Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shiru "munafuki makaryaci mayaudari butulu me zakafadamin?"

Ya cije lips ya rumtse ido zuciyarshi na tsananta zafi ,

Tace"wlh nayi danasanin saninka a rayuwata dama bantaba saninka ba ka cuceni ka zalunceni kuma se Allah ya sakamin "zuciyarta na zafi kuka ya kwace mata tafashe da kuka me sauti,

Ya bude idonshi jawur yana kallonta yakasa gane ta ina zai bullowa faseelat suyi zaman lpy tamkar yadda sukeyi da aysha yanzu kuwa yadau laifin saboda kaurace mata da yayi bayan hakan bai tunanin bata lpy ba,

Tana kuka tace " katashi kafita a dakina banason ganin ka karka kara zuwamin kaje can wurin masoyiyarka uwargidanka uwar yayanka"
[1/12, 12:59 AM] SHALELE😍: Pay and read for sell
07063721063




54



Manzon Allah (S.A.W)yace umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna sadaka ne.




Ya jawota jikinshi dasauri da niyyar rarrashi,

Ta janye ta matsa can nesa tana cigaba da kuka tace "karka kara yunkurin zuwa kusa dani jikina bana banza bane nasan mutuncin kaina nasan ina da daraja haryanzu"

Kamar zai kuka yace"dan Allah ki saurareni fasee..."

Tace"yimun shiru fahad ka bani mamaki matuka ina cikin gidan ka for almost 3days baka ganniba baka leko dubani ba baka kira wayata ba saboda dani da babu duk daya?" Ranta na kara kuna

Zuciyarshi na tafasa yace"dan Allah kisaurareni wlh bansan baki lpy ba"

Ta dagamai hannu idanunta kulle suna cigaba da zubar da hawaye tace"banason jin komi ba bakinka zai yimin bayanin komi ba halayyarka da ayyukanka ka zasuyi "

Ta bude ido tana mai wani kallo idonta na hawaye tayi murmushi tace"kuma jikinka ma ya nuna kana cikin kwanciyar hankali da koshin lpy"

Murmushin sosai ya doki zuciyarshi ya sunkuyar da kai ya dago muryarshi sanyaye yace"nasan ban kyauta ba daban nemeki ba don Allah kiyi hakuri I'm regretting plss forgive me wlh bansani ba"

Ta tabe baki still hawaye take zuciyarta takasa dena suraci dukda maganganun da takeyi wani daci da bakinciki ketaso mata inta kalli fuskarshi ta tuno yadda sukai soyayya baya da yadda yake mata yanzu harwani kiba zaiyi bayan ita gata kwance tana jinya?

Tace"wlh bazan cigaba da zama da kai ba seka sakeni inje inda zaa rika ganin darajata a riritani abani duk kulawar data dace inda akasan ni macece"

Wani harsashe me dafi ya soki zuciyar fahad yace"wane irin magana kike faseelat? Meyasa hankalinki ke gushewa kirika fadamin kome da yazo bakinki? nayi laifi kuma na baki hakuri seki hakura"

Tana jefa mai banzan kallo tace"harwani hakuri zanyi bayan Wanda nakeyi bazan iya zama da kai bane wlh, ka sakeni akwai Wanda ke sona zaiyi farinciki da duk yadda ya sameni"

Ya matse face ya hadiyi miyon bakinciki zuciyarshi na tafasa yace"karki sake maganar kowa acikin gidana ke matata ce ni kadai kuma ban aureki don in sakeki ba dani zaki rayu ni da ke se mutuwa zata raba"

Tace "ko?to kana da aiki don wlh bazan cigaba da zama da kai ba kuma kadena kirana matarka saboda banga kana abubuwan daya dace miji ya rikawa matarsa ba"

Kamar zai kuka yace"faseelat kece kike neman saki from me ?saboda dan laifi na zata koda Wanda yafi haka na miki zakiyi hakuri I love u inasonki bai kamata kinamin haka ba"

Tace"banasonka gabadaya na tsaneka da duk abinda ya shafeka kuma kai munafuki ne me fuska biyu"

Ya dafe zuciyarshi yana kallonta idonshi cike da hawaye murya raunane yace"kin tsaneni ?!!!!"hawaye suka zubomai masu zafin gaske ya rumtse ido hakan yasa suka kara kwararowa,

Faseelat ta kauda fuska tana cigaba da hawayenta itama kokadan batason taji tausayinshi bare harta sauya kuduri da ze hargitsa mata sauran rayuwarta,

Ta cigaba da cewa"na tsaneka fahad inajin tamkar bantaba wani sonka ba kabani takardata ka sawwakemin dan Allah "

Ya bude ido hawaye na cigaba da kwararomai yace"ki fadamin komi faseelat amma ki sani sonki yananan cikin zuciyata kuma bazan iya sakinki ba inason cigaba da zama dake harabada"

A fusace tace"karyar banza harni zaka fadawa kana so?meyasa baki ke fadin abinda bashi ne acikin zuciya ba inba munafunci ba"

Ya kalleta fuskarshi marairaice jikinshi sanyaye ya tashi zai fita a dakin,

Tabi bayanshi da kallon banza zuciyarta na tuno mata abubuwa da yayi tace"karka kara shigomin daki ko wani damuwa dani sannan karka sake ka tsaya rabon kwana dani kaje ga matarka ku cinye juna don tsananin so kuma karkayi wani tunanin zan takuraka ka sakeni ko daya kaida kanka zaka sallameni batare da na bukata ba "

Ya juyo ya kalleta ranshi na suya ya juya ya fita kafafunshi na rawa don bacin rai da zafin maganganun faseelat yana zuwa dakin shi ya zube kan bed ya saki kuka,

kuka marar sauti sede idanu da zuciya dake tabbatar dashi,

Kuka yake sosai brain dinshi na juyawa kanshi kamar zai rabe biyu matarshi ce ke neman saki tana fadamai ta tsaneshi ?kuma his first love faseelat d girl daya fara furtawa so ya kuma mallaka mata zuciyarshi,

Aysha ta gama girki shiru mintin zuciyarta bai fito yin break ba tana cikin kananun kaya dark blue jeans da white shirt tabaza gashi ta nufi dakin shi tana turawa ta shiga ta ganshi dafe da zuciyarshi yana cigaba da kuka,

Kafafunta na rawa ta doseshi idanunta na zubda hawaye tana zuwa tai kwance gefenshi ta saki kuka me ban tausayi,

Sautin kukan ta ne yasa yasan ta shigo dakin ya bude ido ya kalleta fuskarta kife tanata kuka,

Ya nemi kukansa ya rasa yayi saurin tashi zaune ya jawota jikinshi tana kuka tana ganin fuskarshi jawur jagab da hawaye tafara nishi sama_sama kamar me asama,

Ya kara tallabota jikinshi jikinshi na tsuma yace"aysha_ aysha menene?"

Ta cigaba da nishi sama _sama idanunta lumshe,

Baisan time daya ajiyeta ba da gudu ya fita ya shiga dakinta ya dauko drugs dinta ya dawo ya tada ta yafara dura mata drugs wani nashiga wani na yowa waje,

Yana cigaba da hawaye jikinshi na rawa ya gama dura mata drugs din sannan yafara magana "aysha ki tausayamin plsss banason ganin ki a wannan halin yana sani damuwa kituna da lpyar babynki"

Aysha ta cigaba da nishi yanata kallonta yana hawaye can zuwa ta lafa jikinta duk ya saki saboda amfanin maganin dakyar ta bude ido tana hawaye ta kalleshi,

Yana hawaye yace "aysha plsss kidena kuka ki sawa kanki damuwa kodan saboda baby"

Ta bude baki zatai masa magana difff ta rasa ina take tuni mutanenta sun bugar daita,

Fahad ya rungumeta ya saki kuka meban tausayi meke shirin faruwa dashi ne? Meyasa yaketa bankwana da farinciki kunci na lullube masa zuci kowa yayi aure yana samun kwanciyar hankali da natsuwa but bandashi abun yana zuwa kamar season ,

Seda yasha kukanshi ya goge fuska tana jikinshi sannan yafara mata addua yana shafa mata a koina,

Ta bude idanunta jawur ta saukesu kanshi ya kakaro murmushi,

Ta rumtse ido batare da tace kome ba,

A hankali yace"sannu kiyi hakuri na tayarmiki da hankali keda babyna"

A hankali murya na rarrabuwa tace"ya..ya.. Meke tsakaninka da anty ?kamata laifine ?ni zanje na bata hakuri "

Ya karayin murmushi yace "bakomai kawai akwai abinda ke damuna ne just pray for me Allah yakawo min mafita"

Ta bude ido ta kalleshi ta medasu ta rufe,

Ta riga tagama gano ba karamin so yakewa faseelat ba harya na mata kuka kamar ba namiji ba kanme zai tsaya yana bata ranshi bayan gata kuma tana kokarin farantamishi tana tunanin bacci ya dauketa,

Ya nata kallon fuskarta ya gane tayi bacci,

Ya lumshe ido muryar faseelat me rikitarwa "na tsaneka banasonka ka sawwakemin " na masa yawo,

A hankali ya kwantar daita ya dauki cikin maganinta yasha ya koma ya kwanta ya dora hannu kanta,

Yana cigaba da tunani idan ya saki faseelat ai baimata adalci ba sannan shi haryanzu yana sonta duk yadda take fadamasa zafafa koda zata fadi Wanda ya fisu zai cigaba da zama daita yanajin watarana zasuyi zamansu lpy irin zaman da wasu maaurata sukeyi zaman jindadi da kwanciyar hankali da mutunta juna.

Itama faseelat yana fita ta duke jikin pillow ta saki sabon kuka ji takeyi kamar ta shako shi ya saketa tabar gidan tun kafin su karasata saboda zama a gidan zai iya nakasa mata zuciya,

Tasha kuka ta tashi tayo wanka ta dawo ta koma kwanciya tana tunanin alhaji nuranta duk wani banzan ciwo da fahad zeyi duk aganinta karyane ga alhajinta da seda ya kwanta asibity saboda rashinta idan dashi ne baze iya jure ganin ta a ramen nan ba ko ita tasan ta mugun ramewa,


Abubuwa da yawa sun faru a cikin 3 days dinnan,

Daga ciki har da nemawa Aliyu auren yar'uwarshi sakeena diyar yayar mamanshi kuma nan da 3 days zaa daura aure kyauta batare da sisinshi ba,

Time da mama ta dawo tafada mai tana murna amma he's not happy at all kullum samira seta kirashi tana kuka tana rokonshi karya saketa yanzu ya zataji In taji an daura mai aure? shi yanason meda matarshi yakasa bata takardar yanason iyayenta subar masa ita ga mama ta daddako aure,

Mama ce ta nema masa hayar gida ba nisa dasu saboda ta rika sanin lpyarsu su duka biyun,

Gabadaya Aliyu baida sukuni duk ya rame saboda tunani,

Bangaren Amarya sakeena ko gyaranta kawai ake kara yi ko dama kunsan sokkotowa bade gyara ba😜 itama ba karamin dadi takeji ba zatai aure a birni tundaga Sokoto har Kano kuma fine man irin Aliyu kai she's fortunate,

Bangaren mansura ma iyayen alhaji jafar sun kawo kudin neman aurenta zunzurutun kudi har million biyu baiko kawai bawai sadaki ba akasa bikinsu nanda two months masu zuwa bayan sun dawo daga saudiya umara itada su mama ,

Mansura bata jindadi amma tadena nunawa yanzu tayi wata dayin bleaching amma haryanzu bata fara baki ba jira takeyi ta je saudiya takara dagewa rokon Allah gafara takoma baka kirin kofin yadda take ma hankalinta zai kwanta,

Baba da mama ko baa magana don murna harta yanuwanta murna suke yaruwarsu tayi goshi suma zasu samu,

Alhaji jafar ko harya fadawa matanshi zai karo aure ta ukkun duk hankalinta ya tashi zaa dena dokinta ,

Gidan alhaji nura cikin hjy abida harya kai 1 month kuma shine right time da alhaji zai san tana da ciki,

Tunda safe yana shirin fita ta shigo dakin shi dukda ba kwananta bane,

Yana dressing ya juyo ya kalleta duk tai haske tayi sukuku ya cigaba da shiryawa yace"hjy lpy?"

Ta zauna kan seat ta kwantar da kai jikin seat din tace"ban lpy?"

Ya juyo yana kallonta yace"tuntuni nake ganin baki lpy kinki yarda akira likita kina cewa lpyarki lau"

Tai murmushi tana lumshe ido tace"eh da lpy ta lau amma daga jiya nafara rashin lpy "

Yace"meya sameki ?"yana duba mirror yana saka hula,

Tace "inajin ina da shigar ciki"

Da matukar farinciki ya juyo ya dawo kusa daita ya zauna yana jefa mata wani kallo yace"dagaske?"

Ta jinjina kai tana murmushi ,

Ya saki murmushin jindadi yace"alhamdulillah boy ya kusayin kane"

Ta jinjina kai tana kara murmushi,

Ya nata farinciki yace"kinsan ko yarannan suna son baby ni kaina nayi missing jariri"

Tai dariya,

Ya rungumeta yana murna yace"tnx u my bride me kikeson kyauta a wurina na wannan albishir medadi da kikamin?naji dadi matuka"

Tai shiru ta girgizakai tace"nothing"tunda de tasamu bai gane ba,

Ya mata kiss yace"dole nabaki kyauta ki kulamin da kanki sosai and zanturo nurse ta dubaki"

Gabanta ya fadi ta turo baki tace"Nide karda ka turota tunda lpy ta lau yanzun tace zatamin allura banaso plsss lpy ta lau"

Ya kureta da kallo sannan ya saki murmushi yace"duk yadda kikeso bari intafi zanyi baki sena dawo"

Ya tashi zai fita ta biyoshi Sega hjy Rukayya ta turo kofa ,

Tana kallon fuskarshi tagane yana cikin farinciki tace"har zaka fita? Allah ya kiyaye"

Yace"ameen kun kusayin jego ku shirya"

Tace "bangane ba?"tana kallonsu,

Ya nuna bayanshi yace" mommynsu is pregnant "

Hjy Rukayya ta saki murmushi tace "lalle kam muna da jego Allah ya raba lpy"

Hjy abida tai murmushi tace"ameen"

Ya fita yabarsu cikin dakin,

Hjy Rukayya ta kalleta ita tun kwanaki ta dan fahimci abidar na da damuwa ashe cikinne to amma batasan meke tsakaninta da mijinta ba bare tasan adadin kwanansu,

Hjy Rukayya tace"maman biyu dan Allah dis time ki haifo mana biyu mu sabinta"

Abida tai dariya tace"to ku mana addua Allah yakawo su"tana dariya ta fita,

Hjy Rukayya tafara kara gyara dakin,

Hjy abida direct dakinta tawuce tana murna ta shige kurya tai dialing number *Jamila* a wayar ta,

Ring biyu jamil HQ ya dauka yace"my sugar "in a sexy voice,

Ta saki murmushi me sauti da numfashi tace" alhaji ya yadda da cikina na shine ya nata murna"

Jamil yace"wow naji dadi hankali ya kwanta ko?yanzu kisan yadda zakiyi muhadu"

Tai dariya tace"karka damu my jamil zan samu time nafito muhuta nima nayi kewarka"

Yace"shiyasa nake sonki sosai abida har cikin raina sonki duk ya mamaye"

Tai dariya tace "bye bacci zanyi"

Yace"yanzu?"

Tace"Allah bacci nakeji kuma me nauyi nadade banji sakwat irin yau ba kamar na sauke wani nauyi nakeji"

Yayi dariya yace"hmmm_ hmmmm Allah duk kika yadda nakamaki sena fanshe duk kwanakin da na nema bansamu ba, ai bacci lpy a shafamin baby na"

Tai dariya takashe wayar tana farin ciki ta shafi cikinta idanunta lumshe tace"yaro dangatan daddy's "

Ta sauke ajiyar zuciya ta kwanta kan bed tana ta murmushi tana hango haduwarsu da jamil bacci medadi ya kwasheta,

12:00pm Fahad ya Riga tashi yayo wanka ya sauya kaya ya dawo ya zauna bakin bed yayi tagumi kamar ya tada aysha kamar ya kyaleta tausayin baby yakeji batai break ba da kuma ita kanta dole tana jin yunwa,

Bayan mintoci yana zaune yanata kallonta tafara motsi ta bude ido ta dorasu kanshi ,

Yayi murmushi yace"sannu princess"

Tai shiru tana yamutsa fuska,

Yace"yunwa ko?"

Ta daga kai ta dora hannu a cikinta ta girgizakai,

Ya sakeyin murmushi yace"mutafi nabawa baby abinci"ya tallabo ta,

Ta saki murmushi tana yamutsa fuska ya dauketa ya nufi Palo daita,

Tsaf bakowa ya ajiyeta dining yayi saving Quaker oat da madara da Irish yafara bata ,

Ta bude baki tana amsa tana kuma dauko Irish tana samai a baki da daidaya yana amsa yana cinyewa,

Yanata bata harta koshi sannan yasha ya kuma daukarta suka koma falo ya kunna musu kallo ya rungumeta suna yi,

ya hana aysha girkin rana da rana zasu fita restaurant suci,

Bayan sunyi axahar sun sake wanka ya nufi dakin faseelat gabanshi na faduwa,

Ya tura ya shiga tanata kallon wayarta tana karanta littafin raggon miji na SHALELE tai kamar batasan dashi ba,

Yayi tsaye gabanta yana kallonta ganin bata da niyyar dagowa ta kalleshi a hankali yace"faseelat ki tashi ki shirya zamu fita cin abinci"

Ta dago fuska tana wurga mai harara tace"da dani kukeci?kaga wani salon yaudara kuma dan Allah kabani wuri Malam"

Ya rike kugu yana kallonta da takaici yayi murmushi me ciwo yace"nine mayaudari?"

Tai banza tatashi ta dauko earpiece ta dade kunnuwanta,

Ya cigaba da kallonta ranshi na baci ya juya ya fita,

Tai tsoki tace"aiba mayunwaciya ka auro ba"

Ya fita yanata calming kanshi kar mood dinshi ya sauya aysha ta shiga bacin rai ya koma gunta yana ta murmushi hannunta cikin nashi suka fito suka tafi restaurant cin abincinsu,

Alhaji yana cikin farinciki matarshi is pregnant tace batasan komi amma dukda haka seda yayi mata transfer na 1million yayi waya akawo masa sabuwar mota fill dal light blue color me kyau,

Yana komawa gida seda ya biya dakin hjy abida tanata barci abinta yayi murmushi ya dauki key din motarta ya fita wurin motar cos anjima zaa kawo sabuwar a fita da wannan ,

Yana zuwa ya bude ya yafara dubawa ko akwai wani abu aciki yanaso data fito daukar mota taga sauyin sabuwa batare da tasani ba,

Yanata dubawa bakomai ciki yana bude lokar gaba yaga takardu bawasu takardu bane sena gwajin jini da sukayo ita da jamil HQ ajiye .
[1/14, 8:33 PM] SHALELE😍: For sell 07063721063



55



Manzon Allah (S.A.W)yace Wanda ya lazimci istigfaree Allah zai yaye masa dukkan kunci kuma zai azurtashi ta inda baya tsammani.




Ya daukosu ya fito a motar ya kai duba gunsu kenan yaji ana order bakin gate bai karanta komi aciki ba ya dega result da sunan asibity a sama ya meda kallo gun gate da megadi ke hangamewa sabuwar mota dall fill yar karama dede mace ta kutso kai cikin gidan,

Ya nannade takardun yasa aljihu dede motar ta karaso parking lot din,

Matashin daya tuko motar ya fito yana faraa ya sunkuya ya mikawa alhaji nura hannu,

Alhaji ya mika mai hankalinsa kan motar sannan ya juyo yace"gaskiya mota tayi kyau"

Matashin yayi murmushi yace "muna godiya alhaji"

Alhaji ya bude motar ya kara dubawa sannan ya fito ya gwada mishi motar abida yace ya dauka ya tafi zasuyi magana da manager,

Matashin ya dau motar ya tafi,

Alhaji nura ya ciro takaddun a aljihu batare da shaawar sanin na miye ba ya medasu cikin lokar ya rufe motar ya koma cikin gida,

Dakinshi yawuce yayi wanka sannan ya fito dining,

Hjy Rukayya tayi serving dinshi yafara ci yana kallonta yace"na sauyawa abida mota naga taki bata tsufa ba amma kema zan sauya miki very soon"

Tai murmushi tace"ni na yafe mota ta lpyarta lau kuma ni bancika fita ba kamarta in ma na tashi wani lokaci data yara ake kaini nagode sosai Allah yakara budi ya sauki mommynsu lpy"

Yayi murmushi yace" ameen"

Ya cigaba da cin abinci,

Dede time din hjy abida ta fito tana jin yunwa tazo dining din ta zauna ta kalleshi tace"sannu da zuwa alhaji"

Yace"yawwa "sannan ya kalleta yayi murmushi ya cigaba da cin white rice dinshi da vegetable source,

Hjy abida tafara serving kanta,

hjy Rukayya tace " kinsha bacci"

Hjy abida na cigaba da zubawa tace"wlh ko magana banasonyi yunwa na cina"

Hjy Rukayya tai murmushi tana kallonta suka cigaba da cin abinci ita kuwa hartayi nata tare da zuria,

Bangaren fahad ko bayan sun dawo daga restaurant a falo suka zauna aysha ta kwanta jikinshi shi ko kanshi a jikin seat sukai shiru har bacci ya dauketa,

Shi ko fahad tunanin faseelat kawai yake balain tsoron tunkarar dakinta yake saboda maganganunta marassa dadi musamman in ya tuno saki data nema kuma yana kara ganin be kyauta mata ba,

Bangaren jameela ko yanzu sabon wulakancinta kullum yawo se dare ta dawo gabadaya Khalil baida natsuwa ya rasa ta ina zaifara sauya jameela jiyake kamar ya tunbuke duk mugayen dabi'unta ya zuba mata sabbi masu kyau,

Da daddare aysha tayi girki hakanan taji faten shinkafa takeso kuma shine ta dafa yaji nama da daddawa da kayan kamshin barkono se kamshi yake ga allaiyahu ansa aciki,

Bayan sunyi ishai suka zauna a dining table din,

Aysha na niyyar fara serving ya kalleta yace"jeki kirawo faseelat"

Gabanta ya fadi jin ta kira faseelat bata nuna ba amma tana jin tsoro ta nufi saman domin kiranta,

Kallo daya ya mata ya gane a tsorace take da zuwan sede shi bazeiya zuwa ba shima,

Aysha na isa tafara knocking a hankali ,

Jin knocking din yasa faseelat dake zaune tana shan tea ta meda hankali gun kofar,

Aysha ta cigaba da knocking tanayi tana dakatawa,

Faseelat ta kwara baki zatai magana se kuma ta fasa ta tashi ranta bace taje ta bude kofar da karfi ,

Aysha bata koji alamun zaa bude kofar ba taga yadda aka bude ta da karfi tai saurin matsawa baya gabanta na faduwa ,

Faseelat tai tsaye tana binta da makaskancin kallo wannan yar kuciciyar diyarce kesa mijinta ihu itace mowa duk girmanta ya zam na banza ta kwacemata miji a dage tace"lpy meya kawoki?"tana binta da harara,

Jikin aysha ya fara dan rawa hannunta biyu hade gu daya tana matsa yatsu a tsorace tace"yayane yace kifito muyi dinner"

Rainin hankali kenan ita zai aikowa ta fito dinner last 3days da ita sukeyi?

Ranta bace tana mata banzan kallo ta kwatsa mata tsawa "kee!!!!! "

Jikin aysha yakara daukar rawa saboda bacin rai da tsoronta,

Faseelat tace"daga yau karki kara tako saman nan kinaji na ?idan kika kuskura kika kara takoshi zakici ubanki duk wannan kukar aljanun dake kanki se sunfita shegiya me kama da aljanu bacemin dagani"ta karasa a tsawace,

Aysha tai mata wani banzan kallo ranta bace ta juya ta nufi kasa zuciyarta na zafi ,

Faseelat tai tsaye tana kallonta zuciyarta na fada mata ta samesu dining din tabuga masa warning karya kara aiko mata me siffar aljanu part,

Aysha ko tana taka bene zuciyarta na kara bugawa ranta bace yake ta manta last a mata fada a gida kowa yana kafa_kafa da duk abinda zai bata mata rai amma yanzu wata na zaginta tana kushe halittar ta tana kuma ce mata shegiya,

Tana jin juwwa ta cigaba da takawa zuwa kasa,

Tunda tafara saukowa hankalin fahad ke kanta ya kuramata ido ganin kamar bata ko kallon gabanta tana tafiya kuma very slow,

Tana zuwa last step tai luuuuuu zata zube kasa da gudun tsiya zuciyarshi kamar zata fito jikinshi na mazari ya karasa wurinta yayi saurin tallabeta tafada jikinshi,

Ya karasa zama kasa domin kafafunsa bazasu daukesa ba ya kurawa face dinta ido idanunta lumshe alamun aljanune suka bugar daita,

Kallonta ya cigaba dayi zuciyarshi na zafi besan lokacin da hawaye masu zafi suka zubomai ba ya cigaba da hawaye yana kallonta tana jikinshi yakasa mata komi,

Dede nan faseelat tayo kasan don kara zazzaga masa kwandon masifa,

Tun kafin ta karasa saukowa take kallon su yana zaune aysha sheme jikinshi hankalinshi kanta,

Ta cigaba da saukowa karar taka step dinta da kamshinta yasa fahad saurin dagowa ya na kallonta,

Tana karasowa ta dage gira tana kara kallon aysha sheme tababbake da dariya tana mamaki ta tsagaita ta rike haba tace"eyeeeee wato harsun taso saboda Sheri toyayi Allah de ya kaimu lokacin da zasu taso dagani seke wlh daga ranarnan kindena aljanu inma na gaskene zasu kama gabansu"

Fahad na kallonta idanunshi jawur zuciyarshi na zafi,

Bata damu da kallon fuskarshi ba da yanayinshi tace"idan har kanason matarka kadena turota wurina kadena banaso idan kaima kanason zaman lpy da lpyarka kadena zuwa inda nake shikenan kun zauna lpy"

"Inko ba haka ba" ta daga ido sama tai murmushi tace"wlh sai kun nemi natsuwa da tunaninku kun rasa bare kuma ita wannan nakasassar tuni zan iya cin ubanta in zane shegen jikin da kake kallo kake jindadi"

Tana gama fada ta nufi dining cike da son bata masa rai ta bude warmers sega fate ,

Tai dariya tace"masu ciki kenan to yayi kyau" ta dauki warmer ta nufi sama,

Fahad na cigaba da binta da kallo tana hayewa ya dukar da kai jikin aysha ya saki kuka zuciyarshi na tsananin kuna he wish zai koma rayuwarshi kamar baya ba tension ba stress na mata amma yanzu abun ya masa yawa ga faseelat balai ga aysha ciwo,

Yasha kuka tamkar mace zuciyarshi tayi rauni sosai babban bakincikinsa inya tuna His faseelat ce takoma haka tunani yake dama can bata sonshi kamar yadda take cewa itama,

Yasha kuka sannan ya dauki aysha ya shiga dakinshi daita ya kwantar daita ya wanko fuskarsa duk don karta gane yayi kuka sannan yazo yafara mata tofi yana shafa mata ruwan,

Aysha ta bude ido ta kalleshi se kuma ta fashe da kuka hawaye na zubarmata masu zafin gaske,

Ya rungumota jikinshi yana shafa kanta yana tapping bayanta ta cigaba da kuka,

Muryarshi duk ta shige a hankali yace"aysha kiyi shiru plsss kidena kuka karwani ciwo ya sameku nayi kuskuren turaki wurinta bazan sake ba"

Aysha ta cigaba da kuka yanata rarrashi sannan tayi shiru tana ta sakin ajiyar zuciya me sauti,

Tana rungume jikinshi harta lafa ya dago face dinta yana kallon idanunta ta lumshe ido taki kallonshi eye lashes dinta sharkaf da hawaye,

In cool yace"I'm sorry aysha banason kina bari wani abu yana bata miki rai banason wani abu ya samu lpyarki data abinda ke cikinki"

"Kiyi hakuri da faseelat kidena damuwa da hayaniyarta na wani lokacine zata sauya insha Allah"

Kusan duk maganarsu da aysha iri daya kan zata sauya,

Aysha ta bude ido yana jajir ta kalleshi ta daga kai a hankali,

Yayi murmushi yace"tnx ki kwanta ki huta"

Ya kwantar daita sannan ya tashi ya fita dakin faseelat yawuce ya banka ciki a zuciye,

Yana zuwa ya samu ta tsatstsakuri faten dama badon ta ci ba don bada haushi kawai, tabar kular bude iskan AC nata bugunshi,

Ya kureta da kallo,

Tai kamar batasan mutum ya shigo ba ta cigaba da kallon TV ,

Ya karasa ya rufe kular ya dauka ya juya zai tafi zuciyarshi nata zafi yanata cijewa yajuyo yace"kirika jin tsoron Allah "ya juya ya cigaba da tafiya,

Faseelat tace" harni zaka fadawa tsoron Allah kai kana tsoronshi ne?ko ita shegiyar aljanar matarka na jin tsoron shine kune zaa fara yiwa wannan Kalmar"

Bai juyoba ya karasa fita gani yake kamar faseelat tanada mental illness da yake motsa mata time to time,

Dining yaje ya zuba abincin a plate yana kyankyaminshi ya nufi dakinshi ya tada aysha yakai spoon bakinta,

Ta girgizakai tana yamutsa fuska ,

Yace"kici kokadanne plss"

Ta kara girgizakai duk abincin da komi ya fitar mata a rai maganganun faseelat sunata mata yawo wai itace shegiya?

Ya tashi ya fita da plate din ya dawo ya

Please Login or Register in order to submit comment