Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tari a hankali Abu Kamar kiftawar Ido saiga Rahab ya rikice da wani irin mugun tari,hankali tashe Lahab ya mike Yana Masa sannu a zatonsa Koh kwarewa yayi,Amma Ina Rahab tari yake Yana sarkewa wani hararwa da yayi ya yunkura zaiyi amai Aiko sai gani Lahab yayi gudan jini bakki Kirin ya Fado daga bakin dan uwan nasa a rude ya mike Yana salati Yana kamasa ganin ya Soma wani irin aman jini Yana wani irin mimmikewa,ihunsa da salati shiya shigo da Addayiya cikin dakin a rikice.





Salati ta sake hade da kamo Rahab in Lahab saban rikita rasa ma mezaiyi yayi da gudu ya fitoh cikin dakin sai Kuma ya koma da Sauri waya ya d'auka ya Kira ambulance sai kuma ya kasa hakuri yadau keyn mota ya dauka yazo ya ciccibi Rahab daya sandare baya Koh motse sai Kuma kunfa dayake fitowa a bakin sa bayan jini ya tsaya,gudu yake Yana kuka Koh takalmi babu a kafarsa ya fita tsakar gidan motarsa ya bude yasa Rahab Addayiya daga ita sai dankwali itama Shiga tayi yaja motar da karfin gaske ya fita a gidan da mugun gudu,daidai lokacin Adewale ya shigo arean ganin yanda Lahab ya fito gidan yasa sa bin bayan sa da motarsa shima.........................








*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*



gudu kawai Lahab yake shararawa Addayiya na baya ta daura kan Rahab a cinyar ta tana tofa Masa duk Addu'an da yazo bakinta"ruwa ruwa zansha ruwa"shine kalmar dake fita a bakin Rahab cikin magagin fitan Rai wani irin Jan birki Lahab yayi da gudu ya balle marfin motar don Babu ruwa a ciki kafa Koh takalmi Babu ya Soma gudu Akan kwalta saura kad'an wani Mai mota ya kadesa shagon wata Mata ya Shiga Babu magana ba kome kawai ya bude freezer ya dau ruwa ya fita da gudu cikin motan ya dawo ya shiga baya Kan d'an uwan nasa ya kama ya balle marfin Goran ya kafa Masa,gadai ruwa ya cika bakin sa Amma Koh kad'an Bai wuce ba sai dawowa da yayi Yana zuba,adaden ruwan da ubangiji ya rubuta Masa zaisha a duniya ya kare,ganin haka yasa Lahab ya Soma kuka,zai fita a sit in ya koma driver sit,sai Kuma yaji an rike Masa hannu da Sauri ya kalli hannun sai Kuma yace"sakeni Rahab sakeni muje asibiti babu abinda zai sameka.






"Lahab kayi hakuri da rayuwa kome yayi farko yana da karshe tabbas nikam ajalina yazo amma nagode Allah daba kaci abincin Nan ba da yanzun dukan mune a cikin wannan hali"kayi shuru sakeni mu tafi kaji Babu abinda zai sameka dan uwa ka manta tare aka haifemu tare zamu rayu Kuma mu mutu tare"?girgiza masa Kai Rahab yayi cikin azaba yace"wannan tsarine na ubangiji duk abinda ya tsara shine daidai Allah ya riga ya rubuta iyakacin rayuwar da zanyi a duniya kenan,naso kafun nabar duniya na Kara ganin mamina amma Dan Allah in tazo bayan babuni kuce ta yafemin duk abinda tasan na Mata Wanda nasani da Wanda ban sani ba kuce Mata Ina sonta,Kamar yanda nakeson ka kaida Addayiya Ina maka fatan Alkhari a rayuwar ka zan kwanta cikin salama mundin na mutu Lahab baka zubda hawaye ba,banason ganin ka kana kuka,sai wata rana"Yana karasa maganar yahau sassakewa la'ilaha'illahlah la'ilaha'illahlah............ Addayiya ta Soma cewa cikin kuka cikin yardan Allah Rahab ya karbi kalmar shahara"la'ilaha'illahlah Muhammadu rasulilah sallalahu allaihi wa sallam,wannan shine kalmarasa ta karshe daya furta a duniya Rai yayi halinsa.






Wani irin kafewa Lahab yayi a cikin motar jijiyoyin kansa kwayar idanunsa wani irin tashi sukayi suka zazzaro saiga jini ya Soma bulbulowa a hancinsa amma Babu Koh digon hawaye Sam babi hawaye a idanun sa, Addayiya kuka take tana maimaita innalilah wa'inna'ilahu raji'un, police ne suka matso kusa da motar ganinta a no packing matsowa sukayi daidai lokacin Adewale ya karaso fitowa yayi a motar shima ya nufi motan su Lahab in,kansa police yasa ta glass ganin wa'inda ke ciki yasa da Sauri ya Soma tambayar lafiya"?Addayiya na kuka ta musu bayani a take sukace Bari su dau Rahab akai hospital girgiza Kai Addayiya tayi tana cewa wani irin hospital Kuma bayan Rai yayi halinsa,Kinga ma wannan babban case ne gubafa yaci,daukar Rahab akazoyi Amma Lahab na damke da hannun dan uwan nasa anyi anyi a banbare yaki sai hakuri ake basa zuwa lokacin zama'a sun cika makil an zagaye motan daker da Nasiya Lahab ya sake dan uwansa da jagoran Yan Sanda aka kaisa asibiti,Lahab na zaune a kofar dakin da aka shiga da dan uwan sa gabaki d'aya kamannin sa ya sauka sai jini dake zuba a hancin sa anyi anyi ya shiga likitoti su dubasa yaki yace a barsa in ma mutuwa zaiyi ya mutu amma yaki kula kowa.





Abin mamaki da Yan Sanda Suka koma gidan don duba abincin wani shago aka saya Amma abin mamaki gidan a bude Suka samu Daman su Lahab Basu rufeba anyi Neman duniya ba'a ga abinci ba sai jinin da yake zuzzube a kasa da Kan gadon na Rahab,waya Ade ya d'auka ya Kira Abbu Yana sanar dashi abinda ke faruwa hankalin Abbu a tashe ya Kira ya jafar da mijin Mami ya sanar dasu akan zasu hau jirgin yawo zuwa London Amma kada ya sanar da Mami abinda ke faruwa harsai sunje London in sun dauko gawan sun dawo hatta jama'an gidan Abbu bai fada musu ba.






Alhaji sulaiman daman Suna falo da matarsa tunda ta tashi da safe Koh abinci bataci ba haka kawai take yawan cemai zuciyar ta na tsinkewa,shiyasa Bai fada Mata ba yadai ce Mata zashi emergency meeting a kwara state,dashi dasu Abbu suka wuce London a ranan sai washe gari Suka Isa zuwa lokacin Lahab duk Mai Imani inya gansa sai yaji tausayin sa gashi Dr yace sai an Nemo babba namiji zaiyi magana dashi ganin su gaba daya kuka suke Inka cire Lahab daya zamo mutum mutumi.





Lokacin dasu Abbu suka Isa anan likita ke sanar dasu cewa poison yaci Kuma a take ya tsintsinka Masa hancin cikinsa Allah ya Masa rasuwa innalilahi mutuwar mahaifinsu sabuwa ya zame musu yau sosai mutuwan yasasu tunawa da baban su,ya jafar har hawaye Saida yayi bincike aka shiga gadan gadan don sunki bada gawan sukace a tsaya ayi bincike amma su Abbu sukace Ina su zasu tafi da gawar kasarsu amasa sallah a binne sa.






CCTV camera dake gidan Lahab da Kuma cikin area aka bibiya tabbas anga wani da masks bayan fitansu Lahab ya shiga ya dau laidodin abincin saidai ba'a ga fuskar sa ba an bibiye camerori harna motar daya saukesa da Kuma Wanda ya dauke sa bayan ya fito a gidan haka zalika an dau wayar Lahab an dudduba anan aka ga shagon da akayi order anje shagon amma Waiter dayakai abincin ance tunda yakai ma su Lahab abinci Bai dawo ba bincike yayi bincike karshe aka rufe shagon kwata kwata magana tayi girma a garin sosai.





Su Lahab sun dau gawar zasu dawo nageria anan yayun sa sukace ya zauna a London bai Kamata ya dawo nageria yanzun ba Amma Lahab Koh amsa Bai Basu ba kuma Bai fasa Shirin binsu ba sufa abin nasa ya Fara basu tsoro tunda Rahab ya rasu shikenan Bai Kara furta Koh eh a bakin Saba sai dai kayi magana ya baka amsa a aikace.






*****************
Allah sarki uwa abinka da social media tuni zance ya karade Koh Ina ba Wanda baiji mutuwar Rahab a jikinsa ba Babu ma Kamar na kusa dashi wa'inda Suka San halinsa bazakaji wani ya aibata bawan Allah Nan ba sai dai kaji ana fadin Alkharin sa,Mami kan tunda taji labarin faduwa tayi a take marabanta da tun tana budurwan rabon dasu dashi toh a ranan sun tashi kame kame akayi da ita wallahi duk Wanda ya ganta saiya tausaya Mata ana samu iskan ya sauka sai Kuma ta kom Suma Kan Suma akayi asibiti da ita.




Dirowan dare su Lahab sukayi cikin NAGERIA duk da dare ne gidan su Lahab makil da Yan uwa na nesa da kusa sun cika gidan tab, shimfidasa akayi a falon Abbu,a daren Abbu ya Soma ma mamacin wanka Lahab na falon Yana taimaka Masa Suka shirya dan uwan nasa har lokacin idanunsa gangataran a bushe, Qur'ani yayun Suka d'auka duka Suna karantawa shima Lahab Yana rike da nasa karatu yake,kwanan ketso da akai Saida Suka sauke Qur'ani cip kafun safiya.





Jama'a sun cika gidan nasu da unguwan gabaki d'aya jama'a ne, a ranan Koh mutum baisan Lahab ba in yaji labarin su sai kaji yace zaije zana'ida Yan garin gombe Basu taba ganin mutuwa Mai jama'a a yanzun ba irin Wanda suka gani a mutuwan Rahab,Mami dake hospital tana farkawa za'a sake Mata Allura ta ringa kuka da magiya akan a barta taje taga gawan danta ta Masa addua ta Masa kallo na karshe, Dr yaso yaki amma sulaiman yace a barta,da taimakon sa aka baro hospital in da ita,tunda ta fito daga cikin mota wasu Mata suka fashe da kuka ganin yanda Amina ta koma Rana daya sai kaji ana ga mahaifiyar mamacin Allah sarki.





Kasa karasowa Kan gawar tahi sai da Addayiya dake gefe tayi kuka harta rasa Inda zata da kanta ta Mike ta Kama Mami Kamar makauniya ta ajeta a gaban gawan,hannu na rawa tasa ta bude fuskar sa Allahu Akbar kamar ka kirasa ya amsa fuskar nan tsab dauke da annuri,ya Allah kaji Kan wannan bawa naka ka Masa Rahama ka gafarta Masa, na yafe maka duniya da lahira d'ana baka tabamin abinda na kwana dashi a Raina ba yaro Mai biyayya,shekaran jiyan Nan ya kirani cikin dare Yana cewa na yafewa Dan uwan sa na daina fushi dashi,Ashe da rabon bazamu sake gamawa ba innalilahi wa'inna'ilahu raji'un Allah kaji kansa da Rahama ubangiji ka haskaka kabarin sa da rahamar ka ka bani hakurin rashin sa da dangana a cikin raina"ameen Ameen Yan falon suke cewa one by one yayun sa sukazo Suka Masa Addu'a.





Mikewa Lahab yayi a hankali Yana takowa kusa dashi Zama yayi ya Soma Masa Addu'a Yana nema Masa Rahama a wajen mahaliccin mu,kana aka dauko gawan a makara Lahab da Abbu sai muzammil da jafar su Suka rike sa aka Soma fita dashi Mami kuka ta fashe da karfi sai Kuma aka ga ta sulale a wajen Addayiya Kam salati take tana Allah ya jikan ka Allah ya maka Rahama yasa can yafiye maka Nan,Lahab Suna fitowa ana Basu hanya kofar gidan su Lahab yayi kad'an masallacin juma'ar unguwan aka wuce dashi don yafi fili Inda kasan sallan edi haka jama'a Suka taru.





Aje makaran sukayi daman an riga anyi Alwala aka Soma daidai ta sahu,juyawa da Lahab zaiyi saiya hange Ade acan gefen wani gida Yana zaune nesa dasu amma Yana hango duk abinda ake ga hawaye nabin gefen kumatunsa Yana sharewa juyawar da Lahab zaiyi wazai gani Nabeel ne tsaye a sahu wani irin super Lahab yayi yasa kafa ya taka kirjin Nabeel har Saida ya koma baya baya ya bugu da kasa ji kake Tim salati jama'a Suka Fara don a zaton su Koh hauka Lahab ya Fara fuskarsa cikin fushi har wani rawa Naman fuskar cikin rawan muryar sa daya kwana uku baiyi magana bane ta ratsa jama'ar cikin yakini da tsananin tsana ya nuna Nabeel kana yace"wallahi tallahi in baka bar wajen Nan ba zanyi ajalinka Kuma ka sani dan uwana Bai mutu a banza ba bakaci banza ba na rantse da sarkin daya busamin numfashi bazan barka ba.




Hayaniya aka Fara ana tambayar lafiya mikewa Nabeel yayi ya karkade jikinsa kana ya juya ya barwajen bisa umurnin wasu don an zati matsalan rashin Rahab yasa sa haka juyawa yayi ya shiga sahu aka tada sallan gawa,ana kammalawa aka d'auki gawan sai makabarta,Lahab da hannunsa ya Kama gawar aka saka a Rami lokacin da aka tura daidai lokacin jini ya Soma zuba ta hancin Lahab har Saida ya zuba a bakin Ramin a hankali ya d'ago sai Kuma mutane Suka soma salati ana cewa yayi Sauri yaje hospital wannan jini yafi karfin habo,kin zuwa yayi ya tsunguna aka binne dashi kana ya tsunguna agefen kabarin yanama Dan uwan nasa Addu'a gabaki d'aya jini ya Bata gaban rigansa Amma Bai damu ba.




Suna fitowa daga makabarta Lahab ya yanke jiki ya Fadi,Saida aka kwana biyar da mutuwar Rahab kafun ya farfado Mami duk tayi laushi tayi kuka tayi kuka harta gode Allah rashin lafiyar Lahab ya Kara daga Mata hankali Kai bama ga ita kadai ba har dangi sun tsorata kada tarihi ya maimaita kansa akan yaran nan,bare da akace Lahab ya samu heart attack shiyasa jini yake fita a hancin sa Kuma sun bada shawa Koda ya farfado don Allah kada aringa abubuwan da zai daga Masa hankali don zai iya rasa ransa gabaki d'aya haka zalika baza'a Kara basa abinci Mai Kara jini ba,farfadowar sa gabaki d'aya saiya chanja shi baya magana baya cewa kome ba uhmm ba uhm uhm sai dai kaga ya sunkuyar da Kai,toh baya Kara dagawa sai yaji Kiran sallah zai tashi yaje yayi Mami Kan intaga Lahab cikin irin wannan yanayi sai kaga ta fashe da kuka,ita a yanzun burinta Lahab nata nada ya dawo tafi kaunar ganin sa cikin walwala inyaso ana kawo Mata karansa tana Masa fada yafi Mata wannan shurun nasa so dubu duniya kenan waya taba tunanin wata Rana Lahab zai zama haka.





A cikin satutuka da Suka gabata kowa na dangin kokari yake yaga yasa Lahab farin ciki Amma Ina Lahab baisan anayi ba Adewale ma wuni yake tare dashi Yana Masa hirarraki amma Lahab Bai dagowa bare yasan anayi, sau uku Inna da mubeena suna zuwa dubasa,Allah sarki mubeena kallo daya zaka Mata ka gane ba karamin damuwa take ciki ba a rayuwar ta, watan su Lahab biyu a hospital aka sallame sa ya dawo gida, Adewale haka zaizo tun safe suna tare da Lahab Yana Masa hiraraki abubuwa, duk da Lahab baya ce Masa kalallahu sai dare yake tafiya abinci wannan Lahab sai anyi da gaske yakeci so daya a rana yawan tasa hoton su Wanda suka d'auka da Rahab yasa aka kwashe duk hotonan Rahab aka boye,sai Kuma ya koma tsayawa a gaban Miro tayita kallon fuskar sa Kamar tababbe.




Zaune yake a garden na gidan su, Ade na gefen sa sai kokari yake yaga Lahab yaci Koh wani Abune amma Lahab yaki,bude gate na gidan Mai gadi yayi sai ga mota baka kirim guda daya ta shigo gidan mutane uku ne suka fito a ciki Suka nufi cikin flat na gidan ba'a Jima ba saiga Addayiya dasu Abbu tare da mutanen sun nufo garden in,wani irin zaku tafi dashi meya muku gashi Yana under medical don haka koma menene bazaizo ba sai yaji sauki"am sorry sir Dole zamu tafi dashi munso tafiya dashi tun bayan mutuwar da akayi amma mukayi hakuri har yakai iyau"





Toh Wai me yayi ne"?wannan Kuma sai kin biyomu zakuji"Kai officer dakata wani irin wulakanci ne wannan da baza'a Mana bayani ba toh wallahi Babu Mai tafiya dashi"muzammil yace don haryau Bai koma ba,gyada kai dayan yayi kana yace"yayi alwashi ga wani yaro Nabeel na ikirarin ganin bayan sa,kana case in kisan da aka taba shariya dashi ya taso sabo iyayen yaro sun daukaka Kara don haka zaku bamushi dole"kaga dakata officer wannan yaro Nabeel da ake magana kowa yasan Nabeel da Lahab haka zalika Lahab bazai taba cutar dashi ba zafin mutuwa ne yasashi furta wannan kalaman maganan case na Abraham Kuma yanzun baida isheshen lafiya so bazamu badashi ba har sai yaji sauki"




Mika musu hannu Lahab yayi baiyi magana ba tsawa Abbu ya buga Masa Yana cewa"Kai Lahab kanka daya kuwa koka haukace ne da zakayi surrender"dan Allah yaya kayi hakuri ku Bari su tafi Dani Kamar yanda doka ta umurta Kuma a shiga kotu na amince da duk wani hukunci da za'a yanke a kaina" Abbu ya wankesa da Mari daidai lokacin Mami ta shigo gidan don itama yanzun kullum cikin zuwa take saboda farin cikin d'anta,har cewa tayi ta yafe Masa duk lokacin da Allah ya bayyana yarinyar zata karbeta hannu bibbiyu,Kuma ta basa dama yanemeta,amma Lahab a lokacin da tayi maganan Nan Koh annuri bataga ya wanzu a fuskar Saba bare ya d'ago Kan nasa daga duke.




Karasowa tayi tana tambayar lafiya shikam Lahab gaba yayi yaje ya Shiga motar tasu aiko sunga hauka Mami bala'i babu Wanda batayi ba Amma Koh kulata basuyi ba haka Suka shiga Suka tafi da Lahab..






**************
Wata sabuwa inji dan caca,zance ya karasa gari akan abinda ya faru kowa zagin Nabeel ya Fara aka abinda ya aikata wasu Kuma Suna cewa ya musu daidai,Abbu yadau lauya akan case na Abraham zancen Nabeel an ajesa gefe dan karamine shikam,in an shiga shariya duk lokacin da akayi zaman kotu Lahab baya magana sai lauya yayi jawabi in ance hakane Koh ba haka ba anan zaice musu hakane babu Koh musu abinda ya Kara Kona ran family sa kenan don sun fahimci so yake ya mutu shima,Mami da Addayiya sunyi kuka harsun godewa Allah jarabawar da Allah ya jarabcesu kenan dashi a shekaran nan Suna Addu'an Allah ya Basu ikon cinyewa.





RANAN TONON ASIRI
Ayau akayi Zama na karshe Babu Wanda Bai hallanta a kotun Nan ba harda peace (Mai aikin su Nnenna da aka Kai prison)family Lahab danasu Nabeel ganasu Abraham Kai jama'a a kotu makil Adewale ne kawai Babu shi Inna sunzo da mubeena Kuma tasa Nabeel ya janye Karan daya daukaka Akan Lahab don shima yanzun yayi kudi sosai Wanda ba'a San daga Ina ba,jinsa yake daidai da uban kowa shiyasa Koh Zama aji ya gagaresa"badon ransa yaso ba ya janye sai don kuka da Inna ta sanya Masa tana cewa zata tattara kayanta ta gudu ta barsu kafun ya janye zancen aka Kama na Abraham kawai,an gama gabatar da shaidu da hujoji Kuma Lahab ya amsa laifinsa na cewa dasa hannun sa aka kashe Abraham kamar yanda ake zargi.




"Abisa duba da hujojin da lauyoyi Suka gabatar, da amsa laifinsa damai laifin yayi wannan kotu Mai adalci ta yankewa Hassan Al'hassan dogo Mai naira hukuncin........................................Ina daja ya Mai shariya"kattafanin kotun sukaji Amon muryar mutumin daya shigo cikin kotun ga Adewale na binsa a baya"mikewa tsaye Alhaji sulaiman yayi jikinsa na wani irin Bari sakamakon ganin Wanda ya shigo cikin kotun yace"kaiiii buba meya kawoka nan haka mukayi dakai baka tashi bayyana ba sai a irin wannan Rana tsawon shekarun nan..........................................






*Naga complain na mutane akan mutuwar Rahab Amma fa kuyi hakuri littafina na riga na tsarasa akan hakan ne,Kuma Inna bite na cire wannan bar wannan daga baya Zan rikice ne kawai in ban mantaba shekaran jiya nayita samun magana akan character in Lahab wasu sunce zasu bar karantawa saboda Babu Wanda Lahab yakejin tsoro kaza kaza kana jiya ance kunci zaima Lahab yawa* 🤧🤧🤧 *

*Kunga ai Inna sake nawa na Kama naku karshe nazo na makale a hanya Ina zare ido Daman shi rayuwa ba kome akeso ake samu ba Daman haka rayuwa take aka rasa uwa ma Kuma mutum ya hakura*




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*



Wani irin murmushi Lahab ya sake yana gyada Kai ganin Wanda ya Jima yanason gani ya bayyana a bayan Ade wato abokinsa Barrister khamal najib,tsawa alkali ya buga da guduman sa don da yawa sun mike tsaye cikin su harda ummu da Addayiya,natsuwa kotun ta danyi kad'an kafun sulaiman ya mike Wai hawan jininsa ya tashi zai koma gida hanasa fita akayi a ciki code in ganin Kamar akwai bayani a bakin Wanda ya shigon,Koh zaka sanar da kotu Kai wanene da Kuma dalilin shigowarsu a irin wannnan lokaci ana tsaka da Sharia"Zama Ade yayi mutumin da sulaiman ya Kira da buba sai Brr daya gabatar da kansa a matsayin lauya Mai zaman kansa Kuma mataimakin lauyan dake Kare Wanda ake zargi,kotu sosai yayi tsit sai ummu dake da zufa sai yanko Mata yake"Kara natsuwa khamal yayi ya gyara zaman rigansa kana ya nemi izinin Fara gabatar da hujojinsa na Kare Wanda ake tuhuma"an baka dama"shine abinda alkhali yace"nagode ya Mai shariya sai Kuma ya juya yace"Kiran buba yayi ya fito ya tsaya a inda masu bada shaida Koh masu laifi ke tsayuwa tambaya Brr ya Soma Masa Kamar haka"Malam Koh zaka iya sanar da kotu cikekken sunan ka"eh Sunana Adamu ja Amma anfi kirana da buba ja"Masha Allah Koh zaka sanar da kotu menene alakanka da family dogo Mai naira da Kuma son halartar shariya tayau daka nema"?




Kamar yanda nace Sunana bubaja Ni ainahin dan nijar ne kamar yanda kowa ya gani Ni buzune,Neman kudi ya kawomu NAGERIA nida iyalina,bamusan kowa a kasar Nan ba tunda mukazo wahala mukesha sai dai mu samu bayan shago Koh gida mu rabe mu zauna muna kwana Ni Kuma Ina Saida shayi.




A hakan wata Rana Allah ya hadani da Alhaji Alhassan Harya daukeni aikin gadi a gidan sa nida iyalina mun koma gidan sa da Zama Kuma Babu abinda Muka nema muka rasa rayuwa ta Mana dadi dayake matar Alhassan macece Mai fada Amma tana da kyauta hakan yasa Muka kashe zuciyar mu dagani har matata Muna cin harziki harda yaron mu.




Nafi shekara ishirin Ina gadi a gidan Alhaji hatta makarantan d'ana shike biya,mun Zama Kamar Yan uwa,yayansa sun giggirma har wasu sunyi aure.




Bayan wasu shekaru zuwa lokacin gidan ya Kara cika ga aure da Alhaji ya Kara ya auro Amina,tunda Alhaji ya auro Amina kullum sai sulaiman yazo kofar gate yayiita min magiya Akan na Kira Masa Amina Koh Kuma ga wasika na Kai Mata amma Koh daya ban amince ba duk yanda yayi ta hadani da Allah naki,ana haka sai kanwarsa ta Fara zuwa gida tana baiwa Amina wasika daga baya Allah ya tona asirin abin Alhaji ya ganosu shikenan sai yasa security a gidan tsaro ya ninka nada.




Shikenan tun daga lokacin bankara ganin sulaiman ba Ni harnama manta da labarin sa,kwasam wata rana saiga yarona ya shigo gidan da gudu ya Kama hannu na Dana mahaifiyarsa Muka nufi sashin mu don yanzun mun Jima da barin bakin gate,hankalin mu ya tashi da abinda ya sanar damu kwata kwata bamu taba kawo hakan a ran mu ba cameran daya dau kome ya bani kana yace in nunawa Alhaji,Kuma ya Kamata mu gudu mubar gidan don Sun gansa dumu dumu Yana musu vedio"shin yanzun kana tare da kemeran ne tsahon shekarun Nan Koh yaya Kuma ya Kamata kama kotu bayani dallah dallah suwa dan naka ya gani"?





Eh dama Yana karatun jarida ne da Alhaji yadau nauyin sa yace min wata Rana sun fito makaranta Suka biya gidan abokin su zai dubasa kutsam sai yaga Khadija(ummu)ta shiga wani gida dake unguwan shikuma yayi zaton Koh gidan Yan uwantane yace Bari ya shiga ciki ya gaidasu saiya bita cikin gidan Yana kokarin bude kofar dakin ya shiga sai ya Fara Jin magana na tashi Nan ya zagaya ta window yasa hannu ta baya ya bude labule wa'inda ya gani a ciki yasa sa daukar camera sa yayi record na kome Yana tsaka da daukane Mutumin ya gansa harma da matar suka bisa shine ya fito a cikin gidan.




A ranan yarona yabi ya rikice akan mubar gidan nace Masa Ni sai na nunawa Alhaji Kuma na Masa sallama bazaiyu nabar gidan baby sallama ba kuma in Muka koma nijar Banda sana'a Koh wani aiki Amma hakan yaron Nan yace sai dai mu tafi shi haka kawai yaji tsoron Zama a gombe,mahaifiyar sa tace ya shirya kayansa zata tafi dashi in yaso inya samu natsuwa sai su dawo in Kuma Basu dawo ba Nina bisu,haka Koh akayi a ranan Suka bar gidan,nayita jiran ganin fitowar Alhaji Amma bansamu ganawa dashi ba Ina zaune Khadija ta dawo tazo ta shiga gidan.





Washe gari abin mamaki saiga Alhaji ya tashi da ciwon kafa hankali na ya tashi naso naje na sanar dashi Amma Kuma saina kasa Koh shiga cikin falon gidan a hakan yayita ciwo wata da watan Ni duk lokacin da na yunkura Zan sanar dashi sai na kasa, har Allah

Please Login or Register in order to submit comment