Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aljihu ya ciro handkerchief yana shinshinawa.


“I loved you so much”


Ya ɗauki tsawo lokaci a gurin sannan ya nufi part ɗinsa. Be daɗe ba ya fito da takarda hannunsa ya kira ɗaya daga cikin direban gidan ya miƙa masa.


“Zaka kai Amira a wannan addireshin, karka yarda ka sauketa ko ina sai nan”


“Toh Ranka ya daɗe”


Ya nufi part ɗin Ummi. Su biyu ya samu a falon Amira ta yi kneel down tana riƙe da hannun Ummi tana kuka, Ummi kuma na hawaye.


“Ki min hallaci Ummi kin riƙe ni kamar ƴar cikin ki, baki taɓa nuna min banbanci da ƴaran ki ba, na yi fatar wata rana zata zo da zan saka miki abunda kika min, Na gode da karamcin ina fatar zaki yafe min duk abunda na miki”


“Ba ki min komai ba Amira sai alheri, Allah ya miki albarka”


Kuka ta yi sosai sannan ta saki Ummi ta nufi ƙofar fita kamar zata faɗi. Kai Ummi ta girgiza ta kalli Abdool ta ce


“Is not fair ya kamata ace mu muka kai ta gida”


Ya ɗago daga jikin ƙofar da yake jingine ya nufo Ummi


“No hakan zai fi mata, dole ta tanadi abunda zata faɗawa iyayenta, idan suka gan mu kawo ta za suyi zaton ko ina son ta ne, kuma dole zasu tambayi inda na haɗu da ita, ni ko kin san gaskiya zan faɗa musu, beside irin waɗannan mutane ba a yawo da su it risk baki san abunda suka tana da ba”


Kai ta kaɗa masa cike da gamsuwar bayanin da yayi mata. Sannan ya juya suka fita tare gurin mota suke je suka tsaya, ita kuma tana daga ciki sai faman kuka take. Hannu Abdool yasa a aljihu ya ciro takardar kuɗi ya miƙa mata.


“Maybe you will need this”


“No i don't”


Ta kawar da fuskarta tare da cewa direba su tafi. Daga Ummi har Abdool tsaye suka yi suna kallonta har aka buɗe musu gate ɗin farko, bayan sun fice aka rufe gate ɗin sannan suka daina hango motar ta.


“Ina jin kamar ba mu kyauta mata ba, kuma bata jidaɗi ba ta ƙi ya tsaya har su Fauza su dawo”


“Zamu iya mata alheri daga baya idan mun fahimci da gaske ta shiryu, ai ƙara haka idan suna nan ai zasu ta kuka suma”


“Allah yasa ta shiryun, but wata rana zamu yi visiting na ta”


Ya miƙa hannunsa yana miƙa.


“Bari na shirya na koma gurin Mai Martaba”


“Okay”


Ummi ta juya. Shi kuma ya nufi part ɗinsa. Cikin rashin jundaɗi ya nufi part ɗinsa, dan bana jin kamar be kyautawa Amira, but he has no choice but to let her go. Cikin mintuna shirin ya watsa ruwa ya shirya cikin manyan kaya dan cox he know how Mai Martaba hate ƙananan kaya, yana fitowa part ɗinsa sai ƙamshin turare ke tashi. In five minutes ya isa kan wuri. He got lucky Mai Martaba be je ko'ina ba, duk da yana da niyar fita yau, sai dai ya tararda fadar cike saboda baƙin da suka zo daga jibiya. Yana shiga suka fara miƙa masa gaisuwa da kirari, hannu kawai ya ɗaga musu ya juya ya fita.


Barori ya samu a babban falon Mai Martaba suna hidimar chanja carpet, da sauri suka zubar da abunda ke hannunsa suka zube ƙasa suna masa gaisuwa. Kamar wanda be gansu ba, haka yayi ya nufi ɗayan falon nasa, zama yayi saman kujera yana duba jaridu, can kuma ya ji gurin is so boring ya miƙe ya nufi can ɓangaren Mai Martaba inda babu wanda ya ke shiga sai iyalansa.


Saman wata kujera ya zauna mai lilo yana kallon pop ɗakin. Zuwa can ya fara jin bachi, daman a gajiye yake. Shigowar Mai Martaba ne yasa shi saurin sauke ƙafafunsa ya tashi zaune.


“Allah ya taimaki Mai Martaba ya ƙara maka lafiya”


Zaunawa yyi da murmushi a fuskarsa.


“Yarima Abdallah, kuma sarkin mu na gobe”


Yayi dariya.


“A dai bar ni a Yariman, har yanzu bana mafarkin zama Sarki”


“Aiko ƙara ja shirya, damin very soon zaka zama Sarki, kasan har yanzu ban faɗa maka albishir ɗin ka ba ko?”


“Shiyasa ma ka ga na zo yanzu”


Mai Martab ya ɗora ƙafa saman ɗaya yana kallon Abdool cike da natsuwa.


“Wato Albishir ɗin ka guda biyu ne, kuma dukaninsu suna da muhimmanci, kuma ina fatar zaka karɓa ka yi na'am da dukansu. Na farƙo dai ina maka albishir da cewar Hajiya Shafa ta baka Zalihatu kyauta, abu na biyu kuma mun yanke shawarar naɗa ka sabon Sarkin Katsina...”


Wani irin kallo yayi ma Mai Martaba kamar Ummi bata faɗa masa komai ba, sai ya sauka ƙasa yana nuna kansa.


“Mai Martaba ni?”


“Kai fa”


Ya faɗa da murmushi a fuskarsa.


“Ka fi kowa karantar waye ni Mai Martaba, ka fi kowa sanin abunda ya dace da ni, ba zaka taɓa zaɓa min sheri ba, kuma na san kafi kowa son farinciki da walwala. Sai dai akwai abun dubawa a maganganun ka Mai Martaba, kamin ni kana da ƴaƴa biyu, waɗanda ko baka raye su suka fi cancanta a ɗora a sarautar nan, bayan kuma Sarkin gari, da Baba Macido ƙanenka ne da ke tunanin idan a yau baka raye, za a iya basu sarautar Katsina, babu wanda zai jidaɗi a cikinsu, idan a ɗauki Sarautar nan aka bani ko da baka raye ballantana kana da ranka kuma kai da hannunka zaka ɗauki Sarautar nan ka ba ni, a iya sanin da na yi ma Sarautar nan, zaɓe ake idan za'ayi sabon sarki, nasan mutane da yawa za su ce ka shigo da sabon tsari ka nuna son kai. Na sani idan cancanta ake dubawa, na cancanta, amman ana barin Halak dan kunya, ni Wallahi ina son aikina kuma ina ƙaunar na mutu ina yinsa”


Mai Martaba yaja wani dogon numfashi ya sauke yana gyara zama. Tabbas Abdool yayi magana mai kyau da kama hankali, hakan kuma ba ƙaramin ƙara burge Mai Martaba ya yi ba, a ƙara karantar irin basira da fikrah da ɗansa yake da ita.


“Haƙiƙa kafi kowa dacewa da Sarautar Katsina, ana son Sarki mai fikra da Nagarta, kuma an fi son Sarki da baya son Sarautar kwata-kwata a ransa. Sai dai hakan be isa yasa na cilasta maka ba, wata ƙila gaba zaka iya neman Sarautar da kan ka”


Hannayensa biyu yasa ya riƙe ƙafar Mai Martaba ɗaya da ke ƙasa.


“Na gode sosai da ka fahimce kuma ka min Uzuri, Allah ya ƙara mana lafiya da nisan kwana. Abu na biyu kuma Mai Martaba na samu matar da na ke so...”


“Namra?”


Yayi ƙasa da kansa yana jin kunya.


“Zamu aura maka duk mace da kake so Babana, ba zamu maka cilas ba, abun da kawai yake da muhimmanci kana son ta”


“Ina fatar hakan ba zai ɓata maka rai ba, kuma ina son na ji ra'ayinka akan auren bazarawa”


“Baka san Annabi S.A.W ya auri Bazawara ba, Nana Khadija ta haifi ƴaƴa ma a wani gidan sannan ta auri Annabi yana yaronsa, balle wannan da ɓata ma haihu ba, indai yarinyar ƴar kirkici mun yarda ka aureta ɗari-ɗari”


Miƙewa yayi tsaye yayi wani tsalle ya dire kamar ƙaramin yaro


“I knew it, daman na faɗawa Ummi tace wai ba zaka yarda ba, har musu take min wai she know you better than i”


Mai martaba yayi murmushi.


“No my son know me better than her”


Rumgume Mai Martaba Abdool yai cike da jin daɗi yana jin kamar ya haɗe shi.






NAMRA POV.


Daga gurin passport tace direba ya wuce da ita gidan su Lamido. Idonta tab da hawaye ta shiga cikin gidan, muryarta kamar wacce zata fasa kuka ta yi sallama. Lamido ne mutumen da ta fara ido huɗu da shi a gidan, kuma ya ƙi ya amsa mata sallamarta balle kauda idonsa daga kallon tarayyar da idanuwansu suka yi.


“Kin zo ban kwanar ne? Ai dama baki dawo ba saboda zaki ƙara saka zuciyana cikin ƙuna ne kawai”


“Don't you happy na shirya da iyayena”


“I won't lie Namra, yes i'm not happy because you are going to leave,kuma ba nine silar wannan farinciki na ki ba bayan wannan shi ne mafarki na a kullum, ina kishin mutumen da ya shirya ki da iyayenki sosai, kamar mutumen da cire min duka tufafi ya bar ni tsirara, kin san ya tozarta ni ko? Ko ba komai idan kika tuna shi zaki yi murmushi ni fa?”


Ta share hawayen da suka zubo mata.


“Namra bata zo gidanku dan ka so ta ba, saboda Namra ta gama so a rayuwarta, na yi rilaya, ɗakin so kuma sai dai wata mai sunana ta shiga amman ba ni ba, ka daina yaudarar kan ka dan Allah”


“Daman na tsammaci haka, saboda ni ba Yarima ba ne, kuma ba wan....”


Hannu ta ɗaga mishi ta tsaka mishi tsawar da tasa su Neina fito daga cikin ɗaki da gudu.


“Shi haka yayi ya yaudare ni, wani namiji ba zai ƙara burgeni ba, put this in your mind i will never ever ever ever love someone again”


Murmushi yayi yasa kai ya fice. Neina ta nufo tana tambayar abunda ya faru.


“Babu komai kawai na zo na yi muku bankwana ne anjima kaɗan zamu wuce”


“Ƙaraso ki zauna mana”


“Ba sai na ƙaraso ba, direba yana jirana a waje”


Sai kawai ta rumgume Neina ta fashe da kuka.


“Zan dawo Neina, rabuwa ba mutuwa ba ce kun min halaccin da ba zan iya mantawa ba”


Nan Neina da Uwani suka saka kuka, dan Maryam bata nan a lokacin. Kamar ba zasu rabu ba haka suka riƙa riƙe juna suna kuka kamar an yi mutuwa, har maƙota suka leƙo suna kallon ikon Allah.


Namra na komawa aka aiko musu da abincin rana, lokaci na yi direba ya zo ɗaukarsu zuwa airport, kamar su ake jira suna isa jirgi ya kama hanyar sokoto. Suna sauka Abbah yayi ma direbansa waya ya zo ya ɗauke su, kuka sosai Namra ta riƙa yi cikin motar ta daman tun a jirgi ta fara abunta, sam bata ji daɗin kalaman da ta faɗawa Lamido ba, sai dai bata da wani zaɓi sai wannan, ga kuma kukan rabuwa da Neina, da kuma kuka dawowa sokoto birnin shehu birni mai albakar da karamci tare da iyayenta komai ya zame mata kamar sabo, bama kamar ta motarsa ta nutsa kai cikin gidan duk an fence shi an sabunta komai saboda bikin Maryam da za'ayi.


Suna jin mota duk suka fito waje har Hajiya Barau da Zinatu da zo jiya suna jiran Abbah da Anty su fito. Abbah ne ya fara fita daga cikin motar sannan Namra ta fito fuskarta da hawaye. Wani irin ihu Maryam ta saka taje a guje ta rumgume Namra suka fashe da kuka, sannan Hindatu da Aisha suka je suka rumgume ta, suma suka saka kuka, Hajiya Barau ce Mamaki ya hanata komai har Abbah da wuce da Anty Amarya sannan ta nufi Namra kunya kunya.


“Wai Namra ce nake gani nan ni mamaki ma ya hanani komai”


“Itace Hajiya, Abbah yaje ya taho da abar sa”


Cewar Maryam tana sharewa Namra hawaye. Sannan suka riƙa hannunta suka nufi cikin gida da ita.




YASMIN POV.


Lokacin da ta bar gidan mijita sai ta nufo gida, sai dai bata yarda ta nunawa mahaifiyarta damuwarta ba, gudun kar ta hana ta aikata abunda take da niyar yi, wuni ta yi a gidan suka sha fira kamar ba komai sai dare ta fito suka koma gida ita da yaranta da kuma mai aikinta. Bata tarar da Uzair cikin gidan ba hakan yasa ta ɗan ji sanyi dan bata ƙaunar ganinsa a yanzu. Abunda kawai take da buƙata ya za'ayi ta haɗu da Namta akwai buƙatar ta tattauna da ita kamin ta fallasa Uzair, ma'ana ta jawa Namra haƙƙinta ko zata samu sanyin zuciya akan abunda ya aikatawa ɗan sa. Haka ta kwana tana tunanin mafita washe gari ma kasa zuwa aiki ta yi duk da tana da cases a kotu, da an kira ta sai tace bata da lafiya ne. Uzair kuma be kwana a gidan ba, da alama akwai gun da ya kwana, sai dai hakan be dame ta ba ko kaɗan tun da tasan wanene shi a yanzu. Bayan ta gama waya da wani Barrister, sai ga kiran Mahaifiyarta ya shigo wayarta.
Bayan sun gaisa take labarta mata ance Namra ta dawo, kuma wai Abbah ne yaje ya taho ta ita, Yasmin ta nuna murnarta sosai daman abun nema ya samu. Dan haka tana kashe wayar ta aje little Namra ta shiga wanka, tana fitowa ta yi ma mata sannan suka shirya daman Adnan yana makaranta. Ƴar aikinta kawai ta bari a gidan ta nufi gidansu Namra.




Tana fita Uzair na shigowa, ciki wani irin yanayi ya buga ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.


“Sannu da zuwa”


Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.






TEEMA POV.


Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.


Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.


Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.


“Kan Uban nan, uban wa zaku jefarwa da jaka nan? Ku kwashe su da sauri ku kai su ɗakin ku, kuma kar a sake zama min saman kujera, wannan ai rashin tarbiya ne manya su zauna a kujera ku ku zauna ni ba zan ɗauki wannan ba”


Ulfa ce uwar tsoro da sauri ta nufi jakarta ta ɗauka ta nufi ɗakinsu. Ezzah kan banza ta yi kuma ta ƙi sauka daga saman kujerar.


“Ke dan Ubanki ba da nake ba”


Sai a sannan ta ɗago kai ta kalleta.


“Mu a saman kujera muka saba zama”


Ta faɗa tana sauka ƙasa, badan hannun Teema da ke da rubutun ba da babu abunda zai hana ta dake ta.


“Wallahi kuka kuskura min rashin kunya zaki wahala a gidan nan”


Sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu, Ulfah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin tana leƙo ta shige da sauri.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *79*


Su Maryam na wucewa Zinatu ta rufa musu baya ita ma tana murmushi. Hajiya Barau kuma ta koma part ɗinta, bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki wayarta ta kira Uzair. Bugu biyu ya ɗauka, saman-sama ya gaisa da ita saboda shi ma be cikin daɗin rai, sannan ta labarta masa Namra ta dawo, he was shocked and surprise, sai ya ji maganar kamar daga sama.


“Da gaske kike yi?”


“Wallahi da ido na na gani, yanzun nan Alhaji ya dawo tare da ita, kasan na labarta maka ai Sarkin Katsina ya aiko ƴana nemansa ni na ɗauka ko wani abu ta yi, sai gashi kuma na ga sun dawo da ita”


“Aurenta ya mutu ne?”


“Bari naje gurin Alhaji na ji”


“Okay ki sanar da ni duk abunda kika ji”


“Tau”


Tana kashe wayar ta nufi part ɗin Abbah. Ko da ta shiga yana banɗaki, har ta zauna sai kuma ta yi saurin tashi ta koma part ɗinta, fruit ta yankawa Abbah ta saka madara, ta ɗauka ta nufi koma part ɗinsa. Wannan karon zaune ya same shi saman gado yana waya, sai ta zauna kusa da shi tana riƙe da fruits, sai da ya gama wayar sannan ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.


“Hajiya fatar dai lafiya”


“Lafiya ƙalau bana da ikon da zan zo na ga miji na ne? Ga ɗan abunda na haɗa maka, abinci na kan wuta ban ƙarasa ba”


“Ai bama na ma jin yunwa kamin na taso sai da muka ci abinci”


“A can gidan Namra?”


“A'a a gidan Mai Martaba Ahmad Mai-doki Sarkin Katsina, dake Kaduna”


“Ban gane ba, baka labarta min zaka dawo da Namra ba, duk lokacin da na tambaye ka sai ka ce min wani babu wata matsala dai, ya akayi ka dawo da ita bayan kace ba zaka karɓe ta ba?”


Wani kallo Abbah yayi mata.


“Ya kike magana kamar wacece bata ji daɗin dawowar Namra ba? Komai ta yi min aduniyar nan she still my daughter, ko lalacewa ta yi dole za'ace ƴar gidan nan ce, ballantana ina son ta, kawai dai ta ɓata min rai ne kuma ta gane kuskurenta”


“Ta gane kuskurenta kamar ya? Alhaji yanzu baka tunanin mutane zasu zarge ka akan ka yi magana kuma ka zauna? Wannan ai talalace ka yi mata yarinya ta yi laifi kuma yanzu da miji ya wulaƙanta sai kace kayafe mata haka ake yi?”


Abbah yayi murmushi, yana gyara zamansa.


“Baki gane abun ba ne Hajiya wato da muka sauka Katsina...”


Ya kwashe labarin abunda ya faru ya faɗa mata, daman can Anty Amarya ce ta hana a faɗawa kowa wai tana son kawai su ganta ne. Mire baki Hajiya Barau ta yi ta miƙe tsaye.


“Yanzu Alhaji im ban da su mai da wani iri sai da Asim ya gama wulaƙanta ta ya sake ta sannan yanzu su haɗa baki da uwarta su nemo wani a kai ga Sarki, wannan ma ai rainin wayo ne, yarinyar ta yi wasa da hankalinka, yanzu kuma kai har ka yarda ta gane kuskurenta haba Alhaji wannan ai ka bata damar ƙara aikata abunda ta aikata ne kawai”


Wani wawan kallo Abbah ya watsa mata.


“Na bata damar, ko yanzu Namra ta kawo min wanda take so zan aura mata, daman na lura da ke ba son yarinyar nan kike ba, mi ko duk wanda be son Namra bana son shi, dan Namra jinina ce, ƴata ce, ina kula da yadda kika ɗauki matar nan ita ba haka ta ɗauke ki ba, baki son ta ita da yaran ta, ana gobe za mu bar garin nan nan cikin falon nan nawa kika saki wata magana wai Allah yasa Namra bata yi mana jaye-jaye ba, a gaban uwarta amman ta miki kawaici ta tashi ta bar miki falon bata ce komai ba, shiyasa na zaɓi zuwa da ita na ƙi na tafi da ke, iya haƙuri matar nan ta nayi yinsa da ke amman ke baki ga, ina kula da abun nan da Namra ta yi kamar daɗi yayi miki, ba zan ɗauka ba kar bakin ki ya sake furta mummun kalma akan ƴaƴana!”


Ta riƙe baki.


“Alhaji kai kake faɗa min wannan maganar akan Namra? Daga na faɗa maka gaskiya har kace wai bana son ta ita da uwarta? Kuma ka ce baka da so na saboda ƴarka? Anya banza matar nan ta barka Alhaji”


“Ba banza ta bar ni ba, ta kula da ni fiye da yadda kike tsammani, dan tana son ki ke da ƴaƴanki, ba kamar yadda kike nuna mata ba, kuma daga yau sai yau, kar wani munafurci da wata magana marar daɗi ta sake fitowa bakinki akan Ƴaƴa ko wannan matar tau a bakin auren ki! Kar wacce ta aake tadarmin fitina yadda na ga dama haka zan yi a gidana”


Mutuwar tsaye Hajiya Barau ta yi a gurin, tana mamakin Abbah ta ya juye kamar ba shi ba, wai yau shi yake faɗa mata wannan maganar, har yake cewa bakin aurenta. Uffan bata yarda ta sake cewa ba, ta nufi ƙofa cike da nauyin jiki fice sun-sun-sun, hannayenta a baya tana jin kamar an ɗora mata dutse saman kai.


NAMRA POV.


Cikin falo suka riƙa hugging ɗin juna ita da ƴan'uwanta, suna jin kamar su haɗe juna ita da su, sai faman kuka suke. Anty Amarya ta fito daga bedroom ɗinta fuskarta da dariya ta ce


“To ko haɗe ta zaku yi?”


“Anty Faɗa mana yadda aka yi ta yarda ta biyo ku kuma har Abbah ya amince”


Aisha ta faɗa tana laƙƙame da wuyan Namra.


“To ku sake ta taje ta yi wanka ta shirya zan baku labarin komai”


Aisha da Hindatu ne suka saketa yayinda Maryam ta laƙƙame hannunta suka nufi bedroom tare. Bayan sun tashi Zinatu ma ta tashi ta nufi part ɗin Mahaifiyarta. A sannan ne Anty take tambayarsu yaushe Zinatu ta zo.


“Tun ranar da kuka tafi, wai faɗa tayi da mijinta ya ce taje gida, shi ne wai ta baro masa yaransa”


“Subhallahi, miya haɗa su haka?”


“Wallahi bata faɗa ba, ai kin san Hajiya ba zata bari ta faɗi gaskiya ba, dan ita Hajiya ma ce mana ta yi bikin Maryam ta zo”


“Tau Allah ya sauwaƙe yayi mata mafita, ku tashi ku girka mana abinci dan ni dai ba zan ci taliya ba”


Hindatu ta mike tsaye tana dariya.


“Komai kuke so za a muku, sai ku ba mu labarin abunda ya faru”




A ɗaki da suka shiga Namra take labartawa Maryam irin abunda Asim yayi mata, da yadda ta yi rayuwa gidansu Lamido da kuma haɗuwarta da Abdool ya yadda ya haɗa ta da su Anty.


“Ke ni wallahi na jidaɗin da auren ya mutu kuma cikin ya zube, dan zai iya cewa ya maida ki ko dan ɗansa ko kuma ya ce zai maida ki kamin ki cika idda amman yanzu ba ciki ba goyo dole ya ƙyale ki dan ubansa, tsinan nen banza”


“Ba laifinsa ba ne Maryam, laifina ne a gareni ya ga wannan damar kuma ni na zaɓe shi sama da iyayena. Amman yanzu Alhamdulillahi tun da Abbah ya ƙarɓe ni”


“Gaskiya nima na jidadin hakan ciwon Anty zai warke, kuma za'ayi biki da ke, amman dai wannan yaron son ki yake ko?”


“A'a ba so a tsakanin mu, bikin wa za'ayi?”


“Bikina mana ni da Hindatu sati mai zuwa za'a ɗaura aure, Wednesday za'a fara biki”


“Amman shinw ba a faɗa min ba?”


“To ba kin zaɓi wasu family sama da mu ba”


“Haba Maryam, ai komai na zama ni ƴar'uwarku ce jininku, be kamata ku min haka ba”


Maryam ta laƙƙamo kafaɗarta tana dariya.


“Ai yanzu kin dawo ma hanya, komai da ke za'ayi Maman su Babanmu”


Ɗan Murmushi Namra ta yi ta miƙe ta shiga wanka. A wunin ranar haka suka riƙa treat ɗin Namra kamar wata sarauniya, sai faman dare-dare suke suna rumgume ta. Suna cikin haka sai kawai ta fashe musu da kuka da kuma dariya lokaci ɗaya.


“Ban taɓa tunanin rayuwa zata dawo haka ba, i miss my family a lot”


Hannu Aisha tasa ta share mata hawayenta, sannan ta miƙa mata wayarta da ke ringing.
Namra na karɓa ta zaro ido.


“Asim ne”


“Asim”


Maryam ta amsa da ƙarfi, kana ta ce.


“Ba ni shi”


Anty ta ɗaga mata hannu


“No barta ta yi picking mu ji me zai ce”


Sai da ta yi ajiyar zuciya sannan ta danna picking ta kara a kunne.


“Hajiya Namra kenan! Ina kika shiga na yi nemanki cikin garin Katsina da kewaye baki ciki”


“Ina kake tsammanin zan kasance bayan gidan Ubana”


“bakya giɗan ubanki kam dan na bincika aka ce min baki can, faɗa min inda kike je? Karki damu da tambayar da nake miki ina son naji lafiyar Baby na ne”


“Bka da wani Baby Asim saboda ka zaɓi rabuwa da ni ne saboda shi”


“Yanzu kuma ina son abuna sai yaya?”


“Amman babu kaskantacce wulaƙantacce wawa kamar ka Asim, yanzu da baka da kunya zaka kira ni ka ce min wai lafiyar cikin ka zaka ji?”


“Bana da damar hakan ne? Ai Allah ya ɗora min haƙƙin kula da ke har sai kin haihu, kuma dole ne na bincika ko da kina da buƙatar wani abun sai a kawo miki”


“Kai har kana ganin ka yi arzikin da zaka iya ɗaukar nauyin cikin ka, ka daina wahalar da kan ka dan ni yanzu babu ciki a jikina kuma karka sake kirana”


Tana kaiwa nan ta kashe wayarta tana huci. Anty bata muƙatar ta faɗa mata dalilin kiran nasa dan ta fahimci komai. Ko minti biyu ba tayi ba ya aiko mata sako.


_Wallahi duk kika zubar min da ciki sai mun shiga kotu da ke_


Namra na gama karanta ta nunawa Anty.


“Karki sake ɗaga wayarsa karki sake ce masa komai, har sai mun ji abunda Abbah ki zai ce”


Maryam ta yi ƙwafa.


“Wallahi samun family masu haƙuri irin wannan yana da wahala, wlh da wani guri ne da sai an wulaƙanshi kam uban nan...!”


Anty ta nuna ta yatsa.


“Maryam ki cire wannan zafin ran da kike da shi, aure zaki yi kuma mace kike, abunda duk haƙuri be baka ba rashinka be baka shi, duk wanda ya ci amana kin taɓa ganin ya

Please Login or Register in order to submit comment