Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

in zaizo fira yana zuwa shi kadai,

Tana shiga ya sauke numfashi yana mata kallon soyayya ,

Itama ta kalleshi ta saki murmushi tace"sannu da zuwa"

Ya nata kallonta yace"dear kece?"

Tai murmushi tace"ni ce my dear "

Ya kureta da kallo duk ta rame da wata irin murya yace"nayi kewarki sosai"

Tai murmushi tanamai kallo me kashe jiki tace"nima nayi missing dinka "

Yace"hope wannan karon bazaki bari wani yakara shiga tsakaninmu ba?"

Ta daga kai tana murmushi tace"ni takace dear kai kadai nakeso "

Yace"ko gobe ina iya turowa ko?"yana murmushi,

Tai dariya tace"bayan kwana biyu de "

Yana dariya yace"kinsan a tsorace nake kar amemeta baya na wahala na shiga yanayin rayuwa"

Tai shiru zuciyarta badadi tace"nasani dear kayi hakuri plss"

Yayi dariya yace"alhamdulillah finally zaki dawo gareni"

Ta jinjina kai,

Sukayi shiru sunata kallon_kallo suna sakarwa juna murmushi me sanyaya zuciya,

Faseelat ta fara dauke ido ta kalli time tace"dear zakai late"

Yayi murmushi yace"banason barinki inaji kamar na daukeki mutafi tare"

Tai murmushi tace"ka kwantar da hankalinka ni takace"

Yana murmushi yace"semunyi waya ko and zandawo anjima"

Tai murmushi tace"u r welcome"ta fita yabi bayan ta da kallo nothing change from her sede duk ta rame,

Yanajin matukar farinciki ya wuce office,

Da rana ya dawo gida cin abinci suna cikin cin abincin ta kirawo ya dauka dasauri yakara kunne,

Tai murmushi tace"dear ya gajiyar aiki ?"

Yace"lpy lau dear nadawo gani inacin abinci fatan kema kinci?"

Tace"no but yanzu zanci"

Ya ajiye spoon din hannunshi yameda hankali sosai kan wayar yace"plsss kici abinci dear duk kin rame"

Tai murmushi tace"ba problem na abinci bane kaine problem din dazaran na sameka hankalina zai kwanta"

Yayi shiru yana sakin murmushi,

Su hjy Rukayya nata kallonshi,

Faseelat tace"bye sekazo" takashe kiran

Alhaji yabi wayar da kallo yanata murmushi,

Hjy abida da tsohon ciki ta tashi ta nufi dakinta ranta bace,

Hjy Rukayya ko kallonshi kawai taitayi,

Bayan sungama cin abinci ya kalli hjy Rukayya yace"kiramin abida Ku sameni sama"

Tace"to"ta nufi dakin nata,

Abida na kwance duk yau batajin ta dede hakanan take dauriya Sega hjy Rukayya tazo kiranta ta tashi ta nufi saman tana kumbure,

Bayan sun zauna alhaji na kan seat suna gefe_gefenshi ,

Alhaji yana latsar waya ya dago ya kallesu yace"inason muyi mgna ne"

Duk sukayi shiru sunata kallonshi,

In cool yace"aure zan kara nankusa in Allah yaso"

Dukkansu gabansu yafadi sede hjy Rukayya ko nunawa batai ba,

Yayin da hjy abida seda mararta ta juya,

Ranta bace tace"haba alhaji yanzunnan harwani aure zaka kara duk zuriar da Allah yabaka basu isheka ba se ka karawa kanka wani nauyin"

Alhaji da hjy Rukayya sunata kallonta ,

Tace"to wlh ban yadda ba nasan bawacce zaka auro se wannan tsinanniyar yarinyar data taba zuwa nan me siffar yan'iska"

Ran alhaji bace yace"wai abida meyasa bakinki baya furta alherine ni nafadi wacce zan aurane last time ma datazo kince mata karuwa haba"

Hjy abida tace"to mecece inba karuwar ba wlh baka isaba"mararta takara juyawa ta dafe ciki tai kasan kujera tana nishi tana "ahhh wayyo cikina wayyo cikina"

Alhaji da hjy sukayi kanta tana durkushe tanata nishi alhaji ya rike ta yana "sannu abida ko labour ne sannu" hankalinshi a matukar tashe ya kira nurse,

Ya koma yakara riketa su duk lissafinsu se karshen wata zata haihu gashi tana labour,

Hjy Rukayya ma nata mata sannu hjy abida kuwa nata murkususu can zuwa se faya tafashe ruwa yayo waje,

Hankalin alhaji tashe yace"haihuwa ce ciremata pant dasauri "

Ya rike abida da dubara hjy Rukayya ta cire mata pant din,

Hjy abida ta na duke tanata nishi da hada zufa ta rirrike seat yayinda hjy Rukayya da alhaji ke rike daita suna mata sannu ,

Bayan mintoci babyn tataho hjy Rukayya ta amsheta tanata tsanyara kuka "inya !!!inya!!!"

Dedenan nurse ta iso ta amshi jaririyar ta fara kimtsata hjy abida na duke tanata zufa mahaifa tafado nurse tazo ta dubata tai mata dinki don tasamu karuwa sosai yarinyar kuwa kosassa daita me lpy,

Alhaji nura ko yana rungume da jaririyar daketa kuka yana rirrigata yana mata kallon kauna sosai yake cikin farincikin haihuwa yarinyar fari tas daita ya yinda duk kamannin nata na jamil HQ ne.
[1/25, 8:02 PM] SHALELE😍: 69

Bayan angama kimtsa su nurse ta rubuta mata drugs ta tafi,

Hjy abida tai kwance kan bed din alhaji tana hutawa ,

Itako hjy Rukayya ta fita ta nufi dakinta domin hadamata ruwan zafin wanka,

Alhaji ya meda kallonshi wurin hjy abida idanunta lumshe zuciyarta na zafi wai wadda ta kwada mata mari itace alhaji zai auro shikenan tazama bora yar kallo ,

Alhaji nata murmushi ya matsa ya zauna kusa daita yace"sannu abida"

Ta bude ido ta watsa mai harara ta medasu ta lumshe,

Yana murmushi ya kanga babyn yace"kibude ido kiga kyautar da Allah yabamu"

Zuciyarta ta yanke tafadi jin furucinshi ta bude idanu ta dorasu kan babyn da keta kuka,

Yana murmushi yace "ki amsheta kibata tasha"

Zuciyarta badadi ta tashi zaune ya dora mata diyar tabata nono takama tafara sha,

Hjy abida ta kureta da kallo sak jamil yadda take tsotson ya tuno mata ubanta jamil ta dago ta kalli alhaji yanata faraa yace"kinganta me kyau kamarki"

Ta harareshi ta dauke ido,

Cikin rarrashi yace "abida ki kwantar da hankalinki aurena bayana nufin rabuwa dani ba inason kara raya sunna ne amma kinsan inasonki sosai kece tauraruwata"

Abida tace"yi shiru alhaji base kace komi ba wlh yanzu haka bawacce kakeso cikinmu kamarta yanzu inta shigo yakenan ?dama tafadamin seta fiddani gidannan to kabani takardata tunyanzu don bazan dauki raini ba"

Alhaji na mata wani kallo yace"faseelat ba haka take ba tade fadane kawai amma ba abinda zai faru kuma kinsan bazan iya rabuwa dake ba ni duk inasonku gabadaya bawacce zan iya rabuwa daita"

Tace"hmmmm!!"ranta bace ta rasa ma abun fada,

Ganin yarinyar tadena Jan nonon ta janye ta meda a riga,

Alhaji ya mika hannu ya amsheta yanata kallonta ya dagota sama da niyyar mata huduba,

Abida tace"jira wane suma zaka samata?"

Alhaji yayi shiru murya sanyaye yace"faseelat "

Hjy abida me zatai ba dariya ba dariyar takaici da ganin ya rainata ta tsagaita tace"wlh bade diyata ba kabari seka aureta inta haihu seka sawa yar sunan uwar karshen soyayya kenan bani diyata"ta mika hannu,

Alhaji nata kallonta yayi karamin murmushi shide yasoyiwa faseelat takwara,badon ranshi yaso ba yace"wane suna kkso?"

Tace"suhailat"tana jefamai harara,

Yace"Allah yarayamana suhailat"yafara mata huduba bayan yagama hjy Rukayya tazo takama hjy abida ta kaita dakinta ta shiga wanka,

Ta dawo alhaji yanata kallon yarinyar a ranshi yana tunanin cikin dangi yarinyar ta dauko hjy Rukayya tazo kusa dashi zata amsheta tai mata wanka ta leka fuskar yarinyar da murna tace"me kyau daita tubarkallah"

Ya dago da murmushi yace"saura ke"

Tai karamin murmushi tace"ni ai nagama sede muyi fatan Allah yarayamana Wanda yabamu"

Yace"ameen "in cool yace" bakice komi ba akan auren"

Tai shiru nazarinta shi bai damu da mace ba amma zai karo wata itama duk bukatunta zai rataya kanshi don de baxata iya masa wannan maganar ba,

Yace"kinyi shiru"

Tai murmushi tace"Allah yasa alheri yabada zaman lpy yabamu hakuri da juna amma akwai matsala zama da abida daita yadda na lura duk basu da hakuri gaskiya"

Alhaji yace"problem din abida ne shiyasa banan zan kawota ba zan zabi cikin gidajena amma faseelat batada matsala"

Hjy Rukayya tai shiru tuno yadda faseelat ta kwadawa abida mari tace"kawota nai mata wanka"ta amshi diyar ta fita,

Yayi shiru yana nazarin yadda abubuwan zasu kasance nangaba,

Abida na fitowa wanka ta kira jamil ya dauka yace"my sugar ya babyna?"in sexy tone,

Tai murmushi tace"nahaihu na haifi kyakkyawa kamarka"

Yayi ihu yana murna yace"nagode sugar da kika haifi jinina naji dadi sosai tnx u Allah yabaki lpy ya babyna tana lpy?"

Tace"suhailat na lpy sede nice I'm not fine na wahala harda stitches akamin"

Yace"oh God "tare da dafe goshi yace" ki kula sosai ki warke da wuri muhadu inga yadda twins dina suka kara cika naga gudan jinina tsokata"

Tace"tom"tana faraa,

Yace"ki turamin pic din baby naji kince suhailat ko?"

Tace"eh inason sunan "

Yace"nice name turomin ita naganta"

Tai murmushi takashe kiran ta fara shafa can Sega hjy Rukayya da baby tasha makeup tazo ta kwantar daita tana murmushi tace"bari naje nakawomiki abinci nasa aimiki farfesu da kunun shuwaka"

Abida tai murmushi tace"nagode mommynsu"

Hjy Rukayya ta fita bayan ta fita tadauki pics din ta turawa jamil ,

Jamil ya haukace yayita murna yayi diya yanajin mugun sonta,

Alhaji tuni yayi waya ahadamai kayan baby da kuma kayan suna kuma ayi akwati biyu na hjy Rukayya,

Da dare yanata farinciki yayi wanka ya saka kaya yayi kyau ba laifi ya nufi gidansu faseelat seda yatsaya ya siyemata kayan makulashe dayasan tanaso sannan ya karasa,

Faseelat na kwance kiranshi yashigo ta dauka a hankali tace"dear shiru inata jiranka"

Yayi murmushi yace "kiyi hakuri ina kofar gida yanzu haka"

Tana murna tace"ganinan fitowa"ta saka after kan kayan baccin jikinta ta fita,

Tana shiga motar ta cika da kamshinta,

Alhaji yace"I'm sorry nayi late "

tanawa alhaji kallo me karya garkuwar jiki tace"kasa duk hankalina ya tashi harna fara kuka"ta karasa tana dariya,

Yayi dariya yace"I'm sorry inatason tahowa abubuwa suka rikeni nasamu karuwa a gidana"

Faseelat tace"alhamdulillah!!" tana murna tace"mace ko namiji?"

Yace"kune akasamu"

Tai murmushi tace"gaskiya ina murna sosai Allah yarayamana diyarmu akan sunna "

Yace"ameen"

Suka cigaba da firarsu ta masoya bayan lokaci ya fiddo ledar shopping ya mika mata yace"kayannan sunyi missing dinki nima nayi missing siyosu wani time bana hakura harse nasiyo su na rabawa yara"

Ta amsa tana murmushin jindadi tace"nagode sosai dear Allah yabarmu tare harabada"

Yace"ameen seda safe ki kula da kanki kuma kiyi mafarkina"

Tai murmushi me sauti tace"kayi nawa kaima good night "ta bude ta fita kamar kullum seyabi bayanta da kallo saboda yadda yake matukar shaawar jikinta tuno wani yayi amfani daita not once yasa murmushin fuskarshi ya bace ya girgizakai yanajin kishi ya tada mota ya koma gida,

Yana shiga bangaren abida ya nufa tana kwance tana waya a sannu itada angon karni jamil shigowarshi yasa takashe wayar tana bin jikinshi da kallo ansha gayu dagani daga zance yake,

Yana faraa ya matsa yace" abida ya jikin?"

Tace"naji sauki"fuskar ta daure,

Yace"sannu "ya dauki babyn ya mata kiss ya fita ,

Tabi bayanshi da harara tanajin mugun haushinshi ta dauki waya ta kira jamil suka cigaba da firarsu,

Bayan two days

Tunda faseelat taji abida ta haihu tasa ran zuwa donyi mata barka tana fatan sudedeta nangaba ,

Rabia ta rakata sukayo akwati karami daya na kayan baby da laces guda biyu masu tsada 30k duk daya,

Akwatin cike suka dawo gida ta shiga dakin Ummi ta ajiye kayan tana dan murmushi tace" Ummi kinga kayanda nasiye zan kaiwa Matar alhaji data haihu"

Ummi ta kalli kayan tace"kinyi kokari ko Allah yasa alheri Nide fatana faseelat kiyi aure ki zamanki gidan mijinki injiki shiru yafimin kwanciyar hankali"

Faseelat tace"insha Allah Ummi nida alhaji se mutuwa kiyi hakuri "

Tace"to Allah yasa donni lamarinki akwai tsoratarwa nan kika ki alhajin kk zabi fahad kuma kindawo alhajin Allah yabaki ikon hakuri"

Tace"ameen anjima kadan da laasar zamu tafi barkan nida rabia "

Ummi tace"Allah yakaimu"

Faseelat ta tashi tafara shirin tafiya,

Tayi simple makeup ba jagira bakomi se lip glow da powder tasaka doguwar riga milk ta yafa bakin gyale tana cikin shiri rabia ta shigo domin Dole taje barka harda tsarabar kayan baby nata tayi,

Faseelat ta karasa shiryawa suka fito ta fiddo mota zasu tafi Sega roshni tai parking ta fito ta leka motarsu tace" ina zuwa haka ina shigowa kuna fita?"

Rabia tace "matar alhaji ta haihu zamuje barka"

Roshni tace"bari na rakaku semu dawo tare inason muyi mgna da amaryar alhaji nura"

Faseelat tai mata wani kallo suna dariya tashiga suka tafi,

Bayan sun isa har ciki suka shiga da mota faseelat tai parking suka fito rabia taja akwati itako roshni ta rike Leda suka nufi ciki,

Suna zuwa falon da akwai mata harda diyan alhaji nura da yayiwa aure hjy Rukayya naganin faseelat taganeta tana murmushi tace"maraba Ku zauna maraba"

Su faseelat suka zauna suna dan murmushi suka ce "ina yini?"

Hjy Rukayya tace "lpy lau"

Sukace"ansamu karuwa Allah yaraya"

Hjy Rukayya tace "ameen ameen sannunku angode"ta tashi ta nufi part din hjy abida don ta Sanar mata anzo ganin baby,

Hjy abida ko tana wanka ta dawo tana dan murmushi tace" kushigo"

Suka tashi suka nufi dakin abida suka zauna saman kujera hjy Rukayya ta dauko babyn roshni ta amshe tanata kallon yarinyar,

Duk suka dukufa kallon baby,

Suna cikin haka abida ta fito daga wanka kallo daya tayiwa faseelat taji kamar taje ta shakareta tai wurinsu dasauri donta amshe diyarta da suke ta ma kallon kurilla,ta karaso gabansu tana huci ta wafci diyarta duk suka dago suna kallonta ,

Ran hjy abida bace ta kalli hjy Rukayya tace"mommy donme zakibawa yaniska diyata irin Wadannan ko hannunsu bazakaso su taba danka dashi ba"

Faseelat ta matse lips yayinda su rabia keyiwa abida kallon mahaukaciya,

Roshni ko taji haushin Kalmar saboda yarinyar hannunta take,

Hjy Rukayya tace"haba abida be kamata kina haka ba barka fa sukazo kiyi hakuri arabu lpy"

Hjy abida tace "barkar munafunci sun kwaso kafa gulma daganin kwamne kawai"

Ta kallesu tana hararansu tace"seku tashi kutafi idan kungama abinda yakawoku"

Roshni taja tsoki tace"sakarai dake in aka ganki kamar wayayya amma katuwar yar kauye ce inba jahilci ba ai anbar irin wannan kishin yanzu"

Faseelat tai saurin mikewa ganin zaa memeta baya rabia ma ta mike tanason tofa albakacin bakinta tai shiru,

Hjy abida ranta bace tace"duk siffofinkune kika fada marassa kamun kai yan tasha anyi kwantai ba mashinshini shine aka likewa alhaji wlh kiyi gaggawar komawa inda kikafito don alhaji yafi karfinki"

Ran faseelat bace taja roshni dake jin kamar ta dauke hjy abida da mari,

Rabia tabi bayan su bayan tagama watsawa abida harara wai sun rasa mashinshini,

Harsun kai kofa hjy abida na tsaye rungume da yarta tace "wa kuka barwa wannan matsiyatan kayan kuzo Ku kwashesu kuyi gaba da abinku idan kunason badasu inda zaai murna kukaisu gidan iyayenku matsiyata"

Dukkansu suka juyo faseelat jitakeyi kamar ta tsaya tai mata Tass duk da haka ta bude kofa tafita su roshni ma duk suka fita suna kallonta,

Bayan fitarsu Hjy Rukayya data rike gemu ta nata kallon abida tace"abida baki da hakuri ko miskala zarra ,meyasa kk hakane ?sunzo barka suga diya su tafi miye aciki"

Abida tace"in barka zasuyi suje suyiwa alhaji bani ba data gama dallawa mari"tana gama fada ta juya ciki da diyarta rungume,

Hjy Rukayya tabita da kallo sannan ta fita itama ranta bace saboda abinda hjy abida tayi,

Su faseelat na barin kofar gidan motar alhaji ta karaso yabi tasu da kallo ganin motar faseelat hankalinshi ya tashi ya fito ya nufi cikin gidan dasauri yasan baxaa kwashe lpy ba,

Yana shiga ya nufi dakin abida dede ta fito ta jawo akwatin kayan kiiii zata kaishi waje,

Yana mata kallon mamaki yace"wannan kayan fa"

Tace"bansani ba nafada masu niba matsiyaciya bace dazaa kwaso tsumma akawomin"

Ya kalli kayan yace"ina zakije dasu?"

Tace"waje bola zaakaisu nanne dede su don wlh suhailat bazata saka kayanba and ni ba zan ko bawani su ba akaisu bola mahaukata su tsinta"

Alhaji nura yayi tsoki ranshi bace yace"anji kawo idan bakiso akwai masu sawa kuma karyarki kicewa kayannan na matsiyata idan bakiso ba dole "yaja akwatin daga hannunta,

Ya kwashi ledar kayan rabia ya fita,

Yana fita tai tsoki tace"inba iskanci ba ni zata zowa barka tariga tagama shanyeka tagama bude maka kafa tun a titi se rawar kai kake kamar zaka auro kayan kwarai"tana ta masifa ta koma wurin yarta ta rungume,

Alhaji na fita ya nufi part din hjy Rukayya ya shiga tana zaune tare da haseena suna labarin aurenshi,

Ranshi bace ya mikawa haseena kayan yace" kisawa baby"

Ta amsa tace "nagode daddy"

Hjy Rukayya taga ranshi bace tace"kayi hakuri dan Allah "

Yace"abida bata da kirki wlh ina laifin Wanda yazo maka murna"

Tace"eh kayi hakuri kasan masu jego akwai daukar abu da zafi"

Yace"ita haka dama take kuma ni bazan laminta ba"

Tace"kayi hakuri"

Yanajin sauki_sauki hakurin da take bashi yace "kizo ki serving dina" yawuce dakinshi,

Haseena ta kalli mommynsu tace"wai meyasa small mommy take hakane tasan bai lpy"

Hjy Rukayya tace "inta karasashi aita huta tunda auren yakeso ai duk tsiyarta seyayi" tana gama fada ta tashi ta fita,

Haseena tai shiru tana kwatanta hakurin mommynsu ko rabinshi bazatayi ba ko itace akazo zataji badadi sede bazatai wulakanci ba amma yadda ta lura kamar mommy bataji komiba dukda itama badadin a ranta,

Faseelat suna cikin mota roshni se tsoki takeyi duk bayan second,

Rabia tace"ai inaji ko batare da kowa ba sena dawo gidannan sena meda mata mgna saboda muba kwantai bane se mun darje"

Faseelat na driving ranta bace amma tace"dan Allah kuyi hakuri kuba kusan yadda takeji ba ku kyaleta kawai ita tasani nataba fuskantar hakan time da naji ni a matsayin Amarya ba uwargida ba"

Rabia tace"yama zaki hada ninasan wlh bazaki wannan wulakancin ba don budurwar mijinki tazomiki barka an daura aurenne ?ta jira a daura mana ke daita ce hakan yafaru da tuni ta kone kun"

Faseelat tace"Nide kuyi hakuri plss tawuce bazan kara zuwa gidan ba saboda kar rayuka su baci yauma nayine saboda alhaji amma tunda naga kullum matsala zuwa na ke kawowa nadena gabadaya"

Roshni ta jinjinakai tai shiru wai ita zaa kira yariska?tabbas yariskar ce kuma zata nunawa abida hakan,

Bayan sun isa sunata labari harsun manta sunata dariya alhaji dayaga ma cin abinci be hutaba yayo gidan,

Yana zuwa ya kirata ta dauka tare da cewa"my dear"cikin salo,

Ko murmushi yace"ina kofar gida"

Ta tashi zaune tace"OK ganinan"ta dauki gyale ta fita,

Tana fita taganshi ranshi bace cikin sanyin murya tace"my dear yana ganka ranka bace?"

Fuskarshi bawalwala yace"kiyi hakuri dear banji dadin abinda hjy abida tai ba kiyi hakuri plss"

Faseelat tai murmushi tace"ai batai komi ba munje da friends dina mun mata barka muka dawo"

Yayi karamin murmushi yace"eh but nasan halinta kiyi hakuri saboda ni ana fada miki kalamai marassa dadi"

Tai murmushi tace"bakomai my alhaji kasaki ranka ko zanji sanyi a raina"tana mai kashe masa ido,

Alhaji ya saki murmushi tare da ajiyar zuciya yace"haka yayi?"

Tai dariyar dake sashi shidewa ta jinjina kai tace"harnaji sanyi"

Ya nata kallonta yace"nagode amma dear haryanzu bakice komi ba "

Tai shiru sannan tai murmushi tace "ko da wane lokaci katuro na kagara na ganmu muhalli daya"

Ya saki murmushin jindadi yace"nagode aikuwa cikin satinnan zanturo dear nakagara na mallakeki"

Tai murmushi tace"su rabia na ciki zan koma"

Yace"OK kigaidaminsu especially rabia"

Tace"zasuji bye se gobe"

Ya bude baki yana mata wani kallo yace"zan dawo anjima "

Tai dariya tace"sekazo"ta fita ta rufe motar tashige gida,

Ya sauke numfashi yanajin sonta yana yawo cikin bargon jikinshi ya tada mota ya nufi gida,

Bayan ishai ya omer yazo faseelat taje dakin kanta kasa tace"Ummi alhaji yanason turowa... maganar aurenmu"tanayi kanta duke,

Omer yace"kice yaturo kuma wlh idan kk kaso auren nan se ranki yayi mugun baci kisani kedashi harabada"

Ta kalli ya omer tace"kuyi hakuri Yaya dan Allah kubar tuna baya"

Ummi tai karaf tace"gwara ya fadamiki ai saboda ke bakisan ciwon kanki ba"

Tai shiru,

Omer ya kalli Ummi yace "sati daya dall zaa sa bikin suyita tafiya yadena zarya anan ba dare ba rana"

Ummi tace"ka kyauta ko"

Faseelat ta tashi tana murna ta fita ta haye bed ta rungume pillow burinta kenan ayi bikin taganta tare da alhajinta zata mallakamai komi yayi yadda yaso daita,

Bayan kwana ukku alhaji ya turo neman aurenta akabashi ita kudin neman aure million daya zaai biki sati na sama ran Saturday,

Bayan wadanda suka nemo masa auren sundawo masa da labari medadi yana murna ya nufi gidansu faseelat,

Ta fito da hijab jikinta tadorata kan kananun kaya tanata kamshi,

Yana binta da mayen kallo kamar ya hadiyeta yana farinciki yace"alhamdulillah dear next week iwar haka kinzama matata I'm very happy "

Tanata murmushi ba karamin dadi takeji ba ta rufe fuska,

Ya nata binta da mayen kallo yace"wait wait ina kikeso muyi honey moon dinmu USA ,India ,China ,France, ko ina"

Tai murmushi ta girgizakai tace"madeena a can nakeso"

Ya jinjina kai yace"babban birni kenan insha Allah a can zamuje muyi honeymoon dinmu wata daya"

Ta kalleshi tace"har month kamar yayi yawa"

Yace"ni kuwa kamar yayimin kadan"

Sukai dariya tare suka fara shirye_shiryen inda zasuyi event da yadda komi zai tafi,

Daganan su faseelat suka fara shirye_shirye again wurin maman mujaheed ta siye kaya sabida wadancan sunyi amfani sabida tana jin sauyi sosai a jikinta niima kowane time ta cigaba da using (kunemi kayan maman mujaheed test and truth ba tsada se amfani👌)

Ummi ma seda takawo tata gudumawar,kuma kullum seta fita gyaran jiki domin rikita alhaji,

Su faseelat suka fiddo ankon atamfa purple da fari wacce zasuyi dinner,

Cikin kwana ukku alhaji ya hada lefe nagani na fada akwati ashirin da hudu reras yayinda yayiwa su abida set daya guda hudu ya kuma ba kowace million biyu suyi hidima abida duk hankalinta ya tashi bata tsaye bata zaune yayinda hjy Rukayya ba ruwanta yadda alhaji ke dokin gwara ayi ko hankalinshi zai kwanta,

Ita kuwa Amarya 5millions ya damka mata tai hidimar bikinta,

Wanshekare akai suna akasawa yarinya suhailat kamar yadda takeso sannan sukasha party a wani hall ,

Su friend din faseelat sunta zarya ganin lefe gashi yabasu Million daya suyi abinda zasuyi dasu zainab aketa hidima,

Yayin da invitation keta yawo na auren alhaji segashi office dinsu fahad sabeer ya dauko yakawoshi wurin fahad a office dinshi ya ajiye mai kan tebur,

Fahad ya dauka yana kallon sabeer ya karanta invitation din yana nazari da akwai alamar tambaya sosai faseelat tace auren dole zaai mata dashi batasonshi segashi kuma taje gidanshi sannan last ta fito daga motarshi tana kuka yanzu kuwa zata aureshi akwai alamar tambaya meyasa tana sonshi ta zabeshi?

Sabeer na kallonshi yace"badadi ko?"

Fahad ya kalleshi yayi tsoki yace"to miye ai ba abun mamaki bane"

Sabeer yace"kafada de kayi loosing seka shirya zuwa daurin aure da dinner"

Fahad ya rika jefamai wani kallo,

Shi ko ya tashi ya fita yana dariya baiga dalilin da zaisa ya saki faseelat ba yadda take nunanna dagani zatai dadin sha,

Fahad ko kasa yin komai yayi ,yayi shiru yana tunani gabadaya ya rasa kanshi wani iri yakeji,

Bayan 3 days


Yau daurin aure gabadaya alhaji be runtsaba saboda murna tunjiya yake tarbar baki daga kasashe dake fadin duniya yana cikin mugun farinciki kamar me,


Itama faseelat murna tanata washewa tasha gyara skin dinta lubus simul tasha kunshi da kitso ,

Da misalin karfe 1:30

[1/26, 6:32 PM] SHALELE😍: 70


Da misalin karfe 1:30 aka daura auren alhaji nura da gimbiyarshi faseelat akan zunzurutun kudi million 1 ,daurin aure ne daya samu halartar manyan mutane masu kudi da fada a ji ,

Alhaji farincikin da yake ciki baya misaltuwa kai daganin fuskarshi zaka sheda hakan yanata faraa abinshi yayi auren soyayya da duka matanshi amma se yakejin wannan dabanne,

Su faseelat gidansu zainab suke setting se washewa take abinta a kagare take su mikata gidanta,

Bayan daurin aure anyi reception kowa ya tafi anata shirin fita dinner karfe 5 ,alhaji ya dan samu sarari wurin karfe 3 ya nufi gidansu zainab,

Yana zuwa yayi parking nesa da kofar gida ya kira number faseelat ,

Faseelat na zaune da daurin kirji kawayenta nata kara dirjeta da dilka da turaruka don taji dadin zautashi kiran ya shigo daf zai tsinke ta dauka da farinciki tace"mijina"

Alhaji ya saki murmushi me sanyaya rai yace"matata inafatan kina lpy?"

Tace"uhmm"tana jin mugun dadi,

Yace"ok gani kofar gidan setting kifito inason ganinki"

Ta kalli jikinta tace "ayya sorry dilka jikina"

Yace"dilka ?duk kyawunki plss and plss kidena ba kanki wahala kina da natural kyau da komai"

Tai dariya tace"nadena dear kayi hakuri sai anjiman"

Ranshi badadi yace"a kagare nake naganki"

Tace"me too plss kayi hakuri anjima kadan"

Yace"OK kushirya da wuri bye"ya kashe kiran ya sauke huci ba don ransa yaso ba ya tafi,

Itako yana kashewa taiwa wayar kiss duk suka dau shewa kasancewar ba auren fari bane se abubuwa suke ba kunya,

Karfe 4:40 motoci suka fara fakawa kofar gidansu zainab yayinda faseelat sungama shiri,

Da rabia da zainab ne suka fito daita yayinda wasu suka rike gownt dinta dake jan kasa,

Suna doso motar da alhaji ke ciki ya kureta da kallo ta glass wani friend dinshi ya bude suka sata gidan baya ita da alhajinta sannan suka rufe suka nufi motocin da zasu shiga,

Tunda ta shiga motar tunanin alhaji ya tsaya ya kureta da ido yanajin kamar ya jawota ya rungume ta hadu karshe ga kamshinta me rikita maza,

Itako ta cikin net dake rufe da fuskarta take kallonshi tana sakin murmushi,

A hankali ya matsa ya dage net din fuskarta ta sakarmai wani murmushin da yasashi sakinshi dasauri yana meda numfashi,

Ya dade yana meda numfashi yana hamdala sannan ya kama hannunta daya ya rike hannun very soft ,

Bayan kowa yagama hallara suka nufi hall ,

Hall din cike yake da manyan mutane maza da mata yayin da hjy Rukayya da diyanta duk sunzo amma banda abida tana gida kwanciyarta bakinciki kamar ya kasheta,

Gefe daya ga securities na ta yawo,

Suna isa aka bude musu suka fito still yanmata suka kama long rigarta suka rike, hannunta cikin na alhaji suka nufi cikin hall din yanmata na gaba yayinda friends dinshi ke baya,

Suna shiga akai playing wani love tone

Please Login or Register in order to submit comment