Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jindaɗinta akan barin gidan da Rashida tayi ta ƙara mallakarsa, sannan Hajiyarsa tana yawan tunasarda shi akan ya kawar da idonsa gareta, duk wani abun da zata yi ya riƙa sa mata ido.


Tana yawaita bibiyar shafinsa na facebook da instagram da whatsapp, wai ko zata gano idan hankalinsa ya karta kanta amman sai ta ga tsaɓanin hakan, dan har text take masa amman baya mai da mata amsa daga ƙarshe ma sai ya saka ta a blacklist.
Yau kam ta kuɗiri aniyar tura Asmee dan ta binciko mata irin zaman da suke, tun da ta san Kalsoom ta yarda da Asmee kuma zata iya bugun cikinta dan ta ji labarinta, idan ma suna zaman lafiya ko a yanayin fuskarta zata iya karantar hakan.


A gogon ɗakinta ta kalla taga 10:36Pm, ba laifi dare ya ɗan fara sai dai hakan be hana ta janyo wayarta ta kira line Asmee ba.


“Ƴar gari... Yanzu ko na ke maganar ki da Oga”


“Uhmm gulmata kuka yi kenan?”


“A'a Wallahi kawai yana yabon halin ki ne, wai duk yadda kike da haƙuri ace Hilal ya sake”


“Ke dai bari, ai sherin kishiya sai Allah, ni so ma nake kije gobe ki bincika min gidan nan, ya zamantakewar su yake”


“Zan ko miki haka, nima Wallahi ina son zuwa dan naga idon munafukar”


“Da Sassfe zaki je dan Allah lokacin da Hilal.yake gida”


“Karki samu matsala Asmee ce fa ƙawarki”


“Na gode ki gaishe da ogan na ki”


“Zai ji mu kwana lafiya”


Rashida ta kashe wayar tana kallon ƙanwarta Safiya dake tsaye jikin ƙofa riƙe da littafi.


“Shigo mana kika tsaya bakin ƙofa kina kallona”


Ta shigo tana ɗan murmushi


“Wallahi Anty ni jikina duk a mace yake”


“Saboda me mutuwa aka yi?”


“A'a, kin san mun fara zuwa asibiti yanzu...”


Ta ɗan yi shiru tana tunanin ƙarasa zancen, dan tana jin nauyin karya alƙawarin data ɗauka a asibiti na cewar ba zata faɗawa kowa wanda ta gani ba, idan ta shiga sashen masu hiv da sarin tb.


“To shine nake neman addu'ah, idan mun gama zamu fara exam”


“To Allah ya taimaka ya bada sa'ah, nima ina son ki min addu'ah Allah ya maido da hankalin mijina gare ni”


“Adda Rashida kenan, kina damuwa da abunda be kamata ki damu da shi ba, mijin daya juya miki baya meye na addu'a ya dawo gareki, bayan ya ci zalinki?”


“Ba a cikin, hayyacinsa yayi min ba, kin fi kowa sanin yadda Hilal yake so na, kawai sherin Kalsoom ne magani tayi masa, yanzu haka ma su Ezza basa jindaɗin zama da ita, so take ta kore kowa ta mallaki gidan”


“Kada Allah ya bata sa'ah, kuma wallahi indai mugun nufinta kenan sai ta ga abinta, ai karka bi mutum da sheri ka bar shi ya bika da sherin abun zai koma kansa”


“Ba zan bata damar haka ba, Safiya bata isa ta shiga gidan dana shekara ina ginawa ba a rana ɗaya ta rusa min kuma ta kore min ƴaƴa ta mallake min miji sannan na bar ta”


“Ki ƙyale ta ki bar ta da Allah, idan ma wani asirin ne tayi miki Wallahi zai karye zata dawo nadama lokacin da bata da amfani”


»“Haka ne Allah ya shige mana gaba”


“Amin dan Allah ki ma daina sa ran ki a damuwa”


“Ina nan ina addu'ah komai zai dai-daita inshallah”


“Allah yasa, sai da safe”


Safiya ta miƙe tsaye ta fice zuciyarta cike da tausayin ƴar'uwarta. Rashida kuma ta sauke ajiyar zuciya tana busar da iskar bakinta. Lallai tana ji a zuciyarta, ba a banza Hilal ya barta ba, dan tasan yadda mijinta yake son ta dan kawai ya gano tana tare da wani be isa yasa ya sake ta ba, tasan da ada ne da komai tayi ba zai rabu da ita ba.
Sai dai abunda har yau bata sani ba shine, daga lokacin da mijinki ya gano kina mu'amala da wasu a waje tun kin fita daga ransa kenan indai ya san kansa, kuma komai irin son da yake mki ba zai sake ganin darajar ki ba.




NAMRA POV.


Yau ta farka da baƙinciki da kuma tunanin mafita dan samawa kanfa ƴanci.
I zuwa yanzu ita kaɗai tasan abunda take ji a zuciyarta, idan ta soma tunani har numfashinta yake yin sama, tsabar baƙinciki da damuwa.


Dole ne taje a cire mata robar nan, dan ba zata iya da rikitarwar da jinin yake nata ba, kuma ga matsalar Asim da yanzu babu ruwansa da matsalarsa haka zai yi forcing ɗinta ya yi yadda yake so da ita.
Irin yadda yake mata Allah ya isa akan rashin cire robar da bata yi abun har mamaki yake bata, kamar ba mijinta ba, ko kuma wanda be san addini ba, abu kaɗan zai mata Allah ya isa, ga yawan kusheta da yake, shi dai kullum ya fi son ya ganta a cikin damuwa da baƙinciki.


Ba laifi yanzu dan ya ɗan fara fita, har ya koma aikinsa na ƙira da suke da Ƙanen Babansa, sai dai naira ba zai cire ya bata ba, da sunan ta siye abinci balle cefane, babu ruwanshi da matsalarta, sai dai ita tayi cefane kuma haka zai zo ya zauna ya ci dan bashi da kunya. Ita kuma har yanzu bata yi ƙarfin halin da zata iya hana shi abincinta ba.


“Idan na yi kuɗi, zan auro mace mai kyau mai tarbiya”


Sune kalamansa a kullum kuma sune kalaman da suka fi ƙona zuciyar Namra, a yanzu ne take ƙara tabbatar da son Asim be gama fita zuciyarta gaba ɗaya ba.
Ta maida hankalinta sosai gurin siye da siyarwa, na kayan aiki abinci like magi manja da sauran kayan miya, ba laifi ana siye sosai dan a unguwar ita kaɗai ce take wannan sana'ar hakan yasa ta sabo da mutane har ta buɗe islamiya tana ɗan karantar da su abubuwa game da addini da kuma ƙur'ane.








manage it please.....
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: ~4»»»»9»»»»»~


AMIRA POV.


Ta fara sabawa da Abdool cikin ƴan kwanaki ƙalilan ya shiga ranta, har matsuwa take ya zo ya ganta, dan kullum sai ya zo da safe ya duba ta, da rana ma ya kan zo idan baya da aiki, haka ma da dare sai yayi mata sallama sannan ya wuce gida.


Ta karanci abubuwa da yawa a rayuwar Abdool tun daga yanayinsa na rashin son magana da kuma shisshigi, ba kasafai yake dariya ba, ko murmushi sai idan ta kama ne yake yi.
Sai dai hakan be hana annurin fuskarsa bayyana, ya kan mata kwarjini sosai idan ta kalleshi. Sai dai har yanzu matsala ɗaya ce tayi mata tsaye a rai nasa, rashin sakewa da yake da ita, sannan idan zata shekara tana kuka ba zai iya bata haƙuri ba, sai dai ya tashi ya bata guri. Lokuta da dama ta kam ƙirƙiri kukan ne dan ya tausaya mata amman bata taɓa ganin alamun tausayinta a fuskarsa ba.


Wata ƙila baya da tausayi ne, ko kuma ba shi da kula da lamarin wasu, a yadda ta karanci rayuwarsa kamar ma yana kula ta ne by force.
Abu ɗaya zuwa biyu take ta ƙoƙarin yaƙar zuciyarta akansa, faɗuwar gaban ta take samu idan ta kalleshi, da kuma damuwar da take shiga idan ta wuni bata sashi a ido ba.
Sai dai har yanzu ta kasa, ɗan zuwan nan da yayi katsina ya kwana biyu ya dawo ji take kamar shekara biyu yayi. Tunani take idan ya rabu da ita ya zata kasance? A yanzu kam bata da gurin zuwa tun da Guy son ya mutu, kuma ta san Abdool ba zai barta ta zauna a tare da shi ba, wanda ɗaga ido ma ya kalleta yake masa wuya balle yayi mata masauki a inda yake.

Sai yanzu take nadamar abunda tayi ma Guy son, tabbas bata kyauta ba, dan me zata butulcewa wanda ya ɗauki ɗawainiyarta, dan kawai ta ceci ran wanda kallon ma mai tsada ne?
Lallai tayi kuskure kuma bata bi hanya mai ɓullewa ba. Ya kamata ta yaƙi rayuwarta dan samawa kanta yan ci, taya zata bar Abdool ya tafi haka nan ya barta ta dabon ciwo da kuma na zuciya, bayan duk akansa tayi wannan? Ashe bata cancanci fiye da haka a gareshi ba? Sam bata ga alamar karaminci a tare da shi ba, sam be san darajar ɗan'adam ba, ya kamata ace a iya zaman da tayi yayi ƙoƙarin kawar mata da damuwarta, amman sai nuna mata halin ko'in kula yake mata, sai tambayoyin banza da yake tsare ta da su wani lokacin.


Ta share hawayen idonta ta miƙe tsaye tana shafa kafaɗunta ta nufi window ɗakin tana sauraren zance da zuciyarta take mata.


‘Idan kika na bar Abdool ya kuɓuce min, lallai nayi babbar wauta kuma na yi hasara, taya zan ceci ran mutum kuma ya juya min baya? Ya kamata fa ya nemawa kai na ƴanci haka na yi ta sake har Namra ta ci galaba a kaina, tun da har na butulcewa Guy son dole ne na samu wanda zai maye min gurbinsa.


Sometimes ina abu kamar ba ni ba, zama da Guy son ya kamata ace na ko yi abubuwa da dama, amman sai kasa gazawa nake, a yanzu babu kowa a kusa da ni, ya kamata ace na zama mace. Amman sai kasawa nake, i will fight the spirit ghost of me, i will surely be my own boss, i have to answer my own name’


Ta kai hannayenta ta dafa window, dan ta ji motsin shigowar mutum kuma ta san Abdool ne dan shi kaɗai yake mata haka. Yi tayi kamar bata ji shigowarsa ba ta ƙirƙiri hawaye, ta soma magana cikin sanyin murya kalar tausayi.


“Allah ka zama gata na Allah, bana da kowa sai kai, ya Allah idan mutuwa hutu ne a gareni Allah ka karɓi rai na na huta, Allah na tuba ba zan ƙara ba”


“Ai ba haka ake tubar ma Allah ba”


Ya faɗa yana tsaye jikin ƙofa sanye da ƙananan tufafi, sai faman danna waya yake kamar ba shine yayi maganar ba.
Juyowa tayi ta sauri ta kalleshi like bata ma san yana gurin ba. Be kalleta ba, amman hakan be hana ta ganin ƙwajininsa ba saboda yadda tufafin suka karɓi jikinsa suka masa kyau sosai kamar daman can dansa kawai aka yi tufafin.


Lumshe ido ta yi tana sauraren bugun zuciyarta, hancinta na shaƙar ƙamshin turarensa daya game ɗaki, hawaye ne suka silalo mata.
Yadda zuciyarta take amsa irin kiran da Abdool yake mata ya tabbatar mata da shine mutumen da take mafarki, shine burinta a duniya bata taɓa ɗora idonta akan wani namiji taji abunda take ji akan Abdool ba, ita kwata-ƙwata a rayuwartaa bata taɓa mutumen da take so ba sai Abdool, duk wanda zata so sai dai ta soshi dan kuɗinsa ko kuma da wani abun na dabam.


Amman tana jin Abdool ko bashi da komai zata iya zama da shi, ballantana ma ya haɗa komai da ake so ga namiji, a rayuwarta bata taɓa ganin kyakkyawan mutum kamar Abdool ba, sam be yi kama da ƴan nigeria ba. Ga tarin dukiya da kowa wacce mace take so a gurin Namiji, ga shi kuma ɗan Sarki wata rana zai iya zama sarkin gaba ɗaya.


“Da ace hawaye za su miki magani da sun miki tuni, kuma tun lokacin da kika saka ƙafarki kika bar gidan ku ya kamata ace kin yi kuka kin dawo sai yanzu? Lokacin da nadamar ki bata da amfani, do you know what? I don't believe in fiction, idan har da gaske kin yi nadama ya kamata a ce yanzu kin kama hanyar gidan iyayenki”


Yayi mata maganar ne from the bottom of his heart, like he's seriously saying what is inside him, daman can shi ba mutum ne mai tausayin mace ba, indai zaki shekara kina kuka Abdool kam ko a jikinsa, wata ƙila dan ba shi da lokacin matan ne, ko kuma dan har yanzu idanuwansa basu ga zubar hawayen wacce zuciya take muradi ba. Sannan shi sam baya ganin tausayin ko kuma mutucin yarinyar da ta bar gaban iyayenta, da ma ace korarta suka yi ba ita ta gudu ba.


Babu yadda Amira za ta yi da shi duk da kalamansa sun taɓa zuciyarta, ta daɗe da karantar be iya lafazi ba, kuma babu ruwansa da tauna magana idan zai faɗa.
Sai dai hakan be sa taji haushinsa ba ko kuma ta ji ta tsane shi, sai kusanci da shi take so, dan ta koya masa yadda zai zauna da ita.


“Amman idan na koma da wane ido zan kallesu?me zan ce musu? Ya kake tunanin duniya zata kalle ni?”


“Tun kamin ki baro gidan ku ya kamata ki yi ma kan ki wannan tambayar, idan kika gudu me zaki ce musu? Da wane ido zaki kallesu? Ya kuma duniya zata kalle ki? There's no point of crying dan ke kika sai da mutunci da hannu ki”


Wani irin kallo ta watsa masa da jajayen idanuwanta, sai dai kwarjininsa be barta ta masa kallon daƙiƙa biyar ba ta kau da idon, cikin kakkausan lafazi ta ce .


“Amman mi yasa baka bar ni na mutu ba? So that na huta da rayuwar gaba ɗaya?”


Ya gyara tsayuwarsa ya ɗaga daga jikin ƙofar da yake tsaye yana sa hannayensa aljihu.


“I'm sorry I'm not harassing you I'm just telling the truth”


Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta.


“Park your things, Doc zai baki sallama, around 10am driver zai kai ki gida”


Be tsaya jiran abunda zata ce ba yasa kai ya fice. Rasss! Rasss! Rasss! Gabanya ya yanke ya faɗi.


“Wane gida? Gidan su ko gidan mu? Ko kuma wani gidan na dabam?”


Ta tambayi kanta, dik sanyin ɗaki be hana gumi zubo mata ba. Babu inda ya fi tsaya mata a rai a kamar gidan su. Wayyo Allah ji take kamar mutuwa za tayi idan har aka maida ita gidan su, ita kanta tana son zuwa gidan amman bata iya iyawa, bata san dalili ba.
Ta kasa sukuni sai safa da marwa take har Doc ya shigo ɗakin, bata ga alamun rahama a fuskarsa ba balle ta tambaye ko yasan inda Abdool zai kai ta, kai ba zata iya tambayarsa ba kar Abdool ya zargi wani abu.


Sai kawai taja bakinta tayi shiru, sai dai tasha alwashin indai gidansu ne ba zata taɓa zuwa ba sai dai komai zai faru ya faru.
Sai da likitan yayi mata binciken ƙwa-ƙwaf sannan ya rubuta takardar sallama ya miƙa mata, ya fice. Kamar yadda Abdool yace 10 na bugawa sai ga wani yazo cikin uniform ɗin soja yace mata ta fito suje. Nan ma sai da gabanta ya faɗi.


“Ina... za...mu....je?”


“Katsina yace a kai ki, gidan Mahaifiyarsa”


Ta lumshe ido na wasu ƴan daƙiƙu, wani irin daɗi ya ziyarci zuciyarta har ta samu maida yawun daya tsaya mata a maƙoshi.
Bata buƙatar ɗaukar komai, daman can duk kayan da tayi amfani da su shine ya kawo mata, dan ita ko waya bata da a hannunta balle wani kayan kuma. Farincikin dake zuciyarta ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a fuskarta.


Ko da ta fito Abdool na tsaye kusa da motar, da alama ita yake jira, sai dai kwata-kwata hankalinsa baya gurinta yana wani wajen dabam.
Ɗaya daga cikin boys ɗin sa ne ya buɗe mata mota ta shiga, idonta na kan Abdool.
Yayi kusan minti biyar yana magana da mutanen biyu sannan ya suka shiga motar da take sai kuma wata mota dake gabansu cike da sojoji suka kama. Shi kuma ya juya ya koma cikin.


Juyawa tayi ta cikin motar tana kallonsa. Tana ayyanawa kanta zama abokiyar rayuwarsa, dan wannan karamcin kawai da yayi mata ya isa yasa tayi sha'awar hakan. Mutum me daraja da ƙima kamar wannan? What if ta zama matarsa?






KALSOOM POV.


Tun daga lokacin data fara shan rubutun da Hajiya tasa aka mata, sai ta fara jin sauyi a jikinta, sai mafarkai take wasu ma har bata san kansu ba.
Natsuwar da take ji a yanzu, yana kan tunatar da ita rayuwar rikicin da ta yi a ƴan watanin nan, sai yanzu take mamakin kanta duk wacan abun da ta yi sai ya zama matar kamar mafarki.
Lallai a yanzu ta tabbatar da ta yi wasa da addu'ah, dan bata iya addu'ah safe balle kuma ta yamma da take gani kamar ba komai ba ce. Sai dai har yanzu bata jin ƙarfin yin addu'ah kuma jinin be ɗauke mata ba, amman dai ta dawo normal kamar yadda take, ba kamar baya ba da take jin abu na mata yawo cikin kai kamar tsutsa.


Da wuri ta tashi ta shirya musu abun karyawa, sannan ta tashi yaran duka tayi musu wanka da kanta, Izzah ce kawai bata bari anyi mata ba, sai wani cika take tana batsewa kamar wata babbar mace, ada tana yi a dole dan Rashida na sa, amman a yanzu kan na gaske take dan har cikin zuciyarta take jin tsanar Kalsoom bayan kuma bata mata komai ba, sai dai laifinta da take gani na kore musu uwa da ta yi, sannan tana ganim yadda komai ta yi musu Daddy su ba ya magana.


Sai da Kalsoom ta shirya su tsab sannan ya tura su gurin motar Daddy su ta shiga ɗan ta tashi mijinta.


A bakin ƙofar ɗakinsa ta tsaya ta buɗe maɓallin rigarta sannan ta kunna kai cikin ɗakin. Hannunta tasa cikin gashin kansa tana wasa da shi, amman be motsa ba, badan kuma be farka ba, sai dan daɗin da yake ji akan abunda take masa. Ganin be farka ba yasa ta kwantowa jikinsa ta zira halshenta cikin kunnensa. Still be motsa ba amman fuskarsa da murmushi alamar idonsa biyu kenan.


Hannu tasa ta matse masa hancin iya ƙarfinta, sai ya tashi ba shiri yana kallonta.


“K.e...”


Maganarsa ta maƙale lokacin da yayi arba da rigar bachinta dake buɗe. Rabon da ta masa irin haka har ya manta, Kullum sai dai ya haɗe mata yawu, yau ma yasan haka ne tun da jinin har yanzu be tsaya mata ba. Hannu ya kai ya laƙamo wuyanta.


“Let us enjoy ourselves...”


“No way, yara suna waje suna jiran ka”


Ya dafe kansa.


“Ya Subhanallah, gaskiya I'm tired of driving them to school”


Ta wara ido


“Then teach me how to drive!”


“No, ba zan bari ki yi driving ba, wani zai ganemin wannan kyakkyawar fuskar ba, sai dai na nemo direbe, idan kin san inda zamunsamu direba mai natsuwa ki nemo mana”


Ya yaye bedsheet ɗin dake samansa yaja kumatunta, ya sauka saman gadon ya shiga bathroom. Bakinsa ya wanke da fuskarsa sannan ya fito. Tsaye ya same ta jikin bathroom ɗin tana jiransa.
Ya ɗan risina kaɗan yayi mata kiss a baki.


“My Happiness”


Ta moɗe bakin tana hararsa irin na ma'auratan nan masu cike da shauƙin so.


“Ni kike harara?”


Ya kama kunnenta


“Ouuuch Doc it hurt”


Yana janye hannunsa ita tayi masa yadda yayi mata, ta fito falo da gudu shima ya biyota yana murmushi.


Ganin Asmee yasa dik suka tsaya cak, musamman ita dake ƙoƙarin gyara rigarta.
Be ce da ita komai ba, har sai da ita tabfara gaishe shi sannan ya amsa ya nufi ƙofar fita.
Kalsoom kuma ta koma ta ɗauki hijab tasa sannan ta fito falon cike da mamakin sammakon da Asmee ta yi musu haka kamar mai biyar bashi.


Ita kanta taji kunyar kanta, ga kuma baƙinciki ganin da tayi suna cikin walwala, dan tana taya ƙawarta kishi ne.


“Na doko muku sammako, kuna sha'aninku”


Kalsoom ta yi dariya.


“A'a nace dai Allah yasa ba bashin ki muka ci ba”


“A'a wallahi an kwana biyu ban zo ba shine nace bari na leƙo ki ban sirrin da kika bawa mijin ki ya kori Rashida”


Kalsoom ta rufe baki


“A'a sirri kuma? Ai duk wanda kika ga ta bar gidan mijinta inda akan rashin ladabi da biyayya ne to ita ce ta fitar da kan ta”


“Hmmm ba son ba mu sirrin dai ko, kin ga nima daman yara na kai scul shine nace bari na leƙo na gan ki”


“Aiko kin kyauta, an kwana biyu a a gaisa ba”


“To ai ƙara ni ke ba ko zuwa kike ba”


“Ba ya bari ne, cewa yake baya son ina yawan fita”


“Aikam baya son ki yi nisa da shi, kin ga bari na tashi na wuce sai kin zo”


Har gurin motarsa Kalsoom ta raka ta tana bata haƙurin rashin zuwa da ba ta yi ba, da kuma cewar zata zo idan Hilal ya barta.




ASIM POV.


Ba laifi yau kan yayi wanka ya shirya kansa, ko dan yana jumma'ah ne oho, da wanka ma be dame shi sai dai yayi kanta karya ya fita idan fita ta kama shi.
Bayan sun sauko daga sallah jumma'ah ya nufi gurin aikinsa yana mai jin haushin aikin nasa ace kullum sai ya yi zuga sannan ya samu ƴan kuɗin kashewa shi wannan aikin dik ya takura masa, sai jan tsaki yake yana maganganu shi kaɗai.


Tun daga nesa yake kallon wata makekiyar mota data faka gefen gurin da suke aiki, yana ayyanata a cikin jerin motocin da zai siya idan yayi kuɗi, dan kyawon motar ya ɗauki hankalinsa sosai.


Yana buɗe shagon da suke aikin, mai motar ta zoƙe gilashin motarta tana masa sallama.


“Assalamu alaikum samari”


‘Tab ashe ma mace ce’


Ya faɗa a ransa, a fili kuma sai ya amsa mata baki har kunne.


“Wa'alaikissalam Hajiya ina wuni?”


“Lafiya ƙalau, dan Allah masu aikin nan gurin nake nema za a gyara min gate ɗina ne”


Ta faɗa cikin yauƙi da rangwaɗa kamar ba babbar mace ba.


“Mu ne ai muke aikin Hajiya, ina gate ɗin na ki yake?”


“Kai ...?!”


Ta faɗa tana nunasa da hannunta, mamaki ne ya isheta, yanzu tsalelen saurayi kamar wannan ace aikin ƙira yake, dubi ko shigarsa fa.

“Okay ga kt na idan kun tashi aikin sai kuje gida ku yi min, gate ɗin be ɓalle bane duka rabi ne za'a gyara min”


Ta miƙa nasa katin. Yasa hannu biyu ya karɓa cikin girmamawa kamar wata uwarsa.


“To Hajiya da zarar abokan aikina sun iso zamu je muyi aikin, sai dai baki bamu time ba”


“Ga number waya na nan a jiki kamin ku zo sai ku kira ni”


“To Hajiya za mu zo inshallah”


Ya miƙa masa 5k


“Ga wannan asha ruwa”


Yayi taku tare da nuna kamar ba zai karɓa ba.


“A'a Hajiya ki bar shi”


“Bana mai da kuɗi idan ya fito jakana, so ka karɓa kawai idan ma watsarwa za kayi sai ka watsar”


Yasa hannu ya karɓa yana mata godiya. Ita kuma ta tashi motarta ta kama hanya. Sai da ta wuce ya kalli jikinsa.


“Ita kan ta ta ga ban yi mata kama da talaka ba, wallahi ni babban mutum ne”


Ya juya ya cigaba da buɗe shagon farinciki fal a ransa.




RASHIDA POV.


Ta kasa zaune ta kasa tsaye tun lokacin da Asmee ta labarta mata irin rayuwar jindaɗin da Kalsoom take da Hilal. Kenan ita sun manta da duniyarta? Hilal ya manta labarinta?


“Ina ba za'a shafe ni a tarihim rayuwarsa, ba zai rayu da wata ba sai ni, wata bata isa ta mallake min miji ba. Amman malamin nan ko dai yaudara yake ne? Dan me zai ce min magani yayi alhalin be yi ba”


Tayi shiru tana nazari, wata ƙila ita ma Kalsoom tana shige-shige shiyasa ta shafe ta a zuciyar Hilal gaba ɗaya. Daman idan kana yin abu gani kake kowa ma haka yake.
Wayarta ta janyo ta kira lamanin dan bata jin zuwa can inda yake a yau tun da ko aikin dake gabanta bata gama ba ma, balle ta yi tunanin fita, kuma tasan ko ta fita kamin taje ta dawo dare yayi sosai.


Kiran farko be ɗauka ba, haka na biyu zuwa na uku, amman bata sarara masa ba, har sai da ta jera masa kira kusan 10+ sai da yayi picking sannan hankalinta ya kwanta.


Sama-sama ta gaisa ta shi sai ta koro masa da bayaninsa


“Ina zuwa bari na binciki ƙasa”


Jimmm yayo shiru na ɗan lokaci sannan ya yi gyaran murya yace


“Lallai wannan matar ta sha gaban ki, ta fiki shiga bokaye, shiyasa wannan aikin be yi wani dogon tasiri a gareta ba”


“Kana nufin aikin be kamata ba?”


“Ya kamata amman yana ƙoƙarin fita jikinta”


“Amman idan har ya kamata ai dole Hilal.zai damu, dan bashi da wata mata sai ita kuma har yanzu ban ji ance sun samu saɓani ba”


“Amman ƙasa ta nuna

Please Login or Register in order to submit comment