da Teema da ita kan tasan komai.


“Amman Hajiya ta kyauta, daman ai ni za ci tuni zata sata shi aikata sakin, duk wanda yayi maka haka ga jika kan ai be cancanci zama da ɗan ka dan wata shi zata hara”


Gaskiya kam. Abunda suka mutanen suka masa da shi, sannan ƙananan maganganu suka biyo baya. Teema ta kada baki ta ce


“Gaskiya Hajiyar ta kyauta daman tun tun tun Hajiyarmu take cewa ya kamata ace Hajiya ta saka Hilal ya rabu da matar nan”


Rashid ta kalleta tana murza idonta.


“Hajiyar ku ta san ta ne?”


“Eh sukan haɗu a harkar siyasa wani lokacin, suna gaisawa sosai”


“Allah sarki”


Cewar Rashida. Sai kuma ta kawar da fuskarta tana kallon Asmee irin kallon nan da ita kaɗai ta san dalilinsa.
Teema kuma wani gurin take kallo tana wani tunanin na daban. Sai da aka kira la'asar sannan Teema ta wuce gida, Asmee kam a gidan tayi sallah sannan ta fice bakinta cike da magangu amman bat samu damar yi ma Rashida ba, ganin Safiya duk yasa ta tsargu, hakan yasa ta yi a zamar barin gidan.


Tashi Rashida tayi ta nufi cikin gidan rayuwarta duk babu daɗi saboda abunda take tunanin su momi sun fara nuna mta na ƙyama tsakanin jiya zuwa yau. Babu abunda ke ranta kamar ta bar musu gidan ta kama wani, tasan hakan zai fi mata kawanciyar hankali.




ASIM POV.


Yana ji a jikinsa akwai rashin dacewa a abinda suka aikata. Musamman yanzu da yake jin abu kamar ƙashi ya tsaya masa a takashinsa, ga wani zafi zafi da yake ji kamar an zuba masa barkono. Wasu ƙwayoyi dattijin Alhajin ya miƙa masa kusan kala huɗu ya ce ya sha, daman kamin su aikata sai da ya bashi wasu, tun jiya da dare suke abu ɗaya har yau da safe, sai yanzu nan ne Asim ya samu kansa. Sai a yanzu yake ƙarema Alhajin kallo, tabbasa ya sanshi a cikin manyan mutane. Amman duk misalin da yake masa jiya be gane shi ba sai yau. Daman tun lokacin daya ji sunansa ta ayyana a ransa ko shi ɗin ne, sai gashi mitumen ya fere ma tun daga biri har wutsiya.


“Na bawa Hajiya miliyan biyu ta baka, na siya maka mota ta miliyan uku. Idan ka riƙe min sirrina nan da ƴan wasu watan ni za'a far ƙirgaka a cikin manyan Alhazai. Zan wuce Abuja yau, idan na dawo zan samr ka a nan ko kuma nas Hajiya ta aika min kai a can sokoto”


Alhajin ya faɗa yana shafa fuskarsa. Asim kan daɗi har cikin kai, hankalinsa da zumuɗi gaba ɗaya sun tattara sun koma gida, babu abunda yake ransa kamar motar nan, a take ya ji duk jikinsa ya warysakr kamar babu wani ciwo jikinsa.


Be bar gidan ba sai da ya ci ya ƙoshi, sannan Alhajin yasa direba ya mai da shi gida.
Yana fita cikin motar sai ga Nably ta kira shi kamar ba zai ɗauka ba dan ya matsu ya ga motar da Alhajin yake ce masa. Sai dai farincikin dake ransa ba zai hana shi ɗaukar wayar Nabila ba.


“Hello my girly”




Ya faɗa cikin wani irin yanayi na shauƙi da annashuwa. Ita kaɗan ta karanci hakan a muryarsa.


“Da alama yau akwai labari mai daɗi a tare da kai..”


Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.


“Labari mai daɗi, na kusa zuwa Abuja na gan ki”


“Nikam ba zan iya jura har jibi ba, akwai birthday friend ɗita da za'ayi yanzu take faɗa min ni kuma na ce dole zan zo ko dan kai”


“Wow Amman gaskiya kin kyauta min, i can't wait to see you”


“I can't wait to see you too, sorry zan katse kiran, Momy na kira na zan kira ka idan mun gama”


Hajiya Sadiya ce ta fito waya a hannunta tana faman kiran waya, fuskarta ɗauke da murmushi, ganin Asim.

Shima Murmushin ya mayar mata ya doshi inda take cike da zumuɗi, sai kawai ta jefa mishi keys ɗin mota ta nuna masa motar tana cigaba da murmushi sai ta nufi wani ɓangaren na gidan tana amsa wayar da aka yi picking yanzu.
Wani irin tsalle Asim ya daga tsinkawo motar da yayi, da gudu ya doshi gurin yana wani irin gurnani kamar mahaukaci.


NAMRA POV.


Abdool na fita Uwani ta karɓi takardar hannun Neine ta duba, tana gani tasan cak ne sai dai bata iya gane ko nawa aka rubuta ba, kasancewar ilminta be kai har can ba, zero da ta ga a rubuce sun mata yawan karantawa.


“Minene?”


Neine ta tambaya, cike da son sanin abunda yake ciki.


“Ni wallahi ban gane kan abun ba, amman dai takardar kuɗi ne”


Uwani ta faɗa, dai Namra ta kai hannu ta karɓa tana dubawa.


“Miliyan ɗaya ne cif”


Uwani da Neina sun daki ƙirji tare da zaro ido.


“Miliyan ɗaya?”


Duk mutane da suka shigo cikin gidan duk ko wanne sai da ya riƙe baki, har ga Allah yawan kuɗin suke gani, Namra kam bat ɗauke su a bakin komai ba, abun ka da wanda yasan kan abu. Wani dogon tsaki Lamido yaja ya kawardar da kansa.


“Sam sam sam mutumen be san darajar mutane ba Wallahi”


Aiko yayi ƙoƙori irin wannan kuɗin haka! Ƴaƴan manyan mutane da da zasu taka rai su bar mutum balle har ya baka wannan kuɗin. Shine abunda mafi yawan matan maƙotan gidan suke ta faɗa.


“Ai dole yayi min mana, tun da ya lalata min Napep dole ya bada kuɗin jinya dan siyen wata”


Neine ce ta saka bakinta wannan karon tana nuna Abdool ya kyauta iya kyautawa.


“Wallahi da wani can ba zai kula ka ba Abdool ba gasu nan muna gani ba, wannan kuɗin ka siye sabon Napep har ka rage. A dole ya nuna wannan halin kasan a jinin su yake, babban mutum kamar wannan”


“Da Sarauta kawai zai fi ni, amman ina tabbacin be fini ilmi zamani ba, balle ma na addini, ji yadda yake kallon mutane warwatse”


Har cikin ransa yake maganar yana mai jin tsanar Abdool sosai. Namra kam bata ce komai ba hankalinta ma gaba ɗaya yana wani gurin, sam bata lura da kallon baƙuwar fuskar da mutanen dake shigowa cikin gidan suke mata ba. Murɗawar da taji mararta na mata ne yasa ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu. Ƙasa ta zauna tana riƙe tsararta tana dannar baki alamar tana jin zogi sosai. Tun tana juriya a zaune har ta kasa ta kai kwance tana rumtse ido.






SAI MUN HAƊU BAYAN SALLAH 😍
INA NEMAN YAFIYAR DUK WANDA NA ƁATAWA, ƊAN A'ADAM AJIZINE. WATA ƘILA ZAN KAI BAYAN SALLAH, WATA ƘILA BA ZAN KAI BA. KU MIN ADDU'A IDAN LABARIN MUTUWA NA YA SAME KU KUMA KU YAFE MIN ALFARMAR ANNABIN RAHAMA S.A.W 🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *63*


Kasa cin tuwon masarar Namra ta yi sai kawai ta sha ruwan tulun mai jiƙa maƙoshi kamar ruwan freezer.
Da fulatanci matar da ba zata wuce mai shekaru hansin da huɗu ba ta yi ma yaran magana akan ba su gaishe da Namra ba. Sai duk suka taso cikin ladabi suka gaisheta cikin su har da manyan ƴan'mata da kuma ƙanana. Da murmushi Namra ta amsa su sannan ta maida kanta ƙasa tana murza yatsun hannunta.


“Ban wayence ta ba”


Neina ta faɗa da yaren fulatanci tana kallon Saurayin. Shima da yaren ya maida mata da amsa.


“Ni ban san ta ba, kawai na ɗauko daga tasha ne, sai tace bata da gurin zuwa na taimaka mata shine na kawo ta nan”


“Amman Lamido taya zaka ɗauko yarinya baka santa, baka san inda ta fito ba? Kasan ko wace iri ce?”


“To Inna idan na bar ta can ban san halin da zata faɗa ba, kuma kin ga tace bata da kowa nan”


“Bata da kowa a nan zata zo? Lamido karka mana jaye-jaye muna neman abinda mu ka ci”


Da yaren fulatanci suke maganar, a zahirin gaskiya Namra bata jin yaren duk kuwa da kansacewar kakaninta fulani ne. Amman hakan be hanata fahimtar zancen ne suke ba.


“Ni ba macuciya ba ce lalura ce ta kawo ni nan, mijina ne ya sake ni kuma mahaifina ya riga daya gargaɗe ni akan karna kuskura na je gidansa, shiyasa na zo garin kaduna, amman idan ba ku yarda da ni ba ba zan zauna a nan ba, dan ba zan takura ku ba”


Wannan karon cikin halshen hausa Neinah ta ce


“Duniya ce a yanzu ake tsoron mutane, ba kowa ake yarda da shi ba, amman me kika aikatawa mahaifinki ya yi miki haka kuma a ina mahaifinki ya ke?”


“Mahaifina yana garin sokoto da zama, ni kuma a Katsina nake aure, sai dai ba zan iya labarta muku labarin aure na a yanzu ba, ina neman ku min lamani har zuwa gobe zan faɗa muku ba zan ɓoye ba”


Daga Neinah har Lamido shiru suka yi babu wanda ya iya

Please Login or Register in order to submit comment