Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kurawa Adewale Ido ganin yanda yayi mugun rama daga gani kasan baida lafiya ne,ah ah Adewale Nan ma ya Isa basai na shigo ba.


Kama Isa kazo mu Shiga kawai guy?

dan Jim Nabeel yayi bawai gidan su Adewale bane baison shiga ah ah yau weekend ne taima baban sa na gida yaje yaci Masa mutunci a banza don baida matsala da maman Adewale,no Ade Nan ma is ok daman nazo na tambayeka labarin Lahab ne nayi missing nasa kwana biyun nan Koh na Kira wayarsa baya shiga shine nace bara nazo wajen ka Koh zamuje gidan ya jafar mu dubo sa amma Naga kaima Kamar Bakajin dadi ba ma amma Koh notice babu nazo na dubaka.


Sai murmushi Ade keyi Yana sauraron zuban da Nabeel ke Masa ba gaggautawa sai da ya bari yakai Aya kafun yace,toh yanzun dai wanne Zan amsa a cikin tambayar Nan naka?

Koh ma wanne ka Fara amsa wa.


Ok toh nidai babu abinda ke damuna maganan Lahab Kuma wallahi koni banjin labarin sa jiya ma naje gidan su aka cemin Wai ba'amasan Inda yake ba wallahi Lahab zai kashe Yan gidansu duk ya d'aga musu hankali Kuma Nina tabbatar Lahab ba b'ata yayi ba iyya shegene kawai ke damun sa.


Uhmmm lallai Kam amma kana nufin ba'ama San Inda Lahab yake ba kenan?


Kwarai ma kuwa Nabeel hakan nake nufi.

toh yanzun gidan wa Lahab yashiga kenan?


Wallahu alamu Ina Zan sani Nabeel


Kallon sa Nabeel yayi Jin yace wallahu alamu watoh Koh Yaya Christian ya zauna a cikin musulmai sai ya kwaikwaye maganar bakin su,ok bara na wuce Allah ya sauwaka don nasan dai tabbas baka da lafiya kawai boyewa kake.


Yanzun bazaka zo mu shiga ba?


No Ni bazan shigaba kaga ma tafiya ta sai anjima,Nabeel yace ya Kama tafiya abinsa.


Toh ka gaida Inna.

toh zataji,komawa Adewale yayi cikin gida su.



MAFARKI.................
Assalamu Alaikum wani mutumine kyakkyawa fari tas sanye da farin Kaya hannunsa d'auke da Sanda Yana dogarawa yayi Masa sallama.


Waalaikumu Salam ya amsa Masa sallaman nasa daga zaunen da yake tare da d'aga Ido zai kalli tsohon amma Ina ya gaggara saboda hasken dake kashe Masa idanun.


bazaka iyya kallona ba Hassan tsohon yace Yana wani irin murmushi Mai dan Sauti.


Sosai zuciyar Sa ya tsinke har Saida ya dafe kan kahon zuciyar tare da kokarin d'agowa daga duke da yake Yana son tashi tsaye Kamar yanda tsohon yake a tsaye amma Ina ya kasa ji yayi gabaki d'aya jikinsa ya wani irin daskarewa waje daya sosai yaji wani tsoro ya mamaye Masa zuciya.


Bazaka iyya mikewa ba saidai wani ikon Allah Hassan ka kwantar da hankalin ka bazan cutar da kaiba,magana nake so nayi dakai.


Jikinsa na rawa ya daina yunkurin tashi daga wajen sai dan dago kansa da yayi ya kalli gaban sa katon kogi ne fari tass Mai d'auke da ruwan koramu masu gudana daaga cikin dutse Mai tsawon gaske hannu ya Mika a hankali zaisa a cikin ruwan kogin saboda tsananin sha'awa daya basa yaji an hanka d'asa tare da amon murya ana Masa gargadin kada ya kuskura ya taba ruwan,ja da baya yayi ganin ruwan ya rikide daga fari zuwa ja jazer dutsen dake wajen sun koma bakake.


Hassan kaga kogin Nan?tsohon dake bayan sa har yanzun ya fada.


"Eh na gani"

toh haka kaddarar ka take abu Mai kyau zaka gani ka zata abin sone amma fa ka sani kaddarar kace kaddarar kace tana tinkaro ka tabbas abinda Allah ya tsara dole ne saiya faru amma Ina Mai baka shawara akan duk halin da zaka tsinci kanka Nan gaba kayi hakuri ka dogara da Allah kasawa ranka kome jarabawa ne daga mahallincin mu,kayi kokarin ganin ka cinye jarabawar ka insha Allah Allah zai musanya maka da Mafi Alkhari akwai zazzafar kaddara a rayuwar ka haka zalika akwai kyakkaywar sakamako amma sai kayi hakuri sai kayi hakuri kayi hakuri Hassan.......ka zamo Mai tawakkali.....Allah na tare da Masu hakuriiiiiii...............wani irin zabura Lahab yayi ya mike zaune daga mummunan mafarkin dayayi duk zufa ya jika Masa jiki.


Nnenna dake zaune tun d'azun a kansa tana binsa da kallo ganin sai wani jujjuyawa yake da kansa ga zufa na sassafo Masa,saurin Mika hannunta tayi ta dafa sa ganin ya mike zaune a razane cikin damuwa take tambayarsa"menene mafarki kayi ne Mika gani a mafarkin naka"?kasa bata amsa yayi sai"innalilahi wa'inna'ilahu raji'un dayake ta maimaitawa,itama mikewa tayi da Sauri ta nufi wajen socket ta kunna wutan dakin tare dakai dubanta garesa ganin ya mike da Sauri zai nufi kofa,da gudu tasha gaban sa tare da nuna agogon bango dake makale a dakin"Lahab ka duba lokaci karfe 1:30am na dare Ina zakaje Kuma"?


"gidan mu zanje bansan meke faruwa dani ba a Y'an kwanakin Nan mummunan mafarki nake zanje wajen Mami na"ganin Kamar baya hayyacinsa yasa Nnenna kin basa hanya sai rungumarsa da tayi tabaya ta soma magana"ka kwantar da hankalin ka babu abinda zai sameka sai Rubuceccen Al'amari wannan bani da iko a kansa amma bazan barka ka fita a daren nan ba.


Fizge jikinsa yayi da Sauri ya nufi kof..............



🍀 *by Ruqeenjalal* 🍀




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 65&66

Nufar kofar toilet yayi ya bude ya shiga,komawa Kan gadon Nnenna tayi ta zuba tagumi,Lahab na shiga wanke fuskar sa yayi da ruwa sannan ya zauna akan toilet sit gabaki d'aya damuwa ne shimfide a ransa tunda yake bai taba ire-iren mafarkan Nan ba sai a 'Yan kwanakin Nan haka zalika yasan mafarki ba gaskiya bane amma mafarkin yau ya matukar rud'asa ya Kuma tsaya Masa a wuya,shiru kawai yayi yayi Jim dashi a zaune shi bai fita ba Shi baiyi kome ba.

Nnenna kallon agogo tayi sannan ta Mike ta nufi kofar ban dakin tasa hannu tadan tura kofar Jin a bude yasa ta dakata wa kafun ta soma magana"Lahab lafiya har yanzun baka fito ba"shiru bai amsa ba itama tura kofar tayi ta leko cikin ban dakin Allah ma ya sota akwai wuta,har lokacin Yana zaune shuru,takowa tayi ta shigo ciki a hankali take tafiya Harta iso kusa dashi hannu tasa a hankali ta kamo hannun sa lafiyayyen"Lahab meke faruwa mafarkin me kayi"?


Kallon ta yayi sai Kuma yaji baison sanar da kowa abinda yake mafarki especially na yau,mikewa tsaye yayi har lokacin hannunta na nasa ya nufi fita a kofar binsa tayi a baya har Suka fitoh Zama yayi a bakin gado tare da kallon ta ya nuna Mata gefen sa gyada Kai tayi ba musu ta hau ta kwanta,kashe wutar yayi shima ya kwanta gabaki dayan su shiru sukayi amma kowa yasan dan uwansa baiyi bacci ba.


Har asuba Basu rumtsa ba kowa da abinda ya damesa Wanda rashin baccin nasu lokaci daya ya saukarwa da Lahab da zazzabi a jiki,da asuba ma da taimakon ta ya samu yayi alwala ta shimfida Masa sallaya yayi sallah Yana idar da sallan Dr ya shigo ya daura Masa ruwa da Alluran bacci ganin jikin nasa yayi zafi ga rashin bacci yayi musu fad'a sosai ,bacci ne ya d'auke sa itama Nnenna bacci tayi akan kujera.



*******************
a gidan su Nnenna bayan dady ya dawo da yamma har dare baiga wullawan Nnenna ba gashi dai weekend ne bare ace taje school kasa hakuri yayi ya tambaye mom anan take ce masa tun jiya Friday Suka nemi Nnenna Suka rasa ,Sarah taje school nasu akace taje amma tashi da ita.


Aiko ranan mom taga bala'in Dad Wanda bata taba gani ba ta Inda yake shiga batanan yake fita ba sai cewa take daman bata son Nnenna taimama ita ta b'atar da ita Wasa-Wasa fada ya zamo na manya station dad yaje yakai kara Yar d'an uwarsa bakuwa ta bata,sun karbi hoton ta da suna aka Kai gidan TV Koh Allah zaisa wani ya ganta tunda ance bakuwa ce kilan bata tayi Abraham ma daya dawo daga Lagos yaji wannan labari hankalin sa ya tashi sosai.



Nabeel na barin gidan su Adewale shagon dinkin su ya nufa da sallama ya shiga shagon ogan sane da sauran yaran shagon Suka amsa masa Suna binsa da kallo rabon shi da shagon har sun manta sai dai yazo da abokan sa suyita hira,Zama yayi akan keken sa bayan yadau wani tsumma ya kakkabe kuran dake Kai ganin haka yasa ogan sa mikewa tsaye ya Soma magana,kaga Nabeel Mike tsaye bazaiyu kazo ka zauna a shago ba don nasa d'ayan biyu ne wata kil watace zata kawo maka dinki shiyasa kazo ka zauna watoh ka karbi kayan jama'a ka yanke zuwa shago daga karshe yara suzo Suna min rashin kunya a shago tare dajan Allah ya isa,don Kai Allah ya isa bai dameka ba don hakan Mike kabar shagon Nan.

Sunkuyar da Kai Nabeel yayi,don allah oga kayi hakuri wallahi dinki ne zanyi daman akwai wasu Kaya da nake son dinkawa ne.

Wa???badai a shagon Nan ba sai dai kadau keken naka ka tafi gidan ku dashi kaje ka dinka acan bazan iyya ma halinka ba Nabeel.

don girman Allah kayi hakuri oga wallahi dinki zanyi kudi nake su a Yan kwanakin Nan Inna bar shago Ina Zan samu tsoffen customers nawa.

Kai Nabeel wani tsofen customer Kuma bayan bana tunanin akwai Wanda xai sake baka dinki indai yasan ka kayan jama'a guda nawa ne a wajen ka na Allah ya isa?watoh kana son kudi Koh,shiyasa ka dawo ka yago kudin mutane?

Haushi ne ya tsoma Kama Nabeel hakan yasa sa mikewa ya fita a shagon baijima ba sai gasa da Mai bairo Kan keken sa ya d'auka da bodyn keken duka yasa a bairo wasu turaman zanin daya aje a shagon duk ya tattara ya loda a Keke,baibi takan maganan da ogan nasa yake Masa ba ya Soma tafiya Mai bairo na binsa a baya.

Suna isowa kofar gidan su wangale kofar yayi Mai bairo ya shigo da keken cikin gida,mubeena dake zaune ta tasa tuwo a gaba amma bataci ba don kwata kwata taji bata sha'awan cin kome musamman data ji labarin b'atan Lahab don zuwa lokacin labari ya guma unguwan kwana uku ba'a gansa ba,sai Inna dake zaune tana tatan kamu,dukan su da Ido Suka bi Nabeel har ya shigo tsakar gidan sauke keken sukayi damai bairon kudi ya zaro naira 30 ya mikawa Mai bairon.


gaskiya abokina talatin yayi kadan kadai ban 50,kallon sa Nabeel yayi a karkace cikin dan Jin haushi daman ya gama kuluwa da abinda ogan sa ya Masa,Kai da Allah karba ka Ware wani irin na baka 50 daga shagon mu Nan nan kasan layin Nan xaka wani CE na baka 50 sata kake Koh neman kudi kajimin almajiri da iyayi.

ran Alamajirin ne ya baci shima cikin zafin yace,kaga malam ban 50 na ai hakki nane in Kuma bazaka bani ba na barka da Allah.


Inka fasa jamin Allah ya isa Kai shege ne Nabeel yace Yana maida 30 in cikin aljuhun sa,da Sauri Inna ta Mike ganin Mai bairon ya juya jiki a sanyaye ya nufi kofa,Kai yaro tsaya Inna tace tsayawan yayi ita Kuma Inna matsowa kusa da Nabeel tayi tasa hannu a aljuhun sa ta zaro kudi da Sauri shima yasa hannu Yana kokarin Kama hannunta amma Ina ta rigasa d'auka,kudine akalla zai Kai 5k gayan 1k da 200 100 duk a Ciki,naira 100 ta d'auka ta mikawa Mai bairon ihu Nabeel ya sake Yana wallahi Inna ki ban kudina bana so wallahi Inna karki basa dari na,mikawa Mai bairon tayi da Sauri shima ya karba tare dajan bairon sa da gudu yabar gidan cikin Jin dadi.

Zama Nabeel yayi a Kan dutsen dake kasan wajen Yana ma Inna wani kallo tare da Mika Mata hannu ba tare da yayi magana ba,itama dongora masa sauran kudinsa tayi tana surutu,wallahi Nabeel karin ga Jin tsoron Allah Kai Koh tsoron ace an barka da Allah bakaji Koh a jikinka indai akan Allah ya isa ne, Wai a Ina ka Sami wannan mugun haline nacin abin Allah ya isa?

Mtwwwss wallahi Inna ki daina min irin wannan banason sheshege ke babu halin Kiga Ina magana da mutane sai kinsa baki?


Nasa Nabeel nace nasa don kaniyar ka Ina fa rabaka da abin Allah ya isa don wallahi wata rana zakaci abinda zai dameka,Oho dai yanzun ba wannan ba menene yasa ka dauko keken ka ka dawo dashi cikin gida Koh mutuwar zuciyar ce yasa ka dawo dashi gida tabbacin ma babu cigaban zuwa shago kenan Koh?

Kinga Inna nifa ba haka bane abinda yasa Kika ganni ogana ne ya sallameni a shago Kuma fa Inna wallahi tallahi aiki najeyi kinsan nace Miki daga yanzun Ni zanna biyawa Aunty kudin makaranta amma wannan d'an wahalan malam sadam(ogan sa).

Kama baki Inna tayi Jin Nabeel ya Kira ogan sa da wahalalle,amma in ana Neman Mara kunya in an sameka an gama yanzun Koh tsoron Allah bakaji kake ganin tsabar idon rana kace wa sadam wahalalle lallai nabeel?


Nidai duk yanzun abar maganan nan so nake kije ki basa hakuri yayi hakuri na koma shagon kinji inna ta.


Hararan sa tayi kafun tayi magana,Kai Nabeel babu Inda zani bakace Masa dan wahala ba sai ka nemi uwar da zataje ta basa hakuri tana karasa maganar ta nufi bucket in kamunta ta cigaba da tatanta bata ma kara bi ta kansa ba,shima mikewa yayi ya gurgura keken nasa da ker zuwa cikin dakin sa gudun Kar azo ayi ruwan dare,mubeena Kam har lokacin tana zaune a taburma batace musu komai ba.


washe gari da sassafe mubeena na tashi ta kammala aikace aikacen gidan na safe Koko Inna ta dama musu Nabeel ya sayo musu kosai Suka karya dashi kayan wanki mubeena ta fitar duk da jikin nata babu dadi amma haka ta daure take aikace aikace gudun Kar tasa dan uwanta da Inna a damuwa tunda suma basa iyya sakewa mundin tana cikin damuwa,Kuma hakan ya musu dadi dukan su don Nabeel na tashi bayan sun karya keken sa ya fitar tare da wasu zanuwan daya saya musu kayan aiki baiyi dinkin ba ya dauko Yana dinkawa ga mubeena a gefen rijiya tana dauraya yayin da Inna ke kwance a taburma tana fifita da mafici a hannunta.



***********************
da misalin karfe 8 na safe Nnenna ce ta fitoh daga ban daki ta canja Kaya bayan tayi wanka ta wanke kayan jikinta,rike bucket in tayi ta fita a dakin,tsakar asibitin ta fitoh zuwa wajen garden Inda ta Shanya kayan su na jiya cire kayayyakin tayi ta shanja sabo ninkesu tayi ta dawo dakinta aje,har lokacin Lahab bacci yake bai farka ba kudi ta d'auka ta fitoh bakin asibiti takeAway ta musu,mutumin dake kusa da shagon Saida abincin sosai yake binta da kallo sai Kuma ya zaro wayarsa da Sauri ya Kara kallon screen in ganin ta tsallako titi zata shiga asibiti yasa sa binta a baya shima har yaga dakin da ta shiga sai Kuma ya fitoh da Sauri ya tare Keke napep yahau.

Nnenna na shiga dakin àje abincin tayi ganin Lahab zaune matsowa tayi kusa dashi tana kallon sa gabaki d'aya ya sauya hatta fuskarsa ta kumbura hannu tasa ta taba goshin sa shidai sai Ido dayake ta binta dashi,da Sauri ta dau brush nasa tasa maclen "kazo muje kayi brush sai ka samu kaci abinci kasha magani time na wucewa"mikewa yayi Kamar yanda tace a hankali ya nufi bandakin binsa tayi a baya Suna shiga ta basa brush in yayi ta goge Masa jiki tare da fita ta barsa ya karasa sauran da kansa.

Zaune suke Suna cin abinci kowa da tunanin da yake bare Lahab dake ta Sakuran abinci don shi gabaki d'aya yau Innan so yake ya gansa kusa da mamin sa yaji kewanta da son ganinta ya samu ya fada Mata abinda ke damunsa Koh zaiji sauki a ransa,aje spoon in hannunsa yayi ya kalleta"Labiba ki karbo min Aron wayan na Kira gidan mu.


ba musu ta Mike tsaye dan kwalin abayan nurse in ta d'auka ta yafa zata fita a dakin sai Kuma ta tsaya Jin abinda Lahab yace"karki karbomin na Dr Nan ki karbomin na nurse in dake yawan shigowan Nan"?

Ok tace ta fita a dakin bata wani Jima sosai ba sai gata ta dawo da rantsatsen waya Mai kyau touch screen Mika ma Lahab tayi ta koma ta zauna,jujuya wayan yayi a hannunsa Yana tunanin number wa zai Kira yaso yasa na mamin sa ya kirata amma daya tuna yanda Suka rabu akan maganar farida sai yaji shakkan kiranta,dan murmushi yayi ya Soma sanya number dan uwansa ya Kara a kunne tare dakai dubansa ga Nnenna dake cin abinci batama kallon direction nasa.



********************
Rahab bayan sunci abincin dare da mustaph kwanciya sukayi tun mustapha na Masa Hira har bacci yadau mustapha Rahab Kam na kwance idanunsa biyu abinda ke damunsa ya hanasa bacci Koh Ina Lahab ya shiga ga Kuma abinda ya faru a gidan su abin yazo ya damesa Sam baiji dadin abinda Yama muzammil ba duk da muzammil nacin zalinsu Amma fa soyayyar sa ta gaskiya da gaskiya ne duk Wanda zakayi ba daidai ba ya hukunta ka yagama maka kome amma shi ransa ne ya baci Sam baijin dadin abinda yayan NASA kema mamin sa.


Sai can dare ya samu bacci ya dauketa,washe gari da safe salamatu ta Gama musu dumamen tuwon nasara miyan karkashi gashi daman Rahab baison miyan yauki a rayuwar sa tada Masa da zuciya yake dayake salamatu tasan halinsa tun Yana yaro yasa ta aikan mustapha ya sayo Masa dan wake,ya kawo Masa Rahab yaso yakici amma yasan bazasu ji Dadi ba don tun jiya sai rawan kafa suke dashi Suna haba-haba dashi suke yasan in yakicin abincin su baza suji Dadi ba Sam hakan yasa sa karban dan waken yayi yaci sosai Suna Gama karyawa yabi mustapha garejen su Zama yayi Yana kallon yanda suke ta aikace aikacen su na Neman halak sosai yaji zuciyarsa ta tsinke daman haka talakawa suke Shan wahala lallai Allah ya musu gata Koh Basu da mahaifi a raye sun samu gata zasuci zasu Sha sutura Mai kyau makwanci Mai kyau,amma ga wasu da iyayen ma suke nema wa kansu abinda zasu sa a bakin salati tagumi yayi Yana bin jama'an wajen da Ido daga dai ka gansa kaga yaron masu hali Wanda bai Saba da wajaje irin wannan ba.


Wayar sane tayi Kara hannu yasa a Aljuhu ya zaro wayar tasa kallon number yayi ganin new number yasa sa kin dagawa ya maida wayar aljuhu.


tsaki Lahab yaja ganin ya jerawa Rahab har 3 miss call Amma yaki dagawa"Kai Allah ya kyauta maka ace mutum bazai dauki Sabon layi ba Kamar wani dan film sai kuma ya tura Masa sako Kamar hauka"ka dau wayar Nine"


Jin Karan shigowar sako yasa Rahab budewa"ka dau wayar Nine"sosai ya kurawa message in Ido Yana nazari da Sauri Kuma ya Kira layin,dan murmushin Lahab yayi ganin Rahab ya kira, picking in call in yayi yasa a kunne.


Assalamu Alaikum,Rahab yace kamar Mai son tabbatar da abinda yake zargi,shuru Lahab yayi bai amsa ba,mikewa Rahab yayi Jin shuru ba'a amsa ba yasan babu Mai Masa wannan abin sai abokin haihuwar sa, Lahab nasan Kaine Kaine Dan Allah kayi magana Lahab?

"Rahab...... Lahab ya Kira sunan sa ta cikin wayan,jikin Rahab har rawa yake ya Soma magana,laaa dan uwa Kaine Ina ka shiga kasan tashin hankalin da ka samu a ciki kuwa kana Ina ne?


"Ina makama hospital"Lahab ya basa amsa.


What??? hospital fa kace Lahab meya faru dakai meya Kika hospital Kuma na shiga uku.


"Kaga ka kwantar da hankalin ka ba wani abuba ne tsagen Kashi na samu shekaran jiya"

Waro Ido Lahab yayi Wanda yasa mustapha dake gefe Yana gyaran mota ya taso ya taho gare sa,Jin Rahab na cewa,eehh kace tsagen Kashi ka samu innalilahi wa'inna'ilahu raji'un.

Katse wayar Lahab yayi Jin dogon salati da rahab ke zabgawa,ta bangaren rahab Kam tambayar sa mustapha ya Fara meke faruwa ne rahab meya samu Lahab in amma Ina lalubo number Mami yayi ya Kira tafiya ya tsoma Jin number nata na ringing,sai Kuma yaji ta d'auka sai muryar ta tana sallama........



🍀 *By Ruqeenjalal* 🍀




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 67&68

Mami dake zaune a tsakar compound na gidan ta ita da yaranta da mijinta Suna buga basketball gabaki dayansu sanye suke da sports wear nasu,yaranta da Alhaji ne suke ball itakam zaune take a gefe Kan cafet Inda ta shimfid'a tana amsa wayar Rahab,sai Yusuf dake zaune akan keken sa na yara,mikewa tsaye tayi cikin zumudi tace, na'am Rahab meka ce?ta bangaren Rahab sake maimaita mata yayi,Mami Lahab ya kirani.


Wai meya ce maka daya kira kan,Wai Ina yake?

Yana hospital Mami ya samu tsagan kashi ne.

Subhanallah tsagen Kashi Kuma garin yaya,tukunna ma kana Ina ne Kai in yanzun?

Ina garejin su mustapha ne yanzun Zan wuce asibitin.

da Sauri Mami ta dakatar dashi,karka hau Keke ka jirani ganinan zuwa yanzun zanzo na d'auke ka a wajen karka tafi ka jirani bata jira Mai zaice ba ta katse wayar tare da nufar flat nasu,bata ma sanar da Alhaji ba dama hankalin su baya kanta kwata kwata Yana ga kwallo da suke bugawa.


tana shiga cikin falon sai Kuma ta tuna bara ta sanar da yayan su babba(Abbu) number sa ta Kira ta Kara a kunne Yana dagawa Suka gaisa tare da sanar dashi Lahab na asibiti shima sosai yanuna alhinin sa tare da cewa shima gashinan zuwa,wanka Mami tayi ta sauya Kaya daga wando da rigan jikinta zuwa atamfa riga da siket,hijab nata ta jawo ta rufa tare da d'aukar key in mota da Sauri ta fitoh,dai dai lokacin Alhaji sulaiman Suka sakaita da ball in Suna hutawa dukan su akan cafet Inda ta tashi,nufosu tayi tana magana,Abbin mahraz zani hospital yanzun yanzun Rahab ya kirani Lahab na asibiti ba lafiya?

Subhanallah meke damunsa haka mamin yara?ya tambaye ta.

Wallahi Wai ya samu tsagen Kashi bazai wuce a filin ball bane.

toh ai dakin tsaya kin jiramu saimu shiga mu kimtsa mu tafi duka da yaran mu duba jikin nasa?

ah ah bazan iyya jiranku ba kudaiyi hakuri in yaso kuje ku dubasa da yamma Koh da daddare bazan dawo da wuri ba mahraz ya dafa muku spaghetti tana basa amsan ta juya zata nufi parking space nasu,ihu Yusuf ya kurma ganin mamin sa da hijab Kuma ta nufi hanyar waje,kin sauraron sa tayi don tasan daga zaran ta fita a gidan zaiyi shuru ganin tane yasa yake kuka,Kinga dawo kizo ki d'auke sa don Naga kwanan Nan kin tsiri fita kina barin sa a gida Alhaji yace Yana mamakin irin sonda Amina kewa yaranta akan yaranta bata da kawaici especially tagwayen ta don sonda take musu Bata ma yaransa shi.

ba musu tabi umurnin mijinta dawowa tayi ta karbi Yusuf in tare da bude motarta ta shiga ciki aje Yusuf tayi a sit taja tabar gidan hanyar garejin su mustapha ta nufa.

tsaye yake a bakin titin garejin Yana bin mototin dake tahowa daga nesa yayin da mustapha ke zaune a cikin garejin nasu ya sauya Kaya daga na aiki zuwa Mai kyau shima zaibi Rahab asibitin su dubo Lahab,haka zalika shima ya Kira baban sa ya sanar dashi asibitin da Lahab ke.

tun daga nesa Rahab ya hango motan mamin sa fadada murmushin sa yayi Yana daga hannu Kamar wani Bako, murmushi mustapha yayi d'aga cikin garejin ya Masa magana,toh ka hango goggo Aminan kenan?gyada Masa Kai kawai Rahab yayi, parking Mami tayi da Sauri Rahab ya matsa kusa da motar ya bude gaba yadau Yusuf ya shiga ya zauna ya daurasa akan cinyarta Yana Masa Wasa mustapha ma ya bude bayan motar ya shiga rufewa yayi Mami taja motar.

Ina kwana Goggo Amina?

Lafiya mustapha ya aiki?

Mungode Allah,ya Bata amsa kallon Rahab tayi Kai Kuma bazaka gaidani bane Koh me?
murmushi yayi Kai Mami na wallahi zumudi ne kiyi hakuri Ina kwana?

Shuru tayi bata amsa ba shima bai sake cewa kome ba Suka cigaba da tafiya.


*****************
Abbu Suna gama waya da Mami ya mike yad'au Kaya ya sanya a jikinsa fita yayi a dakin tare da shiga dakin Addayiya da sallama,amsa Masa tayi bayan ya zauna yake sanar da ita Lahab na asibiti,sosai ta tsorata tana salati tare da daukar hijab nata have Sunnah tasa tare da gyele ta yafa a kafada

Please Login or Register in order to submit comment