Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR*
*Call 08066268951*131*4#*












_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._














.........Ta ja gwauron numfashi ta sauke tana ƙoƙarin komawa ta kwanta wayarta ta fara vibrate alamar shigowar kira. Ta ɗauki wayar ta duba wake kiran nata, ganin Uncle Usman ne ta sauke ajiyar zuciya a hankali tare da picking kiran ta kara a kunnenta. Cikin muryar dake nuni da damuwa tay masa sallama, ya amsa mata. Ta ce. "Uncle an wuni lafiya?" Ya ce. "Lafiya k'alau Neehal, dafatan kina lafiya?" Ta sauke numfashi ta ce. "Lafiya k'alau Uncle." Uncle Usman ya ce. "Masha Allah, naga kiran ki, ina wanka ne kika kira ni, Allah yasa dai lafiya dan na ji muryarki wani iri kuma kira a daren nan." Idonta ya ciko da k'walla, ta daure ta ce. "Dole ce tasa na kira ka yanzu Uncle, da na so na bari sai da safe amma ina buƙatar magana da kai urgently." Uncle Usman ya ce. "To! Allah yasa lafiya dai?" Ta ce. "Lafiya k'alau, kawai shawararka nake nema akan wani al'amari, Allah yasa bazan takura ka ko Aunty ba?" Uncle Usman ya ce. "Haba babu komai Daughter, Aunty'n ki ta yi bacci ma ita." Neehal ta gyara zama ta bawa Uncle Usman labarin duk yanda suka yi da su Daddy, ta kuma faɗa masa ita bata son Auren. Uncle Usman ya sauke numfashi ya ce. "Mene abun damuwa anan Neehal? Ai wannan abun farinciki ne mu a gurinmu ba kaɗan ba, Ameen mutumin kirki ne, iyayensa ma haka kuma kin fi kowa sanin hakan." Ta ce. "Na sani Uncle, amma Yaya fa, ni dai baza iya auransa ba Allah." Uncle Usman ya yi murmushi ya ce. "Mene da Yayan?" Ta turo baki tana hawaye ta ce. "Kai ma ka san halinsa, kuma yana da mata fa." Ta ƙarashe maganar hawaye na zuba daga idonta. Uncle Usman ya yi ƴar dariya sannan ya ce. "Ina ruwanki da matarsa, zamanta daban naki daban." Ta yi shiru bata ce komai ba. Cikin serious ya cigaba da magana. "Neehal, zan faɗa miki gaskiya a matsayina na uba a gare ki, ki cire wani abu mara kyau na Ameen daga cikin zuciyarki, alkhairinsa da na iyayensa a gare ki zaki duba, ki tuna ajiye komai nasa da ya yi ya ɓata lokacinsa da energy ɗinsa dan ganin ya samo miki mafita a rayuwarki, abun da ya yi saboda ke aiki ne na siyar da rai amma duk da haka sai da ya yi duk dan saboda ya ga ya cire ki daga cikin damuwar rayuwar da kike ciki. Alkhairin iyayensa a gare ki kuma ba zai fadu ba saboda tarin yawansu, ki tuna barazana da Daddy ya fuskanta saboda ke, amma duk dan ganin bai ɓata miki rayuwa ko ya bari an ɓata miki ba ya zaɓi duk wata barazana da abun da za'ai masa, kuma duk saboda ke." Cikin tsananin mamaki ta ce. "Uncle a ina ka san wannan labarin?" Uncle Usman ya ce. "Aunty A'isha ce ta kira ni ta sanar mun tun lokacin da abun ya faru, har ma na kira Daddy da Mama na jajanta musu." Ta jinjina kai kawai. Uncle Usman ya ce. "Ki ajiye duk waɗan can abubuwan dana lissafa miki, ki duba Ameen ɗin shi karan kansa, mene ne aibunsa daza ki ƙi shi? Ɗan Adam tara yake bai cika goma ba Neehal, ki yi addu'a kawai Allah ya tabbatar muku da Alkhairi ya kau da fitina a tsakaninku, amma ta yaya ma zaki ce baza ki amince ba, ko a fuska karki bari ki nuna damuwar da za su gane bakya so, ɗansu ne fa Neehal na cikinsu, ko da basu furta ba amma baza su taɓa jin daɗi ba idan kika ƙi ɗansu, muma baza mu ji daɗi ba." Nasiha sosai Uncle Usman yay mata. Ba dan ranta ya so ba ta ce masa ta amince, zata cewa su Maman ta amince. Yay murna sosai ya dinga saka mata albarka. Sai ɗaya suka gama wayar, ta tashi ta shiga toilet ta canza pad ta dawo ta kwanta. Babu bacci ko d'igo a idonta, idan ta tuna gobe fa tana cewa Mama ta amince shikenan kamar yadda Daddy ya ce za'a fara shirye-shiryen bikinsu sai ta ji hawaye sun zob'o mata, shikenan zata zama Matar Yayanta Ameen shi kuma Mijinta? Idan ta tuna ba son ta yake ba sai ta ji hankalinta ya ƙara tashi, ko kuma idan ta tuno Hafsat da dama can ba k'aunarta take ba, ina ga ta aure mata miji? Amma duk da haka dole zata amince kamar yadda Uncle Usman ya ce mata, Mama da Daddy basu cancanci butulci daga gare ta ba. Ta sha kuka sosai kafin bacci ya ɗauke ta ba tare data sani ba.








Da safe da ta tashi idanunta jajur duk sun kumbura haka ma fuskarta saboda kukan da ta sha, ta shiga toilet ta yi wanka ta dinga dirzar fuskar saboda ta ware, bayan ta fito ta shirya harda ƴar kwalliyarta ta rambad'a kwalli duk dan kar Mama ta gane ta yi kuka. Ƙarfe takwas da ƴan mintuna ta fito ta sauka ƙasa. Ta tarar da Mama a kitchen tana haɗa breakfast. Ta tsaya a bakin ƙofa ta ce. "Barka da safiya Mama." Mama ta juyo ta ce. "Yawwa, kin tashi lafiya?" Ta ce. "Lafiya k'alau Mama." Mama ta ce. "Masha Allah." Tana bin ta da kallo. Ta kirkiro murmushi ta ce. "Bari in taya ki aikin Mama." Mama bata ce komai ba, ta ƙaraso suka ci-gaba da aikin tare. Dauriya kawai take yi amma ita kaɗai ta san halin da zuciyarta take ciki, gabanta sai faɗuwa yake saboda tunanin kar Mama ta tambaye ta abun da ta yanke akan maganar Auran Ameen. Allah ya taimake ta har suka gama aikin Mama bata ce mata ko ƙala ba. Tare suka yi breakfast da Maman, sai bayan sun gama ta tashi zata tafi Mama ta ce ta koma ta zauna. Ƙirjinta na luguden bugu ta koma ta zauna, dan ta san tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi. Mama ta kalle ta na sakanni sannan cikin sanyin murya ta ce. "Kuka kika yi jiya da daddare ko Neehal?" Ta sunkuyar da kanta ƙasa tare da girgiza mata kai. Mama ta ce. "Hmmm, Neehal bazan taɓa yi miki dole akan abun da ba kya so ba, haka ma Dad ɗinki, ki kwantar da hankalinki ki daina damuwa, indai ba kya son Auren Ameen babu mai yi miki dole." Ta d'ago da kanta a hankali tana danne kukan da yake ƙoƙarin kufce mata ta ce. "Da gaske fa Mama ban yi kuka ko na damu ba." Mama ta ce. "Any way dai, ni dai abun da zan faɗa miki karki saka damuwa a ranki, i know You very well, kuma karki tursasawa zuciyarki karɓar abun da ba kya so, rayuwarki ce bata wani ba karki cuci kanki, ki yi abun da zuciyarki bata so." Ta yi shiru bata ce komai ba. Mama ta ce. "Yanzu zaki gidan Sadiyan ne? Har ta kira ni a waya tana kin taho, kamar aka ce mata a hanya kika kwana, ita da bata jira." Ta yi murmushi ta ce. "Auntynah kenan, she missed me that is why." Mama ta ce. "Ki je ki gaishe da Daddy sai ki tafi, make sure kin dawo gidan nan before Asr, zamu je shopping kin sani." Ta miƙe ta ce "Insha Allah." Kafin sha ɗaya ta je gidan Aunty Sadiya. Aunty Sadiya ta tarb'e ta cikin farinciki tare da tsokanar ta da wata sabon gani. Bayan sun gama gaggaisawa suna cikin hira Aunty Sadiya ta ce mata. "What going on Neehal naga kamar kina cikin damuwa?" Ta girgiza kai a hankali tana jin damuwar zuciyarta na ƙaruwa ta ce. "Babu komai Aunty." Aunty Sadiya ta ce. "Baki iya ƙarya ba Neehal, shi yasa kina yi ake gano ki, faɗa mun mene ne? Yanayin ki ya nuna cikin damuwa" Ta yi shiru k'walla na cika idanunta. Aunty Sadiya ta yi ɗan murmushi saboda ta san dawar garin, Mama ta kira su ta faɗa musu komai ita da Aunty A'isha tun jiyan. Cikin lallami ta ce. "Kin yi shiru Neehal." Ba tare data d'ago ba ta ce. "Aunty ban san me zan ce miki ba ne." Aunty Sadiya ta ce. "Abun da yake damunki zaki faɗa mun." Ta turo baki ta ce. "Daddy ne ya ce wai Yaya zan aura." Murmushi Aunty Sadiya ta yi ta ce. "Kamar ya? Wanne Yayan?" Ta ce. "Yayana fa, Aunty ki duba abun nan, ta yaya zan iya Auran Yaya?" Ta yi maganar cikin marairaicewa. "Ta yadda kowacce mace take Auran mijinta mana." Cewar Aunty Sadiya tana dariya. Ta fara hawaye ta ce. "Aunty kin san halin Yaya fa, Ni tsoron shi nake, kuma kuma.... Yana da matarshi fa." Aunty Sadiya ta ce. "Rigimammiya, wannan rigimar taki ai sai Ameen ɗin." Bata ce komai ba sai cinno baki data ƙara yi. Aunty Sadiya ta gyara zama tare da dafa ƙafaɗarta, seriously ta ce. "Neehal! Bai kamata Auran Ameen ya dame ki ba ko kuma ya saka ki cikin damuwa ba, kin san Ameen kin san komai nasa fiye da kowacce mace da zai aura a duniya, haka kema ya san komai naki. You know Ameen is a good person, ke zaki faɗi hakan ga wasu ma. To mene abun damuwa dan kin aure shi, mu kanmu sai mun fi jin daɗi da farincikin hakan, hankalinmu sai yafi kwanciya, bamu da fargabar yanda mijinki zai riƙe mana ke ko kuma fargabar wanne irin ƴan'uwan miji zaki haɗu da su. Batun matarsa kuma ba'a kanta zaki zauna ba ita ma ba'a kanki zata zauna ba, hasalima kowaccen ku gidanta daban." Ta ɓata fuska ta ce. "Ai ita yake so, ni ba ya so na." Aunty Sadiya ta danne dariyar dake ƙoƙarin k'wace mata dan ta gano mutuniyar tata har da kishi a lamarin nata ta ce. "Wa ya faɗa miki? Yana son ki mana, in ma ba ya son ki sai ki koya masa son naki, sai ka ce ba rainon Yaya Fateemah ba?" Ta juya ido ta ce. "Ai nima bana son shi." Wannan karon Aunty Sadiya kasa danne dariyarta ta yi saboda yanda Neehal ɗin ta yi maganar. Ta ɗan dara sannan ta ce. "Allah ya shirya ki Neehal." Nasiha ita ma Aunty Sadiya ta yi mata tare da ƙara nuna mata qualities ɗin Ameen, kamar dai yanda Uncle Usman ya faɗa mata jiya, a ƙarshe dai ita ma ta ce ta dage da addu'a kawai tare da neman zaɓin Allah. Wajen ƙarfe uku ta koma gida, ana yin la'asar suka fita shopping ita da Mama, sai daf da Magriba suka dawo. Bayan Magriba ɗaya daga cikin staff ɗin gidan ya zo ya cewa Mama ta yi baƙo. Ta ce masa ya je ya shigo da shi part ɗinta. Baƙon yana zaune a falon ƙasa ta sauko, mamaki gami da fara'a suka bayyana akan fuskarta ganin Alhaji ne Uban gidan Abban Neehal. Cikin murya mai cike da fara'a ta ce. "Alhaji kai ne a gidan namu yau? Sannu da zuwa." Alhaji Ali ya yi murmushi yana riƙe da sandar dake taimaka masa gurin tafiya ya ce. "Ni ne Hajiya, da fatan mun same ku lafiya?" Mama ta zauna akan carpet ta ce. "Lafiya k'alau Alhaji, da fatan an zo lafiya? Ya hanya? Ya Iyali? Ya ƙafa?" Alhaji Ali ya ce. "Alhamdulillah, komai lafiya k'alau, ƙafa gata nan sai godiyar Ubangiji, a satin nan ma muka dawo daga Saudiyya na je ganin likita." Mama ta ce. "Masha Allah, Allah ya ƙara sauƙi, ƙafar tana yin sauki dai ko?" Ya ce. "Alhamdulillah, ana samun cigaba." Mama ta ce. "Haka ake so, wancan satin nake yiwa Neehal maganar ya kamata ta je ta gaishe ka, sai A'isha ta ce mun itama kwanaki ita ma ta yi zancen hakan a zuciyarta, ta tambaya kuma aka ce baka gari. Ashe kun dawo, Alhaji ka zo da kanka maimakon ka yi waya mu mu zo kai da ba lafiyar ƙafa ba." Ya yi murmushi ya ce. "Ai wannan shine lafiyar, zumunci shine lafiyar ƙafa, babu komai." Mama ta ce. "Haka ne, Allah ya saka da Alkhairi, na ji daɗi kuwa sosai, bari na kira Neehal ɗin ku gaisa." Ya ce. "Toh, Maigidan baya nan ne?" Mama tana miƙewa ta ce. "Yana nan masallacin jikin gida, bari na kira shi a waya na sanar masa zuwanka." Alhaji ya ce. "To babu laifi." Sai da Mama ta fara lek'awa ɗakin su Dije ta je su kawowa baƙo abinci sannan ta hau sama ta kira Neehal. Neehal ta sakko da murnarta dan tana k'aunar mutumin a rayuwarta, ta gaishe shi cikin ladabi, ya amsa sannan ya shiga tsokanarta da ina surukinsa? Yaushe zata kai masa shi su gaisa? Ita dai murmushi kawai take kanta a ƙasa. Sai isha'i Alhaji Ali ya tafi, da yake Daddy ya dawo suna ta hira.








Wajen tara da rabi na dare Neehal tana shirin kwanciya saboda ƴar gajiyar fitar da ta yi dake jikinta, kuma tana son ta tashi da wuri gobe fitar safe zata yi zuwa aiki. Mama ta shigo ɗakin, ta kunna light ta ce. "Ko har kin yi bacci ne?" Neehal ta ce. "A'a, ina dai shirin kwanciya." Mama ta zauna a bakin gado ta ce. "Kin ci abinci kuwa?" Ta ce. "Na ci." Mama ta yi shiru kawai tana kallon ta, ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa gabanta na fad'uwa." Mama ta sauke numfashi ta ce. "Shikenan ki yi baccinki, dama zuwa na yi in duba ki." Ta ce. "Toh Manana sai da safe." Mama ta ce. "Allah ya kai mu." Tare da miƙewa ta fice. Neehal ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi tare da lumshe idonta, ta yi tunanin Mama zancen Ameen ta zo yi mata. Ta tashi ta sakawa ƙofar ɗakin key tare da kashe light sannan ta koma ta kwanta. Washegari kafin 8 ta fita, bata dawo gidan ba sai da 2 ta wuce. Bayan ta yi wanka ta fito daga ɗakinta zata sauka ƙasa ta ɗibi abinci ta ci kamar yadda Mama ta umarce ta, tana buɗe ƙofar falon sama da nufin fita suka yi karo da mutum zai shigo. Ta d'ago kanta da sauri bugun zuciyarta na sauyawa saboda k'amshinsa da ya sanar mata da ko waye tun kafin ta kalli fuskarsa......✍️














*By*
*Zeey Kumurya*
*⚡ NEEHAL⚡*










_By_
_Zeey Kumurya_














*7️⃣6️⃣*












Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*


*I selling MTN data with this cheap price*


*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500


Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*


*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR*
*Call 08066268951*131*4#*












_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._














..........Idanunta suka sauka akan kyakkyawar kamilalliyar fuskarsa mai cike da kwarjini, ta yi ƙoƙarin ɗauke kallon ta daga fuskarsa amma ta kasa. Wani irin kallo yake mata wanda yasa ta ji wani irin abu yana yawo a cikin jinin jikinta, kamar yadda zuciyarta take bugawa da ƙarfi. Kallon sa take yi yau as husband to be not as brother before, tunanin hakan yasa ta ji gabanta ya yi wani irin mugun faɗuwa, ya sakar mata wani murmushi wanda zata iya cewa ba'a taɓa murmushin da ya kayatar da ita kamar shi ba. Ta lumshe idonta da sauri wani baƙon abu yana cika zuciyarta a kansa, like kunya ko tsoro. Ta yi baya da sauri tare da buɗe ido tana ɗan turo baki gaba, zuciyarta ta bata shawarar ta zura da gudu ta koma ɗakinta, har sai ya bar gidan sai ta fito. Ta juya cikin sauri amma ko ɗaga ƙafarta bata yi ba ya kamo hannunta, ta juyo kamar zata yi kuka dan abun da take ji a game shi ƙara yawa yake yana neman hautsina mata zuciya, kuma bata taɓa jin hakan a gare shi ba a rayuwarta sai yau. Ta saci kallon fuskarsa ta ga ya haɗe rai kamar ba shi ya yi murmushi yanzu ba, ya tsatstsare ta da kyawawan idanuwansa wanda suke ƙara mata yawan abun da take ji a kansa a cikin zuciyarta. Murya ƙasa_ƙasa ya ce. "Can't you great me?" Ta shiga girgiza kai tsoronsa na ƙaruwa a ranta, cikin rawar murya ta ce. "Ina yini?" Bai ce komai sai kallon fuskarta da yake yi kamar mai neman wani important thing a fuskar. Ta yi ƙasa da kanta a ranta tana addu'ar Allah yasa Mama ta fito ko ta samu ya bar ta. Tana ji ya saki ajiyar zuciya a hankali sannan ya sakar mata hannu without saying anything ya nufi ɗakin Mama. Ta bi bayan shi da kallo tare da murgud'a baki, ganin kamar zai jiyo ta buɗe ƙofa ta fice da gudu. Ya juyo jin ƙarar buga ƙofa, ya girgiza kai kawai tare da yin murmushi sannan ya shige ɗakin Mama.










Mama tana shirya gogaggun kayanta a wardrobe ya shigo ɗakin da sallama. Ta amsa masa ba tare da juyo ta kalle shi ba. Ya zauna akan bedside drower tare da gaishe ta. Ta amsa masa tana rufe wardrobe ɗin sannan ta ƙaraso ta zauna a bakin gado. Tana duban sa cike da kulawa ta ce. "Ya su Hafsah?" Ya ce. "Lafiya k'alau." Mama ta ce. "Dafatan dai lafiya, tun ranar Friday rabon ka da gidan nan." Ya ce. "Lafiya k'alau Mum, weekend ɗin nan ban fita ba a gida nake wuni." Mama ta ce. "Okay." Sun taɓa hira kaɗan wadda majority akan aiki ne sannan ya yi mata sallama ya tafi. Bata yi masa zancen Neehal ba shi ma bai yi mata ba. Neehal kuwa tunda ta sauka ƙasa tana sauke numfashi ta shige ɗakin su Dije, ko abincin ma bata je ta ɗebo ba saboda tana tsoron kar Ameen ya sakko su ƙara haɗuwa, sai da ta ga fitarsa ta window'n ɗakin su Dije sannan ta fito. Da daddare Mama ta yi mata zancen Ameen akan jin ra'ayinta, dan Kawu Musa yau wayarsa biyu akan jin inda maganar ta kwana. Shiru ta yi ƙirjinta na luguden bugu. Mama dake kallon ta cikin nazari ta ce. "Neehal, ki kalle ni as your Mother ba mahaifiyar Ameen, ki faɗa mun abun da yake ranki kamar yadda kike faɗa mun a kodayaushe kin ji ƴar albarkata." Ta gyaɗa kai a hankali sannan ta ce. "Na amince." Mama ta ce. "Kin amince da me?" Ta kwantar da kanta a ƙafaɗar Mama ta ce. "Kin sani fa." Mama tana murmushi ta shiga shafa bayanta ta ce. "Da gaske Daughter maganar da kike faɗa mun tun daga zuciyarki take, bana son ki yi abun da ba kya so, in ba kya so you are free to say, no body will force you." Ta ƙara shigewa jikin Mama ta rufe fuskarta da hannunta ta ce. "Allah da gaske nake Mama." Mama ta faɗaɗa fara'a akan kyakkyawar fuskarta cikin tsokana ta ce. "Kina son Ameen ɗin kenan?" Da sauri ta cusa fuskarta ta ɓoye a jikin Mama tare da turo baki gaba. Mama ta shafa kanta cikin tsananin farincikin data manta rabon da ta yi kamarsa ta ce. "Masha Allah Neehal, Allah ya yi miki albarka ya inganta rayuwarki, ya baki ƴaƴa masu ladabi da biyayya kamar ki, Allah ya baku zaman lafiya yasa haka shi ya fi Alkhairi." Ta amsa da Amin a cikin zuciyarta. Ba ta kallon fuskar Mama amma a muryarta kaɗai tana jin irin farincikin da take ciki, kuma duk saboda ta amince da Auran Ameen ne, ina ga Daddy? Shi wanne irin farinciki zai ji idan ya ji wannan batun? Su saunawa suka saka ta a cikin farinciki a rayuwarsu? Babu adadi. Kenan data ƙi amincewa haka zasu ji babu daɗi a cikin ransu? Gwara da Allah yasa bata yi wannan gatobarar ba. Ta san bata son Auren Ameen ko kaɗan a cikin ranta, amma ta yiwa kanta alƙawari zata danne ta daure ko a fuska baza ta bari a gane ba, zata saka a ranta Allah ya yi Ameen ne mijinta, zata karb'i Auransa hannu bibbiyu idan Ubangiji ya yi hakan ta kasance. Amma tana mamaki da girmama abun a cikin zuciyarta ba kaɗan ba, YAYANTA MIJINTA, ko a mafarki bata taɓa tunanin hakan zata iya faru ba, ita mantawa ma take akwai aure a tsakaninsu da Ameen. As blood brother desame mother desame father take kallon shi. Wasu hawaye da bata san kona mene ba ta ji suna rige_rigen gudu akan kuncinta daga cikin idonta. Ta ƙara rungume Mama tare da fara kuka a hankali. Mama ta shiga bubbuga bayanta tare da faɗin. "Kunan na mene ne?" Ta ja majina bata ce komai ba. Mama ta d'ago da kanta tana kallon yanda take kukan ta ce. "Mene ne wai?" Ta girgiza mata kai kawai. Mama ta ce. "Iskanci ne kenan?" Cikin kukan ta ce. "Bana son na bar ki ne Mama." Mama ta yi murmushi tana jin tausayinta na cika mata zuciya, ta shiga share mata hawayen fuskarta tana faɗin. "Wa ya ce miki zaki bar ni dan kin yi Aure? Duk sanda kike son gani na zaki zo ki ganni ai." Cikin shagwab'a ta ce. "Ke baza ki zo ki dinga gani na ba?" Mama ta yi murmushi ta ce. "Zan zo mana, Amarya tun kafin a yi Aure har an fara zancen zuwa gida." Ta cusa kanta a jikin Mama cikin tsananin jin kunya. Mama ta ƙara rungume ta a jikinta tana jin tsananin farinciki a ranta, tabbas kamar yadda Daddy ya faɗa bata jin akwai wanda zai kai ta farinciki idan wannan al'amarin ya kasance. Bayan Daddy ya dawo Mama ta sanar masa yanda suka yi da Neehal. Farincikin da ya nuna ba zai misaltu ba, ya kira Neehal ta zo part ɗinsa wadda gaba-d'aya yanzu ta ji tana jin kunyarsa, ya dinga saka mata albarka tare da tarin addu'oi, har da tambayarta me take so ya yi mata a rayuwar nan wanda zata ji daɗi? Ta ce masa babu komai ai ita ya gama yi mata komai a rayuwa. Ta kasa tantance tsakanin shi da Mama wa ya fi wani farinciki da amincewarta. Da daddaren Ameen ya kuma dawowa gidan, Neehal tana falon ƙasa tana kallon wani series firlm ɗin India da take matuƙar so, bata ji sallamarsa ba sai k'amshinsa ne ya sanar mata da zuwan sa. Ai kuwa da sauri ta miƙe ta nufi upstairs, ya bi

Please Login or Register in order to submit comment