Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ke kitchen ya nufa ya buɗe ya ɗauko power horse ya fito falo yana sha. Kansa ya ɗaga sama yana kallon pop zuwa labulayen da aka saka falon, hantin kawai idan ka kalla sai ya burge ka, balle kuma kujera da plasma da flowers, daga kujera har center carpet da labulayen da da fantin ɗakin milk and red ne, dinning area kuma aka ƙawata gurin da red color. Relaxing yayi sama cushion yana furta sunan Namra, a zuciyarsa, haka kawai ta faɗo masa a rai, duk wacan dukiyar da aka narka masa a wacan gidan da Namra ta kama musu haya ubanta ne ya narka masa ita yayinda wannan kuma shi ne ya narka ma Mardiya. Haƙiƙa Namra ta yi masa hallacin da ba duk mace ce take yi ma namiji irin wannan hallacin ba.


“Dole wata rana zaki dawo gare ni Namra, dole idan kika haifa min ɗa ki dawo kina so na idan na karɓe abu na, zaki dawo ki ga yadda Asim yake amsa sunansa a cikin garin Katsina, daga lokacin zan nunawa Ubanki iko na da kuma karfin kuɗi na”


Ya furta yana jefar da kwankwanin power horse ɗin sannan ya ciro wayarsa daga aljihu ya nemo number Sufiyan ya aika masa kira, be damu da ganin dare yayi ba ganin yake tun da yana biyansa kuɗi dole ne ko a wane lokaci ya yi masa abunda yake so.


“Hello oga Allah yasa lafiya ka kira ni a wannan lokacin”


Ya faɗa cikin muryar bachi.


“Lafiya ƙalau, kana da labarin Namra? ”


“Akwai labari oga amman da ka hakƙura har da safe”


“Ba zan haƙura ba, faɗa min kawai”


“Oga wannan monday da ta wuce ta fara zuwa makaranta, na bita har makarantar na ganta Mahaifinta ya ɗaukar mata sabon direba, amman oga sam babu alamun ciki a tare da ita, dole ne idan har akwai cikin da zai tsawon wannan watannin ya nuna ko da kaɗan nan, sam ban ga alamun tana da ciki ba, kuma kaga da tana da ciki da ba zata koma karanta ba yanzu”


“Ka tabbata?”


“Na tabbata oga”


Ya katse kiran yana lasa lips ɗinsa.


“Idan ko har kika yi kuskuren zubar da cikin nan sai kin yi nadama Namra, ke da ubanki sai na kaskantaku”


Yayi ƙwafa tare da busar da iskar bakinsa. Ɗan kishingiɗawa yayi kaɗan sai bachi yayi gaba da shi daman a kwai gajiya sosai a tare da shi. Be yi bachin awa biyu ba ya soma jin hancins ana mugun yaji numfashinsa na sama-sama sai sarƙewa yake, ba shiri ya farka a firgice sai hayaki ya turniƙe masa ido, duhu ya soma gani sai tari yake kamin ya waiga ɗayan gefensa ya hango bedrooms ɗin suna ci da wuta. Wani irin tsalle ya daka ya sai gashi gaban ƙofar falo yana ƙoƙarin ɓanɓanreta amman ina hayaƙi da tsage ƙofar. Mai gadinsa ne ya farko yaga halin da ake ciki ya fita neman jama'a abunka da unguwar masu kuɗi sai kowa yayi maaa banza sai gaba ɗaya mutane suka fiffito, daker aka samu aka ɓalle ƙofar falon, suka fito da Asim, domin hayaƙi ya turniƙe shi tuni ya faɗi a gurin yana haƙi.


Kan kace kwabo sai ga ƴan fire service mota kusan uku aka shiga kashe wutar, amman kamar ana ƙarawa, haka wutar ta riƙa ci har asuba, bata mutu ba sai da ta ƙone komai na gidan.




Ta ɓangaren Mardiya ma ƴan kashe wutar gobara ne suke ta kai da koma amman wutar da ƙi mutuwa, babu abunda yaba jama'ah tsoro kamar yadda wutar take ta sama kamar abar da ake sawa fetur, ba ɗakinsu wutar da tashi ba, amman bata rage komai da yake ɗakinsu Mardiya ba, har da kayan baƙi ƴan zuwa biki sai da wutar da cinye, sannan ka bi sauran ɗakunan gidan duk ta cinye.


Mardiya na maƙota aka faɗa mata, daman tun da aka fara bikin maƙota take kwana ita da ƙawayenta, ko da ta zo wutar ta ci har ta cinye babu abunda ya rage a cikin gidan, a take ta saka kuka ganin komai ya ƙone babu abunda take ji kamar kayan mutane da suka ƙone, babu daɗi ace kaje biki wani abu ya faru. Bata ƙara firgicewa ba har sai da wani abokin Asim ya zoɓya labarta mata halin da suke cikin ma ƙonewar da wacan gidan yayi wanda za a kaita.


Hannu ta ɗora saman kai ta fashe da kuka tana kiran ta shiga uku.




“Allah yasa ba wutar da nake mafarki bace take bi na ba, na shiga na lalace”


Kuka ta riƙa yi kamar mahaukaci sai da ka riƙeta ana bata haƙuri.








RASHIDA POV.


Bayan ta gama sallah azahar ta tashi tayi nafila sannan ta ɗauki carbi tana lazimi, haka take kullum cikin ibada take fatanta kawai Allah ya yafe mata kamar yadda mijinta da Kalsoom suka yafe mata, a iya yanzu ta yarda da ƙaddarar da Allah ya aiko mata kuma ta aminta babu mai iya yaye mata ita sai Allah, tabbas tasan Allah yana son ta tun da har ya ganar da ita tun gabanin ya karɓi rayuwarta.


Ta miƙa lamurranta ga Allah, kwata-kwata ta cire rayuwar daga yin aure dan tasan ba zata samu mijin da zai aureta ba, da ma kuma ta samu bata tunanin zata iya zama aure da namijin wanin Hilal. Daman ta daɗe da aje aikinta, duk wani abunda da take da buƙata Mahaifinta yana yi ma, abokanta kuma suna kawo mata ziyara a gidan, waɗanda suka wayanci miye hiv wasu kuma tuni sun ƙaurace mata gudun kar suma su ɗauka.


Ta ɗauki darasi a rayuwarta sosai, tun daga cin amanar aure da tayi, da kuma neman taimakon wanin Allah wato bokaye da ƴan duba, a iya kallon rayuwar Kalsoom da tayi ta fahimci darasin da yake tattare da itazm, tabbas wanda duk ya miƙa lamurransa ga Allah, lallai Allah yayi alƙawarin jiɓantar al'amarinsa, babu irin shige-shige da bata yi ba wajen ganin da raba Kalsoom da Hilal ko ta raba ta da lafiyarta amman addu'o'in da take suka mata kariya da katangar tsari daga duk wani sherinta. Hakan yasa itama ta tattara lamurranta ta miƙa wajen Ubangiji, ta samu natsuwa da kwanciyar hankali sosai, duk da tasan ciwon dake jikinta ba zai taɓa rabuwa da ita ba, amman tana Allah ya sanyaya mata zuciyarta har ta samu ƙarfin halin sakewa tana fita cikin mutane.


Bayan ta gama istigifari ta ɗauke carpet ɗin ta naɗe ta maida mazauninta, sannan ta nufi kitchen dan ɗora abunda zata ci. Vegetables soup ta girka da white rice daman likita yana yawan faɗa mata ta riƙa cin su. Falo ta fito ta zauna tana cin abincinta hankali kwance tana kallon tv, wayarta ce ta yi ringing sai ta miƙe tsaye ta ɗauko, murmushi ta yi ganin number Hilal a zatonsa zai sadata da su Ulfah su gaisa ne sai kawai ya miƙawa Izzah ta yi masa albishir ɗin Anty su ta haihu.


“Mashallah me aka samu?”


“An samu Baby boy, Momi Mai kyau sosai”


Wannan karon Ulfah ce take magana.


“Allah ya raya ashe kun samu ƙane ko? Ina dady ku?”


“Yana can gurin Anty be san mun kira ba, Momi Boy ɗin kato ne sosai kuma fari”


Ezzah ta faɗa with so much joy and excitement. Idon Rashida ya cika da ƙwalla dan har gobe har jibi tana son mijinta sai dai tasan yayi mata nisa.


“Zan zo gobe na ga Baby kun ji”


“Toh Momi”


Suka kashe wayar, ita kuma ta share hawayen idonta tana tuna lokacin da ta haifi Rafiq yadda Hilal ya dinga ɗauki kamar zai haɗeta ita da yaron.


‘Allah sarki duniya’


Ta yi furucin a zuciyarta, a fili kuma sai ta amsa salamar da Alhaji Bashir yake yayinda yake turo ƙofar falon ya shigo.
[7/21, 10:29 AM] Khadeeja Candy♥: *86*


“Miya kawo ka gidana?”


Murmushi yayi ya zauna saman kujera yana kallonta fuskarsa da annuri.


“Haba Hajiya ai ko baki san inda na fito ba kya saurara min ko?”


“Na fi ƙaunar ganin baƙin maciji da kai, bana son abunda zai sake kusantar da ni a gareka Alhaji bashir dan Allah dan Annabi ka tashi ka fitar min daga gida”


“Ban zo gidanki da wata manufa ba Rashida sai ta alheri”


“Babu alheri a tare da kai, dan Allah ka tashi ka bar min gidana”


“Miyasa kike alaƙanta rayuwar da kika shiga da laifina? Bayan kuma idan baki amince ba ba zan iya miki da ƙarfi ba?”


“Nasan nayi kuskure ai a lokacin shiyasa yanzu na tuba na koma gurin Ubangijina, kuma Alhamdulillah rayuwata da dai-daita”


“Nama ai tuban na yi shiyasa nake son dai-daita rayuwa da taki, har ga Allah Rashida ina son ki ba wai so na zina kawai ba, so na haƙiƙa kawai saboda babu yadda zan yi ne, ni da ke kukan mu munyi kuskuren faɗawa a halaka, ke saboda baki da lokacin da zaki tsaya ki bawa mijinki kulawa shi ma kuma ya baki, ni kuma na kasa ƙara aure duk da ina ganin sha'awar wasu matan saboda sherin da matata ta yi min, yanzu kuma Alhamdullillah na gane kuskurena kuma am ready to marry you idan kin aminta, saboda kin rufa min asiri a lokacin da ya kamata ki tona min, kin rufe bakin ki kin haƙura kin bar ni akan aikina, bayan kuma kina da damar da zaki tona min asiri, ki faɗawa duniya abunda muka aikata”


“Ban shirya aure yanzu ba Alhaji Bashir idan ma shi ya kawo ka ka tashi ka bar min gidana”


“Kin fi son ki yi ta zama a haka? Indai akan Asmee ne karki damu bata isa ta hanani ƙara aure ba yanzu”


“Baka tsoron ace ka auri mai cutar ƙanjamau?”


“Daga lokacin da kace zaka damu da matsalar mutane zaka saka kan ka ne kawai cikin matsala, ni da ke da Asmee duka muna ɗauke da abu ɗaya, miye amfanin ke na ƙyale ki akan gudun abunda duniya zata ce min? Zan yi ritaya gudun kyamar da za a nuna min gurin aiki, amman karki manta ina da hannu jari kuma ina da kasuwancin da zai iya riƙe jikokina ma ba ƴayana da matana kawai ba, ki yi tunani Rashida karki yaudari kanki akan abunda zuciyarki take muradi”


Yana kaiwa nan ya miƙe tsaye ya fice. Da kallo ta bishi tana sauke ajiyar zuciya, sam bata shirya irin wannan rayuwar ba, aure yanzu? Ita da yanzun tana jin ta samu sukuni a rayuwarta, taya zata yi aure ta sake jefa rayuwarta cikin wani halin kuma? Ita kan bata shirya kishi da Asmee ba.


KALSOOM POV.


Hilal kamar ya haɗe yaron dan murna, duk wanda ya ga Baby boy ɗin sai yayi mamaki ace da kanta ta haihu musamman da suka ji gida ta haihu, wasu daga cikin abokansa suka riƙa zolayarta wai ai matar doc ce dole ya karɓi haihuwarta. Hajiya ta nuna farincikinta sosai duk bayan kwana biyu sai ta zo gidan duba jikanta, Salman kam kullum tana biye da hanya, sai da aka kwana uku sannan Rashida ta zo ganin Baby shi ma kuma da dare, ta yi siyayya mai yawa ta kawo, sai dai bata yarda ta karɓi yaron ba duk da Kalsoom ta yi kawaicin miƙa mata shi, bata yi minti ashirin a gidan ba ta fito su Ulfah suka rakota har bakin mota ta basu kuɗi da chocolate.


Ranar suna Baby ya ci sunan mahaifin Hilal wato Abubakar aka yi masa laƙani da Rafiq. Fuskarsa sak ta Hilal yaro ya sha stickers har ya gaji, an raba abubuwa da yawa ranar sunan, da yamma aka yi walima ta gani ta faɗa, kuloli da manyan kofuna da agogo sai har ma da handbags masu kyau, wasu kuma su samu shoes.


An kashe kuɗi da yawa gurin walimar nan kai kace ma yanzu ne Hilal yake samun haihuwar fari, yadda ya zuba mata kayan barka ma a abun kallo ne, ga kuma waɗanda ta samu daga ɗai-ɗaikun mutane ƴan uwa da kuma abokan arxiki.


ABDOOL POV.


Tafiya yake shaddar dake jikinsa tana amsa amo saboda maiƙon da ke jikin shaddar da kuma sabuntakarta.


Ko da ya shigo part ɗin Ummi yana waya da Mai Martaba dake faɗa masa yana nemansa, a falon ya zauna sai da suka gama tattaunawa sannan ya kalli Ummi da ke cikin shirin ta na fita ya ce


“Ummi fita zaki yi?”


“Eh Asibiti zan je na duba Hajiya Sadiya kasan ciwon nata ya zama abunda ya zama, kuma kaima ya kamata ace ka duba ta, tuɓ da ta kwanta asibitin nan baka taɓa zuwa duba ta ko sau ɗaya, wai anya ma ka mata gaisuwar yarinyar ta da rasu?”


Ya shafa kansa yana murmushin rashin gaskiya.


“Kin san ko da ta rasu ina Abuja, amman dai na kirata a waya”


“Abdallah baka da kirki sam, kai kullum aiki ƴan uwanka ma baka da lokacin ziyartarsu? Sai yaushe zaka huta ne?”


“Ai yanzu zani iya zuwa na mata gaisuwar daga nan na duba jikin nata”


“Allah ya sauwaƙe maka wannan rayuwa, wai ya maganar yarinyar nan ne?”


“Muna nan muna ta sutsa kai, yanzu haka maganar da Mai Martaba yake min kenan, yace min yayi magana da Abbah”


“Ban gane ba, ita bata son ka ne?”


“To gani dai wani ne yake min zagon ƙasa, ita kuma tana min jan aji, yanzu haka anjima kaɗan gurinta zanje, domin hankali yaƙi kwanciya tun lokacin da yaron nan na zo gidansu, last week ma da naje gidan kamar...”


Sai kuma ya fasa maganar ya miƙe tsaye.


“Muje na dubata Ummi, sai na wuce airport flight zan hau”


“Ka fara bani labari baka ƙarasa ba, zan ƙarasa”


“Zan ƙarasa miki idan na dawo”


“Ƙanenka dai ga su nan sai himmar fitar da maza suke kai kana nan”


“Nima ina kan hanya”


Dariya ta yi ta miƙe tsaye suka fita tare. Kai tsaye asibiti suka nufa, ko da suka shoga ɗakin tana kwance wata ƴar'uwarta tana jinyarta, ta rane sosai bakinta duk ya bushe, Abdool ya ji tausayinta sosai da sosai, duba da yadda take damawa kuma gata mai jiki amman yanzu ta dawo haka. Tana ganin Ummi ta fara hawaye.


“Nikan tawa ta ƙare, Nabila ta tafi ta bar ni”


“Kiyi haƙuri Hajiya Sadiya duk mai rai mamaci ne, duk haka ƴaƴanki suke mutuwa kuma ki haƙura, na san Nabila ita kaɗai ta rage miki amman Allah baya barin wani dan wani, dan Allah ki sawa zuciyarki sassauci”


Shiru bata ce komai ba, sai hawaye take ita kaɗai ta san dalilin mutuwar Nably kuma ita kaɗai ta san dalilin wannan ciwon nata.


“Sai Yaushe zasu sallame ki ne?”


Ummi ta sake tambaya. Wacce ke jinyarta ta kada baki tace


“Ba yanzu ba, wai sai sun mata aiki”


“Aiki kuma?”
.
“Eh wai wasu abubuwa ne a cikinta masu kamar ƙanƙara sun ce dole ne sai anyi aiki za a cire”


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. To Allah ya sauwaƙe, amman da waje aka je naga sun fi ƙwarewa a irin aikin nan”


“Nima haka na ce mata, amman ta ƙi”


“Allah ya bata lafiya ai da nan da can duk ɗaya a gurin Allah”


Wannan karon Abdool ne ya faɗa yana kallon agogon hannunshi. Dubu talatin da ƴar siyayya Ummi ta aje mata sannan suka taso muna mata Allah ya sauwaƙe ya bata lafiya.


A mota Ummi take ta labartawa Abdool irin rayuwar da suka yi ta ƙurciya, yadda aka riƙa ta a gidansu da kuma irin nasarorin da tada samu a rayuwarta.


“Kai Mai rai ba komai ba ne”


Abdool ya faɗa yayinda yayi parking a harabar gidansu. Cikin yanayin damuwa da jimami Ummi ta fita daga motarsa, shima ya fito yana faɗa mata yanzu zai kama hanya.


“Allah ya tsare ya kiyaye ya kuma kai ka lafiya”


“Amin Ummi”


Sai da ya shiga part ɗinsa ya fito, sannan ya shiga wata motar direbansa yayi driving ɗinsa zuwa airport.






***


An sake fitar da shi waje kamar yadda Abbah yayi alƙawari, sai dai tun daga lokacin Abbah be sake leƙa asibitin da sunan yazo ganinshi ba, wani kuma daga gidan be sake zuwa ba, duk da ƴan'uwa sunta ƙoƙarin shiga tsakani na ganin an sasantashi da Abbah, amman Abbah be saurara ba dan ya riga ya bashi baya a yanzu, kuma duk wanda ya ji dalilinsa dole yayi masa uzuri, dan kaf a ƴaƴan ƴan'uwa Abbah ya fi son Uzair da kowa. Babu wanda be yi mamakin jin abunda Uzair ya aikata ba na neman maza ƴan'uwansa, a lokacin ne wasu ke cewa ashe Namra tana da gaskiya, wasu kuma su labarta tsegumi da zargin da suka ji ana masa, daman abun duniya baya ɓoyuwa. Har kuma tsawon lokacin Yasmin bata taɓa zuwa ta duba shi ba ko da sau ɗaya. Shi kam duk ya biya rame ya lalace, sauƙi ɗaya ya samu yanzu yana iya tashi zaune,ko ya kwantar da kansa, kuma ya kam miƙa hannunsa ya ɗauki abu ko ya karɓo, sai dai bayan haka babu wani abu da yake iyayi ma kanshi.


Bayan ya gama cin abinci likita ya shigo ya duba shi, ya bashi magani sai kuma yayi masa allura, sannan ya rubuta wasu ya bawa Umma yace a siyo masa su. Sai da ya fita Umma ta rafka uban tagumi tana kallon ɗanta, tabbas be kyautawa kansa ba da ya saka kansa a wannan rayuwar, gashi yanzu kowa ƙyamarsa yake ana masa kallon kamar ba mutum ba, shi kansa a yanzu ya gane ba kowa ba ne, duk abokaninsa sun guje shi cikin ƴan watan ni sun manta da shafin rayuwarsa ga matarsa ta nuna masa tsantsar ƙiyayya, yanzu da Mahaifiyarsa bata raye haka rayuwarsa zata ƙare kenan a wulaƙance?


Turo ƙofar da akayi ne yasa duk suka ɗago suka kalli ƙofar daga shi har Umma, Yasmin ce sanye cikin suit da alamu daga gurin aikinta ta biyo asibitin. Ba Umma kaɗai ba shi kansa da yake mijinta sai da yaji tsoron zuwan nata.


“Miya kawo ki mi kika zo ki yi? Ai na ɗauka kina da zuciyar da ba zaki iya taka ƙafarki ba ma a asibitin sai idan ya mutu a akai miki gawa, wai ke nan har kin isa ki wulaƙanta mijinki akan wannan abun daya aiakata, kowa fa be wuce ƙaddaraba, mutane nawa ne suke zama da mijinsu bayan kuma sun san mijin yana aikata irin wannan abun, amman su rufa masa asiri su zauna da shi”


“Matan da suke rufawa mazansu asiri akan wannan aikin suna yi ne akan kwaɗayin kuɗin mijin, ni ko na dan dukiya na auri Uzair ba, wasu kuma suna yi saboda ƴaƴansu, ni ko ya keta haddin ɗa na, ko be faɗa miki yayi raped ɗa na ba? Idan be faɗa miki ba to yau ki sani, kuma dalilin zuwa na a nan saboda ina son na karɓi takardata ne, idan kuma be shirya sakina ba ni na shirƴa kai shi kotu”


Yasmin na maganar hawaye na zuba a idonta, hannu Umma tasa ta rufe baki tana kallon Uzair, furucin da Yasmin ta yi a yanzu yayi nauyi, sai dai ta fahimci gaskiya Yasmin ta faɗa tun da ya kasa ƙaryatata har ma ya sadda kansa ƙasa yana hawaye.
Yasmin ta kalleshi tana share hawayenta


“Ka daina yaudarar kanka da sunan wani yayi maka asiri, mugun abunda kake aikatawa ne ya kama ka, kuma Allah ya yanke maka wahala komai ya zo maka da sauƙi, da ace kana da lafiyarka wallahi da ko wace jarida sai ta buga hoto na da naka, dan sai na bawa duniya mamaki da kai mijina kuma uban ƴaƴana kotu, kuma ko yanzu ka taki sa'ah ne mahaifiyata ta hana ni, amman idan har shiga kotu kake so ka yi ƙoƙarin yin jayayya da ni akan aurena...!”


Juyawa ta yi ta fice tana kuka. Ajiyar Zuciya Umma ta sauke cikin muryar kuka ta ce


“Abun naka har ya ɓace Uzairu, wannan ba halina ba ne kuma ba halin Baban ka ba ne, ban san inda ka ɗauko wannan rayuwarba, yanzu a ce har ɗan cikin ka zaka aikatawa wannan abu? Ko a masu yi ƙoƙarin kare iyalinsu suke kada su faɗa wannan halaka balle kuma har su saka su da kansu, abun da naki ji a redio yau a gidana zai faru? Na yi tunanin ko zafi ciwo ne yasa ka faɗar haka a baya ashe dai da gaske ne, Uzairu baka kyautawa kan ka ba”


Ta rufe fuska tana kuka. Shi kan hawaye yake sai a yanzu yake ayyana zancen Allah na cewar cikin matan ku maƙiyanku, a cikin ƴaƴanku akwai maƙiyanku, ji yake kamar ma shi aka saukarwa ayar dan tsanar da Yasmin ke nuna masa ta yi yawa.


Wasa-wasa abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa magani yake amman babu sauƙi, haka ya kwashe wata shida a asibitin sannan aka sallamoshi ya dawo gida gurin Umma. Daman tun a asibiti aka siya masa keken guragu yana tura kansa a ciki duk lokacin da wani abun uzuri ya same shi ko kuma yayi sha'awar fita waje.


Ranar da Yasmin ta samu labarin ya dawo gida, ta samu Mahaifiyarta a falo akan maganar shigar da shi kotu tun da har yanzi ya kasa aiko mata da takardarta.


“Wai ke Yasmin wace irin zuciya ce da ke haka? Ke bakya ganin tausayinsa ne? Ki duba halin da yaron nan yake ciki wannan kawai be isa ya saka ki barshi da Allah ba, ai da Allah ya tashi kama shi sai ya kama shi ta wannan hanyar da babu wanda ya isa yai masa magani sai shi, ko ba komai fa Uzair ɗan'uwanki ne Yasmin ya kamata ki riƙa tausayinsa, sannan uban ƴaƴanki ne, ko ƙin ki ko kin so kin riga kin haihu da shi, nan gaba kina tunanin yaransa zasu ji daɗi idan suka samu labarin abunda kika yi ma Ubansu?”


Fashewa ta yi da kuka


“Idan na fita wani lokacin har nuna ni ake, na rikice gaba ɗaya yanzu ko gurin aiki ba komai nake ganewa ba, so nake ya sake ni ko na samu sukuni na natsu”


“Damuwace kika sawa ranki, bayan kuma be kamata ya dame ki, tun da ba ke kika ƙaddarawa kanki wannan rayuwar ba, focus on your journey ki cire komai a rankiz ina nan ina miki addu'a da sannu komai zai wuce”


Tashi tayi ta shige ɗaki tana kuka.




NAMRA POV.


Satin Hajiya Barau biyu ta Abbah ya dawo da ita saboda haƙuri da ake bata da kuma ganin idon ƴaƴanta, ita kanta yanzu ta saduda dan satan bata kyauta ba, duk abunda take tana yi ne dan kishin Anty Amarya tana ganin kamar Abbah yafi sonta da ita.
Ga kuma ƴaƴanta da suka sata gaba suka nuna mata rashin jindaɗinsu, ko ba komai dai ya ga ishara a zmfitowar da ƴarta tayi wato Zinatu, yanzu ba Namra ba ce kawai take zawarci a gidan har da ƴarta da uwar miji ta hanawa zama.


***
Anty Amarya na kallonta ta yi murmushi.


“Wannan shaddar duk tsadarta Lamido zaki bawa?”


Ta gyaɗa kai tana murmushi.


“Lallai ana jin Lamido nan, kar fa ya karɓe min faɗar ɗa”


Dariya ta yi wannan yaron tana shafa shaddar.


“Anty kina jin ɗan nan na ki”


“Ai bana da kamar sa ne Namra, kema kuma idan ba kin yi butulci ba baki da kamarsa, abubuwan da kike masa basa min daɗi, yaron nan yana son ki wallahi, kin san yafi ƙarfin wulaƙanci idan ba ke ba babu wacce ta isa ta wulaƙanta namiji kamar Abdallah”


“Ba wulaƙanci ba ne Anty, ni rayuwarsa ce bana so, ya cika zafin kishi, kuma bana jindaɗin abunda yake ma Lamido”


“Ai naji mahaifinki yana zancen sama masa aiki dan yace ya kusa barin driving ɗin ki”


“Saboda me?”


“Nima be faɗa min ba”


Ta faɗa fuskarta da Murmushi. Namra ta baro gurin da take zaune ta zauna kusa da Anty.


“Dan Allah Anty ki faɗa min”


“To aure zai miki”


“Anty Aure yanzu? Ni gaskiya ban shirya ba, halin mazan zamanin nan duk yaushe na fita daga wannan rayuwar kuma za a ce na sake wani”


“Toh sai ki tashi ki faɗawa Mahaifinki ai yana part ɗinsa”


Ta yi saurin rufe baki tana dariya, sai ta tashi ta ɗauki shaddar ta fice. Murmushi Anty Amarya ta yi tana unƙurin tashi ta nufi part ɗin Abbah.


Yau weekend ce daman babu aiki kuma babu wani taro ko wani abun da zai fitar da Abbah, dan haka yana part ɗinsa yana hutawa. Da sallama ta shiga, ya amsa mata yana kallon labaran bbc. Plate ɗin dake kusa da shi da ɗauke ta aje ƙasa ta zauna bakinta ƙumshe da murmushi.


“Yanzu na ke shirin kiranki”


“To Allah yasa samu ne”


“Samu ne kan, ɗana nake nemawa auren ƴarki idan kun aminci”


“Ai Abdool ɗana ne ba

Please Login or Register in order to submit comment