Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ita.


Asymptomatic period


(asymptomatic period) ma`ana lokachin bacewar alamomi. A wannan lokaci cutar bata nuna ko wace alama na rashin lafiya ko ciwo na wasu watanni ko shekara. Amma akwai kwayar cutar a jikin mutum. A wannan lokacin kwayar cutar na dada yaduwa (replicating) da kuma kashe garkuwar jiki (immune system). Sannan a wann lokaci kwayar cutar tafi karfi da kuma yadu ta hayoyin da mukayi bayani a yadda ake kamuwa da cutar.


Advanced infection


(Advanced infection) a wannan lokachi kwayar cutar ta riga tayi damejin garkuwar jiki (immune system) yana daukan lokachi amma idan ya kai wannan lokachi to cutar ta kan zama AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) mutum kan kamu da wasu cututtuka sakamakon damejin garkuwar jiki (immune system damage) zaizama garkuwar jiki bai iya yaki da kwayar cuta. Alamomin wannan bangare sune:


 Hamami
 Amai
 Gudawa
 Ma tsanachin gajiya
 Raguwar nauyi /rama
 Tari da numfashi sama sama
 Zazzabi me tsanani akai akai (recurring fever)
 Kwararraji masu ruwa a baki ko hanchi ko a fata da kuma alaura,
 bushewar makokoro
 kunburin lymph node na gabobi mara warkewa.
 Kidimewa, tabuwar kwakwalwa daga nan kuma watakil sai mutuwa”


Hankalin Rashida ya tashi sosai wasu daga cikin abubuwan da Likitar ta faɗa duk tana jinsu, amman tayi tunanin ko cikine a lokacin. Ji take kamar ace ba da gaske bane




“Amman Dr Bayan wannan babu wata alama da mutum zai iya gano tabbacin yana ɗauke da cutar?”


Ko da ta tura mata saƙon ta riga ta sauka online, a lokacin 10:23pm ne. Kasa natsuwa tayi har sai da ta lalobu number Dr Fatima ta sake kiranta.


“Dr kina min bayan sai kika sauka”


“Eh Wallahi mai gida ne ya shigo”


“Dan Allah ki taimaka ki ƙarasa min, gobe zata rubuta abun yanzu haka duk ta dame ni”


“Okay bari ya gama cin abinci zan hau online”


Daga haka ta kashe wayar tana tunanin nata mijin. Whatsapp ta shiga tana duba last seen ɗinsa, ta ga biyar da kwata na yamman nan. Dp shi take kallo wani hoto ne ya ɗora yana sanye da kayan likitoci yana murmushi. Fashewa tayi da kuka ta rumgume wayar a ƙirjinta.
Sai da tayi kukanta ta gaji sannan ta ɗago wayar ta sake kallon hotonsa tayi masa kiss sannan ta shiga chat ɗin su da Dr Fatima, ashe ma tuni ta turo mata da bayanin bata gani ba.


“Ana gano mutum na dauke da wannan cutar ta tsida ta hayar gwajin jini, (serum), miyau, ko fitsari ta hanyar sanya musu wasu sinadarai dake sanya a gano kwayar cutar aciki wato HIV (human immunodeficiency virus) wadda ita take haddasa AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) wanda mukayi bayani a sama. Anfi gano mutum na dauke da cutar ta hanyar gwajin jini”


Ta haɗeye yawu ya fi sau biyar sannan ta sake aika mata da wata tambaya, wace ita ce dalilin tambayarta tun farko.


“Dr ya mutum zai kare kansa ko kuma wani nasa daga kamuwa da wannan cutar?”


 “Yin gwaji don sanin akwi ko babu.
 Rage yawan saduwa.
 Anfani da roba (condom) wajen saduwa.
 Kiyaye saduwa da mata/maza daban daban.
 Gwaji da kuma maganche cututtukan saduwa STDs (sexual transmitted disease).
 Kiyaye yin amfani da allurar da wani yayi anfani da ita.
 Tabayar likita dangane shan PrEP (pre-exposure prophylaxis) shima wani hanya ne na kiyaye kamuwa da ita wannan cutar


Rashin kiyaye ita wanan cuta kan sa mutum ya halaka da wuri. Ana kiyaye cutar ta hanyar yin anfani da (antiretroviral drugs) magunguna ne da ake afani dasu wajen magance cututtukan virus, kusan ita wanna cuta bata da maganin warkewa sai kiyaye ta, ta hanyar anfani da magunguna da likitan ya dorashi mutum akai”


“Na gode sosai likita Allah ya saka da alheri”


“Ba a son mai cutar yana kusantar hayaƙi, ko cizon sauro ko wani abu makamancin wannan, saboda abu kaɗan yana iya ƙara cutar, an fi mai cutar ya ci abubuwan gina jiki like vegetables”


“Thank you”


Rashida ta rubuta daga ƙarshe, sannan ta kashe wayarta tana hawaye.


“Dole ne naje nayi gwaji dan na tabbatar, wata ƙila ma na ɗauke da cutar, ai za a iya min sheri tun da ba a son zamana da Hilal”


Ta faɗa a fili tana share hawayenta. Sai kuma zancen da Asmee ta faɗa mata ya dawo mata na zargin kanta da take tana ɗauke da cutar, ita kuma ta san tana mu'amala da mijin Asmee. Jefar da fillon dake saman gadon tayi ta wani irin matsa gashin kanta.
Haka ta kwana har safe tana kuka idonta ya kumbura sosai kamar an zuba mata wani abu a ciki, bata fita ɗakinta ba, abincin da Momy ta kawo mata bata ci ba, sai kawai ta shiga banɗaki tayi wanka ta saka abaya, ta fito falo, ba dan tana jin ƙarfin jiki ba, sai dan tafitar ta zame mata kamar dole ne.


Momy na ganinta ta cika da mamakin ganin ta fito da shirin fita.


“Ina zaki je?”


“Ina son na ɗan fita ne, zan je office na ɗauki hutu sai na je gidan Asmee”


“Haba Rashida yanzu cikin wannan yanayin zaki fita sai kace wanda bata son kanta?”


Idonta ya cika da ƙwallah


“Momy ina son fitar ne ko zan samu gwarin jiki, kuma na sha iska, ko damuwa zai rage min”


“Kuma Sisters naki duk sun tafi school balle su raka ki, zaki iya driving ma”


“Zan iya”


“Shiga ɗaki ki ɗauka keys ɗina”


Momy ta faɗa cike da tausayawa. Ɗakin Momy ta shiga ta ɗauki makullin motarta, dan ita yanzu komai nata yana can gidan Hilal babu abunda aka ɗauko.
Cikin ƙarfin hali take driving ɗin, kamin ta ƙarasa office ɗin ta tsaya gefen titi tayi parking, ta kira number Malamin nan. Bayan sun gaisa ta koro masa da bayaninta.


“Malam aiki nake son ka min akan kishiryata”


“Me kike son a mata a kashe ta ko a haukatata?”


“Bana son a mata ko ɗaya, wani daban nake son ka mata wanda mijina zai gaji da ita ya rabu da ita sai ka min wanda zai dawo gare ni, a halin yanzu mijina ya rabu da ni”


“Me kika masa? Ina labarin waɗancan mutanen dana haɗa ku da su?”


“Ba mu yi aikin ba, saboda auren ya riga ya mutu, kuma wallahi ina son miji zan iya mutuwa idan babu shi a kusa da ni”


Ta faɗa cikin wani irin kuka, kamar ance mata malamin yana gabanta ne.


“Ya isa daina kuka, ai wannan mai sauƙi ne, akwai aikin da zamu masa ya dawo gunki da gudu ma, ita kuma za mu sakar mata jini sannan mu saka mata warin jaɓa idan ya gaji da ita zai sake ta, amman zaki kashi kuɗi”


“Kuɗi ba matsala bane zan baka ko nawa kake so, amman ina son a buga min ƙasa a bincika min komai nawa”


“Zan miki haka, duk abunda ƙasa ta faɗi zan faɗa miki idan kin zo, amman idan kin shirya aikin ki zo da tulo da zanen haila wanda ita kishiyarki take amfani da shi”


“Malam ya za'ayi na same shi yanzu, bayan bana gida kuma ai kasan yanzu ba'a amfani da irin wannan abun yanzu duk pad ne ake sawa”


“Pad ɗin shima ai zai yi, ki bincika a bolar gidan, idan kuma ba zaki iya ba, kisa zo ki biya kuɗi mu zamu sa aljani ya ɗauko mana”


“Zan zo nan da kwana biyu, na gode”


Daga haka ta kashe wayar ta ɗora kanta saman sitarin motar, kamin ta ɗago ta cigaba da tuƙin.
Wata pravate hospital ta nufa dan yi gwajin jinin so that ta tabbatar da zarginta.


AMIRA POV.


Har suka sauka garin Abuja bata wani farinciki musamman data ga hoton wanda ake son su kashe ɗin, sai duk jikinta ta mutu, ta tabbatar mutumen ƙwarai ne dan in ba haka ba babu abunda zaisa wasu su nemi a kasheshi.
Mutumen data taɓa gani a tv she can't recall his name, amman dai tasan shine wanda aka taɓa tattauna da ashi akan tsaro har ta ji ya kwanta mata a rai.


“Guy please karku taɓa mutumen nan”


Hancinsa yasa yana gogawa a kumatunta.


“Ina son ki sosai Amira, amman akan aikina zan iya ɓatawa da ke, so ki daina sa baki a kan aikina”


Ya ciro wayarsa dake aljihu ya kara akunne


“Hello ....Okay”


Ya kashe wayar yana kallonta


“Wai ya fita, zo muje”


“Tun yanzu za ku kashe shi?”


“A'a zamu fara farautarsa ne, yana Sahaba Restaurant, akwai yara dana aje Sahaba Hotel, kisa da inda yake, nima kuma can zanje amman sai gobe”


Ajiyar zuciya ta sauke ta janye hannunta daga riƙon da yayi mata.


“Ba zan je ba ku tafi kawai”


Duƙawo yayi ya mata kiss, sannan ya fice.
Ji take bata da natsuwa idan bata faɗawa masa abunda yake faruwa ba, sai dai kuma taya zata faɗa masa bayan shi ɗin babban mutum ne ganinsa ba hakan ake yi ba. Kuma idan har ta aikata ta jefa rayuwarta cikin matsala.
Sai da ta ji tashin motarsu sannan ta tashi ta shiga binciken gidan, har ta samo paper da pen tayi rubutu akai sai ta sanya doguwar riga dan jikinta inner ne kawai ta fito harabar gidan tana dubi-dubi.
Har tayi tunanin ta hau Napep sai kuma ta tuna Abuja ba ko ina ake farin Napep na shiga ba, sai kawai ta koma ciki ta tashi ɗaya daga cikin yaransa ta ce ya kai ta, yaso ya musa mata amman sanin halinta da kuma yadda Guy ke ji da ita yasa dole yaja mota ta shiga suka kama hanya.


Suna isa Sahaba Restaurant, sai ta hango Sahaba Hotel kamar yadda Guy ya faɗa mata. Nesa da gurin tasa ya aje ta tace ya tafi ya barta zata je gurin Guy, ba musu yaja motar ya koma. Sai da ta daina hangosa sannan ta nufi Sahaba Restaurant zuciyarta cike da tsoro gabanta kuma kar ma zai zube ƙasa.


Guy na daga gefe ya hango Amira ta doshi Restaurant ɗin sai waje-waje take.


“What the fuck, me Amira za tayi can ? Ko ta ɗauka ina can ne?”


Ya tambaya yana kallon yaransa da suke tare da shi cikin motar, wanda ko wannensu ba shi da amsar ba shi. Da sauri ya buɗe motar ya tara hannayensa a baki yana mata fiito (shewa) irin na tsuntsaye. Amira na jin kira ta san Guy son ne, maimakon ya ga ta dawo sai kawai ta ranta cikin na kare.




ABDOOL POV.


Ganin kurciyar ta firanye sai kawai yayi musu alama da hannu akan su koma kawai. Shi kuma ya koma cikin gidan, ya kunna tv yana kallon news, lokaci zuwa lokaci yake jan tsaki saboda lamarin nijeria kullum abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, yau wannan kakeji gobe wani kala ne. Idan ma kace zaka maida hankali akan abun sai tunani yayi maka yawa.


Wuni yayi a cikin sallah ce kawai take fitar da shi gidan, sai da dare ya sauya kayan jikinsa ya fita siyen abinci dan be yarda a dafa masa a abinci duk kuwa da kasancewar akwai masu masa dafa masa, amman baya ci sai dai sauran ƴan gida su ci. Ko a gurin siyen abincin ba guri ɗaya yake tsayawa ba, saboda tsaro.
Bayan ya karɓi takeaway ɗin ya biya sai ya juyo ya nufi ƙofar fita. Yana fitowa ya hango budurwa tana gudu iya ƙarfinta ta doso inda yake, kallon mamaki yake mata yana son tantance abunda take ma gudun.
Sauran taku kaɗan ta ƙaraso inda yake, sai ƙarar bindiga ya tashi, cikin wani irin zafin nama ya riƙota dan ya gane ita aka harba, sai dai haka be hana bindigar samunta, sai ta sulale a hannunsa tana banƙarar bayanta saboda zafi da kuma dafin albarushin da taji ya soke ta abaya.


Daga shi har ita tare suka kai ƙasa, cikin hanzari ya ciro wayarsa ya kira yaransa. Sannan ya kira head quarters.










*🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*


*© Khadeeja Candy*


Don't read if you didn't pay...!


*PAGE - 44*


NOT EDITED ⚠


_An kaiwa Major General Abdullah Ahmad Mai-doki hari_


_An yi nasarar kashe waɗanda suka kaiwa Major hari_


_Yarima Abdullahi Ahmad Mai-doki Ɗan sarkin Katsina ya tsallake rijiya da baya_


_Wata yarinya ta sadaukar da ranta saboda ɗan Sarki_


Shine abunda kowa wace jaridar Nigera ta online ta yi ado dashi a fuskarta shafinta, har ma da na ƙasashen waje, bayan mintuna 25 da faruwar lamarin.
Online rumors updated kuma kowa da abunda yake rubutawa, har da masu cewa har shi an harba da masu cewa ma ya mutu, da masu cewa yaje siyen abinci da karuwarsa, wasu kuma matarsa ko dai da irin yadda tayi masa daɗi yake ƙaƙarowa ya rubuta a social media.


Dandazo ƴan jarida suka yi a bakin asibitin da aka kai Amira, dan jin kanun labarai, ko wannen baya son a bashi labari.


Sai dai sojojin da ke zagaye da asibitin basu ba su damar shiga ciki ba, balle har su ɗauki rahoto ko kuma video abunda yake kan faruwa ba.


A bakin kofa Abdallah ya tsaya yana kai da kawo har sai aka fito da ita ɗakin tiyata, bayan an cire mata albarushin.


“Doc is she live?”


Shine abinda Abdallah ya fara tambaya ganin an fito da ita daga ɗakin galalla kamar wanda bata numfashi, a kife take saman gadon asibitin dan a bayanta ne suka mata aikin cirar albarushin.


“She survived, but she's unconscious now and she will take 28 -32 hours before she wake up”


Likitan na faɗar haka ya suka wuce da ita wani ɗakin, tare da wasu Nurses. Da kallo Abdool ya bita sai da duka shige da ita ɗakin sannan ya sauke ajiyar zuciya ya shafa kansa. Sannan ya zauna a kujerar dake gurin ya lumshe ido yana sauraren wayarsa da ke ringing.


Kira ne kan kira yake shigowa, tun wayar tana ringing da vibration ita kaɗai har cinyarsa ta gara amsawa, saboda yawan kira. Shi dai yasan ba zai iya ɗaukar kira kowa a yanzu ba, dan yasan ba zai wuce masu son jin lafiyarsa ba, abu ɗaya yaji zai iya, magana da ƴan jarida dan tabbatar musu da lafiyarsa. Hakan yasa ya miƙe tsaye ya ciro wayar ya miƙa PA ɗinsa dake tsaye kusa da shi.


Wani ɓangare na asibitin ya nufa, inda sauran sojojin suke. Yayi magana da su akan a canja ma Amira asibiti zuwa asibitin sojoji da ke Abuja. Cikin sirri suka kawo wata mota ya shiga yaje gida ya tsimtsa ya canja tufafin jikinsa dan duk sun ɓace da jini.
Army uniform ya saka ya shiga wata motar ya koma asibitin. Ko da ya isa har an canjawa Amira asibiti zuwa asibitin daya buƙata, wajen asibitin ya fito yayi magana da ƴan jarida ya tabbatar musu da abunda ya faru, sannan ya juya ya koma cikin asibiti shima aka soma duba lafiyarsa duk da sun san albarushin be same shi ba.


“Sir Hajiya ta matsa sai ta yi magana da kai, Mai Martaba ma ya kira tun ɗazu kusan sau biyar”


Ya faɗa bayan ya tsare masa ya maƙe guri ɗaya kamar irin ya sha jinin jikinsa ɗin nan.
Sai da aka cire masa abun awan jini sannan ya karɓi wayar. Number Mai maitaba ce wannan karon hakan yasa shi murmushi.


“My Royal Highness”


“Babana kana lafiya?”


“Ina nan ƙalau Mai martaba”


“Babana karka ɓoye min komai”


“Wallahi Babu abunda ya same ni, sai dai yarinya ita sun same ta”


“Ga mu nan gida duk sun rikice sai koke-koke suke, Ummin ka ma ta kirani wai nayi waya da kai? Ta kira ba kai ka ɗauka ba, tana jin dai ko sun same ka bata san halin da kake ciki ba”


“i'm fyn Mai martaba, yanzu nan ma nayi magana da ƴan jarida, da kun kalli news za ku gani ai”


“Wai ya abun ya faru? Kuma su wanene?”


“Wallahi ban san su ba, amman dukan an kashe su, ni ina fito daga restaurant ne kawai sai naga yarinya tana gudu ta doso inda nake, shine sai kawai naga wani ya fito a wata mota dake can nesa da mu, amman haka be hana bingdigar samunta da yake Allah ya rubuto, sai duk muka faɗi, sai na kira boys ɗin mu dake nan gida na faɗa musu sannan na kira head quarter na faɗa musu, kamin su bar gurin sai da suka harbi mutum biyu, kuma duk sun mutu. Sai dai dikansu basu tsira ba sai akayi musu ƙofar rago suna ganin haka sai suka fara buɗawa boys ɗin mu wuta, suma sai suka buɗa musu. Anyi nasara akan su dan an kashe su duka, sai dai suma sun kashe mana soldiers biyu”


“Subhanallah Allah ya tsare gaba, amman ita yarinya ba tare take da su ba?”


“Bana jin haka da ba zasu harbe ta ba, kuma ta zo da wata takardar hannunta an rubuta, wai nayi taka tsan-tsan akwai masu son kashe ni suna bibiyar sawuna, ba zasu min komai a garin Abuja ba har sai na isa katsina saboda sasu akayi”


“Amman ya akayi ita yarinyar ta san da wannan? Anya ba haɗin kai ba ne?”


“Tunanin hakan yasa aka bincika bullet ɗin dan a tabbatar na ƙwarai ne ko roba, an bincika bullet ɗin na ƙwarai ne irin wannan ne da ake shigo da shi ta waje, ta ɓarauniyar hanya, yanzu dai duk wasu tambayoyi sai idan ta farka zamu mata”


“Allah ya tsare gaba, a riƙa taka tsantsan Babana kana wasa da rayuwarka fa”


“Kar hakan ya dame ka Mai martaba, ɗan Adam baya wuce ƙaddararsa, kuma abunda Allah ya kawo babu mahani”


“Haka ne, amman gobe zaka dawo ko?”


Yayi dariya yana mai miƙewa tsaye ya nufi window gurin.


“Gobe kuma? Ai bamu gama meeting ba, akwai wanda za muyi gobe da jibi kamin na dawo”


“Kai ni wannan aiki naka Babana yana tsorata ni”


“To ya muka iya? Dole ne mu saiyardar rayuwarmu dan wasu su rayu”


“Toh Allah ya kyauta. Ga Mamanka zaku gaisa”


Haka Abdool ya bisu ɗaya bayan ɗaya yana gaisawa da matan uban masa da ƙannensa da ƴan'uwansa da suke gidan.
Yana katse kiran Mai martaba ya kira Ummi, ringing ɗaya ta ɗauka tana kuka.


“Son...”


“Ummi I'm fine Wallahi babu abunda ya same ni”


“Ban yarda da kai ba, ai ba zaka faɗa min gaskiya ba, naso na biyo mota saboda babu jirgi yanzu amman gobe da safe zan zo”


“Ummi you don't have to, Wallahi babu abunda ya same ni, yarinyar data tare min bullet ɗin ita aka samu, kuma an yi nasarar kashe su duka”


“I don't trust you”


“If you don't trust me, you should trust yourself, believe yourself remember how you treated your Son he will never ever lied to you”


“You started it”


“No I'm just show it”


“Whatever ni dai gobe zan zo”


“To Allah ya kai mu”


“Amin. Ga sisters naka za ku gaisa sun ta kiran wayarka sai wani ya ɗauka”


Ɗaya bayan ɗaya ya gaisa da su sannan Ummi ta karɓa.


“Ka kira Mai Martaba ɗazu na kira shi yace shi ma hankalinsa a tashe yake be same ka ba”


“Yanzu muka gama waya da shi”


“Okay, Son su waye ne suka maka haka?”


“Nima ban san su ba maƙiya ne kawai”


“Amman ita yarinya ta rayu? Ka santa ne? Ina ka haɗu da ita”


“Na fito ne kawai sai na ganta tana gudu ta doso inda na ke, shine suka buɗe mata wuta, tana da rai amman tana buƙatar addu'ah dan tana cikin mawuyacin hali”


“Allah ya tashi kafaɗunta, ko dan na mata godiya for what she did to our family”


“Ni kaina ina son ta tashi dan akwai tambayoyin da na ke son ta amsa min”


“Allah ya bata lafiya gobe zan zo”


“Ummi”


“Don't!”


Ya riƙe bakinsa kamar tana gabansa.


“To Allah kawo ki lafiya”


Daga haka ya kashe wayar ya juya ya fice daga ɗakin. Ba shi ya bar asibitin ba sai da ya karɓa waya ta fi a ƙirga ɗuk masu tambayar lafiyarsa ne ƴan'uwa da kuma abokan arziki.






NAMRA POV.


Tun da Yasmin ta bar gidan bata fito ko bakin ƙofa ba, balle har ta fito falo, Gwaggo Kulu bata takurata ba, dan tasan halin Namra daman can ba mai son surutu bace balle yanzu data fuskanci kamar tana cikin damuwa.


Duk wainar da ake toyawa a falon Namra bata sani ba, dan hankalinta ma kwata-kwata baya jikinta yana can wata duniyar tana tunanin lamarin rayuwa, yadda ta sauya mata a lokaci ɗaya. Turo ƙofar da Hindatu tayi ne yasa ta dawo hayyacinta har ta ɗan tsorota.


“Anty Namra”


Ta rumgune ta zumuɗi ita da Aisha. Ƴar far'ah tayi irin far'ar nan data zame maka dole tun da tasan ba zuwan daɗi ne ta yi ba.
Sai daga baya Maryam ta shigo dan tun shigowarta tana can gurin Gwaggo tanan mata faɗa akan rashin son zumunci, wai rabonta da gidan har ta manta.


A bakin ƙofa ta tsaya tana murmushi.


“Ta so muje ƴar Anty Abbah yace mu zo muje da ke”


“Da gaske?”


Namra ta tambaya tana zaro ido, irin mamakin ɗin nan da rashin yarda da zancen Maryam. Sai Aisha ta karɓa mata.


“Wallahi kuwa, da gaske shine ma ya kira ki a waya yace muje mu ɗauko ki”


“Ko dai wani abun ai min?”


Ta faɗa da muryar tausayi tana kallonsu, dan bata gamsu Abbah zai ce aje a zo da ita hakan nan kawai ba.


“Babu abunda zai miki baya ma gidan yanzu na fita, Anty ce ta buɗe masa wuta shiyasa ya yarda”


Shiru ta ɗan yi tana tunani, kamin ta miƙe tsaye ta ɗauki jakarta ta rayata, ta kalli Maryam.


“Dan Allah Abbah ne yace na zo?”


Maryam ta dafe kanta.


“Kai ni Allah na, Namra nawa zaki biya ni ne da zan miki ƙarya”


“Ina jin tsoro ne”


“Daman ai kullum cikin tsoro kike”


Ta juya ta fice tana mai jin haushin lamarin Namra. Cikin rashin kuzari ta fito ɗakin tana riƙe da hannun Aisha ta zo ta risina gaban Gwaggo dake zaune falon tana mata sallama kamar wanda bata son zuwa.
Gwaggo na kallon idonta ta kalli Maryam tace


“Duk aka haɗa baki da ke aka yi ma Namra wani abu ko? Heeeee Wallahi sai kin raina kan ki”


Maryam ta ɗora hannu saman kai tana dariya


“Oh Ni na shiga uku, wai fuskata tayi kama da mugaye ne hala?”


“Na dai san halin ki, shegen karanbani da iyayi, kuma na faɗa miki, wallahi ran ki sai ya fi na kowa ɓaci duk aka haɗa baki da ke”


Da dariya ta fita falon. Har gurin Mota Gwaggo ta raka su, tana yi Maryam jan kunne ta daina tuƙin dare kuma ta kula da hanya ban da gudu.


Har suka isa gida gaban Namra be daina dakan uku-uku ba, saboda tsoro da tunanin abunda Abbah zai mata. Lokacin da Namra ta fito motar sai ta ɗaga kanta sama ta kalli gid, idonta ya cika da hawaye, tuna rayuwar da tayi a ciki, da hawaye shaɓe-shaɓe Hindatu taja hannunta suka shiga falo.
Tsaye suka same Anty Amarya tana tsumayinsu, duk wani kunya da take na Namra yau cireshi tayi sai ta zo da sauri gurin ƙofa ta rumgume ƴarta idonta cike da hawaye, haƙiƙa tayi farincikin ganin Namra, sai dai kuma bata jidaɗin ganin yadda ta lalace ba, kamar wance ta shekara tana ciwo.


Maryam ne da Aisha suka ɗauko mata abinci da sha suka jera saman center table. Namra ta kallesu da murmushi.


“Thank you Sisters amman ni ba na cin komai”


“Saboda me? ”


Anty Amarya ta tambaya.


“Namra kamar akwai abunda yake damun ki?”


Shiru ta ɗan yi tana nazarin abunda zata cewa Anty Amarya, dan bata jin zata iya faɗa mata abunda Asim.yayi mata, ta san ba zai mata daɗi ba kuma ba zata ƙyale ba, bayan kuma koma minene itace ta jawa kanta.


“Babu abunda yake damuna, na riga na ci abinci gidan Gwaggo ne, har wanka ma nayi ina shirin bachi suka zo”


“Amman duk da haka Namra kina da damuwa be kamata ki ɓoye min ba, dan nasan wannan zuwan bana banza bane, babu yadda za ayi ki tsallake Asim ki zo nan bayan kin san yana gadon asibiti kwance”


“A...an sallame shi ai, yana gida Mamanshi take jinyarsa shine yace na zo saboda na sha kai da maganar gida ne, nima kwana biyu zan yi na koma”


Anty tayi murmushi, dan tasan ba gaskiya Namra ta faɗa mata ba.
Hajiya Barau ce ta shigo da Sallama tana faɗin maraba da baƙi.


“Yau garin mu? Ina ji maƙi baƙi”


Anty Amarya tayi dariya ta tashi ta shige ɗakinta. A ɗayan kujerar da Namra take zaune Hajiya Barau ta zauna tana satar kallonta, sai fira suke sama-sama tana tambayar labarin Katsina. Sai nanata mata rashin jindaɗin zuwa ganin Asim da Abbah be barta taje ba.
Sai da dare ya raba sannan tayi mata sallama ta tashi ta fice, zuciyarta cike da gulma.


Bayan fitarta Hajiya Barau, Aisha

Please Login or Register in order to submit comment