Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡️🏡
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸ‚ *Rukayya Ibrahim* πŸ‚

✨Tsokaci ALKAWARIN MASOYA na kudi ne gamai bukata naira 300 ne kacal ki zama mace mai aji ki karanta abinda kika sayaπŸ‘Œ
Free page🀧

*EXQUISITE WRITER'S FARUM*

Page1⃣&2⃣
Safiya ce da misalin karfe 7:10pm Ahlin gidan tsohon minister ne, zaune Akan daining babba mai d'auke da kujeru sama da 12 karyawa suke kowa ka gani cikin shirin sa yake na zuwa aiki koh makaranta inka cire matan gidan, Abba ne zaune a kujeran daining inda ke tsakiya, zaikai Akallah shekara 65

sai hajiyoyin dake zaune akan kujerun gefensa, manyan matane masu ji da aje naira da izzah, sanye suke cikin shiga na atamfa dukansu.

mamu uwar gida akallah zata kai 50 sai ummu Amarya mai shekaru 40 sai babban d'ansa Anwar d'an mamu ne zaikai shekara 35 zaune yake cikin shigar office(doctor).

sai mai binsa shareef mai shekara 31 shima yana sanye da suit baki (lauya), sai umaima dake sanye cikin dogon rigan kanti da gyelen sa, daga kaga irin wankan ta kasan yar jami'a ce, zata kai shekara 25 dukan su d'akinsu d'aya ne.

sai babban d'an ummu uzaifa da zaikai 20 yana sanye da jamfa da riga da wando na shadda, kansa babu hula(student).

sai munira mai shekara 17 sanye take da uniform tare da kanwarta zulaihat mai shekara 15 ita tana sanye da uniform, Abinci suke ci hankali kwance yayinda kujeru uku yakasance empty babu kowa akansa.

Addayiya dake zaune a tsakiyar falo ta mimmike kafa tsohowace sosai Amma jin dadi ya boye shekarun nata, sanye take da zani da riga sai d'an kwali data aje a gefe bata d'aura ba tulin gashenta daya rine zuwa fari a bayyane, Abinci take ci kwai ne da Arish sai tie ga bread a gefe, cin Abincin ta take hankali kwance.

Turo kofar da akayi shiya ja hankalin kattafanin su dake falon harda daining Area, duk da kamshin turaren sa ya sanar dasu wake shirin fitowa, Amma hakan bai hanasu juyawa don tabbatar wa kansu shin da uniform ya fitoh koh Ah ah.

Fitowa yayi a kofar, wow masha Allah watoh in Anace maka black is beauty, bazaka tabbatar ba sai kaga wannan Hallintar koh shakka bazakayi ba, bakine mai sheki irin bakikkirin nan, fatar nada masifar laushi har maiko-maiko fatar keyi sanye yake da wando baki, mai roba a kasar wandon, pencil ne ya kamasa sosai bai rufe masa idon sahu ba.

sai boot fari tas baisa wa kafarsa socks ba, hakan yasa ana kallon idon sahun nasa, t-shirt ne a jikinsa white sai rigan da ya daura akai mai hula da dogon hannu, Amma ya bude zip in wanda yasa ake kallon rigar ciki.

ga wani d'an iskan Aski dake kansa ya raruke gefe yabar sakiya da yawa, gashine mai laushi da yawan gaske irin na fulani, ga kwancecen sajensa mai hade da gemu, duk da bai cika masa fuskar ba, Amma daga gani Ana ji da gemun irin na tsiran farkon nan ne na tashe balaga.

Bakin sa pink ne mai kyau dan kankani, hancin sa mai tsahone sosai ga idanu manya kamar na mata, kwayar idanunsa bakine sosai wanda ke matukar rikita mutune a duk lokacin da ya zare maka su yayin da mabi da kwayar ya kasance fari tas gashin giransa mai yawane blutooth ne fari makale a kunnensa d'aya.

Yana da tsawo sosai Amma ba irin har shan innan ba, gashi da kira mai kyau duk da yanzun yake tashen sa, Amma kallo d'aya zaka masa ka gane za'ayi namiji, baxai wuce shekara 18 ba.

Taku yake irin na isasun yaran nan masu ji da lokacin su hade da kuruciya, duk da ya gansu zaune a falo, Amma hakan baisa sa ya nuna ya gansu ba nufar kofar falo kawai yayi.

Addayiya dake zaune a tsakar falo tana cin kaza da romonsa wanda yar aiki ta aje mata, ta mike kafa.

da gangan ya nufi ta saitin da take zaune kamar baiganta ba, ya d'aga kafarsa kamar zai taka kafarta da sauri taja abinta cikin masifa take kallon Lahab.

Amma yaron nan Anyi jarabebbe kai in gari ya waye baka sani surutu ba bakajin dadi, nida gidan mijina da d'ana, bani da sakat sai in baka nan, toh yau duk bala'inka bazan kulaka ba, d'an-banza kawai.

yi yayi kamar baisan ma tanayi ba tafiyarsa yaci gaba dayi.

Abbu dake zaune tunda lahab ya fitoh yake binsa da kallo Ganin yanda yazo ya wuce su, yau koh break in ma bai tsaya yiba, kwala masa kira yayi ganin yana kokarin bude kofar, Lahab!!!Lahab!!

*ALKAWARIN MASOYA Naira 300 ne vie 2185602275 Rukayya Ibrahim UBA bank, koh katin Airtel zaki tura ta wannan layin 08084453785 tare da shaidan biyan ki*

had'a fuska Lahab yayi jin yayansa na kiransa juyowa yayi ya dawo cikin falon har wajen daining Area, ya tsaya a bakin steps in.

Abbu ganin ba gaidashi Lahab zaiyi ba yasa sa kallonsa, Anya lahab rayuwa zaiyu a haka kuwa? kai kenan in gari ya waye sai an maka fad'a, daga safe zuwa dare sai ka samu surutu a gidan nan, mekake so Lahab da ban maka ba?

kara had'a fuska yayi jin Yayan nasa zai fara masa fad'ar daya saba a idon yaransa, "babu"

toh Yanzun ka kyauta kenan ina fa kallonka saura kad'an ka taka mini kafar mahaifiya da wa'inan shegun takalman nan naka?
Addayiya fa ba kakarka bace, koh su Anwar basa mata abinda kake mata a gidan nan.

jin Abinda Abbu yace yasa Addayiya fashewa da kuka, kuma fa umar tun farko saida na nunawa ubanka banason Auren sa da wannan figeggeyar yarinya, Amma dayake budurwar zuciya ne dashi,kaima kabi ka sani a gaba da wa'azi, gashi shi ya tafi ya barni da jaraba ga uwarsu shan tayi auren ta tana jin dadi ni An barni da ciwon baki, Allah sarki.

haushi ne ya kama lahab cikin masifa yace"oh Ashe kishi kike tayi aure bakiyi ba, kema ai bawanda ya hanaki saiki fitar da miji a miki"

kuka Addayiya ta sake, nikam na shiga uku ni Maryamu, toh bara kaji uwarka ce kwad'ayayiya ita da ubanta, ba kunya tazo ta likewa tsoho.

dariya jama'ar dake wajen suka sake Abbu ne kawai baiyi dariya ba saima haushi dayaji ya rasa meyasa kullun sai sunyi fad'a, kuma Lahab ke tsokanar ta daga karshe kuma ya sata kuka,
Habba don Allah Addayiya wannan wani irin magana ne a idon yara?

jin abinda Abbu yace yasa Addayiya had'a fuska taci gaba dacin Abincin ta, tana share hawaye.

kallon Lahab Abbu yayi, yanzun menene Amfanin abinda ka matan nan ta tsufa ma bazaka barta ta huta ba?koh so kake ka d'aura mata hawan jinine?

"kayi hakuri yaya bazan kara ba"

rufe mini baki karawa na nawa kuma lahab,kuma ban gane ba na ganka da wa'innan kayan ina uniform in?

kafun ma lahab yayi magana Umaimah tayi caraf tace Haba Abbu inda sabo yaci ka saba da halin small uncle ka hutawa ranka, kai yaranka basu baka ciwon kaiba zaka sawa kanka ciwo akan sa.

ai Lahab najin abinda tace cikin masifa ya nunata da yatsa"wallahi zanci uwarki umaimah daga yau in ana mini magana kika sake saka bakin ki a ciki yar iska kawai".

mikewa shareef yayi kai wallahi ya isheka haka Lahab mun gaji da iskancin ka a gidan nan?

wani hayyakowa lahab yayi cikin masifa kamar irin zai iyya dukansan nan"toh koh dukana zakayi matsiyacin lauya"

tura kujeran daining in shareef yayi zai sauko da sauri Abbu ya nuna masa kujera da hannu, go back to ur seat shareef, Lahab bappan kane respect him banason haka?

shi ya fara baka respect naka tukunnan kaida kake yayansa, kuma a girme ka haifesa Amma bayajin maganar ka, bayajin kunyar ma su ummu rashin mutunci saini ne dukan sa zai gaggareni.

ai jin yace duka yasa lahab harzuka zai zage shareef sai kuma yayi shuru jin takun sahun kafa a falon, wanda koh shakka babu yasan wanda ke tahowa.

Allahu Akbar tsarki ya tabbata ga Allah, hatta tafiyarsu iri d'ayace kai daga zaran ka gansu basai an fad'a maka ba, zaka bawa kanka amsa da tagwayene, babu abinda ya banbanta su sai abu biyu hali da kuma gyaran gashin su, Amma bayan wannan da koh a cikin gidan su baza'a samu mai banbantasu ba, a hakan ma mutanen waje ba iyya banbantasun suke ba.

karasowa yayi gaban daining in bayan sun gaisa da Addayiya a falo, gaida Abbu yayi da ummu da mamu, yaran Abbu suka gaidashi dukansu duk da mazan sun girmesa hakan bai hanasu basa girman saba.

kallonsa Abba yayi cikin farin ciki, sanye yake da uniform, wandone navy blue, sai riga fari da boot fari na makaranta a kafar sa, hannunsa sakale da school back sai wasu litattafai daya rike, Rahab na tura zuhaihat kafa biyu kazo mu karya, wai kana wanka?

murmushi yayi saida fararen hakoran sa sak irin na Lahab suka bayyana, Eh yaya Assigment nayi da safen nan shiyasa nad'an makara ban shiga wanka da wuri ba.

ok get a seat ka zauna oyya kayi break?

gaskiya Yaya nayi laten almost 7:32 yanzun fa?zan wuce kawai.

hannu Abbu yasa a Aljuhunsa ya zaro 1k mikawa Rahab yayi, gashi ka shiga school cafe ka sai abin break ka tabbatar kafun ka shiga aji ka karya?

d'an rusunawa Rahab yayi ya karbi 1k in hade dama yayan nasa godiya, kallon Anwar yayi, doctor Ya Alkawarin mu na kudin hadisi gobe islamiyya, in ka samu aban yanzun zanbi islamic bookshop in muna dawowa?

hannu Anwar yasa a Aljuhu ya zaro lalitarsa 10k ya zaro ya mikawa Rahab.

hannu yasa ya Amsa cikin murna yace, doctor kudin sunyi yawa hadisin fa 500 ne?

na sani Rahab sauran chengen ka rike a a hannunka.

Lahab dake tsaye a gefe tun fitowar Rahab bai kara magana ba, sai binsu da ido yake, ganin kudin da Aka bawa Rahab yasasa shammatar su ya fizge 11k in ya b'anb'ara da gudu ya nufi kofar falo, a tamanin Rahab ya bisa a guje zuciyar sa na tafarfasa don shi daman mutun ne mai karamin zuciya, duk irin kwala masa kira da suke akan ya dawo kin sauraron su yayi.

Addayiya dake zaune har lokacin fuska a hade, nufar kanta gadan-gadan Lahab yayi da azabebben gudu.

ai mikewa Addayiya tayi jiki na rawa ganin sa ya nufota da gudu itama gudun tasa ta nufi.............

*******************
ENUGU STATE.........
zaune take a kan bench ita kad'ai, kuma benchin a kusurwan aji, ita kad'ai aka ware wa wajen tana zama, gabaki d'aya ta tattara hankalin ta akan malamin dake koyar dasu Math's duk da ba kallonsa take ba.

sanye take da wani kod'aden uniform dogon rigane wanda ya tsaya mata iyya gwuwa, farace irin farin nan da ake kira light, kyakkyawace na bugawa a jarida siririya ce Amma fa Akwai kaya duk da tana zaune akan kujera hakan bazaisa mutun ya kasa gane irin baiwar da Allah ya mata ba, kirjinta a cike yake tam wanda yasa gaban rigan matseta har gaban kirjinta ya kasa rufuwa har ana kallon farin vest inta datasa a ciki shine ya hana ganin Kirjinta a waje, kanta ba hula sai gashinta mai yawa da aka masa kitso uku ya zuba har gadon bayan ta.

Ebo ce irin fararen masu kyau innan toh haka take ita ma, bakinta jajazur maikyau ga hanci mai tsaho, duk da idanunta na boye a cikin medicated glass, hakan bai hana ganin kwayar idanunta dake kallon Allo ba.

masha Allah idanun nan ne irin wanda ake kira da cat eyes kwayar idanunta sky blue ne, gasu masu girma, wanda sanadin su wasu ke kara gudun ta.

kiliilii....killiiliii bugun bell shiyasa malamin fita a ajin, ya rage ita kad'aice a class babu kowa, yamusheshen jakanta ta zaro a lokan benchi budewa tayi ta leka ciki.

kulenta(magge koh kenwa)zaune a kan takardunta abin tausayi, shima jin An bude boron yasa sa kallon ta.

sosai ya bata tausayi yanda bata karya ba, haka shima yau babu abinda yaci, hannu tasa a gefen jakan ta zaro naira talatin jujjuya kudin tayi a hannunta, aje jakan tayi ta mike tsaye ta fita a ajin.

tafiya take kanta a duke fuska a hade sosai, wanda hakan dabi'arta ne bazaka taba ganinta cikin fara'a ba, koh kaga tana surutu da wani, duk inda tazo wucewa haka yara zasuna watsewa Inda sabo ta saba, hakan yasa abin bai damunta sosai.

tun kan ta karaso wajen mai kayan shagon tuni ya ruga a guje ga fita a keus nasa, itama bata wani damuwa ba hannu tasa daga wajen shagon ta ballo madaran 20 da pure water 10 aje masa kudin tayi ta juya ta koma class.

zama tayi a inda ta tashi hannu tasa a boron ta d'auko kulen ajesa tayi akan kujeran, bude madaran tayi ta bula ruwan ta zuba a madaran saida yazo har bakin laidan madara, kafun ta aje pure water kallon kulenta tayi yana zaune kamar mutum ya kurawa madaran ido, d'aukarsa tayi ta aje akan cinyarta tana basa madaran.

sai da ya kusa shanyewa kafun ya Rufe bakinsa Alamun ya ishesa, sauran kad'an in ta shanye batare da taji kyeman bakinsa ba.

haka a daddafe take saboda tsananin yunwar da ke cinta, karfe 2 Aka tashi a school, duk yara suka fifita, itakam zama tayi a class taki fita saboda tasan mundin ta fita, haka yara zasuyita gudu har su shiga kauyen su, shiyasa take jiran su d'anyi nisa kafun itama ta kama hanya.

2:27 ta fitoh a class nasun hannunta rike da jakanta wanda kule ke ciki da takardu, yaran makarantan duka sun watse koh malamai babu, A haka take tafiya A hankali, Nnenna irin mutanen nan ne masu saib'i.

tafiya take Da kafa hankalinta gabaki d'aya yayi gida, ganin yanda hadiri ya hadu sama yayi bakikkirin sai iska dake kad'awa, doguwace sosai tana da wadatantun mazaunai masu d'aukar hankali, iska na kad'awa sai suka kara fitowa sosai.

babu kowa a hanyar wanda hakan bai dameta ba sanin yaune Ake biki a makwantan kauyen su, lokacin da ta tsallake ruwa tazo wajen gonaki.

ji kawai tayi an fizgota ta baya a matukar kid'ime ta juya wazata gani? wasu yan iskan kauyen sune chukwudi da onyebuchi akalla zasu kai 25, fizge riganta tayi taci gaba da tafiyan ta hankalin ta a tashe, sanin halinsu gashi yau babu kowa a hanya.

binta sukayi Chukwudi cikin yaren Ebo yake mata magana, ke Nnenna Mayya mufa ba ruwan mu da maitancin ki, cinki yau zamuyi saboda kin hadune bana wasa ba, gashi bamu taba samun target namu yatafi daidai ba irin yau.

jikinta na rawa ta kara sauri onyebuchi ne yasa hannu ya damko gashin kanta, fusge kanta tayi, da sauri ya wanketa da mari wanda yasa glass nata faduwa.

rumtsa kyawawan idanunta tayi cikin tashin hankali ta sake budesu, gabaki daya dishi-dishi take kallo sam bama zata iyya kane fuskar su ba a yanzun.

da sauri ta tsunguna a kasa tana lalubar glass nata, chukwudi ne yasa kafa ya take glass in dake gefe.

jin karan fashewan glass yasa da sauri tasa hannunta ta saitin wajen tana laluben glass in, tana najinsa ta d'auka, tattabasa tayi, Kawai saita fashe da kuka ganin idanun glass ya bararraje.

dariya suka sake a tare cikin iskanci onye yace mata, yaufa koh Jesus ne ya sauko bazai ceceki ba(wa'iyyazu billah) bare mutum gwanda ki bimu a hankali mu gama abinda muke so, a wajenki mu barki ki wuce, koh kuma mu kasheki kika mana gardama ya karasa maganar da zaro sharbebbeyar wuka.

dubansa tayi idanunta na zubarda ruwan hawaye, sam ba kallonsu take sosai ba, tadai san gasu a gabanta Amma bata kallo normal kamar kowa
"Tabbas kowa zai mutu Amma fa ka sani kai yau kwanan ka ya kare, kafun na mutu kai zaka fara mutuwa, Ajalinka na kusa wannan ALKAWARI ne, ALKAWARIN mutuwa"ta karasa maganar cikin tsantsan bacin Rai.

jin Abinda tace yasa chukwudi sake wanketa da mari mai zafi saida ta zube a kasa, jakarta ya fade Allah ya sota ba'akan jakan ta fadi ba data illata kulenta, jinine ya balle a hancinta.

A take ruwa ya sako da karfin gaske, hannu yasa yajawo riganta sai da ya yage,da karfi ta turesa ta kwashe jakanta da gudu ta ruga.

suma binta sukayi sosai suke tsere har sukazo bakin titi koh gabanta bata kallo saboda rashin glass, gudu kawai take wanda ta fadi yafi a kirga haka zata daure ta mike, da gudun tsiya ta tsallaka titin daya ratsa kauyen su.

suma da gudu suka zo tsallaka titin, ji kake kauuuuuuuuuu wata babban roka tabi ta kansu .

Nnenna dake gudu jin karan yasata tsayawa da sauri ta dafe kirjinta tuno warning inda papa ya mata kafun ta fitoh..............

SANARWA!!!!SANARWA!!!!SANARWA!!!SANARWA!!!

BABU UPDATE NA ALKAWARIN MASOYA
EVERY WEEKEND

✨Ruqeenjalal✨


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

Free page🀧

*EXQUISITE WRITER'S FARUM*

Page3⃣&4⃣
in bata manta ba papa yace mata mundin ta fita gida, sannan ta d'auko masa magana jikinta zai gaya mata, asalima umurni ya bata akan ta rufe bakinta, har taje ta dawo karta kuskura tayi magana da kowa, gashi tajawo wani rigimar kuma.

kuka ta sake mai karfi gashi sai ruwa ake ga rashin glass ga iska na shigar mata ido, gashi bata ganin gabanta sosai,

tafiya kawai take hankalinta a tashe, ta rasa ina zata nufa ba ganin hanya zatayi ba sosai ga ruwa, tafiya take a hankali ga jakanta a sakale a kafad'arta, gajiya tayi ga yunwa yasa ta zauna a jikin wani bishiyar da batasan bishiyar menene ba.

kamar minutes 5 da xaman ta taji abu ya fado a jikinta da sauri ta kwala kara ta matsa gefe, don ta tsorata ainun zuciya mai sake-sake harta saka mata wani abin cutarwa ne.

jin abin bai motsa ba yasata lalubar jakar ta ta bude kulenta dataji yana kuka, aiko tana budesa da gudu ya nufi inda Abin nan yake d'aukowa yayi da bakinsa ya matso kusa da ita ya aje mata a jiki, hannu tasa ta tattaba jin ayabane yasa ta murmushi, duk da ita a d'abiyarta sam batacin abinda ba'a bata ba koh yayane, Amma yunwar da takeji bazai saurara mata ba rabonta da abinci tun jiya.

barewa tayi a hankali tana kai dubanta zuwa ga kulenta mika masa tayi Amma taji bai karba ba alamu dai bazaici ba, daman tasan Bayacin Ayaba, cin Abinta ta shigayi dayake bari guda ya fadi kusan k'walli 15 ne a manne waje d'aya.

bayan ta gama cin ayabar ta, zuwa lokacin ruwa ya d'auke mikewa tayi da jikekken uniform nata a yage, jakanta ta bude ta saka kulenta a ciki shima duk ya jike, tafiya ta cigaba dayi tana kallon dishi-dishi dayake hanyar ba bakonta bane koh babu ido garanti zata gane kauyen su.

tunda ta shigo kauyen jikinta ya fad'a mata ba lafiya, sanin da tamusu war yanzun suna bakin bishiya wasu na caca wasu nashan giya, Amma yau sit kakeji, duk inda ta wuce binta ake da ido wasu yaran kam gudu suke suna bata hanya.

a haka ta iso kofar wani yamusheshen d'akin falange wanda akayishi ciki da falo, sai tsunmokaran su a rarrateye a jikin kwanukan gidan kome nasu a waje yake kama daga bandaki wajen girki kamar dai gidajen inyamurai babu katanga koh makewayi daga an fita a daki toh kamar an fita a kofar gidane.

tura kofar d'akin tayi kamar yanda ta tsammani hakance watoh a bude kamar kullum, da takalmi a kafarta ta shige ciki.

falone d'an kankani sai kujera da katifa mai masifar datti a gefe da tufafi a rarrateye sai risho da takalma da kwalaban giya, wucewa tayi kofar dake tsakar falon, tana shiga dakine karami babu kome sai taburman ta karami da kullin kayanta data d'aure mai datti tamai dashi filo.

aje jakan kulen tayi a gefe ta bude sa a ciki da sauri ya fice a dakin yayi falo, itakam kaya ta cire ta d'aura zani a kirji uniform jikekken ta fitar ta aje a gefe, takardun ta duka ta ciresu ta d'au jakan ta rataya akan igiyar kayanta dake dakin, hannu tasa a gefen katifarta ta fitoh da wani karamin akwatin karfe budewa tayi hannu tasa ta d'auko wani glass in, jujuyasa tayi a hannunta tana tunanin shine kadai ya rage mata in tsautsayi ya rafkawa glass in shikenan bata da wani, sakawa tayi a idanunta, kayan makaranta ta d'auka a hannu tayi waje dashi.

boket nasu dake falo ta d'auka ta fita waje dayake basa shan ruwan sama, sai Amfani dashi kawai suke Amma yau koh tarewa basu samu sunyi ba, ruwan jarka data ibo jiya ta tsiyaye kasancewar tasan tabbas bata da omo bata da kudin su, yasata wanke kayan haka da ruwa zallah ta shanya su.

Ruwa ta ibo takai bandaki duk irin sanyi da ake haka ta kwara ruwan ta fito, dakin ta shiga ganin kulenta rakube yanajin sanyi zani ta d'auka ta lulluba masa, kwanciya tayi akan taburman ta,har bacci ya d'auketa ga kulenta a gefenta shima a kwance.

Nnenna!!!Nnenna! Papane ke kwala mata kira da karfi tun kafun ya shigo falon.

Bude idanunta tayi da sauri jin kiran mahaifin nata, glass nata dake gefe ta dauka ta saka, sanye take da Jess da t-shirt, kod'andu da sauri tafito a d'akin jin ya shigo falon.

"Yes papa barka da dawowa" tace cikin yaren Egbo hade da karban laidan dake hannunsa.

"Yauwa Nnenna ga Abinci saiki ci saya miki nayi a kasuwa yau na d'an samu kudi na sai miki Abinci saikici ai karki mutu da yunwa?

Shuru tayi batayi magana ba ganin yau papa da mutunci ya dawo, harda sai mata abinci zama tayi a falon bayan ta dauko plate, ta bude laidan tuwon Amala ne ta fitar ta juye a plate, bude laidan miyan tayi zata juye sai kuma tasa a hancinta ta tsuntsuna.

Da sauri ta aje laidan tana kakarin amai jin miyar Akwai naman kare a ciki.

Papa dake kallon ta cikin jin haushi yace,kee Nnenna bazakici abincin nan ba kenan again koh dai da gaske ke mayyar ce, naga dai miyace babu nama a ciki koh Alamun nama?

"amma ai miyar naman ce?kuma naman ma na kare ni banzanci nama ba"

Keee mu Egbo ne munacin aladu da kare ke waye da bazakici ba?

"Ni namane kwai banaci koh miyar nama"tace tana Aje miyar a gefe ta kama cin tuwon zallah yayin da papa ke zaune a kan kujera, kallonta yayi sai kuma yace Nnenna?

Yes ta amsa masa

Koh kinsan meya faru da onye da chukwudi kuwa?

Gabanta ne ya fadi Amma ta maze cikin basarwa tace, "no pappa"

Thank god daya kasance babu ruwan ki a maganar nan, babu wanda yace akwai hannunki, kinsan kuwa d'azun da rana onye da chukwudi babban roka tabi kan onye ta markad'a masa kai atake ya mutu, chukwudi kam ya samu karaya uku yana asibiti har yanzun baisan wake kansa ba.

"Mai motar ya tsayane"?

No bai tsayaba gudu yayi, akwai wasu mutane a bakin titin sune suka gaggauta kaisu asibitin cikin Enugu.

"Toh god ya basu Lafiya"

Emeen daughter god bless u yarinyata bata da rike kowa a zuciya duk abinda suke miki a kauyen nan kina musu Addu'an samun sauki?

Shuru kawai tayi tacigaba dacin tuwonta yayinda kulenta ke lashe miyar.

*********************
Ta bangaren Lahab da gudu ya haye Addayiya data ruga gefe ta zauna Amma tsabar masifa saida yabi ta kanta ya haye, Rahab kam gefe yabi.

Da gudu ya bude kofar falon ya

Please Login or Register in order to submit comment