Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nan, sai ya gangara gidan su nabeel don shikam gaskiya yasha mamaki kwarai wallahi ace yau kwanan sa hudu basu gansa ba su kasa zuwa neman sa koh suje gidan su.

Yana zuwa gidan su nabeel suka gaisa a inna harma tana tambayar sa lafiya baizuwa kwana biyu? (D'an mutum kenan duk yanda kake kinsa randa baka gansa ba sai kaji wani wuri naka sakayau)anan yake sanar da ita baida lafiya ne.

Tare da tambayar ta su nabeel, ce masa tayi ai sun tafi jogging, fita yayi a gidan ya nufi hanyar filin ball da suke zuwa exercise aiko yayi sa'a tun daga nesa ya hangosu suna motsa jiki, hannu ya d'aga musu yana kwana musu kira, amma gabaki d'ayan su sukayi kamar basu gansa ba abin yayi mugu-mugun basa mamaki lokacin da ya iso inda suke yaga nabeel na kokarin barin wajen, da sauri ya rike hannun sa "haba guys kwana biyu baku ganni ba amma kuka kasa nema na"?

Wani kallo nabeel ya masa cikin yaushi yace, mtwsss eh taya zamu neme ka bayan kana school sannan a gidan ku ba'ason mu rabe ka, toh muma yanzun m................

✨Ruqeenjalal✨





πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

✨Tsokaci ALKAWARIN MASOYA na kudi ne gamai bukata naira 300 ne kacal ki tuntube ni ta layin nan whatsApp only 07044407979πŸ‘Œ

Last Free page🀧


*EXQUISITE WRITER'S FARUM*


page 2⃣9⃣&3⃣0⃣
Don haka muma yanzun bamu ba kai?

"Wai menene niban gane ba kunje gidan mune daman"?

Munje mana wannan d'an iskan yayan naka ya........., ai lahab bai bari nabeel ya karasa ba ya wanke sa da lafiyeyen mari cikin hakin bacin rai yace" wallahi karka kuskura ka sake zagan mini yaya kaji na gaya maka duk rashin kunyan ka a bayana kake, don uwarka na taba zagin wani naka ne don ya kuntata mini.

Hannu nabeel ya d'aga ya wanke lahab da mari shima jin ya zagi uwarsa, aiko take lahab ya shuresa ya buga a kasa take fad'a ya barke a tsakanin su, sosai lahab ke jibgar nabeel adewale yayi iyya kokarin sa don raba fad'an abu yaki lahab na jibgar nabeel, shikuma zuciya na cinsa yaki barin fad'an daga karshe dai har jama'an dake gefe suna exercise, aka zo aka kakka masu amma nabeel yaki barin fad'an sai zagin wa'inda suka rirrikesa yake, wai sai dai a barsa ya buge lahab.

Wani ne a cikin su yad'au waya ya kira Bappan sa a waya, akazo aka jasa aka tafi dashi kafun mutane suka watse, kallon lahab adewale yayi, gaskiya friend nayi mamakin abinda nabeel ya aikata maka?

"Manta dashi kawai adewale gani yake yafi kowa zuciya baisan akwai maza bisa kansa ba, wai ma meya farune Adewale ban gane abinda yake ma masifa akai ba, me uncle ya muku ne"?

Wallahi lahab munzo wajen ka kawai ya kikirbemu wai bamuje school ba, shine shi kuma nabeel yad'au zafi baka sanar damu yazo ba mukaje gidan ku neman ka, ashe ka shiga school koh note babu, nima banji dadi ba gaskiya?

"Am sorry amma ban zati don brother na ya buge nabeel zai hau haka ba, ka dube jikina"lahab yace yana kwabe rigan sa.

Jesus menene haka lahab mezan ganin nan?

"Wallahi kaga jikina dukan da muzammil ya mini kenan kwana biyu bakwa gani na"

Cap Allah ya sauwa ka amma guy ka daku fa iyya dakuwa ma kuwa.

"Ka bari kawai Adewale ai shiyasa nace wallahi bazani makarantan ba sai dai ya kasheni"

Da mamaki Adewale ke kallon lahab, gaskiya aboki wallahi kana da taurin kai na rantse nidai gobe school zani, bansan koh nabeel zashi ba?

"Kai karka sake kira mini sunan shegen nan a kusa dani"

Ok yanzun ina muka nufa kenan da sassafen nan lahab?

"kai muje gidan ku ka chanja kaya mu fasa gari wallahi na gaji da zaman banzan nan zama waje d'aya ba dadi sam"

Ok muje lahab amma fa kasan old man na gida fa?

"Toh ni ina ruwa na tsoron baban naka nake ne"?

Ah ah yi hakuri man muje.

Kama hanya sukayi suka nufi fita a filin ball in har sun bar filin kamar daga sama suka ga Muxammil a tsaye a gaban su fuska ba walwala, hade fuska yayi sosai yana kallon lahab, amma kai dai lahab Allah ne kadai zai gyara maka ka, shige mutafi tun raina bai baci ba.

Bin gefen muzammil yayi ya nufi layin su ba tare da yace kome ba, kallon adewale uncle yayi, ka wuce kaje ka sanya uniform wallahi naje school naku bakaje ba, nida kai yana maganar yabi bayan lahab da sauri gudun karya arce.

Lahab na gaba Uncle na baya a haka suke tafiya har suka shigo cikin gida yana tura kofar falon ya shiga, Addayiya ce zaune sai Abbu ga inna ma zaune sai masifa take.

Karaso mutumin banza, addayiya tace tana kallon lahab.

Hararan ta yayi"wallahi nidai ba mutumin banza bane atoh"

Rufemin baki koh namaka abinda yafi na jiya d'an iska zauna anan, yana maganar yana nuna masa kasan tiles, kin zama lahab yayi sai da abbu yasa baki kafun ya zauna.

Kallon sa abbu yayi, yanzun lahab ka kyauta kenan kaje ka kama abokin ka kamasa duka kasan yaron laulayine dashi haka ake abota da dambe?

"Wallahi yaya shiya fara wai fa akan uncle ya bugesa shikenan yace wa yaya d'an iska shine na babbuge sa"

Kallon sa muxammil yayi nine dan iska kuma nabeel ne yace?

"Eh yaya"

Kamin daidai tashi ka tafi ka sanya uniform maza-maza 'yan uwan ka sun tafi makaranta.

Ai jin haka tuni inna ta soma bala'i don an gansu talakawa shine za'a cucesu a hanasu kuka, Allah ya isawa jikan ta, addayiya dai sai hakuri suke bata ita da Abbu amma muzammil kam mikewa ma yayi yabi lahab d'aki yana jiran sa ya gama shiryawa yakai sa makaranta.



*******************
Nnenna daren jiya koh lafiyayyen bacci bata samu ba wani irin tarine yake damun ta tanayi tana aman yawo mai yauki,haka ta tashi da safe da taren kamar zata mutu, koma bata fad'awa kowa ba, haka take ta fama da azaba.

Tana tashi da safe koh aikin sharan ta kasa don tana farawa da kura ya shigar mata hanci ji tayi kamar numfashin ta zai d'auke.

Hakan yasata kasa aikin gashi Dad bai kwana a gida ba sunje wani gari yad'a addinan su, gashi Abrahama bai isa ya shiga harkan ta mom nanan ba.

Yau peace doya ta soya musu da miya, har Nnenna ta iba mom ta kwace ta mayar kitchen tace tunda batayi aiki ba bazata bata abinci ba, Allah sarki rabon Nnenna da abinci tun daren shekaran jiya amma jiya cur abinci mai nama ake koh ta iba ba ita keci ba.

Ba yanda ta iyya haka ta sanya uniform nata ta d'au jakan ta datake jinsa yau ya mata mugun nauyi harda kule a ciki don har yanzun ba'asan tana zuwa makaranta da kule ba, fita tayi a gidan tana takawa da kafa ga kirjinta dake mata nauyi sosai ga tari ga nauyin jaka kallonta ma yau ya kara duhu duk da akwai glass a fuskar ta ga jiri dake dibarta, a haka take tafiya kad'an ta huta ta tafi kad'an ta huta.




********************
Lahab na sanya uniform abinci ma muzammil ya hanasa ci haka ya tura keyar sa har cikin mota suka wuce school.

Suna isa office suka fara nufa sosai ya kara jaddadawa disple kula da lahab, tare da karban number sa, har class ya raka Lahab kafun ya tafi, yana tafiya lahab dake zaune a bench sai malamin su dake koyar dasu, ga disple a tsaye a window, shammatar su lahab yayi ya hau window d'aya kusurwar ajin ya dirka.

Disple ma da gudu yabi ta cikin ajin ya hau window ya dirka yana bin lahab da gudu lahab na gudu, a haka suka soma zagaya makarantan sai da suka shigo tsakiyar makaranta disple ya fara cewa malamai a taro masa lahab, aiko take aka fara tare-tare sai lahab yazo saitin ka sai ya kauce yabi d'aya gefen, abinka da mayen ball, ana haka disple saura kad'an ya kama lahab kawai ya shammace sa ya kauce take disple ya fadi ji kake timmmm.

Me yara dake classes nasu zasuyi in ba dariya ba, da gudu lahab yayi cikin gonaki, daidai wani bishiyan gadina yahau har reshen sama ya zauna.

Disple na samu ya mike cikin burga ya bi bayan lahab cike da kunya, amma yayi iyya dubawan sa bai fahimce inda lahab ya nufa ba, dole tasa sa komawa cikin makaranta, amma yaki kiran muzammil kaman yarda sukayi duk abinda lahab yayi a kirasa a sanar dashi, gudun kar muzammil yaki kara masa kudi kamar yanda yace masa muddin ya saka lahab zaman class duk wata yana da 10k.

Lahab kam gyara zaman sa yayi akan bishiya ya zaro wayar sa yana dannawa duk da yana jin yunwa amma baici ta sauka yanzun ba don get na school in d'aya ne.



*************************
Nnenna ba ita ta isa school ba sai kusan 10 na safe, lokacin an fita break ma tana shigowa mai gadi ya hanata shiga duk yanda tayita masa magiya ki yayi karshe ma sai yaje ya kira principal, yana zuwa yace mata bafa zata shiga school in ba, haka tanaji tana gani aka hanata shiga.

Zama tayi a bakin get na school in sai tari take da amai, wanda yasa maigadin bude karamar kofa ya lekota tambayar ta yayi lafiya koh dai bata da lafiya ne?

Kuka ta sake tana had'asa da iyayen sa akan yabarta ta shiga ciki, amma yaki karshe dai daya tausaya mata yace zai barta amma karta shiga aji tunda dai principal ya hana bai kamata ya barta ba.

Gyada masa kai tayi ta sabe jakanta tashiga cikin makarantan direct hanyar da ta saba zama watoh gonar makaranta gunta nufa a hankali take tafiya tana dafe kirjinta harta iso gonar, nusawa tayi ciki sosai har gindin bishiya ta zauna tana haki.


Lahab dake saman bishiyar jin motse yasa sa kara labewa da kyau gudun kar a gane akwai mutum akai.

Tari Nnenna ta fara da karfi tana amai ga kuka data fashe dashi na wahala, jin kukan mace da tari yasa lahab leko kansa ta gindin bishiyar, ga mamakin sa mace ya gani zaune ga dukkan alamu Christian ne kanta a duke tana amai.

D'aga kafad'a yayi irin ba ruwan san nan yaci gaba da abunda yake, amma dai ya kasa samun nutsuwa jin yanda take tarin tana kiran jesus.

Daga kan bishiyar yaji karan bugun bell da sauri ya duba agogon hannun sa 10:30 watoh sai lokacin aka koma break kenan, amma har lokacin Nnenna tari take tana haki kasa hakura yayi ya kama reshen ya dirko daga saman itacen.

Nnenna dake duke koh d'ago kanta batayi ba saboda hakin da takeyi, binta da ido kawai lahab keyi zuciyar sa na wani irin wawan bugu, tsungu nawa yayi a gabanta,"ke baiwar Allah lafiya"?

Koh D'agowa batayi ta kallesa ba, duk da taji mutum a kusa da ita harma magana yake cikin hausa don ita bajima take ba, amma halin da take ciki bazai bari ma ta saurare waye bane.

"Ke ba magana nake miki bane kin mini banza sai kije shan ki mutu tunda baki san hanyar clinic b......bai karasa ba ya dakata saboda d'ago ido datayi ta kallesa, gaban sane ya fadi cikin tsananin tarin mamaki da Al'ajabi wannan kuma yaushe ta shigo school nasu ga kyaun ta har yanason yafi karfinta.

Da sauri ya mike zai bar wajen, cikin gegeta Nnenna da numfashin ta ya soma d'aukewa ta kamo hannunsa, magana take son masa amma tari yaki barinta sai sarke ta yake, kara matsowa kusa da ita yayi shima yayi linkdown kamar yanda tayi, yana rike kafad'ar ta ganin jikinta sai bari yake,"wai lafiya baiwar Allah ba baki da lafiya bane? kije clinic mana"


Baya baya tayi luuuu zata fadi, da sauri yasa hannu ya tarota ta fado a kirjinsa, bugawa kirjin nasa yayi da karfi fiye da da, wannan abune daya zo masa a bazata koh yace sabo a rayuwar sa, tunda ya girma yayi wayo koh wasa da mata bayayi bare ma har su taba masa jiki, inka cire muharraman sa, sai yau ga yar inyamurai dumu-dumu a kirjinsa.

Hankalin sa a tashe ya soma girgizata jin gabaki d'aya ta sake numfashin ta baya fita, "nashiga uku kar yar mutane ta musu a hannuna" yana maganar yana mikewa tsaye ciccibar ta yayi da dukkan karfin sa ya wanshakalar da boronta da wayan sa ya goyata a bayan sa da gudu ya nufi school Area da ita.


School clinic ya nufa da ita Allah ya sosa ma an koma break babu dalibai a waje, kuma hankalin su bai kawo kansa ba, da gudu ya shiga cikin clinic sai kwalawa Dr kira yake su karan kansu Dr da nurse hankalin su ya tashi ganin Nnenna koh motse babu.

Kwantar da ita akayi a gado bayan karban ta da akayi a bayan lahab, a take likita ya rufu a kanta, pharmacy aka je aka karbo ruwa dasu Allurai shap-shap aka d'aura mata ruwa nurse tazo ta d'auki jinin ta zuwa lab.

Lahab dai na zaune a Kan kujera a bakin d'akin ya zabga tagumin tausayin baiwar Allah nan kome ke damunta sai Allah, yana nan zaune sai ga principal ya shigo da sauri yana tambayar wace yarinya ce aka kawo, anan lahab ke sanar dashi shima bai santa ba.

D'akin da take kwance ya shiga ganin Nnenna ne yasa sa fita da sauri yad'au waya ya kira mom, amma kusan 2 hour's babu wanda yazo daga gidan su Nnenna, karshe dai dole tasa principal d'auko wani Dr daga babban asibiti sukayi su biyu ana ta kokar tawa sai kusan 1 na rana Nnenna ta gane hankalin ta.

Likitan ne ya fitoh a d'akin kallon lahab yayi dake zaune a kujera ya buga tagumi, kai ne ka kawo ta?

"Yes sir nene ya jikin nata"?

Da sauki iyayen ta sun zo ne?

"ah ah sir principal yace ya kira mom nata amma har yanzun shuru ba wanda yazo shiysa ma na zauna nake jiran su zo kar na tafi a nemi wani abu bamai sayowa"


Karka damu duk abinda za'a mata daman d'awainiyan makaranta ne, don daman a cikin school fees naku akwai kudin jinya, sannan ka sameni a office zamuyi magana.

"Ok Lahan yace ya mikewa yabi bayan Dr.

Suna zuwa office likitan ya masa nuna da kujera ya zauna, ba musu lahab ya zauna yana kallon likitan jin tambayar da ya jefo masa wai yasan Nnenna?

"Gaskiya Dr ban santa ba"

Ok koh ka san gidan su koh wani nata?

"Gaskiya Dr ni ban taba kallon ta bama sai yau wani abun ne ya faru"?

Gaskiya kam ga dukkan alamu yarinyar nan bata tare da iyayen ta.

"amma likita meyasa kace haka"?

Lahab dole nace haka kaga yarinyar ulcer ne ya kamata tana zama da yunwa, koh nace ana mata horo da yunwa don ba yanda za'ayi mutum najin yunwa yakicin abinci har ya masa illah haka, a kalla rabon ta da abinci Almost 24 hour's kenan, bataci kome a cikin taba kuma tana jin yuwa banda hakan ma, tana zama da yunwa sosai gashi ulcer ya mata mugun kamu.

Lahab kam"subhanallah kawai yace yana mamaki ace yarinya za'a iyya sata a school nasu amma ace a binda zataci ma y gagare ta gashi daga gani kaga yar manya ba wahalalliya bace.

"toh yanzun likita ya za'ayi principal yace min ya kira mom nata har yanzun batazo ba nima ina tantama anya a wajen iyayenta take kuwa"?

Will yanzun dai zata iyya farfado wa zuwa karfe 3 koh 4 so anason daga ta tashi in aka zare mata ruwa a samu a bata wani abun taci mai d'an ruwa ruwa bamai nauyi sosai ba, don hanjin nata ya murde dole sai an samu abu mai sauki-sauki an bata daidai yad'an warware.


Lahab dake sauraron sa yace "toh likita kamar me dame zan sai mata kake ga wanda ya dace taci"


Eh kaidai abinda baida nauyi sannan baida yaji baida sanyi kuma baida tsami zaka iyya bata.

Da sauri lahab ya mike ya fita a clinic in kama hanyar cafe yayi cikin hanzari jin ana kiran sallan azahar kawai saiya nufi masallaci Alwala ya tsunguna yake sai ga Rahab da mamaki yake kallon d'an uwan nasa har ya matsa kusa da shi, Lahab daman kana cikin school inne?

"Oho shine amsar daya basa, yamike yayi cikin masallaci a ciki ma ya hadu da nabeel amma kamar bai gansa ba, ana idar da sallah ya nufi cafe hannu yasa a Aljuhu zai taba wayan da sai yaji wayam"subhanallah da sauri ya nufi gona yana Allah-Allah kar wasu sunje wajen sun kwashe masa waya a kasa.


Aiko yayi sa'a kamar yanda yabar wayar haka ya dawo ya same sa harda jakan Nnenna da glass nata daya fadi, duk ya d'auko bakka jakan yayi yafi toh a wajen, direct cafe in ya wuce yana tura kofa suka had'a ido da Adewale dake zaune akan kujeran daining dake wajen shida nabeel, d'aga masa hannu kawai lahab yayi ya nufi wajen mai abincin.

Ordern ferfesun kaza yayi sai fruit salad da kwai dafefe a take Away duka tare da ruwan gora mara sanyi, sai kuma yayi ordern doya dafeffe da zaici da miyan kazan shima.

kudi ya biya ya karbi laidodin ga jakan makaranta a bayan sa, yazo zai fita a cafe in mikewa Adewale da Rahab sukayi sukabi bayan sa, da sauri suka tsaida shi suna tambayar sa lafiya laidodin hannunsa nan fa, ga jakan mata a kafad'ar sa bangaje su yayi ya wuce abinsa dukan su suka bisa da ido harya mule.

Yana isa clinic in, direct dakin da aka kwantar da ita ya nufa yana d'aga labule idadunsa suka sauka akan ta, ita kadaice a dakin tana kwance akan gado tana bacci an cire mata takalmin kafarta aka bar socks, rigan ma an zare mata na uniform daga ita sai vest gabaki d'aya gashin kanta a wargaje sai fuskar ta dayayi fayau fari tas.

A hankali ya karaso bakin gadon aje boron yayi a kasa sai abincin daya aje akan drower kusa da magangu nan ta, zuciyar sa na bugawa ganin ta a haka yasa sa d'aukar zanin gadon dake nade a gefe ya lulubawa kafafunta zuwa kirjinta ya kara gudun fankan sanin da yayi saboda zafine taima ba'a rufeta ba.

Zama yayi a gefe koh abincin ya kasa ci, bayan awa d'aya likita yazo ya kara dubata sannan ya cire mata laidan ruwan dake hannunta.

Sai kusan 4:30 har Lahab yaje sallan la'asar ya dawo ya zauna kafun nan Nnenna ta farka, Alhamdulilah tana farkawa bata farka da tari ba, a hankali ta bude idanunta tana yawo dasu asaman silif na dakin, ganin duhu-duhu take, hakan yasa ta taba idanunta taji ba glass da sauri ta fara yunkurin mikewa.

Lahab dake zaune ganin ta farka kuma tana son tashi yasa sa mikewa da sauri ya iso bakin gadon yana mata sannu cikin turanci.

Gyada kai kawai tayi bawai don tana kallon saba, harta mike zaune, yaye zanin gadon tayi ta zauna ta jingina da gini kafafunta na lilo a bakin gado, tare da dafe kirjinta jin har yanzun nauyi yake mata.

"Sannu ya jikin naki"

"A hankali a karon farko ta basa Amsa da sauki"

Allah kara sauki yace, yayin da ita kuma tayi shuru batace ameen ba don ba haka ta saba ba.

"Pls help me, ka bani glass nawa in yana kusa"

Glass in ya d'auka ya mika mata hannu tasa a hankali zata karba by mistake hannunta ya taba hannun nasa da sauri ya sake glass in jin wani bakon Al'amari mai kamar shock da special feeling.

Subhanalalh yace yana kallon glass in ganin fashewa yayi a tiles"am sorry wallahi glass in ya fashe fa"?


"What kana nufin kace min Goggles ina ya fashe kenan? Shika d'aine dani fa haka kakeso na ringa tafiya bana kallo sosai"


"Kiyi hakuri in aka sallame ki zan sai miki wani"

"Toh kai wanene bansan kaba sannan nan inane na ganne akan gado gashi ina jin warin asibiti"

"Asibiti na kawo ki baki da lafiya"

Shuru tayi tana tunanin lokacin da take gindin bishiya tana tari tadai san akwai mutum agun amma batasan wanene ba, kallon sa tayi duk da bata kallon nasa tass sai yama-yama"ayya jakana"?

"Karki damu jakanki na nan" ya karasa maganar da mika mata roban takeAway dake d'auke da ferfesun kaza.

Hannu tasa ta amshi roban da sauri kuma ta maida masa tare da girgiza masa kai idanun ta na zubar da hawaye.

Da mamaki lahab yace"menene tsoro kike zan cutar dake koh me"?

Ah ah banason wannan ne kawai tana maganar tana nuna kwanon dake hannunsa da yatsa.

"Ikon Allah bakin ce baki gani sosai ba? ya akai kika kare wa kwanon kallo har kikasan meke ciki"?

Ai ina da hanci kuma yanajin kamshi, ta basa amsa tana mamakin kanta da surutun da take, kamar ba Nnenna Obinna ba.

Aje roban yayi ya d'au na fruit salad ya mika mata da sauri ta karba ta soma sha a hankali bai wuce shukali uku tayi ba ta yamutsa fuska ta aje roban a gefe, shima bai tambaye taba illa bare kwai dafefen yayi kuda uku yasa a marfi ya aje mata a kan cinya.

Komawa yayi ya zauna jin yunwa na neman hallaka sa bude doyan yayi ya zuba miyar kazan a ciki yadau shukali ya soma ci.

Kukan kule da motsen da jakan Nnenna keye a kasan tiles ne ya basa mamaki, "ke menene a jakan nan naki"? Ya tambaye ta.

"Oh my god cat nawa ne a ciki"

Cat?yasake maimaita tambayar cikin mamaki yasa hannu ya bude zip na boron da sauri ya koma baya ganin kulentan nan haka kawai suna had'a ido yaji tsikar jikinsa na tashi gashi kulen shi sam baima masa kama da fuskan kulen gaskiya ba, ganin fuskar kamar zubin fuskar mutum.

Da sauri kulen yayi jump daga cikin jakan ya fitoh da gudu yayi kan kwanon abincin lahab baki yasa zai d'auki naman, cikin zafin nama lahab yasa kafa yayi shoot dashi sai da ya had'asa da jikin ginin d'akin, wani irin kara kulen ya sake kamar ba kukan dabba ba ya fade tim a kasa, a take yamike kwance kamar wanda yayi dogon suma.

Kara Nnenna ta sake tana kokarin sauka a gadon tana tambayar lahab meyake faruwa meya sami kiki.

Kin magana lahab yayi ya barta tayita zagayen dakin tana neman kulen amma bata gane inda yake ba, kuka ta sake da karfi wanda yasa Nurse's dake zaune a station nasu sukayi saurin shigowa dakin suna tambayar lafiya?

Itace ta basu amsa tana neman kulenta yayin da lahab ya koma yayi zaman sa yana cigaba da kallon abin al'ajabi koh yunwar da yake ji ma sai yaji bazai iyya cin abincin da kule yasa baki zaici ba.

Da mamaki likita ya shigo yana kallon ta lallai jikin mara lafiyar mu yayi kyau harma neman kule take, ita dai batace kome ba sai da nurse ta d'auko kulen ta mika mata mata, tattabasa tayi sai kuna ta kara fashewa da kuka jinsa a longobe kamar sumemme.

Lahab kam cikin jin haushi yace"Dr asallame mu kawai naga kamar taji sauki gashi yanzun kusan 5 ake nema na yamma "

Ah ah lahab jikin dai da saura ka bari na d'aura mata karamin ruwa bazai wuce 1 hour ba.

Ok kawai yace yana mikewa tsaye ya fita a dakin itama da taimakon nurse ta koma kan gado ta zauna, shinfid'a kulen tayi a gefe ta kwanta kusa da shi.

Lahab na fita shop yaje ya sai mata sabon glass,yana dawowa ruwan na karewa bata glass in yayi ba musu ta karba cikin murna ta sanya a idanunta tana masa godiya.

Sallamar su likita yayi lokacin 6 yayi na yamma ana ma shirin kiran mangariba gabaki d'aya hankalin lahab na gida yasan dai yau baisan wace karyar zai suburbud'a ba bare ma yanda ya ringa ganin call na jama'an gidan su, amma yayi biris bai d'auka ba harda na muzammil.

Rigan ta Nnenna ta saka tare da d'aukar kulenta lahab yad'au mata jakan suka fita a d'akin shidai sai binsa take da kallo, koh ba'a fad'a mata ba tasan musulmine, koh yaushe ana sanar dasu musulmai mugaye ne, amma ita mutum biyu ta hadu dasu masu

Please Login or Register in order to submit comment