Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya dauketa yakaita ciki idanunta kulle yana gefe ganin jikinta ya dena rawar yasa shi ya kai hannu ya rike breast dinta tai saurin bude ido ,

Yafara dariya tai karamin murmushi dayafi kuka ciwo ta rumtse ido,

Yana dariya yace"yau anmatana harda fitsarin kwance"

Ta rufe ido da hannu tana turo baki tace"Yaya!!!"

Ya rufe baki ya daga hannu yayi shiru,

Bayan yagama gasata still ya mata wanka ya medata dakin,

Ya shiryata suka kwanta yana rungume daita,

Cikin dare fitsari ya tadata kafin ta shiga toilet ya kufce mata yanata bacci bai jiba ta karasa tai sauran ta dawo ta goge wurin takoma ta kwanta,

Da asuba ya tadata yafita masallaci yana dawowa yafara nemanta duk yadda takeji tai shiru yafara sex daita yana jin matukar gamsuwa daita,

Still shiru take juya kai ne nata da rawar jiki seda ya gamsu iyakarshi sannan ya sauka yana sauka tatashi dasauri zata shige toilet saboda fitsari tana sauka fitsarin yafara bin kafafunta se tai tsaye tana kallon kafafunnata sunata rawa ga fitsari nabi tana mamaki,

Aliyu ya taso dasauri wurinta ya riketa yana kallon kafafunta da fitsarin zuciyarshi fall tsoro ya dago yace"sakeena lpy kike?"

Idannunta suka kawo ruwa tana danne kukan dake zo mata seda ya kwacemata tafashe da kuka tana cije da lips dinta,

Aliyu yajawota jikinshi ya rungumeta yanajin mugun tausayinta kukan na dokar masa heart .
[1/18, 5:59 PM] SHALELE😍: Pay and read 07063721063



60



Manzon Allah (S.A.W)yace Ku magance bakinciki da damuwa da yin sadaka Allah zai yaye muku cutarku kuma zai temakeku akan makiyanku.



Nace sakeena secondary kadai tayi primary nakeson cewa kaina na zafi sosai a tabonan a tabocan kuma kullum typing duk yadda ake Sena samu nayi shiyasa wani abun se anwuce intunosa wani kuma ina mantawa dasakashi kwata_kwata plss idan kunji shiru kurikamin uzuri ina gwagwatuwa sosai🥴


Idanunshi suka cika da hawaye shima yanajin kamar yayi kukan,

Tanata kuka batsaiko a hankali yace "shittttt!!" Acikin kunnenta muryarshi na rawa yace"kiyi hakuri kidena kuka plsss"

Tai shiru tanata sakin doguwar ajiyar zuciya tanajin kamar ta cigaba da kukanta saboda azabar da takeji ,

A hankali yace"ya kufcemikine?"

Ta jinjina kai idanunta kulle,

Yace" duk nine ko?kiyi hakuri zan dena miki da zafi"

Tai shiru suna tsaye ya medata kan bed ya kwantar daita sannan ya dawo goge fitsarin nata bayan ya kwara ruwa akai still yakara zuba lemon fresh yayi mopping wurin sannan yaje yahada mata ruwan zafi ya dawo ya dauketa ya kaita ciki ruwan zafin daban takejinsu jijiyoyinta takejin duk sun saki hakanan tayi hakuri ya mata wanka yayi ya shiryata ya kwantar daita sannan ya fita kitchen yafara hadamusu breakfast ,

Tai kwance tai shiru tana ta tunani wasu nayin fitsarin kwance na yarinta amma ita tsaf tataso ba fitsare_fitsarennan yau gashi ita fitsari ke kufcewa da wayonta tanata tunanin bacci ya dauketa,

Cikin baccin ta kuma tsula fitsarinta ta farka a firgice jin fitsari na zuba tafara kuka tana jin mugun tsoron al'amarin,

Aliyu yagama breakfast lpy lau yayi yan share_share da mopping yana dawowa ya sameta zaune tanata kuka marar sauti fuskarta jage_jage da hawaye idanunta warwaje zallar tsoro,

Jikinshi na rawa ya karaso wurinta ya haye bed din ya jawota jikinshi idanunshi suka sauka akan lemar dake kwance inda take ,

Yayi saurin kallon kasanta yaga kayanta jike hankalinshi tashe yace"innalillahi wainna ilaihi rajiun !!! mike faruwa ne haka?"yana cikin duhu sosai,

Sakeena ta cigaba da kuka tana ta kallon fitsarin,

Duk jikin Aliyu ya mutu ya saketa ya koma bakin bed ya dafe kai yana tunani zuciyarshi cike da tsoro kar ace yayiwa diyar mutane illa,

Gabadaya ya rasa meke masa dadi a rayuwar sam bazaiso wani abu yasamu sakeena ba saboda lokaci daya sonta ya mamaye zuciyarsa kuma she's like sister iyayenta sun bashi kyauta idan wani abu ya sameta ya kenan?

Ranshi na suya ya juyo yana kallonta yana zaune bakin gadon a hankali yace "sakeena"

Taki kallonshi tanata hawaye,

Yajuya sosai ya kamo hannunta yace"don't worry bawata matsala bace kitashi muje na sake miki wanka mutafi asibity"

Batace komi ba tana cigaba da hawaye ya zubamata idanu yana cigaba da tausayinta sannan ya tashi ya dauketa ya sake mata wanka ya shiryata shi kuwa kaya kawai ya saka suka fito falo ya rungumeta dakyar yabata ruwan tea tasha kadan, shiko tashin hankali bai bari yasa wani abu bakinshi ba ya fitar da mashin dinsa yadawo ya kama hannunta suka nufi waje yanata kallon kafafunta da tunda yayi first night har zuwa yanzu bude take tafiya dasu dukda bata nuna wani ciwo ,

Suna zuwa ya hau mashin tasamu ta hau dakyar suka nufi wata prvt Hosp,

Ba layi sosai amma akwai mutum biyu kafin suga likitar suka zauna a seat yana rike da hannunta dukkansu fuskarsu bawalwala ta ta ko a kumbure tasha kuka,

Ko 5mnt da zama basuyi ba tafara jin fitsari tun kafin tai wani yunkuri sede taji yana zuba abinshi,

Hakan yakara daga mata hankali tai saurin kwantar da kai jikin kafadarshi tana hawaye sosai,

Hakan da tayi bai dauka komi ba seda yaji dumin hawayenta ya dago fuskarta a hankali yace"minene? "

Ta nunamai jikinta da hannu, dan lekawar da zaiyi se ganin ruwa yayi kasan kujerar jikinta kuwa duk ya jike,

Gabanshi ya yanke ya fadi yana kara tsorata cikin jarumta da rarrashi ya zagayeta da hannunshi yace"its okay zai dena kiyi shiru"

Tai shiru kamar yadda ya bukata har layi yazo Kansu yana rike daita suka tashi suka shiga ciki ya zaunar daita ya zauna,

Doctor din ta kallesu tace masa" mi ke damunta?"thinking that cikine,

Fuskarshi bawalwala yafara mata bayani "she's my bride duka satinta daya jiya muna tare se fitsari ya kufcemata ina tunanin duk rashin sabone segashi daga daren zuwa yanzu tayi fitsari kusan ukku a jiki"

Likitan tai saurin meda hankali gun sakeena she's young daka kalleta dukda haka tana neman karin bayani tace"sakeena ya kkji miyasa fitsarin ke kwacemiki?"

Sakeena kanta sunkuye tace"ban saniba zuba kawai yake "

Likitan tai shiru tana nazari duk alamu sun nuna takamu da yoyon fitsari VVF,

Ta kalli Aliyu tace "plss excuse us"

Ya tashi ya fita cikin zuciyarshi yanata rokon Allah ba wani illar yayiwa lpyar sakeena ba seyaji Duk ya tsani Kansa,

Yana fita likitan tace"kinajin zafin wurinne?"

Sakeena ta daga kai ,

Doctor tace"ya kkji jijiyoyin wurin kina kokarin rike fitsarin yaki ?koko zafin ne kawai problem? "

Sakeena tace"banajin dadi inason na rike fitsarin amma bayayi seya zubo"

Likitan ta tashi tasa hand glove ta gyara bed dake gefe tace"come and lay here let me check u"

Sakeena na tsorace taje ta kwanta kan bed din,

Likitan na kallonta tace"sorry "tafara zare mata pant dake jike ta cireshi ta bude kafafunta sosai tafara dubata wurin yayi jawur duk gashin da Aliyu yayi sannan da dan kari jikinta,

Tana cigaba da dubata ta dandago ta kalleta tace" sorry "tana kallon yarintarta dagani tanajin jiki hannun mijinta,

Sakeena batace komi ba,

Bayan tagama dubata tagama gane problem din sannan takoma kan seat ta zauna sakeena zata tashi tace" just lay there "

Tayi rubuce_rubuce sannan ta leka ta kira Aliyu,

Aliyu na zaune yayi jingum ji yake kamar yakoma yaji me ake ciki ta leko kiransa ya tashi dasauri ya shiga da adduoi bakinshi,

Da glass a idonta ta nata kallonshi tace"matarka bata lpy sosai yoyon fitsari ke damunta sannan akwai tear jikinta so u have to stay here for a while saboda a kula daita hartasamu lpy zamu baku gado "ta mika mai wata takarda

Tunda tafara mgna zuciyar Aliyu ke lugude wani azababben ciwon kaine ya tasomai lokaci daya ya amshi takardar a hankali yajuyar da kai yana kallon sakeena idanunta kulle tana fahimtar duk bayanin da suke saboda ba turancine zalla ba bata taba ganin me yoyon fitsari ba se a film din azeema inda akaiwa yarinyar rape a kauye takamu da yoyon fitsari for a year tanata fama dashi bata warke ba hankalinta a tashe yake amma kuma hawayenta sunki zubowa zuciyarta ce kawai ke lugude,

Doctor ce ta kira nurse tace su bita,

Ya tashi ya kama sakeena suka fita ,

Har wani daki babu kowa ciki saboda small asibity ce ya temakawa sakeena ta kwanta a bed jikinshi duk yayi sanyi kamar yayita zunduma ihu yakeji da wane ido zaije yafadawa hjyarshi halin da ake ciki da wane ido zai kalli iyayen sakeena bata yiwuwa tai jinya ta warke basu sani ba kanshi na mugun ciwo ya zauna kan seat dake Kusa daita ya dafe kai yayi shiru ,

Sakeena na kallonshi a hankali ta riko hannunshi dake jingine a gadon,

Ya dago ya kalleta yanajin tausayinta sosai kuma duk baya ganin laifinsa saboda yana bakin kokarin sa wurin rangwantawa,

Cikin sanyin murya tace"yaya kayi hakuri zansamu lpy"

Ya zuba mata ido yana ta kallon ta hawaye ne suke kokarin zubowa a face dinsa takara cewa"zanji dama nan kusa"

Yana meda hawayen ya shafi kanta cikin dauriya yace"insha Allah kiyi hakuri bansan haka zai faru ba "

Ta girgizakai tace"Allah ne ya kaddara hakan yaya"

Yayi shiru yana cigaba da kallonta ya tashi ya fita,

Bayan fitarshi ta lumshe ido ko kadan batajin haushin mijinta ko tsanarshi tanajin cewa zata warke watarana kuma Allah ne yake kawo cuta lokacin da yaso tunda de ita ba raping bane by force halal dinshi yakeyi

Bayan fitarshi yaje yayi paying da kuma duk necessary abunda ya kamata ya dawo ya zauna sunata kallon kallo ba dadewa sosai doctor da wata nurse suka shigo dakin ya tashi ya fita zuciyarshi raunane ,

Sakeena ko ba yadda ta iya duk dauriyarta takara akan ta baya ,

Sukai mata stitch sukasa mata ledar fitsari da duk abinda ya kamata sannan suka fita ,

Kamar karya dawo dakin ya daure yadawo ciki yanajin matsanancin faduwar gaba,

Time da yaga ledar fitsarin dake jikinta kadan ya rage ya fadi yayi saurin rike gado kanshi na juyi,

Idon sakeena kulle wani iri takeji gabadaya jikin kamar ba nata ba ya karaso ya zauna ya kamo hannunta ya rike da hannu biyu yana kallonta da tausayi yace"sannu sakeena Allah yabaki lpy"

Ta dan bude ido ta kalleshi ta meda ido ta rufe ,

Ya cigaba da rike hannunta yanata binta da kallo har bacci ya dauketa ,yanajin tayi bacci ya tashi ya fita domin fadawa mahaifiyarshi tasan halin da ake ciki,

Yana zuwa gidan dakinta ya wuce direct yayi zaune ya tallabe kai da hannu biyu ,

Bata dakin tashigo ta sameshi a haka tana kallonshi tace"Aliyu lpy kazo kayi tagumi da hannu biyu?" tasamu wuri ta zauna ,

Zuciyarshi na ciwo ya zare hannun ya sadda kai kasa bakinshi na rawa yanason fadamata ,

Tace"Aliyu mike damunkane?"

Jijiyoyin kanshi rudu_rudu yace"anyi admitting dinmu asibity?"

Mama ta fiddo ido gabanta ya yanke ya fadi ras_ras tace"meya samu sakeenar?"

Zuciyarshi cunkushe idanunshi jawur yace"yoyon fitsari"

Gabanta ya wani irin bugawa ta dafeshi dasauri tare da furta"innalillahi wainna ilaihi rajiun Aliyu yoyon fitsari fa kace sekace me haihuwa?"

Hawaye suka gangaromasa ya gogesu yana cigaba da kallon kasa,

Mamanshi ta kureshi da kallo idanunta jawur tana matukar tsoron alamarinshi tace"Aliyu yaya kake abunnan ne wai har kasa matarka yoyon fitsari ?innalillahi wainna ilaihi rajiun ni yanzu da wane baki zan fadawa mama abinda ke damun yarta?" tana hawaye ,

A hankali yace"kiyi hakuri wlh bada son raina hakan ta faruwa ba"

Mama ta mike tsaye ta zari hijab tana sawa jikinta na tsuma burinta taga sakeena tace"wlh Aliyu kai abun tsorone inata hangowa wane irin sex ne zaisa mace yoyon fitsari iyayen sameera basuyi laifi ba da suka anshe diyarsu tashi mutafi kasani jin kunya wlh duk dangi koina se sunji lalurarka"

Tai waje dasauri tana harmutse tana fita tacewa kanwar Aliyu" suwaiba natafi asibity kiyi abinci zaizo ya dauka"

Wacce aka kira suwaiba tace"mama wa ke bai lpy?"

Mama tace"antinku ke yoyon fitsari "

Suwaiba ta kwalalo ido tana kallon mama,

Mama ta wuce ta fita,

Aliyu ya goge hawaye zuciyarshi na zafi ya tashi ya fita ,

Suwaiba tabishi da ido tana kallonshi shi bawani kato ba,

Suna tafiya kan mashin bawanda yace uffan mama abun tsoro yake bata 1week da aure se yoyon fitsari shi ko Aliyu jin balain haushin kanshi yake har suka isa,
still sakeena nata bacci Wanda harda ramakon na jiya dabaai ba, mama tashigo dakin kallo daya tayi mata hawaye suka kara yawaita a idonta da tasan hakan zai faru dabata nemo ma Aliyu aurenta ba ansa yar yarinya cikin matsala,

Aliyu kasa shigowa yayi dakin ya samu wuri ya zauna ya buga tagumi,

Can zuwa mama ta fito ta amshi wayarshi yanajin kamar karta kira ta kira mamar sakeena,

Bayan sungaisa tafadamata sakeena bata lpy ,

Abinda mamar tafara tambaya meya sameta da kyar tana zufa tafada mata mamar sakeena ta girgiza matuka duk nan kusa dasu bata tabajin labarin sex yasaka VVF ba cikin sanyin murya tace "Allah yabata lpy insha Allah in munsamu lokaci zamuzo dubata Allah ya sawwake"bata kara cewa komi ba takashe wayar,

Bataso gobe su dauki hanyar ganota kamar basu kyauta ba sabida lalurace kuma mamar zataji wani iri shiyasa bata ko fadawa babansu ba se bayan kwana biyu sannan .
[1/19, 1:06 AM] SHALELE😍: Pay and read 07063721063



61



Da Aliyu da mama suke jinyar sakeena seda akai two days sannan iyayanta sukazo dubata iya karta ido da dan murmushi kwanansu biyu suka koma mama da Aliyu suka cigaba da jinyarta,

Jinyarta sukeyi amma bazaka gane wake ciwon ba domin ko duk sun rame saboda damuwa,

Bayan 3 weeks ne su mansura suka dawo daga saudiyya tayi wulik fiye da bakinta a baya kunsan daga cikin illar bleaching duk time da zai bar fatarki zaki kara baki fiyeda baya sannan in baai saa ba yakan feso kuraje sosai a jiki fata ta kan bushe tayi ba kyau to hakanne ya faru da ita sede dukda haka tana cikin farinciki tana jin kamar Allah yakara mata wata niima ne daga cikin niimomin da yayi mata,

Jirginsu saukar asuba yayi thermocool kuwa a kagare yake ya saka amaryarsa a ido yana mugun kewarta,

Karfe 10am alhaji thermocool yayi parking hadaddar motarsa bakin kofar gidansu ya fito ya jingina da motar yana kallon gidan yanajin dole ya turo a musu gyaran gida ya Ciro waya yayi dialing no din mansura wadda yayi saving da amaryata,

Ta dauka tanata farinciki da walwala tace"mijina"

Yayi murmushi wani sanyi yana ziyartar zuciyarshi yace"na iso amaryata"

Tace"sannu da zuwa kuma ganinan fitowa yanzunnan"

Yayi murmushi ya kashe kiran,

Mansura dake kwance tundazu tayi wanka ba make up jikinta se mai data shafa ta tashi ta dauko zungureriyar hijab dinta harkasa ta saka bayan ta soka hannuwa acikin hannun hijab din,

Tana fitowa ta nufi kofar gida wurin angonta thermocool,

Yana tsaye yaga fitowar bakar fata da hijab har kasa ta dososhi kokadan baiyi tunanin mansurarshi bace duk da tsayin da komai yayi kama daita,

Ta karaso tana murmushi ta dandago sannan ta sunkuyar da kai tace"barka da zuwa"

Thermocool yace"yawwaaaa"yanajan maganar murya irinta mamaki yana kallon goshinta da kafafunta da hannuwanta dake bakake sam bai ganeta ba shide yasan fara ce matarshi maybe wannan ko kanwarta kowata daban,

A hankali yace"ammm shiga ciki ki kiramin mansura"

Mansura ta dago da muguwar faraa tana kallonshi tace"alhaji baka ganeni ba?nice fa mansurarka ashe zakai saurin mantani just a month kawai"

Ya zuba mata ido yana kallon ta tayi bakikirin hakoranta ko sunyi fesss tunda yake bai taba shaawar bakar mace ba shiyasa baya ko tayawa,

Fuskarshi yamutse yace"mansura meyasameki haka?duk kinyi baki ko jinya kikayi acan "

Tana ta murmushi tace"a,a mekagani?"

Yace"kinga duk yadda kikayi muni kikai baki ga wasu rashes mike damunki"yana cigaba da yamutsa fuska kamar yaga kashi ,

Ta sunkuyar da kai tanajin takaici tariga tasani kyawunta yakewa bawai kyawun dabia kowani abu yakeso ba,

Yana ta kallon ta yace"mansura ko kayan makeup dinki suka karene?"

Tai murmushi tai shiru,

Yace"OK "ya koma mota ya fito da 1k bandir biyu ya mika mata yace" gasu kije kisiya wasu bansan ganinki haka"

Ta kalli kudin ta girgiza kai tace"aa nagode"

Yace"meyasa ?plss ki amsa kisiyo kayan makeup duk kin sauya"

Ta dago da murmushi fuskarta tace"dama haka nake wannan shine true color dina"

Thermocool ya kara zuba mata ido still kudin na hannunsa a hankali yace"naji but ki amshi kudin kije kisiyo kayan makeup "

Taki amsa tai shiru kanta kasa,

Ya meda kudin yace" OK kifadamin wane kalar product kike amfani dashi zansa akawomiki"

A hankali murya sanyaye tace"bana shaawar shafa komai nafiso in tsaya ga natural color dita"

Yace"haba mansura kinga yadda kika koma kuwa ?dan Allah ki temakamin ki gyara kanki"

Mansura tace"nifa.. dama tsautsayine yasa nai bleaching kuma yanzu bazan karayiba "

Ba ai masa musu amma wannan amaryace baariga ankamata tashigo hannu ba bare ya jibgeta bayajin dadin musu kokadan da rarrashi yace"haka kikeso ki zauna my bride?duk kinyi baki kinsauya gashi nan da one month bikinmu ?"

Mansura tace"kayi hakuri ni bazanyi komiba"

Ranshi bace ya fiddo kudin daga aljihu yace "ki amsa kije kisiya kayan shafa nace"yana bata command

Mansura ta kalleshi ta kalli kudin batada niyyar amsa tace"dan Allah kayi hakuri "

Yace"shiittt!! baaimun musu koda wasa ki amsa kije kisiya kokuwa inkawomiki duk kalar product na keso"

Ranta badadi in cool tace"alhaji meyasa zaka damu da man da nike shafawa tunda ni kakeso ba jikina ba"

Ya danyi shiru yana calming kanshi yace"but dukda haka bazanso ina ganinki haka ba"

Tace"to haka nike shiyasa tun farko naso fahimtar da kai amma kaki ganewa kafadamin kanasona a haka yanzu kuma kana nuna bani kakeso ba kalar jikina kakeso ni kuma bazan kara bleaching ba saboda nayi nadama na tuba ina rokon Allah yafiya haryanzu"

Thermocool idanunshi jawur yake kallonta duk ya nemi son nata ya rasa shide burinshi farar mace sannan abi dokarshi shine,

Ranshi bace yace"cikin matana gabadaya ba baka kuma bazan fara dake ba idan kin shirya aurena ki gyara jikinki idan kuma kinki to ki dauka ba maganar aurenmu"yana gama fada yajuya yashiga mota yabar kofar gidan,

Mansura na tsaye tabi motar da kallo memakon taji kunci aranta se karin farinciki dake tsatstsafomata ta koina domin a ganinta aurenshi babbar jarabawace gareta ko takirashi musiba duk namijin da bazai nuna maka hanyar lahira ba duniya kawai yasa agaba aiba alheri tare dashi,

Ta saki murmushi ta tabe baki tana jin takaicin maza su basa duba komi se kyau komin jimawa kyawun zai gushe akwai kaddara akwai tsufa amma sude mekyau ta sauke numfashi tana hamdala acikin zuciyarta maybe ta tsallake rijiya da baya,

Tana shiga dede mama ta fito da baki ta musu rakiya zasu wuce mama ta kalleta mansura ko ta gaidasu ta wuce ciki,

Kallo daya mama ta mata taji bataji dadin ganinta haka ba kuma ta tabbatar daga wurin alhaji take tana dawowa ta wuce dakinta mansura na kan bed tana ta dialing no dinshi amma yaki dauka still faraa takeyi tana dariyarshi,

Shigowar mama yasa ta gumtse fuska,

Mama na kallon ta tace"bade wurin alhajin kikaje haka ba?"

Mansura ta kalli kanta rigar jikinta sabuwa dall fill amma kuma mama na cewa haka a hankali ta daga kai ,

A fadace mama tace"dan baki da hankali?ko powder bazaki shafa ba zaki fita bare kuma zizara dan gazar dinnan"

Mansura tai shiru a hankali tace"mama dama don ya kara sanina sosai shiyasa naje haka baima ganeniba gashi yace dole sena koma shafamai inde inason aurenshi"

A fadace mama tace"kingani ko dan ubanki arziki na kiranki kina tureshi da tsiya"

Mansura ta dandago ta kalli mamar ta kuma sunne kai tace"wlh mama da inkara sauya halitta gwara na mutu banyi auren ba yafi idan de yana sona zai dawo in kuma dama kyawun yakeso shikenan seyaje yasamu dedeshi "

Mama na kallon ta ranta bace tace"kuma seki tanaji kudin biyanshi komai daya miki ke alhaji ai rufin asirinki ne damu gabadaya "

Mansura tace"mama ko dana aureshi in nadena bleaching din fa shikenan zai dena sona"

Mama tace"toya dena sonki mana wata tsiyace kuma da kita zama haka ba miji ai gwara a kiraki karamar zawara"

Gaban mansura yafadi ta dago fuska tana kallon mama hawaye na daf da zubomata tace"mama ba duniyar nakewa ba lahirar nakewa rayuwar ta duniya duk wasa ce lahira itace hakikanin rayuwa ita nake tanadi ba anan ba da bansan kwana ko minti ko second nawa ya rageminba"

Mama ta dan sauko jin ana ambato kiyama cikin sanyin murya tace"to mansura kiduba fa idan yace abiyashi kudadenshi ya zamuyi?"

Mansura tace"Allah zai kawo mafita kuma addua na aiki mama idan mukaita addua se Allah yakawo saukin abin ko yanemi kudin se Allah yakawo hanyar biyanshi"

Mama tace "hmmmm" dedenan kannenta suka shigo suna murna sosai mama ta juya ta fita tabar dakin tanata sakawa da warwara,

Kannenta suka zauna sunata kallon ta suka fara tambayar mike faruwa ganin duk jikinsu ya mutu jiki sanyaye tafadamusu,

Dukkansu sukaita kallonta suna ganin tana wasa da damarta daya takasa hakuri tace"anty ki koma shafa manki wlh koina duk munbi munfada yayarmu zatai aure cikin daula"

Mansura tace"Ku sekuyi nikam aa"

Daya tace"ni wlh baban khalifa ke siyomin da kanshi ko baida kudi sunkare inyana ganina bayajin komi barema kafin sukare wasu sun iso"

Maganar tabawa mansura dariya tanaganin duk basusan ciwon Kansu ba tace"Allah yabaku lpy Ku duka "ta tashi ta fita toilet don ta basu wuri suji dadin gulmarta,

Mama sukuku take tanata tunanin abinda zaije ya dawo,

Yayin da thermocool shima ya rasa natsuwarsa tunanin fuskar mansura ada data yanzu yake kokadan bazai iya aurenta hakanan,

Hjy mnsura ko wasai kamar anzare mata kaya tanata babbadawa abinta batada matsala,

Da baban mansurar yadawo mama ta sanardashi halin da ake ciki tsayawa yayi yana dogon nazari daga bisani yace"Allah yazaba abinda yafi zama alheri"cos duk yadda sukaso da son abun mansura tafisu gaskiya,

Yau da daddare Aliyu yana zaune yana bawa sakeena abinci a baki tanaci tana kallonshi duk yafada a hankali tace"yaya Aliyu munkusa barin asibitinnan kowa ya huta "

Yayi tsaye dabata abincin maganarta ta ta kada masa gaba cos ko yau sunyi magana da doctor cewar dasauranta tanade samun sauki sosai,

A hankali yace "meyasa kikace haka sakeena?"

Tai murmushi tace"zanji sauki ne kafin gobe"

Ya dage gira yana sakin murmushi yace"Allah yakaimu goben mutafi gida amma bazaa barni na sake ba ko?"

Ta dukar da kai tana murmushi ,

Ya debo abincin ya cigaba da bata taci abincin sosai fiye da yadda takeci kullum sannan tace takoshi ya ajiye abincin yabata ruwa da drugs sannan yafara janta labari sunayi kadan_kadan ,

Sega mama ta dawo daga gida ya tashi tsaye zai tafi ya kalleta yace"sakeena seda safe"

Tai murmushi tana kallonshi harya juya ta kirashi" yaya"

Ya juyo ya dawo a hankali tace"nagode"

Ya kalleta yadanyi murmushi yana mamakin godiyar time daya shi da mama sukace"godiyar mi kike?"

Tai murmushi ta juyar da kai batace komi ba ,

Aliyu yayi murmushi ya juya ya fita,

Mama ta zauna kusa daita tana kallonta duk dan jikinnan ya koma saura,

Jinyar me irin lalurar akwai gajiya seda hakuri sosai hakane gun mama ba hutu kokadan dare nayi tafara bacci daga kan kujerar datake zaune sakeena ko idonta biyu bacci ya kauracewa idanunta cikin zuciyarta tunanin iyayenta takeyi da yanuwanta tanajin kamar ta bude ido ta gansu gabanta duka so biyu sukazo ganinta saboda nuna kara da cewa duk dayane datana hannunsu da awurin su mamar ,

Can cikin dare mararta ta rika juyi juyi ba dan kadan ba tanajin matukar azaba ta rika cije lips zufa na karyomata kota ina wani abu takeji yana tunkudo HQ dinta yana fitowa ga wata lema dataji tana mamaye wurin duk dauriyarta takasa tafara kiran "mama!!!mama!!" Cikin muryar wahala,

Mama ta bude idonta ta saukesu kan tashin hankali jini na bin ledar fitsari wani kuwa ya bata jikinta,

Mama ta rafka salati "innalillahi wainna ilaihi rajiun sakeena!!! innalillahi wainna ilaihi rajiun"muryarta da jikinta na matukar rawa ,

Sakeena ta rirrike hannuwan mama jikinta na makyarkyata tanata hada zufa ,

Mama na zubar da hawaye ta janye dasauri ta fita kiran likita gabadaya ba doctor se nurses biyune ke kula da patient din yara da manya da akai admiting suka dawo dakin da gudu mama nata kuka tana innalillahi wainna ilaihi rajiun,

Zuciyar nurse dinma seda ta buga dagani tadade tana bleeding din tafara kokarin ta na tsayar da jinin dasauri ganin aikin seda me temako yasa ta juya ta cewa mama ta kira mata nurse suka dawo tare dakin mama nata kuka sosai takasa barin dakin,

Suka cigaba da kokarin tsayar da jinin bayan minutes sannan suka samu jinin yatsaya still wani na dan zubowa kadan_kadan nurse din mace ta ruga dauko jini sede babu ko Leda daya a asibitin jikinta na rawa ta dawo dakin tana kallon dayan nurse din tace" babu jini a blood bank dama ?naduba babu"

Ya dafe kai yace"dazun akasawa wata jinin "

Hankalin nurse din tashe tacewa mama"mama tana bukatar jini da gaggawa kuma babu anan idan akwai Wanda zaizo yanzu a diba asamata urgently "

Mama tai saurin zuwa ta dauki wayarta yadda jikinta ke rawa zallar tashin hankali seda

Please Login or Register in order to submit comment