Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

martani ,

Suka cigaba da kissing joystick dinshi ta mike sosai sannan roshni ta zare jikinta ,

Ya kuma jawota taki ,

Ya zuge zip dinsa ya fiddo joystick din yana nishi yace"suck me plsss"

Ta harareshi tace"yau gabadaya wunin Amarya ne ka koma gunta ta sama maka natsuwa"

Yayi murmushi yana ganin tana wasa yace"plsss mana baby"

Tace"ai se kayi in kanaso seka biya sadaki sannan jiya ma mantawa nayi ne"tana gama fada ta bude motar ta fita tana shuumin murmushi don tagama shirya haka zatai ta masa zaifi saurin turowa ayi auren su,

Jamil yaja siririn tsoki ya zuge zip dinsa ya tada mota ya nufi gida,

Roshni kuwa tana komawa gida taiwa wani saurayinta waya yazo su fita domin itama tsuminta ya tashi,

Jamil na zuwa gida ya nufi kitchen wurin hjy abida ya rungumeta ta baya yana shafarta yana yi mata kisses,

Ta juyo tana kallon yanayinshi ya riketa jikinshi ya matso da baki zai dora anata,

Jikinshi nata kamshin turaren roshni ita tasan tataba jinshi wani wuri kuma daga jin shi na mata ne idonta ya sauka ga gefen kuncinshi sawun lips din roshni,

Zuciyarta ta harba hawaye suka cikamata ido tai saurin kauda nata bakin tana hawaye tace"jamil meyasa kakemin hakane ?meyasa zaka rika bin mata bayan gani dama can baka dena biyarsu ba kace kadena baka tsoron ka kwasomana cuta?haba jamil meyasa kakeso ka samin ciwon zuciya I'm not well wlh amma kanason karasa tarwatsamin zuciya"

Jamil ya saketa yana Sosa kai yana duba jikinshi,

Ta juya ta kashe gas ta fita a kitchen din tana kuka me taba zuciya,

Jamil ya kara kallon jikinshi yace"menene?"

Yabi bayan abida daki tana kwance kan bed ta kife tana kuka,

Ya isa wurin mirror yana kallon fuskarshi domin ya karyatata Sega kisses da janbaki har saman goshi,

Yace"kashhh"a hankali ta yadda bamai ji ,sannan ya juya wurin abida ya hau kan bed din yana bata fuska yace"dan Allah kiyi hakuri sugar wlh bazan sake ba kuma ba abinda kike tunani bane "

Ta dago fuskarta shabe_shabe da hawaye tana kallonshi ,

Yayi alamar tausayi yace"kiyi hakuri"

Ta mike dasauri ta bude wardrobe ta jawo ATM card dinta ta hau gadon ta kamo hannunshi ta damka mai tana zubda hawaye tace"idan kudine matsalarka ga katina ko nawa kakeso ka dauka amma don Allah kadena bin mata kazo gida kowane lokaci idan kana bukatar hakan"

Ya cire hannunshi batare da ya rike ATM din ba yace"abida ba don kudinki kawai nakesonki ba kirike katin ki idan ina da bukatar kudi zan tambayeki nafada miki ba abinda kike tunani bane kuma zandena ki kwantar da hankalinki"

Ya rungumota jikinshi yana tapping bayanta,

Takasa yin shiru tana jin matsanancin kishi,

Cikin kunnenta yace"I'm sorry sugar kidena zubar da hawayenki plss nadena"

Ganin fa ba shirun zatai ba yasa ya zuge mata zip yafara shafar soft jikinta yana sakin sexy numfashi a hankali tai shiru tana ajiyar zuciya ya cigaba da rikitata,

Faseelat na asibity saboda hawan jininta baa sallameta ba ta kara muguwar rama sosai wani lokaci tai ta hawaye inta tuno alhajinta da yaronta,

Su daddy kuwa na cigaba da shirye_shiryen bikinsu yayiwa mommy da hjy Rukayya set din akwatuna iri daya mommy ta sake kara gwangwajewa tana ta kara gyara jikinta tana ganin kamar tsufane yasa daddy zaiyi aure,

Ranar Friday aka daura auren a masjid mutane sun halacci daurin auren sosai,

Da dare daddy ya shigo gidan mommy na tare da yara suna kallo kananun sukaje suka tarboshi suna murna suna "oyoyo daddy sannu da zuwa"

Mommy ta mike tsaye tanata sakin murmushi tace"sannu da zuwa"

Ya kalleta yace "yawwa" yana jin matukar farinciki,

Hannunshi daya rike dana yaran yazo ya zauna suka cigaba da kallo ,

Karfe tara dede hjy Rukayya tacewa yaran su shiga su kwanta suka nufi dakinsu kamar yadda tace,

Tana murmushi ta mike tsaye tace"bismillah"ta dauki ledar da yazo daita suka nufi ciki,

Har bedroom dinta ta ajiye ledar ta nuna mai bed ya zauna yanata murmushi yace"amarya nifa ba bako bane"

Tai murmushi tace"hakane nan ai gida ne"

Yace"yawwa "yana murmushi yace" kinga na manta ki kaiwa yarannan nasu naman kidawo muci namu don yunwa nakeji sosai"

Tai murmushi tace "to" ta bude ledar ta fiddo daya ta fita waje
Can zuwa ta dawo suka zauna cin abincin daddy nata binta da sexy smiling ya rika bata a baki suka gama sukai salla sannan suka hau gado bacci hjy Rukayya ta koma can karshen gado jinta take wani iri tana jin nauyi yau gata kwance ba da alhaji ba zuciyarta takasa natsuwa time da daddy ya gangaro wurinta yafara rikita mata brain daya kusanceta yasa mommy tagane maza suna suka tara daddy yafi alhaji shekaru amma ya fishi iya sex da dadewa fiye dashi tun kafin ya tsufa daddy kuwa ya cigaba da aikin lada,

Suna tare suna farinciki mommy ko ita kadai takasa bacci da tana upstair ta sauko kasa ta kuma komawa sama zuciyarta nata harbawa ta koma kan bed tanata hango daddy da wata dakyar bacci ya dauketa can cikin dare,

Washe gari aka sallami faseelat daga asibity suka fito Ummi na rike daita ya omer na bayansu suka fito daga asibitin fahad yazo zai wuce kenan ya hangosu bai gane faseelat sosai ba su Ummi da ya omer daya gani yakara tabbatar mai faseelat ce,

Ya tsaya yana kallonsu ta cikin glass idonshi cike da hawayen tausayinta ,ya omer ya bude masu mota suka shiga ya shiga suka nufi gida,

Fahad ya koma gida kanshi na mugun ciwo ya dafe kai ya rasa yadda zaiyi ,

Aysha ta shigo ta zauna gefenshi zuciyarta sosai take ciwo duk time data ganshi haka ,

Da sanyin murya tace"Yaya ciwon kan ne?"

Ya mata shiru ,tace"Bari na kawo magani?"

Batare da ya dago ba yace"aysha plss leave me alone"

Idonta jawur tace"to"ta tashi ta fita ta koma dakinta ta kwanta tana hawaye,

Fahad nata tunani ya kasa hakuri ya tashi ya fita ya nufi gidansu faseelat yayi parking bakin kofar gidan,

Can zuwa wani matashi ya fito daga wani gida kusa dasu yayi saurin tsaidashi yace"dan Allah ko matar gidannan faseelat ta haihu?"

Matashin ya kalli gidan yace"eh but naji suna cewa ko yaron ya rasu"

Zuciyar fahad tai mummunan faduwa yana jin matsanancin tausayin faseelat bai san time da matashin yawuce ba yana tsaye yayi shiru,

Can zuwa ya koma mota ya nufi gidan ya omer ,

Yayi saa ya sameshi suka gaisa ya mishi gaisuwa sannan ya nufi gida duk yadda yaso karya kira faseelat yakasa ya dauki waya ya kira no dinta,

Ta dauka muryarta very cool tace"assalamu alaikum"

Yace"waalaikumussalam queen ya hakuri?"

Tace"alhamdulillah"idanunta na kawo ruwa tana jin kamar tai kuka,

Yace"Allah yasa me ceto ne"

Tace"ameen nagode sosai "takashe kiran,

Ta rufe fuska da hannu tafara kuka,

Shi kuwa yadda yaji muryar yakara tada mishi hankali ko kadan baida natsuwa,

Tun daga time din time to time yake kiranta su gaisa iyakarsu gaisuwa kawai,

Faseelat tunanin dear dinta take tayi tana samun tsarki ta fara azumi saboda tasan Allah na amsar adduar me azumi tana ta yiwa mijinta adduar samun rahmar Allah ,

Bayan sati ta yi shawarar fara yiwa alhaji sadaka akwai almajirai da yawa da abincin cinsu ya ga garesu wasu kuma neman kudin abincin kawai suke tana iya basu dari biyu ko biyar amma bazata iya siya musu abinci medadi ba ,akwai almajirai da suke taruwa bakin masallaci duk ranar jumaa don samun kudi zata rika kai musu abinci da abin sha tana rabamasu da yan kudade domin neman rahma wa mijinta ,take away bazai ishi mutum yaci ya koshi ba tayi shawarar rika siyo robobi masu murfi don zuba abincin a ciki zata rikayi musu sobo ko kunun aya ko lemuka ko dinja tana raba musu duk ranar Friday ,

Ranar alhamis ta fita da niyyar siyo kifi seta gitta shagon Aliyu bata taba kula da shagon ba se yau ta wuce ta nufi kasuwa da niyyar zata dawo ta sayi kifin da zatai using dashi duk da shagonshi karamine amma tasan kila bazaa rasa adadin datakeso ba inta rika siye gunshi shima ta temaka mishi yafi taje ta siya a babban wuri ,

Tana dawowa daga kasuwa tayi parking kofar shagon ta nufi ciki tana sanye da black hijab me hannu tai sallama,

Aliyu ya amsa yana kallonta,

tace"sannu dan Allah kifi nakeso kwali 3"

Yace "to hjy"

Tace"nawa ne kudin?"

Yafada mata ta fiddo tabashi ,

Ya amsa yace"nagode sosai"ya dauki kwali biyu yaronshi ya dau daya suka kai mata mota ,

Ta shiga ta nufi gidansu da baida nisa daganan ,

Yaran yakoma ciki aliyu ko yayi tsaye yabi motar da kallo ga mamakinshi seya ga ta tsaya bakin wani gida kusa dasu ta fito ta bude gate ta shiga da motar ciki,

Yayi tsaye shi kanshi baisan meyasa yake kallonta ba harwani lokaci sannan ya koma ciki,

Faseelat da Ummi Su suka sha aikin soya kifin da dafa abinci da hada sobon bayan antaso masallaci wurin karfe ukku ta kwashi abincin a mota tasaka hijab da nikab ta fita dashi har bakin masallacin ta rabawa almajirai sauran ta nufi wani masjid ta basu tare da 200 dinsu cikin ledar sobo sunata adduoi ta koma gida tana farinciki,

Rasuwar alhaji takara nutsar daita ita kanta tasan ta sauya kuma tayi hankali ba kamar can baya ba ganin duniyar take kalilan na dan lokaci kuma haka ya kamata kowane musulmi ya kasance,

Ran Monday fahad yazo kofar gidansu sannan ya kira ta ta dauka tai shiru,

Cikin sanyin murya yace"zaki iya fitowa?"

Tace"kana kofar gida? "

Yace"eh"

Tace"OK ganinan"takashe kiran tai shiru tana jindadin yadda yake nuna kulawarsa akanta amma ya zata koma gidanshi ?wace kalar rayuwa zasuyi bata gama tunanin ba ta jawo hijab ta fita,

Ta bude motar ta shiga kanta sunkuye,

Yana ta kallonta yace"ya kk?"

Tace"lpy lau ya su twins?"

Yace"suna gaisheki"

Tai murmushi ta dan kalleshi ya sakarmata murmushi ta kauda fuska idanunta cike da hawaye tana tuno can baya time da yake zuwa gunta kamar haka,

Ya danyi shiru sannan yace"faseelat haryanzu kina sona? I mean zaki kara aurena?"

Tai shiru tana tunanin rayuwar gidansu ta kalleshi tace"amma kasan problem da mukaita samu baya"

Yace"that was a past komi ya sauya kema kin sauya faseelat, insha Allah zamu zauna lpy kuma bazan hadaku gida daya ba, plss ki amince wlh inasonki na rabu dake amma nakasa mantaki acikin rayuwata"

Tai karamin murmushi tace"nima inasonka daddyn twins "

Ya saki dogon murmushi ya dafe heart yana jin sanyi yace"tnx u my Queen "

Tai karamin murmushi ,

Ya cigaba da janta fira tana meda mishi kadan _kadan sannan sukai bankwana ya tafi itako takoma gida,

Tun daga time din suka bude sabon shafin soyayya har charting sunayi faseelat ko pics din su twins ma ta dora a kowane profile na social site nata soyayyar su tadawo sabuwa dall ,

Bangare guda Aliyu yakasa natsuwa duk time daya ganta yakejin feeling da yawa a kanta, saboda yanzu harsun saba hargida suke kai mata kifin in ta kira tanaso saboda sunyi exchanging numbers,amma kuma yasan ta fishi tana hawa babbar mota tana hjy a babban gida me zatayi dashi me shagon kifi da mashin roba_roba da karamin gida?,

Mommy da hjy Rukayya sunata zumunci don hjy Rukayya duk jumaa seta tura yaranta gaisheta itama tana lekawa Sam basu samun matsala Suna manta cewa kishiyoyine su,

Bayan wata daya jamil ya tura gidansu roshni neman aurenta akabashi dama suna kagare su rabu daita akasa biki 1 month kacal,

Yana shakka ya dawo gida suka zauna dining cin abinci ,

Ya nata dan tsakura hjy abida ta kalleshi tace"kaci abincin mana"

Ya ajiye cokali cikin sanyin murya yace"sugar akwai maganar dana keso muyi"

Tace"inajinka minene?"

Yace"amm_amm dama inason in kara aure"

Gabanta yayi mummunar faduwa har cokalin hannunta ya subuce tace"aure jamil?"

Yace"kiyi hakuri plss ki fahimceni inason kara aure da inje ina bin mata waje kara nai auren"

Hawaye masu zafi suka fara wanke mata fuska tace"da me na rageka jamil? Ko bana biya maka bukata?"

Yace"ko daya kinamin komi sugar inason kara aurenne saboda in kara samun natsuwa ki fahimceni"

Ta share hawaye tace "shikenan jamil Allah ya bamu zaman lpy" ta tashi ta wuce ciki,

Yayi zaune Yanajin tausayinta yasa zatai ta masifa amma ba tayi ba ya tashi yabi bayanta domin rarrashinta,

Bayan kwana biyu fahad yazo kofar gidansu faseelat ya kira ta a waya,

Ta dauka yace"ina kofar gida "

Tace"shine kazo baka fadamin ba azumi nake"

Yayi murmushi yace "to asha ruwa lpy"

Tace"kagaidamin aysha"takashe wayar,

Yayi murmushi yana mamakin dalilinta duk in tana azumi bata fitowa idan yazo ko tace karyazo tana azumi,

Bayan ansha ruwa ya kira ta yana cikin bedroom,

Ta dauka tana murmushi,

Yace"sawwama ansha ruwa lpy?"

Tace"lpy lau"

Yace"inafatan baa manta dani cikin adduar ba?"

Tai dariya tace"ban manta da kai ba"

Yana murmushi yace"ina da tambaya minene dalilin rashin fitowa idan nazo kina azumi ?nakasa ganewa"

Tai dariya tai shiru ,

Yace"answer me mana meyasa?"

Tana dariya tace"yunwa ko"

Yayi murmushi yace "dafatan kinsha ruwa yanzu?"

Tace"ehm"

Yace"to ganinan in kawo kayan buda baki in samu ladan me azumi"

Yana cikin fadar hakan aysha ta shigo kuma taji meyace,

Faseelat tace"sekazo"

Yakashe kiran yana murmushi ya duka ya dauki keys,

Gaban aysha na faduwa walwalarshi ta yawaita these days tanata mai kallo da alamar tambaya tace"Yaya ina zakaje ?"

Yayi murmushi yace "wurin faseelat"

Kamar an dokawa aysha guduma a heart kamar zatai kuka tace"Yaya kaifa kace bazaka dawo daita ba meyasa kake zuwa wurinta?"

Murmushin fuskarshi ya bace ya kamo hannunta har kan seat ya dorata jikinshi cikin sanyin murya yace "aysha faseelat ta sauya ba faseelat da kika sani bace ada tana bukatar kulawa tana da bukatata"

Yana maganar zuciyar aysha na lugude tace"aurenta zakayi? "

Yace"eh ina tabbatarmiki zaman zai sauya ba irin na da ba"

Juwa ta kwashe aysha tai kwance jikinshi a sume ,

Ya dafe kanshi yana jin ciwo daga magana shikenan ranta ya baci meyasa bazata fahimta ba?

Yafara mata tofi yana shafa mata a face ranshi na zafi shi gaskiya yanason faseelat yanason dawo da ita,

Aysha ta farfado da kuka tana hawaye ta rike mai hannu tana cewa"dan Allah yaya karkadawo daita inajin tsoronta sosai dan Allah karkamedota "

Fahad yafara share mata hawayen yace"aysha faseelat na sonki yanzu bazata taba cutar ki ba ta sauya ta koma abar tausayi ki tausaya mata mana"

Ta zare jikinta tana kuka ta fita a dakin ta shiga nata tana kuka sosai kamar ranta zai fita bazata iya juraba taga yayanta yana soyewa da wata ba ita ba,

Fahad yabiyo bayanta yanajin ciwon kukanta ya zauna kusa daita yace"aysha idan har tsoronta kikeji ba gida daya zaku zauna ba ki kwantar da hankalinki"

Cikin kuka tace"wlh yaya bazan iya juraba bazan iya ba zuciyata bugawa zatai"

Yana mata wani kallo yace"haba aysha meyasa zaki rika daga hankalinki bayan Kinsan baki lpy faseelat ce fa bawata ba"

Tace"yaya don Allah karka aurota dan Allah ka rabu daita "

Fahad yayi zaune yana kallonta tana ta darzar kuka baya jindadin kukan kokadan amma kuma bazai fasa ba,

Ya kalli agogon hannunshi takwas ta kusa ya tashi ya fita don kaiwa faseelat kayan buda bakin da yace,

Aysha nata kuka ta dago tana kallon bayanshi tana kuka ya fita yabarta bayan da ba haka yakemata ba meyasamu yayanta tunkan ya medota yafara sauyawa ,

Tana kuka ta dauko waya ba tare da tunanin komi ba ta kira no din mommy,

Mommy ta dauka da faraa jin sautin kukan yar'amana yasa ta mikewa tsaye cikin tashin hankali tace"daughter meyafaru ?"

Aysha na kuka tana sheshsheka takasa cewa komi takashe kiran,

Mommy ta sake kiranta tana ta ring baa dauka ba cikin tashin hankali ta hau sama ta dauko mayafi da key ta nufi gidan,

Fahad ya siyo mata fruit da drinks da roast meat yana zuwa ya kira faseelat ta fito tana sassanyar murmushi ta shiga motar,

Yana sukuku yake kallonta ta kalleshi tana murmushi tace"ina kayan buda bakin?"

Ya nuna mata back seat ta kalli ledojin tace"amma u r late ni nakoshi ka koma dasu"

Yayi murmushi yace "ai yadda yunwa ke hanaki fitowa nasan abincin da zakici ba kadan bane "

Tai dariya tace "to nagode sosai Allah yakaimu time da kanka zaka rika bani a baki zanfi ci da yawa"

Yayi murmushi yace"yaushe ne Queen ? Ya kamata a daura mana aure hakanan I'm eager"

Tai murmushi tace "ni ba ruwana kasamu ya omer Ku tattauna yafi"

Yayi murmushi yace "insha Allah very soon "

Ta tsaya tana kallon shi tace"lpy naganka haka kamar baka jindadi"

Yace"rashin ganinki ne yasa"

Tai murmushi ta sunkuyar da kai,

Yace"kije kiyi buda bakin se munyi waya anjima"

Tace "a,a se gobe de "

Yace"meyasa ?"

Tana dariya tace"seda safe"ta fita ta bude baya ta dauki ledojin ta fito ta shige gida,

Ya girgizakai ya nufi gida brain dinshi nata tunanin yadda zai shawo kan aysha,

Gida ko mommy tazo ta samu aysha nata kuka ta jawota jikinta hankalinta tashe tace"aysha ki fadamin mike damunki?"

Aysha na kuka tace"mommy yaya zai medo faseelat don Allah kibashi hakuri mommy tsoronta nakeji sosai"

Mommy tai shiru yo yama zaai ta yadda wancan karan ma bayadda zatai ne amma wannan karon bazata yadda ba ,badole aysha taji tsoronta ba mace babba ga iyayi kamar yar bariki ,

Tace"kiyi shiru bazai medota ba kidena kuka daughter " ta cigaba da rarrashinta,

Fahad yana shiga gidan yaga motar mommy fake sosai zuciyarshi ta buga ya kure gidan da kallo yanajin tsoron shiga zuciyarshi na tunanin aysha ta kirata wata kuma ta karyata hakan aysha bazatai haka ba ya fito ya nufi ciki jikinshi sanyaye ,

Aysha na jikin mommy tun dazu ya shigo dakinta tana jikin mommy tanata ajiyar zuciya gabanshi yayi mummunan faduwa,

mommy ta dago tana jefamai wani kallo,

Ya karaso ya zauna kasa yace"mommy sannu da zuwa"

Tace"yawwa son ashe aure zaka kara batare da kafadamin ba?"

Ya kalli aysha ya kalleta yace"mommy faseelat ce"

Ranta bace batare da daga murya ba cos tasan danta sosai baseta yi hakan ba,

Tace"eh ita kadena maganar medota gidannan tunda daughter bataso kuma kasan bata lpy "

Idanunshi jawur yana tuno halin da faseelat zata shiga da halin da zai shiga saboda yana sonta sosai yace "mommy dan Allah kiyi hakuri"

Mommy ta nai masa kallon mamaki tace"fahad ni zakarikawa musu? Saboda nace karka medota?"

Kanshi sunkuye ya girgizakai yana hawaye yace "kiyi hakuri mommy faseelat ta sauya sosai"

Mommy tace"to yayi kyau son kadawo daita tunda kana sonta kuma gwara ita dani"

Ta mikar da aysha na jikinta tace"mu tafi gida idan shi yadena sonki ni inasonki"

Fahad ya dago yana hawaye ya mike tsaye yace"mommy dan Allah....

[2/9, 10:19 AM] Maman Mamy: 85



Yace"mommy dan Allah kiyi hakuri karki tafi da aysha wlh inasonta ba yadda zanyi na hadata da faseelat "

Mommy tace"to kafasa auren don kuwa ban dauko aysha don ta rika kuka ba "

Ya jinjina kai,

Ta meda aysha ta zaunar daita tace"kiyi hakuri aysha kidena kuka kinji inasu twins kitashi ki dubosu"

Ta daga kai itama mommy ta fita daga dakin ta nufi gida ranta badadi fahad na mata musu akan maganarta ,

Mommy na tafiya fahad na tsaye yaketa kallon aysha tana kwance idanunta lumshe tana ta ajiyar heart,

Zuciyarshi na zafi yace"aysha meyasa zaki fadawa mommy bazaki bari nafada mata da kaina ba? banji dadin hakan ba, bakison abinda nakeso aysha faseelat ta sauya ba wacce kksani bace yanzu inasonta sosai kuma ko ban aureta ba kisani inasonta kuma bazan dena ba harabada"yana gama fada ya fita a dakin ya koma nashi ya zauna ya dafe kanshi kamar zai rabe biyu yana zubda hawaye kokadan bayason yin abinda mommy bataso ko tabashi umarni yaki bi amma yazaiyi da faseelat ?idan ya gujeta bakaramin damuwa zata shiga ba kuma bai mata adalci ba,

Aysha ko maganganunshi ba karamin ciwo suka mata ba wai zai cigaba da sonta har abada tafara wasu sabbin hawayen tana jin kishi na kara taso mata,

Kan fahad na ciwo ya tashi yayo alwala ya kabbara sallar ishai yanata rokon Allah yasa mommy ta amince cos ita kadaice keda matsala amma daddy baya da matsala kuma dama kishi bazai bar aysha ta yadda ayi auren ba,

Itama ayshar alwalan tayo ta kabbara salla tana rokon Allah ya rage mata kishin nan kuma yasa kar ayi auren inde faseelat din ba alheri bace acikin rayuwar su,

Faseelat tagama salla ta dauko fruit da ya kawomata tanasha tana murmushi ,


Bayan kwana biyu fahad yaje ya samu daddy yafadamai saboda zuciyarshi takasa hakura kullum seyaje gun faseelat in ma bai jeba itake kira tace yazo ta ganshi,

Yana fadamai wanshekare tunda safe daddy ya koma gidan mommy na zaune tana karanta jarida ya shigo ya zauna,

Ta zare jaridar tace"sannu da zuwa"tana ta murmushi,

Fuskarshi daure yace"hjy meyasa zaki hana son medo faseelat tunda yanason medota?"

Mommy ta kalleshi tace "saboda bana sonta ko time daya aureta da farko don ba yadda zanyi ne biki ya riga ya gabato amma ai ta mishi girma "

Daddy yace"me tayi miki da kike cewa bakisonta?tunda kin auramishi aysha ya amince seki hanashi auren wata bayanta ?kuma ko shekara 60 gareta ai idan ya aureta ba haramun bane"

Mommy nata kallonshi tace"kara ta yakawo maka kenan? yanason ya dawo daita to bari in kirashi yazo ayi komi gabanshi"

Ta dauki waya ta kira fahad,

Ya dauka yana cikin mota zuwa office tace"kazo gida yanzun nan "tana gama fada ta kashe kiran,

Fahad ya cire wayar a kunne kamar zaiyi kuka ya juya ya nufi gidan ya shiga ya samu daddy nata fada itako tana karatun jaridarta,

Ya zauna kasa kanshi sunkuye yace" mommy ina kwana?"

Tace"yimun shiru son nafada maka kada kamedota shine kaje kafadawa daddynka saboda mace kakeson bijiremin ?to bari kaji ba aysha kadai ke bata son auren ba har nima banaso tun farkon aurenku batamin ba na kyaleka ne kawai ka aureta tunda yanzu ka zabeta ka saki aysha seka aureta din"

Fahad ya dago fuska yana hawaye yana kallonta,

Daddy ya dafe kanshi dake ciwo yace "saboda me zai saki matarshi ? Wai meyasa baki da lissafi?"

Batace uffan ba ta tashi a zuciye ta haye sama,

Daddy ya kalli fahad yace"kaje ka cigaba da shirye_shiryen aurenka"

Yana hawaye yace "na hakura daddy tunda mommy bataso shikenan ko da nayi bazanji dadinsa ba "

Daddy yayi shiru fahad ya tashi ya fita ya nufi office idanunshi jawur ,

Yana zuwa office ga aiki gabanshi amma Sam jikinshi ba karfi ya kwanta jikin seat yana tunani,

Bayan minutes sabeer ya shigo yayi tsaye kanshi yana cewa"lpy daddyn twins? "

Fahad ya dago ya sa handkerchief ya goge idanunshi ,

Sabeer ya zauna yana fadin "mike damunka kuma?"

Fahad yace"inason meda faseelat Aysha bataso mommy kuma ta hana nakasa ta yadda zanyi in tunkareta da maganar"

Sabeer yayi tagumi yace"amma meyasa mommy zatai haka faseelat abar tausayi ce sosai ta rasa abubuwa da yawa a rayuwarta"

Fahad ya girgizakai yace"plss ka samu faseelat kuyi maganar "

Sabeer yace"ni? Wlh kunyarta nakeji bazan iya ba ,bawai na sameta ba ko haduwa banaso muyi daita "

Fahad yayi shiru yana tunanin saboda maganar ne,

Sabeer yace"kayi hakuri tunda mommy bataso kayi kokarin cireta a ranka amma gaskiya kayi missing mata Allah I'm telling u"

Fahad ya kara shiga tunani,

Ana tashi office ya koma gida aysha na school twins na falo ya daukesu yayi musu wasa ya wuce room ya kwanta yanata tunani,

Karfe 6 ya tashi ya tafi dauko aysha school tunda tashigo motar batace komi ba shima baice ba kwanan nan shiru suke basu cika mgna ba,

Can zuwa ciki_ciki tace"yaya dan Allah kadena fushi dani bana jindadi kayi hakuri kishinka ne yasa nai haka"

Yayi murmushi me ciwo yace"aysha ni bana fushi dake damuwa ce kawai tamin yawa amma zuwa wani lokaci kome zai wuce"

Tai shiru duk maganar da zaiyi bata jinta da dadi damuwa ta mishi yawa damuwar faseelat kenan?

Suna isa gida ta fita ta nufi ciki jikinta sanyaye yabi bayanta da kallon tausayi duk tabi ta rame saboda jarabar kishi ya girgizakai ya juya ya nufi masjid,

Bai fito ba seda akai ishai yana fitowa masallaci kiran faseelat ya shigo wayarshi data kira se gabanshi ya fadi ya dauka ya kara kunne yana dan murmushi,

Tace"sweety yau kamanta dani ko? Ba kira bakomai"

Yayi murmushi yace "kiyi hakuri"

Tace"banyi ba ina jiranka idan kazo to na hakura"

Yace"to ganinan zuwa"

Tana jindadi takashe kiran,

Gabanshi na faduwa ya nufi gidansu ,

Ta fito ta shigo motar tana faraa ganin yau yafi kullum kara ramewa tace"dear don Allah meke damunka duk kabi ka rame ina aysha ?"

Yayi shiru ,

Tace"ba zaka fadamin ba? to kunyi mgna da ya omer kuwa?"

Nan ma yayi shiru,

Tace"magana nake fa don Allah mike damunka ne?"

Ya kalleta idanunshi jawur yayi saurin sunkuyar da kai ya dora handkerchief a idonshi yana fitar da zafafan hawaye ,

Hawaye suka cika idon faseelat tace"innalillahi wainna ilaihi rajiun kuka kake dear don Allah minene ke damunka?"

Ya dade yana hawaye ya dago yace "kiyi hakuri faseelat ba zamuyi aure ba"

Hawayen idanunta suka fara zuba tace"but why?minene laifina?"

Ya girgizakai yace"bakiyi komiba Queen inaga Allah ya riga ya tsara ke ba matata bace "

Faseelat na hawaye

Please Login or Register in order to submit comment