Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

especially matasa The great footballer zai ziyarce kasar sa na haihuwa, ayau ga Family ma gabaki d'aya Suna cikin annashuwa Kiran waya Kam Lahab Harya gaji dashi Wanda abokai ke Kira su Kara tabbatar da zuwan nasa a yau ne,shigowa dakin Nnenna tayi ta Shiga toilet ta had'a Masa ruwan wanka kana ta fito tana cewa Koh Ta fasa tafiyar ne,lokaci nata tafiya baida niyar tashi yayi wanka.





Mikewa yayi ya shiga ban dakin wanka yayi ya fito ta taimaka Masa ya sanya tsadadden wani sport wear wando dogo na roba sai riga a ciki ya Kara da jacket,boot ya sanya a kafarsa ya dau hulan sanyi ya rufe Arnen askin dake kansa irin na Yan ball,kallon matarsa da yaransa dake Kan gadon yayi tana zaune tana kallon sa,masowa yayi ya manna Mata kiss a kumatu,d'an hararansa tayi tace"sai ka makara Koh? Ade na jiranka a falo tun d'azun na fitar maka da bag's naka tunda baka son akwati"nafasan zakiyi kewata Koh ince kin Fara ma tun yanzun"hawaye ne ya gangaro Mata da Sauri tasa hannu tana kokarin gogewa Kama hannun yayi ya manna lips nasa a fuskar ta ya tsotse hawayen"duk lokacin da kikayi kewata ki kirani ban yarda kimin asaran hawayen kiba"?





Gyada masa Kai tayi kana ta Mike tsaye sanya hijab tayi da Sauri ya kalleta yace"Ina Zaki Kuma"?zamu rakaka airport"no basai kinje ba kinsa ansan Zan bar kasarnan yau so dole zamu Hade da Yan jarida don haka ki zauna kawa"da Sauri ta dau nazeefi shi Kuma yadau nazeefa tace"muje na rakaka Koh compound ne toh"fita sukayi a dakin Ade Suka samu a falo sai duba agoge yake ganin su yasa sa mikewa tsaye ya fita waje Suna binsa a baya Muhammad da jidda ne Suka Shigo Suka musu sallama kana Lahab ya baiwa matarsa nazeefa hade da shafa Kan yaran ya shiga mota Ade yaja Suka bar gidan cike da Kewan juna.







NAGERIA
5:30pm jirgin su Lahab ya sauka,bag's nasa guda biyu ya d'auka ya goye daya a baya ya rike daya a hannu kana Ade na d'auke da nasa kowa ya gansu yaga zaratan samari masu ji da naira da tashen kurunciya,sauka Lahab Suka Soma daga steps Yana sanye da bakin glass a fuskar sa ga gemun Nan ya cika yasha cum taku suke da Ade a hankali Suna saukowa,Aiko Nan hasken camera ya Soma haskasu ji kake rass rass kess kess,hannu Lahab yasa a hankali ya dan Kare fuskar tasa sai Kuma ya sake hannun nasa Yana kallon jama'ar da aka Bari suka shigo filin saukar jirgin,,tunda yake a rayuwar sa Bai taba zaron zai Zama wani haka ba.



Fitowarsu waje tuni Yan jarida Suka rude da jefo musu tambayoyi shidai Lahab Koh daya Bai amsa ba sai jifa jifa Ade na Basu amsa kasancewar abotar dake tsakanin su yasa duniya tasan da Ade na hannun daman Lahab ne"d'aga Ido Lahab yayi Nan ya sauke akan Anmar da Shareef harma da umaima dake ta washe Masa Baki da Sauri Shareef ya nufesa jakan sa ya karba shi Kuma Ade ya nufi papa daya nufosu gaisawa sukayi cikin mutunci da Lahab kana Ade yabi mahaifan nasa shikam Lahab duk rungumar yayan dan uwan nasa yayi cikin farin ciki da kaunar juna Suka rungunsuma sai unguwan su.





Hira kawai ke tashi a motar kowa na zuba Inka cire Lahab da in sukayi magana sai dai yayi murmushi kawai Shareef sai cewa yake Ashe da rabon Lahab zaiga bukin sa shidai Lahab nasa murmushi ne,kawai surutu da tsokana irin nada duk sun ragu kad'an sai fara'a ga wani irin chanjawar da sukaga bawan Allan nan ya musu gabaki d'aya Lahab ya cika ga Kiran karfi naira da wayewa sun Kara ratsashi sosai,tunda aka nufo layin nasu yakebin koh Ina da kallo babu abinda ya sauya sai abinda baza'a rasa ba,horn Anwar yayi Mai gadi ya bude gate in Suka Danna mota ciki, fara'ar sa ta Kara fadada ganin ahlinsa gabaki d'aya sun fito tsakar gida Suna tsumayen isowar sa sauka yayi a motar a hankali idanunsa suka fada ana Mami dake ta murmushi,da gudu yaji an rungumesa ta baya Yana juyowa yaga dan uwansa Kara rungumar juna sukayi Sosai very tight na yaushe gamo.





Zazzaune suke a falo sun tasa lahab a gaba Addayiya Kam sai kuka take gwanin tausayi,tunda Lahab ya shigo gidan saboda wani irin change da yayi gabaki d'aya kamannin su da Rahab yaja baya kad'an yanzun mutane zasu iya Ganeshi saboda d'aga karfe da buga ball da Lahab keyi jikinsa ya fi nadan uwan sa ciki,mikewa Lahab yayi yazo ya rungume Addayiya sosai Yana Jin kaunar tsohowar har cikin ransa,hannu yasa Yana share Mata hawaye yace"Wai Baki murna ne tsohowa na dawo Anya kinaso Inna koma na sake dawowa Kuwa? tunda kuka kike,da Sauri tace"ah ah kukan murna ne Kuma bazan Kara ba"?dariya kawai Yan falon Suka sake Mami kauda hawayen idanunta tayi cikin happy.





Lahab bayan ya fito wanka masalanci ya wuce shida sauran mazan dake gidan,Yana dawowa aka zauna cin abinci ana ta Hira gawanin ban sha'awa ga umaima da baby boy nata dan shekara kusan biyu da watan Ni haka ma Aisha yarta ta girma,Yusuf in Mami ma an girma Allah sarki dayake Rahab na dawowa hutu shiyasa Bai wani ki Lahab ba.





Kwance Lahab yake da Rahab a daki sai Hira Rahab ke Masa ya Masa na wancan ya Masa na wannan shima Lahab ya sake jiki sai Hira yake har bacci ya dauke rahab,wayarsa Lahab ya zaro ya kunna ganin karfe 12 na dare ne yasan zuwa yanzun safiya ne Kiran ta yayi da sauri ta d'auka vedio call Suka ringa Hira ta jera Masa yaransa a screen ya kalle su kafun sukayi sallama lokacin har 2 na dare yayi ya kwanta bacci ya dauke sa,washe gari da safe bayan dawowar su sallah Lahab bacci ya koma bashi ya tashi ba sai kusan 10 na safe ya fita ya karya tare da gaida jama'ar gidan.





da yamma ligis Lahab na kwance a falo sai Jin surutan samari yake a kofar gida ba'a Jima ba saiga Mai gadi Wai dandazon yaran dake team nasu Lahab ne suka had'a zuga sunji Hassan Lahab ya shigo kasa amma Mai gadi ya hanasu shiga Koh tsakar gidan,mikewa Lahab yayi ya sauya Kaya ya fito Aiko Yana turo gate in wani irin ihu matasan Suka sake har Saida suka cika unguwan da muryoyinsu Wanda yasa wasu Mata masu gulma fiffitowa su baiwa idanunsu abinci.





Kudi Lahab ya zaro ya mikawa wani babba a cikin su yace a raba Aiko zo kaga Kura shikam tuni ya wuce cikin gida ya barsu Suka gaba gurnanin su suka watse.




Lahab ya zaga cikin dangi sosai babu Inda Bai zaga ba har wajen mama yaje(maman Muhammad) Kuma duk inda yaje sai ya Mika musu wani Abu duk da suna da arziki Amma akace Mai baka yanaso a basa haka Mai arziki baikin kyauta duk dukiyar sa, Adewale yazo wajen Lahab Yana tambayar sa Koh Nabeel yazo wajen sa, amma Lahab yace ah ah baizo ba,Ade yayi yayi dashi akan suje su gaida Inna amma Lahab yace bazashi ba,sai ya zauna sosai yake kewar matar sa don a kalla Suna waya sau biyar a Rana wani lokacin in Bai samu lokaci ba cikin dare ma suke waya.





Satin Lahab daya a nageria ya tada maganar komawa Nan Abbu yace waneshi Bai Isa ba sai ya kammala hutun sa duka amma Lahab yace shikam gaskiya zai tafi Yana da wasa,Mami ta rantse bazai koma ba sai yayi wata biyun nan,anyi auren Shareef a idon Lahab Kuma Alhamdulilah biki anyi an gama lafiya satin Lahab yanzun uku da zuwa nageria,kawai su Abbu suka waye gari babu Lahab ya tattara yanasa yanasa ya gudu basuma San da zancen ba sai da suka ga Bai kwana a gidan ba,ran Mami ya mugun baci bana Wasa ba lokacin da Rahab ya sanar da ita,Kuma ta kudiri aniyar Lahab na kammala karatu bazai cigaba da Zama a wajen ba.





Nnenna Karan kanta Bata san da zancen dawowar sa ba kawai cikin dare ta gansa ya diro ba karamin mamaki Tasha ba,da ta tambaye sa lafiya yace lafiyar kenan kewarta yayi.





Babu Wanda ya Kira Lahab daga gida akan gudun nasa haka zalika shima Bai Kira kowa ba sai dan uwan sa hatta Ade baisan da maganar guduwar sa ba sai bayan ya tafi,Kuma Bai kirasa ba.




Adewale ya kammala hutun sa lafiya ya dawo sun cigaba da karatun su yaran Lahab sai girma suke dad'awa da wayo.







*****************
Yau tunda Nnenna ta tashi takejin zuciyarta na tsinkewa Wanda Bata San dalilin ba, breakfast suke a dinning su biyu sai yaran su dake zaune a falo Suna Wasa,kallon ta yayi yace"Wai wife meke faruwa ne tunda Muka tashi da safe Naga Koh kuzari Baki dashi wanka wannan yau Nina ma yaran Nan gabaki d'aya na ganki lagwas"?gashi yanzun ma tunda muka zauna breakfast na kusan tada plate nawa ke Koh spoon biyu Mai kyau bakiyi ba"?Dan ajiyar zuciya ta sauka kana ta zame tagumin dake kumatunta tace"wallahi dear tunda na tashi yau nakejin wani irin faduwar gaba da damuwa Wanda Ni Karan kaina bansan dalili ba"?




Uhmmm toh Allah ya rufa asiri kinsan wani lokaci shedan ma na haka sai ya saka maka faduwar gaba"gaskiya ne amma wallahi na rasa peace of mind Ina ji Kamar wani Abu na Shirin faru..........."kul karki Soma babu abinda zai faru damu sai Alkhari"gyada masa Kai tayi Suka cigaba dacin abincin badon hankalinta ya kwanta ba mikewa Lahab yayi bayan ya goge bakin sa ya dau school bag nashi Yana Mata sallama Harya sa hannu zai bude kofa yaji anyi knocking,budewa yayi da mamaki Muhammad ne da gani Kuma hankalin Sa a tashe yake"Lahab kana da labarin abinda ke faruwa kuwa? da Kai kuwa a nageria"rass rass haka gaban Lahab ya Fadi amma yayi ta maza yace"subhanallah meke faruwa"?




rike baki Muhammad yayi yace"Ina wayar ka"a fusace Lahab yace wani irin Abune haka in zaka gayamin ka fadamin Ni wayata tun daren jiya da aka damen da Kira cikin dare na kashesa Kuma yanzun makaranta zani"uhmmmm wayar sa Muhammad ya zaro ya daddanna kana ya mikawa Lahab,amsa Lahab yayi sai Kuma ya zare Ido sosai Yana kallon screen in, a hankali ya koma baya-baya ya Mannu da jikin kofar falon wani irin zufa na karyo Mata a hankali ya Soma furta kalmar innalilahi wa'inna'ilahu raji'un,tare da sulalewa ya zauna Muhammad ya karasa Masa"Adewale ka cuceni"shine kalmar da ya Fara fitowa daga bakin Lahab ransa yayi mugun baci har jijiyoyin fuskarsa Suka tashi baro baro.




da gudu ya fito daga flat nasa ya nufi nasu Lahab hannun sa d'auke da waya cikin tashin hankali turus yayi ganin Lahab zaune dabas a kasa ga Muhammad a tsaye a kansa,nufar Lahab yayi Yana cewa"mun shiga uku Lahab kasan cewa................kasa karasa maganar yayi saboda wani irin mugun kallo da tunda yake da Lahab bi taba tsammanin Yana da irin Saba,shiya maka Masa tare da mikewa ya cakumo kwalarsa da karfi..........................................






*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*




Adewale meyasa zakamin haka meyasa"sakeni Lahab muyi magana wallahi kaji na rantse maka Ni bansan yanda akai hotunan Nan suka fita ba"in baka sani ba toh waya fitar kenan waya fitar kenan"?Kaine dai ka d'auke hotunan Nan Kuma a wayar ka suke wazai fitar"?




Muhammad sai kokarin kwace kwalar Ade yake a wuyan Lahab amma Abu ya gagara Jin ihun tsawar Lahab shiya saka Nnenna saurin fitowa,da gudu ta nufesu tasa hannu tana ma Lahab magana akan ya sake Ade amma Lahab yaki data shiga tsakani suma bangajeta yayi harta kusa faduwa"don Allah Lahab ka sakeni a zatona jimawar da mukayi Koj Wani akace maka nama haka bazaka yarda ba Kuma zaka tsayamin akan gaskiya ta amma yau Ni nake rantse maka ka kasa yarda har kana rikemin kwana"Ade yace cikin damuwa don shi yasan dai bbu Wanda ya nunawa hoton Nan.




Jikin Lahab yayi sanyi a hankali ya sake Masa kwalar sa ya koma ya zauna anan bakin baranda ya rike kansa"tambayar abinda ke faruwa Nnenna tayi? wayar hannun sa Ade ya Mika Mata,amsa tayi"hoton sune ita dashi lokacin da take da ciki Suna tsaye a tsakar gida sai Kuma wanda aka d'auka a hospital ranan da ta haihu duk su biyu da yaran su, sai Kuma Wanda aka d'auka Suna zaune a falo Koh wata biyar hoton baiyi ba, posted nasu akayi tare da dogon sharhe Kamar haka"shahareren dan wasan kwallon kafan Nan Wanda akafi sani da Hassan Lahab mazaunin America a yanzun an gano yana tare da wannan makashiyar Nnenna obinna tsohowar class mate nasa Wance aka taba kamasa akanta na zargi, Suna zaman dadiro harda yara biyu ba tare da sanin iyayen su ba.





Kuka Nnenna ta sake da karfi shikenan abinda suke gudu ya faru amma Koda sunan Wasa Bata taba tunanin ta wannan tsigar asirin nasu zai tonu ba"matsowa yayi kusa da Lahab tasa hannu ta rike nasa a hankali ta Soma magana"Lahab ka sani daman irin wannan Rana na zuwa duk boye boyen mu Koh guje gujen mu amma nima banji dadi datazo ta wannan tsigar ba,amma ka sani dai-dai da Rana daya ban taba kawowa raina Ade zai aikata Abu makamancin haka ba,wata kil wani ne ya aikata hakan saboda ya shiga tsakanin ku karfa ka manta ba kowa keson ka da Ade ba bugu da Kari Ade ya riga ya zamo wani bangaren naka bai cancanci haka ba"



Tsungunawa Ade yake da niyar yi zai baiwa Lahab hakuri da Sauri Lahab ya tarosa hade da rungumarsa Yana bubbuga bayan sa a hankali yace"kayi hakuri abokina raina ne kawai ya baci amma tabbas nasan Wanda ya aikatamin wannan Abu Kuma na Jima da gane sa, fuska biyu garesa shiyasa na yakiceshi a cikin rayuwata amma wannan Karo Zan basa mamaki"da Sauri Ade yace"waye kenan"girgiza Kai Lahab yayi ya sake Ade ya Shiga cikin falon binsa sukayi a baya zaune suke dukan su Muhammad da kansa ya kulle tambayar su yayi daman ba aure Lahab sukayi ba?,anan Adewale ke warware Masa kome sosai yayi mamakin abinda Lahab yayi Kuma sosai ya Masa Nasiya akan rashin Jin da yake dakin Jin maganar magabatan sa,haka zalika ya basa shawara akan boye boyen Nan ya Kare ya tinkare iyayen sa da maganar kawai Kai tsaye ya fad'a musu gaskiya.





Amma Muhammad kana ga babu matsala kuwa kasan fa ita Nnenna zargin kisane akan ta komawar su nageria babban hatsarine fa gwara ya zauna anan maganar tayi sayi kafun Nan,hakaKo akayi Muhammad sosai ya musu wa'axi jikin Lahab yayi sanyi sosai haka itama ta shiga damuwa wayarsa Kam Sam Bai kunna tanaba daren ranan Koh bacci Bai samu ba washe gari ya tashi da zazzabi Mai zafin gaske da ciwon Kai duk yanda taso suje clinic ki yayi yace bazashi ba.





Magana tayi girma a nageria Koh Ina ka leka zancen ake, ashe daman Lahab da yarinyar Nan Suna tare amma yayunsa sukayi tsayuwar daka da naira aka sakesa magana sosai tayita karade Koh Ina da Koh Ina,abinka da nageria babu Inda zaka zaga babu hoton Lahab da family sa,ga case in Nnenna ya Zama sabo, nageria ta Mika bukatar ta ga America na son kamo Lahab a dawo dashi amma Suka kasa samun daman hakan saboda matukar amfani da Lahab yake dashi agunsu haka zalika sukace au Basu da kundin laifinsa Koh daya haka Kuma su a wajen su haihuwa ba tare da aure ba ba abin tashin hankali bane,dole nageria ta hakura yau kwana uku da faduwar abin Lahab Kam ciwo yaki ci yaki cinyewa zazzabi yaki sauka da ciwon Kai ga nazeefa ma na fama da ciwon ciki amma Ita Nnenna ta kaita hospital Kuma jikin nata da sauki sosai.




daren yau Kamar bazai Kai safiya ba saboda yanda ciwon ya tasar Masa ga amai duka, hankalin ta ya tashi Kuma ta tsorata da ciwon nasa don duk yabi ya rame, tunda abin ya faru Koh abinci baya ci sai ruwa,kuka ta sanya Masa da asuba akan kin zuwa hospital da yayi gashi Yana tashi zaije yayi Alwala ya Fadi a toilet,gari na wayewa ta sanya Sabon kuka tare da Kiran Ade yazo tare da ita da Ade Suka basa Baki daker ya yarda Ade zai rakasa suje hospital in,Kaya ya sauka Suka tafi,lamarin kasar turawa su abinda ya faru bai wani Zama abin magana ba Koh labarin abin ba'a Yi,daga isan su Lahab aka kamasa a gado tare da daura Masa laidan ruwa da allurar bacci saboda tsawon kwanaki daya d'auka Bai rimtsa ba.






Sai yamma lis aka sallamo sa daga hospital in Suka nufo gida,tunda Suka tinkaro gidan nasu yakejin wani irin mummunan bugawar zuciya,kamar zatayi tsalle ta fito daga kirjinsa amma sai Kara maimaita kalmar innalilahi wa'inna'ilahu raji'un kawai yake Yana dafe da kirjin,a hankali ya malle marfin motar ya fito a sannu yake takawa Kamar zai Fadi da Sauri Ade yasa hannu ya bude Masa kofar falon yana binsa a baya da laidan magani,turuss yayi ya Lahab ya tsaya a tsakar falon tare da durkusawa daga tsayen da yake zuwa zaune,saboda mutanen da ya gani a falon"Mami ce da wata kawarta Mara mutunci,ga Nnenna zaune akasa Kamar wata marainiya ta wufi y'ay'an ta a gaba Kamar kace kit ta ruga da gudu"karaso bakin munafuki algungumi d'an iska"Mami tace tana mikewa tsaye cikin kakkauran murya tayi maganr babu Koh dogon sassauci a cikin furucinta.





Hawaye ne ya cika a kunyan idanunsa amma ya kasa daga kafarsa daga Inda yake"bazaka karaso bane Koh Sai Nina karaso"?mikewa yayi a hankali ya taho gareta dukawa yayi akan kneel nasa ya riko kafarta kana ya bude Baki da niyar baiwa mahaifiyar tasa hakuri ji kake kauuuukauuuukauuuuu Mami ta wankesa da wasu irin razanannun Maruka masu gusar da tunani take hancin Lahab ya fashe saiga jini Shaaa,Bai damu da jinin ba ya sake yunkurin Kama kafafunta kafar tasa ta hankad'asa gefe.




Sai da ya buge da center table,da gudu yaransa suka nufi uban nasu Suna kuka tun ihun farko da Mami ta daka Masa, Suka tsorata suka Soma kuka, Nnenna ma da gudu ta nufi mijin nata rigan nazeefa ta cire tana tare jinin dake biyo hancin sa,mikewa Mami tayi da Sauri ta Shiga kitchen saigata ta fito da wuka gadan-gadan tayi Kan Nnenna lura da hakan yasa Lahab zabuda da Sauri ya ture hannun Nnenna daga jikinsa ya turata gefe har Saida ta Fadi da ita da yaran akan rashin sani ta sauka a hannun nazeefi wani irin kukan azaba yaron ya sake Wanda Koh tantama babu kariya ya samu a hannu"nuna Nnenna Mami tayi da wukar tana zare Ido tace"wallahi summa tallahi Kika kuskura Kika Kara tinkarar yarona Koh inuwar sa saina daba Miki wukar nan Inga waye ubanki,Yar iska karuwar mayya kinzo kin likema yarona Yana mutuwa akanki harda haifan shegu toh wallahi badani ba kaf zuriyana dana ubansa babu shegu baza'a Fara akansa ba.





Lahab da hankalin sa ya tashi da Sauri ya nufi nazeefi don ganin meya faru dashi"wallahi tallahi Inka Kara taku daya a wajen saina tsine maka albarkan jikinka Lahab,karkaga kowa ya zuba maka Ido kafi karfin kowa toni uwarka Zan nuna ikona,tsayawa Lahab yayi Bai Kara Koh taku daya ba yanajin wani irin zafi a ransa Jin kalar kukan da dansa yake itama nazeefa tana tayasa Nnenna sai faman girgizashi take amma yaki shurun,shima Lahab baisan lokacin da kuka ya kubuce Masa ba, Adewale dake tsaye a tsakar falon har yanzun wani irin kukane ya tawo Masa da Sauri ya fita a falon ya wuce flat nasa dakin sa ya shiga ya kulle Yana sakin kukan tausayin yaran sai Kuma ya sake fitowa ya koma falon, karasowa yayi yasa hannu zai d'au nazeefi da niyar kaisa hospital yaji Mami tace"toh bakin munafuki d'an arna dakai da yar'uwar taka kunzo kun likewa d'ana, waya sani ma Koh kaika Mata cikin......haba Mami haba Mami wannann wani irin magana ne Taya zakina shegantamin yara tass tasss Mami ta sake wanke fuskar sa da Mari kana ta nuna Adewale"Kai aje yaron Nan"?





Mami ciwo yaji fa a hannu"uwarka nace uwarka dan iska kawai sakeshi ya mutu ma Mana dan ubansa"keee ta nuna Nnenna mike maza ki tattara shegunki kubar ma d'ana gidan sa Koh a mafarki karki sake tunanin Zaki Kara rayuwa dashi shegiya mayya makashiya Ashe kina Nan kina like da dana ya makale Miki baya ji baya gani toh wallahi daga yau kome yazo karshe indai Nina tsunguna na haifi Lahab,mikewa Lahab yayi da gudu ya nufi Mami dukawa yayi ya Soma wani irin kuka Yana Bata hakuri akan dan Allah kada ta koreta dan Allah wallahi ya tuba yabi Allah bazai Kara rashin ji ba,tsawa Mami ta bugawa Nnenna tare da nuna Mata kofa"dan Allah mama kiyi hakuri Bari naje daki na dau kayana"Nnenna tace hawayen tausayin kanta dana yayanta harma da mijin nata Yana ratsata ga yayanta sai kuka suke.





Waye uwarki Allah ya tsareni da had'a zuriya da mayu,Kuma Uban me kika zo dashi gidan Nan bare har Zaki dau Abu?babu abinda Zaki d'auka karuwa kawai"rumtsa Ido Lahab yayi yanajin kansa na wani irin juyawa Jin sunan da mahaifiyar sa ta Kira matar sa dashi"ah haba hajiya Amina ki barta ta dau Koh suturun su ne,da Visa tunda Kinga tana tare da yara"kawar Mami da jikinta ya gama sanyi ta fada don harga Allah sun Bata tausayi.





Babu abinda zata d'auka taje ta mutu da yaran, Khadija bazaki fahimci yanda nakeji a Raina bane da ace wani nakine yayi abinda Lahab yayi da wallahi baza kice haka ba,tafiya Nnenna ta Fara a hankali zata fita a falon da Sauri Ade ya matso kusa da Mami ya Soma Bata hakuri akan ta bar Nnenna ta dau wasu abubuwan daker de aka samu Mami ta yarda zuwa lokacin har Nnenna ta fita a gidan da gudu Ade ya kirata ta dawo dakin ta shiga ta aje yaran akan gado sai kuka suke nazeefi har hannu ya kumbura yayi dam dashi jajazer kuka ta Soma a hankali ta jawo akwati ta bude, Madaran yaranta ta Soma sanyawa a ciki sai pampas nasu da kayan su dasu flask kayanta Koh kala daya Bata d'auka ba na yara take sawa, ta Shiga Neman visanta don ba ita ta aje ba Yana hannu Lahab.





Har lokacin gwuwowin sa na kasa hawaye baibar zuba ba mikewa yayi a hankali ya nufi dakin da Nnenna ta shiga Mami dake zaune sai huci take tsawa ta daka Masa tana tambayarsa Ina zaije namamajo duk ya Kare a gindin karuwa"dan dakatawa yayi sai Kuma yace dan Allah Mami kiyi hakuri na dauko Mata visan ta don Bata San Inda na aje ba"wani uwar harara ta watsa Masa,kawarta tace yaje,da Sauri ya shigo dakin daidai lokacin tana zuge zip na akwatin karasowa yayi bakin gadon da Sauri yasa hannu ya d'auki nazeefi tare da d'aga hannun aiko Nan yaro ya Kara karfin kukan har wani kwarewa yake gabaki d'aya sun cika dakin da kara,aje yaron yayi ya nufi Nnenna da tunda ya shigo dakin bata d'ago Ido ta kallesa ba rungumar ta yayi a hankali kana yace"dan Allah Nnenna kada ki tafi,sai Kuma ya mike da Sauri ya fita a dakin,sai Kuma ya dawo dauke da wani envelope ya shigo dakin Mika Mata yayi yace"gashi visan ki na ciki da ATM card nawa kidau yaron Nan kuje hospital a duba hannun sa,kome ya Kama kiyi kawai sannan dan Allah karkibar London ki zauna daidai kome ya daidaita ga wayarki zamuna communication"?





d'aga Ido tayi ta kallesa sosai jikinta yayi sanyi ya bata tausayi ita Karan kanta tasan Lahab na sonta so na gaskiya bana Wasa ba"Lahab kayi hakuri amma wannan karon ya Kamata nayi abinda ya dace"zaro Ido yayi yace"meya dacen kenan kike nufi"?dafa sa tayi a hankali Suka zauna a bakin gadon yasa hannu ya dau yaronsa Yana girgizawa"Lahab banason Inga an cigaba daga inda aka saya ya Kamata wannan Karo na yankewa kaina abinda ya dace Koh na zauna dakai toh bani da kima a idanun dangin ka kallon karuwar Nan har abada shi zasuna min,don haka Ni Zan tafi ban maka Alkawarin Zama a London ba amma na maka

Please Login or Register in order to submit comment