Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Rai aikai farin ciki ya Kamata kayi sai Kuma ta Mike ta shiga toilet tare da banko Masa door,fita yayi a dakin ya wuce flat na Adewale zaune ya samesa Yana karyawa abincin gaban nasa Lahab ya Iba da yawa kana ya koma dakin Nnenna ya aje Mata yabar gidan,haka Suka cigaba da rayuwa kwata kwata Nnenna ta d'auke wuta fadan Mai ciki Bata shiga harkan Lahab abinci ma badon karta mutu da yunwa ba da bazataci ba gashi inta dafa da kanta baya Mata Dadi a Baki amma dataga uwar Bari ci take shi Kuma Bai fasa kawo Mata ba,tun tana dari dari karya sa Mata maganin zubda ciki harta cire tunanin abin a ranta amma Sam Bata yarda sun sake kwana daki d'aya ba ta tatttarasa ta watsar duk lokacin da taji sha'awa na taso Mata saidai ta shiga ruwan dumi shima Bai wani shega harkan nata iyakansa bata abinci akan kari yazo ya duba yanda ta waye gari.




*************
Wasan Lahab ya Fara gaba gaba don yanzun Yana iya barin kasan America ya tafi har wata kasa ball sai dai duk lokacin da zai tafi zai barwa Ade nauyin kula dacin Nnenna Kuma ba laifi shima Yana iya bakin kokarin sa,yau Monday Nnenna ce ta fito daga dakin ta sanye da siker da riga ta dau jakanta ta rataya a kafada sai takalmin ta flat gashinta a sake har gadon baya fitowa tayi daga part nasun ta fito compound na gidan,Lahab dake zaune a waje Yana Shan iska mikewa yayi ganinta tsaye a bakin titi.





Ina Zaki"?kauda fuska tayi ba tare da tayi magana ba,"ba magana nake Miki ba"?Nan ma shuru ta Masa ta tare taxi zata Shiga hannu yasa ya fizgota saura kad'an ta buge da marfin data bude janta yayi Suka koma ciki cikin bacin Rai yace"har zanna tambayar ki kina rainamin wayo Ina Zaki a hakan babu lullubi"kaga Lahab baison surutu da ranan Nan akan me Zan fada maka Inda zani,maganan lullubi Kuma Ni ba musulma bace"dagata yayi sama Suka koma ciki hijab karami ya d'auka ya saka Mata tare da kwace jakan budewa yayi ganin takardun asibiti ne hannunta kawai ya Kama ya rike jakan a daya hannun sa Suka fita daga gidan.




Asibiti Lahab ya wuce da ita aka Mata awo ba karamin shauki ya shiga ba lokacin da likita ke sanar dasu tagwayene a cikin Nnenna amma Bai wani nuna murna a fili ba,wayarsa ya d'auka ya d'auki hoton na'ura daya nuna yaran baro baro Suna kwance gasunan mitsitsi dasu yan 6 month's,kana ya dauketa tana zaune akan gado lokacin likita na Mata bayani ya had'a harda likitan dashi ya d'auki hoto likita sai dariya take don wallahi ita abin ma dariya ya Bata don kwata kwata Basu wuce 19year's ba a lokacin,Suna fitowa Suka samu wata Mata da miji zaune Suna jiran su fita Suma su shiga cikin matan ya girma don zaikai wata 8 sai kallonsu Mata da mijin Suke shidai Lahab baice kome ba ya Kama hannunta Suka fita, saloon ya kaita aka wanke Mata Kai da kafa ya biya duka,don lokacin cikin nata har ya fito ras dashi kowa ya ganta yaga Mai ciki ga jiki data juga Kamar me wuyanta har wani guru guru yayi na jiki ga haske Wanda Bai sani ba zai tsammaci bata had'a dangi da bakaken fata ba.







*********************
Su Lahab an kammala exam na karshen shekara Kuma na chanja aje sun samu dogon hutu na karshen shekara tunda Yan nageria sukaji kammala exam nasu suke sauraron ranan da uban gayyan zaice zasu kamo hanya,Lahab yayi kudi iya kudi yanzun Harya mallake gidan kansa a turai da mototi,sai dai har gobe Basu dawo normal da Nnenna ba lokacin da yaji bukatar matarshi ya tasashi a gaba yaje neman hakkinsa tace batasan zancen ba,shikenan shima ya ajeta a gefe yasa karatu a ga Kuma Alhamdulilah abinda ake tsammani shiya samu yau sati guda da kammala jarabawan,zaune yake a falo shida Ade Suna hiran wasan da Lahab a buga anan Ade ke kawo Masa zancen komawar su gida"gaskiya Ade kayi tafiyarka kawai wallahi Ni bazan iya zuwa Koh Ina ba"




da mamaki Ade yace saboda me"saboda bazan iya tafiya nabar Labiba da cikin 8 month's a jikinta fa,karfa ka manta dogon hutu Muka samu akallah mukai 2 to 3 months a chan nasan halinda zata Shiga bayan babu mu Ina wallahi ah ah"kaga Lahab Bai Kamata ka musu haka ba nasan kana da uzuri a gaban ka amma fa ka sani Suma Suna da hakkin akan ka,Mamu shekara guda Bata saka ka a idanunta ba haka ma Rahab tuni sun koma nageria Kai ake jira"Wai Ade da wani yare Zan maka bayani ka fahimta ne nace maka bazan iya tafiya nabar Nnenna ba"





Amma Lahab tunda Allah ya hore maka why not ka samu wata dattijuwan baturiya ta zauna ta kula maka da ita ko haihuwarce ya tashi ai akwai wata a kusa"wani banzan kallo Lahab ya Masa irin na baka da hankalin Nan"Ade taya Zan bar matata a hannu bayahudiya salon a haifamin yara biyu ta sabe daya ta gudu Koh ace sun mutu saboda da Bata da tsayaye gwara Ina Nan"shuru Ade yayi h?ar Lahab ya gama surutun sa kafun yace"toh nidai Ina kewar kasata Kuma zanje Naga iyayena"Allah ya bada sa'a babu Inda zani harsai Naga gudan jinina a doron kasa"yanzun me zakace musu a matsayin excuse naka"




Cewa zanyi Muna da wasa a France kawai"uhmmmm shine abinda Ade yace Suka cigaba da Hira Nnenna dake cikin kitchen tanajin duk abinda ke faruwa sosai taji zuciyarta tayi sanyi Jin Lahab har yanzun ya damu da lafiyar ta Koda yake ai ya damu da lafiyar ta ya bai damu da lafiyarta ba ai da ta Jima bata gidan sa,ta yarda Lahab na sonta baba Wasa ba.






Allah sarki Lahab bai sanar da gida bazai dawo ba har Saida Adewale ya koma nageria kafun ya sanar dasu sosai ran Mami ya baci tayita fada Akan wasan banza zaiki dawowa hakuri kawai ya Bata,yau tun safe lahab Suka shirya dashi da Nnenna zasu hospital cikin Nan gashinan tirim a gaba sanye take da polon wando sai riga bankacece har gwuwa Mai dogon hannu cikin Nan a gaba gyale tayi rafen nasa a kanta,ta sanya boot a kafarta,Lahab ma sanye yake da kananu kaya,motar ya bude Mata ta shiga Suka wuce hospital,Suna Isa facemask ya d'auka ya sa gudun kada mutane su Soma daukarsu hoto a watsa a duniya ya shiga uku tunda yanzun shima ya Zama popular Koh Ina ya Shiga hotuna ake masa,yauma anyi sa'a sun hadu da mutumin da suke yawan haduwa dasu in sunje asibiti awo matar sa mai ciki Amma ayau sun hadu dasu ne lokacin da suke Shirin shiga mota sai ga Matar da mijinta sai wata tsohowa da baby a hannunta daga gani haihuwa matar tayi Kuma an sallame su,Suka nufi motar su Suma ba tare da sun kula dasu Lahab ba duk da daman duk haduwar su basa magana duk da bakaken fatane sai dai su ringa kallon su Lahab shikuma kallon ke hanasa musu magana tunda barikine kowa zaman kansa yake ba irin Naija bane mutun zaice wane ya ganni Bai gaisheni ba"





Shiga Nnenna tayi Lahab ya shiga Harya tada motar bayan ya zare facemask in fuskarsa sai Kuma ya tsaya ganin motar gayen Taki tashi gashi lokaci d'aya aka Fara yayyafi fitowa sukayi daga motar zasu koma cikin hospital in,da Sauri Lahab ya fito a motarsa hade da musu sallama,da mamaki mijin ya amsa hade da basa hannu Suka sake gaisawa,kafun Lahab yace in babu damu suzo su shiga ya rage musu hanya,tsohowar taso ki amma data ga Nnenna a cikin motar saita amince suka shiga baya gabaki dayan su Lahab yaja mota.





"****************
Kamar nasan fuskar nan taka in ban manta ba Kamar Hassan Lahab Koh?"gyada Kai kawai Lahab yayi,wow gaskiya naji dadin haduwa dakai Ni Sunana Muhammad Auwal wannan iyalina ce Hauwa amma ana kiranta da jidda sai mamata gata ?"nima haka" shine abinda Lahab yace,shuru mutumin yayi ganin Kamar Lahab baison hiran,tsohowar Kam kasa hakuri tayi tace"yaro wannan Yar uwarka ce"saboda ita haka kawai taji ta Kosa Taji menene a tsakanin su tunda matar d'anta tace Mata ai Suna haduwa dasu a hospital sa'i da lokaci Suna zuwa"har Lahab ya bude Baki zaice matar sane Nnenna ta rigashi da cewa"kaninta ne"wani kallo Lahab ya Mata amma baice kome ba yaji matar na hausa da d'anta don a zatonta ko su Nnenna basajin hausa don Basu Mata Kama da Yan nageria ba Nnenna tafi Mata Kama da Yan Ethiopia harda Lahab in ma duk da bakine amma kyakkyawa ne sosai,gulmansu ita da matar suka Fara tana cewa ai wallahi itama Saida tayi tunanin Koh Yan uwane amma meyasa kullum Lahab ke rakota,da Sauri mijin yace"gaskiya mama ya Kamata kuyi shuru babu Dadi Kuma cikin mutane kuma yare zasu tsargu bare Kuma wa'innan da kuka jefawa tambaya.





Murmushi Lahab yayi don yasan Nnenna ba wani fahimtar hausan take ba"mata tsohowan ne tasake jefowa Nnenna tambaya tace"aiko gaskiya yayi tsawon kafa dubeshi Kamar wani yayanki amma ku Yan Ethiopia ne"?haba dan Allah mama kiyi shuru Mata"yaron ya tareta da Sauri Lahab ma juyowa yayi yadan kallesu kana yace"munata tafiya Baku fadamin address naku ba"fada Masa sukayi da mamaki yake kallonsu don kuwa gidan sane manne dana mutumin amma baice musu Suna waje daya ba don baya fatan yayi makwantaka da tsohowar Nan sarkin surutu.





Wuce kofar gidan sa Lahab yayi ya tsaya a kofar gidan mutumin bude kofar sukayi Suka fiffito mikawa tsohowar laima Lahab yayi dake cikin motar sa gudun sanyi kada ya Kama babyn,sai a lokacin ya musu barka da samun haihuwa itama Nnenna ta musu barka harda karban baby tayi ta kalla kafun ta maida musu, number Lahab mutumin ya karba Yana ta godiya kana Suka shiga ciki Lahab Kam reverse yayi ya nufi nasu gidan.




tunda cikin Nnenna ya shiga wata tara shikenan Lahab ya tattara wasan kwallo ya aje a gefe ya koma zaman gida tunda babu makaranta Suna jiran lokacin haihuwarta,yau tun safe lahab yace Nnenna ta shirya bayan sunyi breakfast shiryawa sukayi ita dashi Suka fito zasu fita sayyayyan kayan yara da zasu sayo yayi-yayi ta Masa list yaje shi kadai tace shida baya kaunar yaran yake ba tasan bazai sayo Abu Mai kyau ba,lokacin da Suka fito compound ganin da gaske zata bisan yasa da tsayawa yace"Amma so kike kije ki haihu a hanyane Koh"ai Dr yace saura 2 weeks"da dariya yace waike kin amince da maganar Dr Koh yau in Allah ya nufa Zaki haihu"da masifa tace koma me zakace kace sai make"abinka da gidan turawa na wancan gidan na kallon na wannan kawai cikin magana sukaji an kwala Masa Kira Yana juyawa da mamaki ba kowa bane sai tsohowar Nan tsaye a baranda tana murmushi tare da tafa hanneye daga nesa yaji muryarta Kamar Ansa lasfika tsabar karfi tana cewa"daman Nan ne gidan ku D'an ball ban sani ba ai dana ringa shigowa na huta da zaman kadaici, Kanna kowa saina ringa zuwa wajen mamanka...............................








*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*



Wai menene haka don Allah meyake damunki"?girgiza Kai tayi tana kokarin kaucewa zata aje laidodin sake Mata hannu yayi ya kwace laidan yaja hannunta ya Kamota Zama yayi da ita a bakin gadon shima ya zauna kana yace"Wai meke faruwa ne na ganki cikin damuwa Kuma kincemin babu kome"?matsa Mata yayi lalle saita fada Masa meke damunta kuka ta fashe dashi sosai cikin Sauri ya rungumeta gam a jikinsa ya koma baya-baya ya kwanta da ita a jikinsa,Yan@ kwance a dollof ita tana kwance a kansa,hannu yasa ya kashe wutan.




Labiba"ya Kira sunan ta a hankali kin amsawa tayi har lokacin hawaye bai tsaya a fuskarta ba,a hankali ya manna bakinsa a kumatunta hawayen Nata yake lashewa,lumshe Ido tayi tana d'an sake jikinta a nasa sosai ya lashe hawayen tas Kuma hawayen ya daina zuba,dan Jan lips nasa yayi a fuskarta har zuba gefen lip's nata sannan ya tsaya Yana bin fuskar da kallo,idanunta a lumshe suke jira kawai take taji saukan lips nata a nasa amma taji ya tsaya cak,dan bude idanunta tayi sai Kuma da Sauri ta kauda nata saboda tsayuwa da yayi kawai Yana kallon ta,"kin koshi da abincin Koh a kawo Miki wani"?girgiza Kai kawai tayi batace kome ba,sakin murmushi yayi a hankali ya zamar da ita a jikinsa ya kwantar tare da gyara Mata rufuwa shima ya rufu tare da kamo hannunta ya rike Yana bin fuskarta da kallo kawai.




A hankali ta matso kusa dashi tare da manna jikinta a nasa,waro Ido yayi da mamaki sai Kuma yasa hannu ya dagata jabal ya daura a kansa,lip's nata ya Kama amma bai tsotsa ba kawai mannawa yayi da nata,dan Jimm tayi sai Kuma ta Kama lips nasa na kasa cikin sanyi ta tsotsa,Kama nata yayi Suka hau bawa juna hot kissing sosai salon wasan ya chanja duk wani kunya kunya gabaki dayansu ajesa sukayi a gefe sosai Lahab ke sarrafa matarsa yayinda ita Kuma ke basa goyon Baya dari bisa dari,lokacin da kome ya kankama Lahab yasha mamaki matuka Kuma ya rude don dadin da yaji na yau ya d'ara na Ranan dadin da yaji sosai.




Lokacin da nutsuwar sa ta samu kokarin tashi yake a kanta da Sauri tasa hannu ta Kama waist nasa gam,Wanda hakan ya fahimtar dashi cewa itama tana bukatar nutsuwarta duk da akwai mutuwar jiki da gajiya a jikinsa hakan baisa sa kasa tallafawa matarsa ba sosai ya tallafeta har ta samu natsuwa,mikewa yayi a hankali ya d'auki towel NASA wanka yaje yayi kana ya fito mikewa tayi itama ta shiga toilet in kafun ta dawo Harya chanja zanin gadon ya kwanta,tana fitowa Zama tayi daga ita sai towel,shuru shuru yaji Bata hau Kan bed in ba kallonta yayi kana yace"lafiya bazaki kwanta ba kinsan karfe nawa yanzun"?shuru ta Masa Bata hauro Kan gadon ba,shima Bai Kara magana ba ya gyara kwanciyar sa so yake ya samu bacci kafun asuba don gobe Suna da training da sassafe,amma kasa baccin yayi ya sauka akan gadon d'aukarta yayi gabaki dayanta yazo ya kwantar akan gadon ba tare da ya damu da towel in jikinta ba ya lulluba Mata blanket.



************
tashi tayi ta zauna again Wanda hakan ya saka sa sake tashi agogo ya gani kusan 2:30 na dare tsaki kawai yayi yace"Wai don Allah wannan ai d'aukar alhakine ya Zaki kasa bacci ki hanani nima"?a fusace tace"toh ninace maka karka kwanta ne"toh Taya Zan kwanta kina zaune"a hankali tace"yunwa nakeji"wani kallo ya Mata sai Kuma ya tashi tsaye hannu yasa ya taba jikinta Jin sanyi babu zafi yasa sa komawa ya kwanta abinsa Bai Kara magana ba ya barta a zaune bacci barawo yayi awun gaba dashi.






da asuba Lahab daya farka da mamaki Nnenna ya gani d'aure da towel Kamar yanda ya kwanta ya Barta idanunta biyu da mugun mamaki yake tambayar ta Wai Bata kwanta ba?kin amsa Masa tayi yasa hannu zai tabata kawai ta turesa Saida ya koma Kan katifa ya kwanta,bata Kara magana ba shima gyada Kai yayi irin lallai innan ma, ya mike Alwala yayi yazo yayi sallah duk tana zaune,Kaya ya chanja ya fita waje da asuban amma shuru babu kowa shaguna duk a rurrufe dakin wani makwancin sa ya shiga yadau fresh milk guda biyu ya kawo Mata kin karba tayi Wai tayi fushi daker ya samu ta karba tana Sha Koh aje goran batayi ba ta Soma amai Kamar zata amayar da hanjin cikinta sosai tayi aman lokaci d'aya wani irin zazzafi ya rufeta,daukarta yayi ya Kai toilet tare da wawwanke Mata jikinta ya fito da ita, Kaya ya sanya Mata ya kwantar da ita akan gado kafun yazo ya gyara wajen da ta batan.




Wanka yayi da misalin karfe 6 zuwa lokacin wani irin bacci yayi gaba da ita so yake suje asibiti Kar ciwon yayi tsananin amma ganin tana bacci tunda bata samu na daren jiya ba sai yayi tunanin bari ya barta sai ya dawo,kayan ball yasa wando da riga sai takalmi ya fita a dakin, direct training ya wuce basu Suka bar wajen ba sai kusan 9 na safe daga wajen wajen Saida abinci ya wuce kaza yasai musu sai kayan ciye ciye na laida Incase kada ta bukace Abu lokacin da bazai samu ba shiyasa ya sama Mata irin su cake su pizza duk ya sassaya sosai ya Mata sayayya.





Lokacin da ya dawo ya samu ta farka zaune take gabaki d'aya ta jirkita ganinsa da laida Koh barin ya ajiye batayi ba ta kwace tare da budewa cake Inda ta gani a ciki shita warware da Sauri ta Soma ci ci bana Wasa tama cake in ba,shidai Lahab idone nasa ba bakin magana amma yasan tabbas Bata da lafiya wallahi irin wannan haukan cin Kamar Wanda ta shekara da yunwa,Kamar d'azun da asuba tana gama ci sai amai,ganin haka yasa Lahab cewa ta tashi su tafi asibiti amma kai da fata Nnenna tace ita lafiyarta klau babu Inda zata,taba jikinta yayi yaji babu zafi Kamar d'azun, tambayar ta abinda zataci yayi tace apply,mikewa yayi yaje ya jido apply kwali guda fresh dasu yazo ya jera Mata a daki Aiko shikenan Nnenna ta samu abinci Bata da aiki saicin apply tunda kome taci amai yake sata Amma Banda shi.





Lahab yaga ikon Allah gabaki d'aya Nnenna ta sauya ta Zama mabukaciya don tun tana kunyarsa tana jiran shiya Fara tabata Harya kasance ita ke nuna tana sonsa a aikace ba'a bayyane ba,shima Yana iya bakin kokarinsa wajen sauke nauyin da Allah ya daura Masa akanta Koh da kuwa baya mood,ga cin apply ga fad'a fushi da mita duk yanzun Nnenna ta koya cikin satin da sukayi harta chanja Sosa ga yawan zazzabin asuba da kuma yamma, sai yace su tafi asibiti tace bazata ba suyita fada Harya hakura ya kyaleta.




Sun samu nasara sosai Lahab Yayi bajinta a wasan da suka buga yasha musu sosai,hakan yasa sa daukaka sosai,sun koma gidan su,sannan team nasu sun basa kudi sama da million biyu cikin abinda Suka samu saboda bajintarsa cikin kudin ya baiwa Ade have million sannan ya turawa Rahab 300k ya baiwa uzaifa 200k tunda Sunsan Inda kudin ya fito lokacin da ya tura musu basuki amsa ba account ya Kai Nnenna ta bude ya zuba Mata kudin da shayibu ya basa nata kana ya Kara Mata 100k a ciki,Lahab a sannu sannu ya Fara Zama sannan ne a fagen kwallon kafa don sosai ya iya buga wasa hakan yaja Masa farin jini da daukaka har yasa wasu team Fara daukar sa haya Yana buga musu Wasa ba tare da sun damu da kankantar sa ba kudi kuwa sosai ya Soma damkarsu sosai Kuma Alhamdulilah Lahab mutum ne da baida gyashi kome ya samu sai ya tsamma Rahab dake India da uzaifa haka zalika zaisa wa Nnenna a account nata duk da Bata cin Koh sisi haka zalika Adewale don yanzun tuni Suka bar gidan da suke lahab ya Kama musu gida Mai zafi wadacece Suka koma ciki don wani sa'in sai afi wata Ade Bai hadu da Nnenna ba waje d'aya sai in ya shigo part nasu Lahab ga moto Lahab ya saya ya saima Ade duka rayuwa tayi Dadi bana Wasa ba tuni papan Ade yayi sanyi lokacin da ya kawowa Ade ziyara yaga yanda Allah ya daukaka Lahab Kuma Yana taimakon dansa har dawainiyar makarantan Ade yanzun Lahab keyi,Amma tuni ya manta da zancen wani Nabeel don tunda yazo kasan Bai taba kiransa ba saidai in Suna waya da Ade in Yana gun shine inya tambaye shi sai Ade yace gashinan su gaisa.





Lahab sun koma makaranta tuni har semester yayi nisa yaso yasa Nnenna a makaranta Amma babu Hali tunda Bata da shaid'an takardun Gama secondary,ga rigimar da take fama da ita nata na masifa ga yawan ciye ciyen kayan fruit don yanzun tabar apply ta koma kankana da mangoro Koh Kuma abarba.




Lokacin da labarin Lahab ya Fara zaga katsa tuni Yan nageria Suka Soma Jin labarin sa wani Dan naija best footballer Kuma very young a turai gashi da farin jini bana Wasa ba duk channel na sport ba'a rasa nasa a ciki,lokacin da labari ya Fara riskan Mami tunda ba kallon kwallon take ba sai Yan uwa ke kiranta Suna cewa sunga Lahab na ball a TV koransa tayi tana Masa fada akan an turasa karatu yaje ya Kama abinda bazai amfane saba Bata yarda ba,Aiko waya yayiwa Abbu ya sanar dashi dare da Masa Alkawarin insha Allah zai kammala karatunshi tare da sakamako Mai kyau daker dai Abbu ya sauko ya baiwa Mami hakuri ya cigaba da Wasa tunda sunga kokarin da yayi a karatu.






tun safe Lahab ya fita Bai dawo ba saboda Wasa da suke bugawa Mai zafin gaske bashi ya dawo gida ba sai kusan 2 na dare,shigowa falon yayi ba tare da ya kunna wutan ba ya wuce sait nasu bude dakin su yayi ya shiga da sallama,dan waro Ido yayi ganin wutar dakin a kunne ga Kuma Nnenna kwance a bargo"Kai amma yarinyar Nan bakiji taya Zaki kwanta da wuta a kunne"kashe wutan yayi ya zaro tafkeken wayarsa dake bag dake bayansa ya kunna hasken waya aje bag in yayi yadau towel ya nufi toilet wanka yayi kana ya fito,daure da towel in kayan bacci yasa ya fita a dakin kitchen ya wuce ya tare coffee nasa Mai zafi ya zauna a dinning dake cikin kitchen in ya Soma Sha Saida yasha Rabin cup kafun ya mike.




d'akin ya shiga tare da matsowa kusa da gadon hannun sa yasa ya warware blanket Inda ta lulluba zai kwanta da Sauri ya sake blanket in, saboda turirin da yaji ya fito daga cikinsa har yanajin wucin numfashinta Mai zafi Ashe idanunta biyu sai rawan d'ari take hannu yasa ya tabata da Sauri yaja baya zafi jikinta jaujau"subhanallah Labiba tun ba yauba nasan baki da lafiya amma rashin jin da Kika kakkabawa kanki yanzun ya hanaki Bari muje hospital"?kasa amsa Masa tayi bakinta ya bushe sosai hakoranta har haduwa suke da juna,mikewa yayi da sauri ya nufi wardrobe nata budewa yyi ya dauko Mata wando da riga amma irin bujennan masu Fadi yasa Mata hijab ya dauko cikin Wa'inda ya sai Mata duk da ba amfani yake dasu ba Kuma hijab in irin have Sunnah ne.






A daren nan Lahab ya dauketa sai Wani hospital Mai tsada, a cikin daren Nan aka amsheta zuwa lokacin zazzabine yaci karfinta sosai ruwa Suka daura Mata tuni tayi bacci sai gwaje gwaje da aka mata,a asibitin Lahab ya kwana tare da ita tana farkawa da safe ta Fara Neman abinci Kuma ta tashi garau abinta,fita yayi ya sai Mata abinda zataci taci kana aka sake daura Mata ruwa.




8:21pm zaune Lahab yake a Kan kujeran dake dakin dayake kowani mutum d'aya dakinsa ne guda ba'a had'a wani da wani zaune take ta tasa kaza a gaba tana ci hannun ta d'auke da ruwa a makale, don Koh barin a cire batayi ba ta Soma ci shi Kuma Lahab ya Barta Bai Kira nurse ba gudun kada ace ya kawo cinnedu amusu dariya,wayarsa ne yayi Kara zarowa yayi yayi picking up"Lau Ade Labiba ce babu lafiya Muna hospital amma karka damu fa jikin da Sauki sosai"yayi shuru Yana sauraran abinda Ade ke cewa sai Kuma yace"no ka tafi school kawai yauma sukace zasu sallame mu basai kazo ba sai Kuma ya katse wayar"Kara kallonta yayi ganin tana tauna kashin kaza"Amma wallahi kin chanja haba Dan Allah kece ci Kamar me Amma Baki karuwa sai ma rama da kikeyi sai haske amma dai ba kome hips da breast sun ciki"?





Kala batace Masa ba dan yanzun Sam babu irin kunyan da a tsakanin su bare taji kunyar sa Koh kunyar abinda yace"amma dai da ace bakicin nama har yanzun da anyi babu ke tsabar dadi

Please Login or Register in order to submit comment