Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jamaa ba bacci su Umma da kannenta sunata kuka,

Gidansu amisha anty batool kadaice takasa zaune takasa tsaye tayi nan tayi can hankalinta tashe tana matukar tausayawa amisha kuma tana tsoron farkawarta da neman jawabi wurinta da polices zasuyi da tsayuwarta kotu,

Iyayen shareef ko banda kuka ba abinda sukeyi tuni suke asibitin suna kai kawo basu san miye makomar dan nasu ba

In the morning.......



(Zakaita iya boye laifukanka don tsoron dumin mutane da zubewar mutunci kowani abu daban amma in Allah yaso seya bankado asirinka kowa yasani in yaga dama yana iya bari se bayan ranka sannan ya tona maka asiri kana kabari wasu na tsinemaka wasu na neman tsari da irin halinka very few ne zasu nema maka gafara kasance me aikata aikin kwarai koda yaushe).
[2/4, 10:31 PM] Maman Mamy: 80



Tunda sassafe iyayensu Mimi da Jameela sukaje amsar gawarwakin yayansu domin kaisu gidajensu na gaskiya ,

Bayan angama bincike kan gawarwakin akabasu suka tafi dasu akai musu salla aka kaisu makwancinsu,

Daddyn Mimi na cikin tashin hankali sosai yana ganin laifinsa da Mimi na gabanshi yana kula daita da movement dinta da batayi irin wannan rayuwar ba don soyayyar hjy bazata bari ta mata tarbiyya yadda ya kamata ba gashi suntafi lokaci daya ba hjy ba mimin mutane nata dandazon yi masa gaisuwa ya nufi asibity wurin shareep domin ya riga yayafemai shareep yana girmamashi sosai yabashi diya ya amsa hannu biyu duk da bata gari ba yanzun wannan tsautsayin bai kamata yasha wuyarshi ba,

Idon shareep biyu ya farko baya um baya um_um sama kadai yake kallo jefi_jefi hawaye masu zafi na bin fuskarshi yanzu shikenan Mimi ta tafi? Ai bai harbeta ba koda zai harbeta bazai kasheta ba yanzu shikenan ta mutu tabarshi kuma shi din yakashe rayuka har biyu wai meyasa yayi haka? Yake tambayar zuciyarshi yana cikin danasanin kashe Mimi ,

Daddy ya shigo dakin ya zauna gefenshi,

Shareep ya rumtse ido yana jin kunyar daddy ya zabeshi cikin maza dubu amma memakon ya rike masa yarsa da daraja seya kasheta,

Daddy yace "son ya jiki?"

Shareep baice uffan ba idanunshi suna zubar da hawaye ,

Daddy ya share hawaye yace"kayi hakuri nasan babu dadi sosai amma naso ka danne zuciyar ka baka dau irin wannan hukuncin ba,na yafemaka shareep insha Allah bazan bari ai maka tsatstsauran hukunci ba "

Shareep ya bude ido yana hawaye yace "I want to die too banason cigaba da rayuwa cikin kunci I'm in so much regret ban harbeta ba daddy ba ita na harba ba"

Daddy yace"its OK Mimi ta riga ta mutu ni nariga na yafemaka da zaniya da bazan bari ai maka komi ba sede ko iyayen dayar yarinyar kayi hakuri"

Shareep ya cigaba da hawaye daddy na zaune ya tashi ya fita zuciyarshi na ciwo ya nufi police headquarter yaje yafadamusu shifa yayafe kisan diyarsa suka shaidamai shareep me laifine se hukuma ta hukuntashi koda yayafe bare ba ita kadai ya kashe ba ya kashe jameela da jikkata amisha,

Ba yadda daddy yayi ya hakura ya koma gida yana cikin tarin bakinciki,

Da rana uncle ismaeel ya iso suka nufi asibity tare da anty batool baiji dadin samunta gida ba duk da itace tafada mai amisha ba lpy sukaje asibitin har time din amisha na kwance batasan ina kanta yake ba ganinta da breast guda yasa anty zubarmata hawaye na tausayi uncle yakara rikicewa ya fara neman yadda zaa fiddata waje domin dubata,

Dakyar ya samu damar fita daita bayan cuku_cukun gaske suka nufi Australia daita tare da jamian tsaro,

Suna isa aka amsheta aka fara neman hanyar ceto rayuwarta ,

Shi ko Khalil kamar marar lpy yake yau yakasa zuwa gidan su mansura saboda tashin hankalin mutuwar jameela ,

Da marece sosai roshni da tagama sace zuciyar jamil HQ sunata holewarsu ya kawota kofar gidansu faseelat,

Ta bude kofa zata fita ta juyo tana kallonshi tana yaushi tace"my kazo ka daukeni nan da 1hr mu wuce"

Jamil HQ yana lumshe ido yana jefamata sexy look lips dinshi cikin baki yana tsotsar na kasan yace"OK sweet da zaran kingama just give me a call"

Ta lumshe ido ta turo lips tai masa kiss batare da ta dora lips din jikinshi ba ta bude ta fita,

Jamil ya kwantar da kai jikin seat ya shafi gashin kanshi yana cije lips yana mugun jindadin muamala da roshni ya tada mota ya tafi,

Roshni ta shiga gidansu faseelat, faseelat na zaune tana Jan casbi cikinta kawai take kallo tana matukar farinciki duk time daya motsa ko da alhaji ya mutu zata rika ganin jininshi tare daita, sega roshni ta dago fuska tana kallonta da murmushi tace"yan mata"

Roshni tai karamin murmushi tana jin tausayinta Allah yaga zuciyarta ba haka taso ba so tayi ya saki abida bawai yafadi ya mutu ba abun haushin ma ko sakinta baiyiba bawanda yasan komi akan diyar daba tashi ba takara tsoki tana rike da abida seta dandana gudarta dama kawai take jira,

Ta zauna kusa daita tace"maman biyu ya nauyi?"

Faseelat tai murmushi tace"ba nauyi kice ya baby na"

Roshni tai dariya tace"to ya baby na? Nifa na kagara ki haihu "

Faseelat tace"seki bari time din ya cika hjy"

Sukai dariya tare roshni tace"dama cewa nai bari na zagayoki naga lpyarki"

Faseelat tace"nagode ina lpy "

Roshni tace"rabia fa?"

Faseelat tace"Amarya zakice tana busy shirye_shiryen biki"

Roshni tai yake tana kara tausayawa faseelat,

Ummi ta shigo tana murmushi roshni ta gaidata,Ummi tace"faseelat omer ke tambayar me zakici?"

Faseelat na murmushi tace"kifi Ummi idan yakawo kar a soya ki gasaminshi "

Ummi tace"to kuma na kwadamiki zogala akawo?"

Faseelat ta gyada kai a hankali tana matukar jindadin yadda umminta ke kula daita da abinda ke cikinta da ya omer shima kullum cikin yi mata hidima yake,

Ummi ta fita ta dawo da kwadon zogalen yaji kuli da veggies da kwai faseelat tasaka spoon tafara ci jikinta sanyaye ta kalli roshni tace"kici"

Roshni tace"wannan seku manya"sukai dariya

Ta kira jameel yazo ya dauketa suka nufi hotel inda zasu kwana yau shide jamil dangata ya taso, yayi abiyashi but yanzu abun ya juya yayi ya biya roshni nata kwalkwalar abunta,

Bayan 2 days kwana ukku kenan sannan amisha ta farko a firgice tana matsanancin kuka zafin da takeji bazai misaltuba ji takeyi kamar taje lahira ta dawo bata tsammanin rayuwa bakinta abinda yake fada shine "uncle uncle dan Allah kayafemin " tana ganin yafiyarshi ko ta mutu kila ta samu sassauci tadade tana lalata da matarshi da danshi shida ya mata favor ya daukota daga gidan marayu ya kawota gidanshi,

Anty duk ta hirgice tana bata hakuri tayi shiru bayan ta lafa uncle ya shigo dakin ta kalleshi tana zubar da hawaye idanunta jawur,

Uncle idanunshi cike da hawaye yace"sannu amisha"

Amisha tace"uncle ka yafemin dan Allah mutuwa zanyi "

Ya girgizakai yace"meyasa amisha ?meyasa zaki rikabin mace yaruwarki Meyasa? I was thinking that idan kingama school na hadaki aure da taufeek but kinje kina aikata nonsense "sam baigane hakurin me take bashi ba,

Hankalin anty batool yayi mugun tashi jin wai zai hadata da danta bazaiyuba amisha na niyyar magana tai saurin rufemata baki tace" kiyi shiru harkisamu lpy aikine jikinki"

Dole amisha tai shiru tana kara tsanar kanta tana kuma jin tsanar anty cos duk laifintane,

Uncle ya juya ya fita ranshi bace ,

Amisha ta cigaba da hawaye ,

anty ta cire hannunta fuskarta hade tace"ki rufawa kanki asiri kiyi shiru idan bahaka ba zai zare hannu cikin lamarinki kingane"ta tashi tabi uncle dasauri tadesan yanzu bayadda zaai ya hada danta dame nono daya,

Amisha ta cigaba da kuka a hankali ta dora hannu inda take jin muguwar azaba ta jishi shafe rufe da bandeji tafara sabon kuka me tarin bakincikin rasa breast dinta daya,

Wanshekare aka sallami shareep aka meda shi cell aka tsareshi harse amisha ta warke domin itace babbar shedar fadin kome ya faru shi kuwa yanata fadin shine amma duk da haka ana jiran amisha,

Cikin cell yake amma yana samun baki manya_manyan mutane na zuwa wurin shi dakinshi komi akwai abinci se anzo tambayarshi me zaici but baya bukatar abinci yadda yakejin rayuwarshi mutuwa kawai yake tsammanin hutunshi ,

Da marece Khalil da ya dan farfado daga jimamin mutuwar Jameela yaje musu gaisuwa har hjy seda yakai tai musu tanata kara godewa Allah da yasa Khalil ya rabu da Jameela kafin mutuwarta ,

Ya nufi gidansu mansura karo na biyu,

Mansura ta fito ta gaisheshi ya amsa yanata murmushi batako damu da yawaita kallon fuskarshi ba fuskarta hade tace"dan Allah Khalil karka sake dawowa gidanmu karka hadani da iyayena kaje can kasamu dede kai ni baajinka bace irina bata kamaceka ba"

Ya hade hannuwa wuri daya kamar zaiyi kuka yace"dan Allah kiyi hakuri mansura wlh ina tsananin sonki rasaki babbar asarace gareni"

Ta kalleshi tace"nafadamaka kadena zuwa se anjima"ta juya ta wuce cikin gida,

Khalil yabita da kallo ya dade tsaye sannan ya shiga mota ya tafi gida makoshinshi na mugun zafi,

Da dare mansura tafara tunani kode yanasonta din dagaske? Ko ya gane kuskurene kace kai se kalar fara kakeso bazaka nemi zabin Allah ba karfa tai sakaci? Gwara de tafara istihara idan har ba alheri bane shi da kanshi zai janye batare da ta cigaba da wulakantashi ba,

Ta tashi tayo alwala ta kabbara salla,

Shi ko Khalil beyi bacci ba saboda tunani,

Wanshekare ya shigo dakin hjy ya dauki mus'ab yana kallonshi shi babban burinshi ya samu me tarbiyya da zata kula da yaranta da kuma mus'ab kamar nata kuma baya tunanin kowa se mansura,

Hjy na kallonshi tace"wai Khalil mike damunka ko haryanzu mutuwar Jameela bata sake ka ba?"

Ya girgizakai yayi shiru,

Tace"to minene? ko halin naka zakai se abu yayi tsami kazo kafada?"

Yayi shiru can zuwa yace"hjy dan Allah kimin wani temako"

Hjy tace "Allah yabani iko minene?"

Fuskarshi sunkuye yace"na kamu da son mansura ita kadai nake burin aure dan Allah ki temakamin nayi zarya taki saurarana"

Hjy tai dariya tace"baka ce fa kafara son bakakene?"

Ya dago ya kalleta fuskarshi kamar yayi kuka yace"hjy kinsan nayi nadama dan Allah ki temakamin "

Hjy tace "to Allah yabani iko"

Yayi shiru baice komiba ya tashi ya fita,

Hjy tabishi da kallo tana jindadin hakan da can baya ya auri mansura da zai aureta yayita wulakantata amma yanzu yasan amfanin mace bawai don shaawa da kwalliyabane abinda yafi shine kasamu me tarbiyya da addini me kuma sonka zata cike maka duk sauran gurabun ,

Ta sauke ajiyar zuciya aikuwa bazatai sanya su rasa yarinya me hankali kamar mansura ba gwara taje ta samu mama,

Tana gama abinda takeyi tai wanka ta goya mus'ab ta nufi gidansu mansura,

Mama ta tarbeta suka shiga ciki suka gaisa ta sauko mus'ab mama ta amsheshi tace"ina mamanshi?"

Hjy tai murmushi tace"ta rasu har daita custum dinnan ya harbe"

Mama ta girgizakai tace"Allah yajikansu"

Hjy tace "ameen akwai maganar data kawoni "

Mama ta meda hankali gunta tana sauraranta,

Hjy tace "khalil yayi nadamar abinda yayiwa mansura shi da kanshi ya sameni yace in temakamishi taki sauraranshi bansan ma yana zuwa wurinta ba dan Allah kuyi hakuri akan abinda ya faru baya gabadaya Khalil din ya sauya ya kara natsuwa kibawa mansura hakuri ta saurareshi"

Mama tace"kwana biyu ana aikowa kiranta dana tambayeta setace ba ita ake nema ba na sanya mata ido ,insha Allah zata saurareshi kuma nagode sosai da kauna"

Hjy tace "ni keda godiya idan ta amince tana son shin se ai musu aurensu kinga munyi tuwona maina"

Mama tai murmushi tai shiru suka dan kara labari ta tafi tana tafiya mama ta shiga dakin mansura tana latsar waya ta tsaya gefe tana kallonta tace"mansura ashe Khalil ne keta sintiri kofar gidannan kina wulakantashi?"

Mansura tai saurin ajiye waya ta kalli mama tana kame_kame tace"eh..eh shine amma wlh ban mishi wulakanci ba"

Mama tace"to me kike masa? Kinganki kishiga hankalinki tun wuri ina laifin Wanda yace yana sonka?"

Mansura tace"mama da bakinshi fa yacemin bayason bakar mace kuma ni banmishi ba yanzu kuma seya dawo yace yana sona"

Mama tace"shirmen banza "ranta bace

"Idan da yace bayasonki yanzu bayana sonki ba koko bazai taba sonki ba tunda yace bayasonki can baya? mutane nawa suke sonka su dawo suna kinka nawa daga son yake komawa kiyayya?kuma shi khalil ko dan mamanshi ai kin saurareshi matar dake sonki tana yabonki duk inda ta zauna "

Mansura tai shiru,

Mama tace"to ya turo mamanshi ya bada hakuri ya rage naki yanzu"ta fita a dakin,

Mansura ta kwanta kan bed ta lumshe ido ita ba ruwanta da kyau na mutum ko kudinshi ta samu na gari Wanda ke sonta tsakani da allah zai kuma kula daita shine burinta idan har Khalil din ne mafi alheri Allah ya zaba mata mafi alheri,

Washegari Sega Khalil ta fito tayi simple makeup ta karaso tana dan murmushi,

Murmushinta da yagani ne ya sanyaya mishi rai ya washe baki ya sauke ajiyar zuciya yace"barka da fitowa gimbiya"

Tai murmushi tace "ina kwana?"

Yace"lpy lau ya mutanen gida?"

Tace"lpy lau"tai shiru

Yace"mansura ina kara baki hakuri akan kuskuren da nai a baya"

Ta kalleshi tai murmushi tace "ya wuce tunda yanzu kanason baka gaka ga mansura"

Yayi murmushi ya cije lips yace"nagode"

Tai murmushi itama suka cigaba da fira jefi_jefi,

Da zai tafi sukayi exchanging numbers suka fara soyayya me tsabta,

Karshen week akayi bikin rabia faseelat batasamu zuwa ba tade siya mata kayan kallo gudumuwa Ummi taje akasha biki daita sannan aka kai Amarya gidanta,

Amisha nata jinya har 2months sannan aka sallamesu suka dawo Nigeria bayan sati suka shiga kotu ,

Duk tabi ta rame kamar ba ita ba tana cikin nadama da dana sanin abinda take aikatawa gata da breast daya takoma musaka,

Shareep duk yayi baki ya rame shima ,lauyoyi kuwa suka gabatar da Kansu ,

Aka fiddo amisha don tafadi abinda ya faru ta fito tana hawaye ta zumbula katuwar hijab jikinta ,

Alkali yace"kifadawa kotu abinda ya faru ranar da aka sameku gida me no 10"

Amisha nata hawaye kanta sunkuye ta rufe baki tana hana kuka kwacemata amma ina seda ya kwacemata tafara kuka duk kotun takarade da sautin kukanta alkali ya buga guduma so baadadi taki yin shiru securities suka jata waje ,

Lauyan gwamnati ya kalli shareep yace"ranar ukku ga watan ukku ansamu gawarwakin yanmatan gidanka tare da kai a sume ko zaka fadawa kotu abinda ya faru ?"

Shareep yace "eh ni na kashesu"

Lauya yace"kana nufin kai ka harbesu da hannunka?"

Yace"eh ni na harbe su"

Lauya yace"me yasa ka kashesu ?"

Shareep yayi shiru,

Lauya ya sake memeta tambayar,

Still shareep bai bada amsa ba,

Lauya ya juya yace"ya me sharia a ranar ukku ga watan ukku shareep ya bindige matarshi da kawarta tare da jikkata daya daga cikinsu saboda ya samesu suna lalata a dakin baccinshi"

Shareep ya sunkuyar da kai yanajin mugun zafin kalaman lauyan fadin suna lalata,

Lauyan ya kira megadi ,
Megadi ya shiga cikin kanta,

Lauyan ya koma gefenshi yace"me kasani akan abinda ya faru ranar ukku ga watan ukku?"

Megadi ya memeta abinda yafada a police,

Lauya ya kalli alkali yace"ya me sharia bincike ya gama tabbatarwa da shareep shiya kashe matarsa da kawarta shima ya amsa lefinsa da kansa muna neman kotu ta gaggauta yanke masa hukunci batare da jinkiri ba"

Lauyan shareep yace "objection my lord me laifi ya amsa laifinsa ne batare da ya gama warkewa daga ciwon da zuciya da kwakwalwarshi ke ciki ba muna neman kotu ta bamu lokaci mukara bincike sosai "ya koma ya zauna,

Alkali yayi rubuce_rubuce yace" kotu ta saurari bayananku sannan ta daga kara har zuwa next month daya ga wata da Wanda ake tuhuma da amisha zaa cigaba da tsaresu har zuwa lokacin"

Daganan kotu ta tashi Sam shareep baiji dadin hakan ba shi yayi kisan me zaa jira? Kwata_kwata baiso aka daukarmai lauya ba,

Ana shariar yan jaridu da gidajen TV da radio suna dauka suka fara baza shariar don mutane Susan me ake ciki ,

Aka tafi da shareep da amisha prison ,kuka kawai amisha takeyi wata zuciyar na jindadi dabata mutu ba saboda tayi nadama wata zuciyar najin gwara mutuwa da wannan rayuwar kunyar kowa yasan ita yar madigo ce har tabi Mimi har gidanta Zaa cigaba da mata kallon yariska har karshen rayuwarta,


Cikin kankanen lokaci akasa bikin mansura da Khalil 1 month kacal idan yazo fira basa wani jimawa suke rabuwa a waya sukan dade watarana but wani lokaci 3minutes ma yayi yawa suke sallama,

Yadda yake sonta yake kula daita shi yasa tafara sonshi ,

After weeks saura sati daya bikin su Khalil yazo kofar gidansu ta fito tana ta sakin murmushi suka gaisa ,

Yana ta farinciki shima yace "Amarya dame_dame kuke shiryawa na bikinmu?"

Tana murmushi tace"bikin bakake ne fa harwani shagali zaai?"

Khalil yayi dariya yace"ni nafara yin fushi yadda kike kiran kanki baka saboda matata farace Tass bakisan hasken zuciyarki duk ya haskaka sauran jikinki ba?"

Tai dariya tace"karkayi fushi wasa nake"tana mai wani kallo da murmushi fuskarta,

Khalil yayi murmushi shima yace"dame_dame kikeso ayi?"

Tace"walima da waazizzika zamusha a gida ku kuma kusha taku walimar bayan daurin aure don nuna farincikin aurenmu"

Yayi murmushi yace"duk yadda kikace blacky"

Tai saurin kallonshi tare da cewa "LAAAAA"tana dariya,

Yayi dariya shima sannan yace" aike kikafada bani ba"

Tai murmushi tai shiru,

Ya shiga mota ya dauko mata kudi dunkule sunfi 100k yace"kiyi hidimar da zakiyi lalle kitso dasauransu irin na amare"

Ta amsa tace"nagode"tana boye fuska,

Ya zunduma hannuwa cikin aljihu yana kallonta yace"Toni zantafi"

Tace"Allah yakiyaye sai ka dawo"

Yace"ameen kije gida"

Ta kalleshi ta nufi gida yayi tsaye yana ta kallon ta harta shige sannan ya shiga mota ya nufi gida ranshi fess,

aka cigaba da shirye_shiryen biki Khalil ya saida gidan da suka zauna da Jameela Sam baya son ko kallon gidan yana tuno kazantar da akayi cikinsa ,

Shida hjy suka zabi karamin gida madedeci aka gyarashi don yiwa amarya Jere,

Dashi da hjy da dangi suka hada lefe akwati 6 makil da tsadaddun kaya aka kai gidansu mansura,

Saura kwana 5 bikinsu mansura aka koma kotu domin cigaba da sauraren kara,

Bayan kowa ya hallara alkali ya shigo aka fara gabatar da shariar,

Alkali ya tambayi shareep "ka tabbatar kai ka kashe matarka da kawayenta?"

Shareep yace"eh Nina kashesu"

Alkali ya kalli jamaa yace"kotu bata da lokacin batawa munason Ku gabatar da duk shedunku domin zartar da hukunci cikin lokaci"

Lauyan shareep ya tashi ya bukaci amisha a kanta a kasa amisha ciki,

Lauya yatsaya gefenta yace"malama amisha kotu naso ki mata bayani minene ya faru ranar ukku ga watan ukku"

Amisha ta share hawaye tace"ina gida kawata ta kirani akan tayi missing dina tanason ganina na shirya na nufi gidan ina zuwa na samesu da kawarta Jameela shine nayi joining dinsu a bed muna cikin halin bansan kowaye ba sede naji harbi daganan bankara sanin ina nike ba"tanata hawaye,

Mutane nata kallonta ,

Lauyan yace"kina nufin bakisan wa yayi harbin ba?"

Tace"eh"

Yace"A ina kikasan mimi tun yaushe kike tare da ita?"

Tace"shekara biyu kenan munhadu daita a school"

Yace"dama kin dade kina bin mata yanuwanki?"

Ta kalli anty ,anty ta sunkuyar da kai ,

Amisha tace"eh"koda zata tonawa anty asiri sede tafadawa uncle ba a bainar jamaa ba saboda daukar nauyinta da sukeyi da kuma dawainiya daita,

Lauya ya karkace kai yace"shekara nawa kika dauka kina less?"

Tai shiru sannan tace"biyar" ta rage musu yawa don rufin asiri,

Lauya ya kalli alkali yace"yame sharia wannan shine ainihin gaskiyar abinda ya faru batasan kowa ya harbeta ba megadi ya samu shareep da bindiga ne kawai yana niyyar kashe kanshi amma beda tabbacin shiyayi harbe_harben tayiwu cikinsu ne idan mukai duba da yadda suka dade suna aikata fasikanci a doron kasa ba abinda bazasu iya ba ina rokon kotu ta wanke shareep domin bashi ya aikata laifin ba yana amsa laifin daba nasa ba saboda bakincikin cin amanarsa da matarshi keyi bayan idonsa nagode"

Alkali nata kallon amisha ta glass tana ta hawaye yace "ke musulmace?"

Ta daga kai tace"eh"

Yace"kinsan abinda kike aikatawa yana daga cikin munanan laifuka a musulunci? "

Ta girgizakai,

Yace"kikace ke musulmace Bakisan girman laifin da kikeyiba kenan? Bakisan Allah ya halakar da mutanen annabi lud saboda maza na bin maza yanuwansu ba?"

Ta girgizakai tace"bansaniba "

Alkali ya kalli mutane yace"ina mahaifin amisha?"

Uncle ismaeel ya matso gaba,

Alkali yace"Kaine mahaifinta?"

Uncle ismaeel yace"a,a bani na haifeta ba nine de nake rikonta na daukota a..."

Wata matashiyar mata dazata kai 38 ta tashi hawaye na zuba a fuskarta tace"karya kake wlh kaine mahaifinta kai kayi silar zuwanta duniya"

Kowa ya juya yana kallon Matar jin wata sabuwa,

Alkali ya kurawa Matar ido ta glass sannan ya kalli amisha dake gefe ya meda kallo gun matar yace.....
[2/5, 9:56 PM] Maman Mamy: 81


Yace"wacece ke?meyasa kkce shine mahaifinta ?"ya jero mata tambayoyin lokaci daya,

Uncle ismaeel wani irin kallo yake jefarta dashi cike da tashin hankali da mamaki,

Matar na hawaye tace"nice mahaifiyar amisha ni na haifeta bayan na azabtar da rayuwarta,shekarun baya da suka wuce lokacin ina shekara 18 na hadu da ismaeel na fito kenan daga supermarket daganan muka kulla soyayya me karfi dashi yana nunamun tsanananin soyayya se aka medashi aiki kasar waje bai fadamin hakan ba yade nemi yardata mufita waje mushakata mudawo,

Inaso in leka waje ban taba lekawa ko Niger republic ba na amince batare da sanin kowa ba nabishi muka tafi wajen namanta da kowa muna tare muna nunawa juna soyayya,

Iyayena sun shiga tashin hankalin rasani sunsha nemana suna fadin cewa anyi kidnapping dina basusan ni da kaina nabi saurayina ismaeel ba bayan lokaci nafara laulayi hankalina yayi mugun tashi saboda ban shirya ciki ba ban shirya a kirani yariska ba ban shirya batawa dangi da iyayena suna ba ban shirya haifar shege ko shegiya ba ina cikin tashin hankali na fadamashi ya siyo wani magani nasha naita bleeding ya daukeni ya kaini wurin wani likita ya temakamin jinin ya tsaya muka dawo hotel muka cigaba da soyayyarmu bayan wata 2 cikin jikina ya sake bayyana nashiga tashin hankali ya kara siyo drugs nasha naita bleeding ya daukeni a haukace ya kaini asibity dakyar suka ceto rayuwata muna dawowa yafara shirin medani gida ,

Nasha kuka nasha mamakin ismaeel duk soyayyar da yake nunamin dama zai iya guduna?, yabani wasu kudade ya kaini airport na rikeshi ina kuka ina rokon yabarni har in haihu sannan na koma Nigeria saboda nima inatsoron kara yunkurin zubarda cikin ,yanajin kukana ya fizge yayi tafiyarshi na dawo Nigeria nakasa nufar garin iyayena a wannan halin hakan yasa na tafi wani kauye na nemi temakon wata mata bayan na mata karyar mijina ya rasu,

Na zauna daita har wata takwas saboda yunkurin zubar da cikin da mukaitayi yasa naki haihuwa in time, wani lokaci ina kuka tsanar dana kewa ismaeel yasamin tsanar cikin jikina Ina dukanshi duk da nikejin ciwon bayan wata takwas shekara daya da cikin amisha na haifeta ,

Ina warkewa naiwa Matar bankwana na nufo Kano gab asuba muka iso ban iya nufa gida da amisha ba nasata a kwali na ajeta a bola nai tafiyata batare da jin tausayinta ba,na koma gida yanuwana sukaita murnar dawowata na zauna lpy ba tsangwama bakomi cikin farinciki da walwala,

Ina tunanin gobe zan samu miji jibi zanyi aure amma shiru kuma ina da bukatar hakan se time dinne nafara tunanin ya ta ko tana raye ko ta mutu? na koma bolarnan dana ajeta babu alamar antaba yada jariri awurin na dawo ina kuka inajin danasanin yardata gashi yanzu dukda asirina ya rufu nakasa auruwa bare har in samu wasu yaran ,

Ina gida naga hoton me kama dani a asibity kallo daya nai mata nasan cewa yata ce tun time dinnan nike bibiyarta nakasa tunkararta na fadamata nice wannan danai watsi daita na ajiyeta a bola, ban damu ko duniya zatasan me na aikata ba amma inason diyata inason rayuwarta"

Kotu tayi tsittt ita kadai ake saurare,

Uncle nata zufa yana cikin tashin hankali,

Amisha hawaye kawai takeyi tana kallon Matar suna kama sosai daita,

Matar ta kalli uncle ismaeel tace"ko kamanta Hajara masoyiyarka ?ko zaka karyata cewar ba kaine mahaifin amisha ba?"

Uncle yayi tsitt cos baya da gaskiya yanata hada zufa,

Alkali nata kallonshi yaji yayi magana amma shiru ,

Alkali yace" alhaji ka amince da maganar matarnan?"

Uncle ismaeel yace"ehh!"yanajin matsananciyar kunya,

Amisha ta fiddo ido tana kallonshi dama tana tarayya da kanintane da kuma step mom dinta kanta yayi wani irin juyawa tai luuuuu ta zube cikin kantar securities sukai kanta dasauri aka fita daita zuwa asibity,

Mamanta na tsaye nata hawaye tana ganin jin yadda akasameta ne yasa ta somewa,

Tundazu jikin anty keta rawa gabadaya hankalinta na neman barin jikinta da diyar mijinta take ta lalata? Fitar da akai da amisha yabata damar ficewa tai gida tanata hawaye wato uncle yabarta gida hakanan shi kuma ya tafi yana hutawarshi da matan banza ta nufi gida tanata hawaye,

Alkali da duk mamaki ya cikashi akwai tarin tambayoyi da zaiyi ya daga karar zuwa next week aka kama shareep aka medashi cell,

Hajara ta nufi asibity tana kuka sosai ,

Uncle yakasa tafiya gidan ya nufi asibity wurin amisha tabbas

Please Login or Register in order to submit comment