Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gidan mu, koh zan manta da hidiman kowa wallahi baxan manta dake ba kin mana goma sha tara wanda koh mahaifiyar mu bata kula damu ba kamar yanda ke kika kula damu, don Allah ina rokon ki ki sanar dani abinda ke faruwa"?


Shuru tayi tana kallon lahab sai kuma a hankali ta kamo hannunsa, lahabu bawai banason fad'a maka bane nasan halinka ne shiyasa?

"Insha Allah babu abinda xai faru waye ya zageki koh wani abin aka miki"?

Lahabu babu abinda aka mini a gidan nan daman yarona kuda d'aya da Allah ya bani ne yana da sikila tunda aka haifesa yake fama da jinya ba'a wata biyar sai an daura masa laidodin jini, duk Albashina a jinyansa yake karewa Kanaga dai Abinci ma na gidan nan nake ci natafi masa da nasa.

"eh sai mai yafaru gogoji"?lahab ya kara tambayar ta jin tayi shuru.

Shine wannan karo koh wata biyu baiyi ba daga jinya aka sake bukatar wani jinin don tun jiya yana asibiti gashi bani da wasu kudin a guna, shine nacewa Mamun ku akan tamin magana da Alhaji ina son magana dashi don Allah.

Shine ta tambaye ni meyasa nakeson magana dashi saina gaya mata akan inaso ya taimake ni da kudin aikina na wata biyu zan ma d'ana jinya in ya samu lafiya saina cigaba da aikin har na gama na wata biyun ma.


Shine tace wai baza'a bayar ba kuma na kuskura na gayama Alhaji a bakin aikina tunda daman ita ta d'aukeni aiki, kuma bazan tafi ba saina gama aikina nayau, ta karasa magana cikin kuka.

"Ran lahab a bace yace, kenan yanzun d'anki na asibiti kikazo kina aiki kika barsa"?

Don Allah Lahab karka nema mini magana kabar maganan nan kawai na yafe insha Allah zanje na samesa lafiya.


"Wani irin koshin lafiya bayan kin zabi aiki sama da d'anki, taya zaki amince da abinda mamu ta fad'a bayan kinsan Imani bai wadace taba"?


Don Allah lahab kayi shuru ka daina magana da karfi kar ajimu, yanzun innaje naxo na rasa aiki fa a ina zan samu wani aikin da zan tallafawa rayuwar d'ana?


"ki tashi ki fita a gidan nan ki jirani a kofar gidan su adewale ina zuwa"ya karasa maganar da mikewa tsaye.

Da sauri gogoji tace, mezakayi lahab na rokeka karka jawowa kanka wani rigimar kuma? kadai san mamu akwai iyya munafurci abinda bakayi bama tana kitsawa ta fadawa Alhaji bare kayi.

"Karki damu gogoji kedai ki jirani kawai ina zuwa inta tambaye ki ina zaki kice Kiranki akayi daga asibiti jikin yaronki ya tashi kuma karki kuskura ki tsaya koh tana miki magana ne, muje oya"yace yana kama hannunta suka fita a kitchen in, bayan ya kashe gas data ke girki dashi..

Bai saketa ba saita suka zo mahaden falo ya sake mata hannu tare da nuna mata hanya ba tare da yayi magana ba, itama ba musu ta d'auki hIJAB nata ta wuce falon.

Shikam sashin su Mamu ya wuce tura kofar sashen yayi a hankali yana bin koh ina da kallo tsarin gininsu ba irin nasu bane duk da suna flat d'aya, amma an tsara musu bangaren su, kofofine guda uku a falon tura kofar mamu yayi ya shiga ciki.

Bincike ya fara mata daga akwati har wardrobe, drower koh ina sai da ya bincika amma ina shuru bai samu koh sisi ba zagin mamu yake a ransa na mako irin nata ita kullum saidai ta samu a jikin Abbu amma baxata ci nata ba.

Jakan hand-back nata ya d'auka ya bude ATM ya gani har guda uku, zaban master card nata yayi ya soka a Aljuhu tunawa da yayi ranan ta aiki Rahab bank dashi, kuma yaji Rahab na tambayar ta ta waya menene pin in ATM in a lokacin suna d'aki.


Da sauri ya fita a d'akin maimakon yabi hanyar falo babba, sai yabi baya wata kofar ya fita a falon su mamu, sai ya bi kofar lambu ya fita a flat in ta baya, ya zagoyo ya fita ta get da sauri ya nufi gangaren layinsu har kofar su Adewale, aiko gogoji na tsaye tana jiran sa.

"Gogoji muje koh"?.

Ina xamuje Lahab?

"Kekam muje mana bakin yiwa mamu sallama ba"?

Eh na mata sallama dayake ma Alhaji na falon bata tambaye ni ina zanje ba, danace mata zan koma gida tace ba damuwa.

"ok muje to"ba musu ta bisa har suka tsallake titin unguwan nasu sai da suka iso wani shagon POS, mika ATM in yayi tare da fadar Pin in yace kuma a cire masa dubu dari uku a ciki.

Ba musu masu Pos suka cire masa kudin dakad'an kadan har suka gama a take ya mikawa gogoji, data sake baki tana kallonsa dubu 150k"gashi gogoji ki masa jinya karki sake dawowa har sai yaji sauki in ma kin dawo ta koreki sauran changen ki kama sana'a dashi Allah ya basa lafiya"

Kuka ta sake Ah ah lahab Aina ka samu kudin nan, dakake bani karfa kaje kasa kanka a rigima nasan halinka?

"Ba wani rigima kudina ne danake tarawa duk randa aka d'auke mu ball a kasar waje sai na tafi dashi"

Toh Allah yayi Albarka na gode maka Allah ya rayaku Lahab ya rage maka fitina

"Kai gogoji zafa mu samu matsala dake tunda kema irin su mami zaki zama"?


Ah ah d'an gidana ba'zama ayi haka ba, kaga tafiyata.

"Am gogoji d'an tsaya don Allah nace ba karki fadawa kowa na baki kudi kinji"?
.

Toh saboda me ?

"Nidai na fada miki, in ba haka ba zaki saka kanki a matsala ehen" kawai yace ya juya ya kara gaba ya barta tsaye agun tana binsa da ido.

Lahab bank ya wuce yasake maida sauran kudin daya cire a Account nasa, master card nata kam wurgarwa yayi a kwalben abinsa bai koma gida ba, ya wuce shagon su nabeel don yasan war haka baya gida, aiko bai samesa a shagon ba, wai Adewale yazo sun fita tare.

Komawa gidan su Nabeel in yayi ya kwanta a dakin sa, bai saurare masifar inna ba kona mubeena.

Bacci yayi sai kusan azahar suka dawo, anan suke sanar dashi ai sunje gidan su ance musu bayanan gashi kamar yan gidan ma neman sa suke, sai kawai suka wuce gona.

"Me kuka samo a gonar"?

Rakene sai yalo, Nabeel ya basa amsa

"lallai fa ai gwara da banje ba yanzun ina abinda kuka sinkon yake"?

Yana tsakar gida inna tace sai dai mu fitar mata dashi a gida bazataci kayan sata ba.

Aiko ku tashi muje wajen audu mai rake ya saye su koh zamu samu na kashewa


"allah ya sauwaka nafi karfin 10k yanzun bare wani banzan rake sai kun dawo"?

Shuru sukayi suna kallon lahab tunda suka ji yace haka sunsan ya nada kudine, shiyasa ba musu suka fita su biyun suka sabi rake da tunben buhun yalo sukayi kofar gida, inna sai kutuma musu zagi take mubeena na tayata.

Suma basu dawo gidan ba har yamma sai kusan 3:30, a waje suka hadu da Lahab daya fitoh masallaci, dukan su a gidan su nabeel sukayi wanka suka shanja kaya zuwa na ball inda suka saya jiya gabaki d'ayan su sanye suke da jese fari sai takalmi baki da socks na ball fari daya kai musu kusan gwuwa, wayar Lahab sai kara take Amma yaki d'agawa harsu Adewale na tambayar sa dalili Amma shuru ya musu, ya kashe ya aje a dakin nabeel

Ball lahab ya rike a hannunsa suka fita a gidan, Kekenapep suka hau zuwa filin ball inda ke tsallaken unguwan su a cikin wani makarantan gwannati don ball zasuyi da yan ungwuwan.


***************
Nnenna na duke a cikin daki tayi kuka harta gaji jikinta sai rawa yake, jin An banko kofar falon yasata mikewa da sauri.

Nnenna !!!! Nnenna come Out?

Jikinta na rawa ta fito a dakin cikin kuka tazo tayi lingdown a gabansa, had'e hanneyenta tayi tana rokonsa, Amma ina kwasheta yayi da kafa ta fadi warwar a kasa kafun ta mike ya rufeta da duka, cikin masifa yake cewa kin cuceni ada ban yarda da duk abinda za'ace mini ba akanki, saboda babu wanda ya taba kamaki kinyi kisa da hannunki sai yau zakije ki kashe yar mutane? banace miki karkije kogi ba ashe sai da kikaje, finzgota yayi ya maka da jikin gini a take bakin ta ya fashe jini ya soma dalala ga glass nata daya fadi a kasa.

Cigaba da dukanta yayi, ashe kece kika kashe onyebuchi yau chukwudi ya farka yake sanar da iyayen sa ke kika ma onye Alkawarin mutuwa shegiyar yarinya duk kin sani a bala'i nayi dana sanin sanin ki wallahi a duniya kin rabani da kowa nawa.

Kuka kawai Nnenna keye tana kare dukan, da gudu wata tsohowar mata ta shigo dakin nasu cikin tashin hankali tazo ta amshi Nnenna a hannun papa kallon sa tayi rai a bace tace.


Mr Obinna duka bashi bane zai gyara kome kuma ina so kasan cewa yarka bata da laifi kai koda tana dashi yau bai kamata kaima ka nemi halaka taba, toh bara kaji yanxun haka yan kauye suna tinkaro gidan ka da niyar kashe yarinyar nan kai ya dace ka taimaka mata.

Cikin tashin hankali papa ya daura hannu akai yana kiran jesus, sai kuma ya ruga da gudu yayi d'akin Nnenna biro da takarda ya d'auko yayi rubutu a ciki da sauri ya fitoh falon.

Nnenna dake kuka a jikin matar ya mika hannu ya kamata ba tare dayayi magana ba ya nufi kofa da ita da sauri ta fizge hannunta tayi wajen kulenta dake zaune kansa a kasa kamar mutum haka ya duka, d'aukar sa tayi da sauri tabi papa a baya.


Suna fita a kofar su da gudu suka kama hanya zasu bar gari koh rabin kauyen basu fitaba suka ga tawaga na binsu na matasa da mata da mazan kauye wasu na rike da sanda wasu wuka wasu jarkan petur.

Gudu papa suke da Nnenna jama'a na binsu ganin suna basu wahala yasa wasu bin shunkut suka tarosu ta gaba sosai jama'a suka kewaye su, wasu mazaje majiya karfine suka tinkare Obinna(papa) suka kamasa rike sa sukayi a gefe suka bar Nnenna a fili tsaye da kule a hannunta idanunta koh glass babu kuma ba kallonsu ma take sosai ba tadai san yau suna cikin tashin hankali da ba'a saka masa rana.

Tana cikin tunanin halinda yau xata kasance kawai taji ihun papa yana had'asu da jesus karsu kona masa yarinya suyi hakuri zasu bar kauyen zasu tafi a garin suyi musu gafara.

Bata ma gama fahimtar kome ba taji an kamata janta sukayi tana kuka tana kome suka daureta da jikin bishiya wasu suka kwarara mata petur a jiki daga sama har kasa,Nnenna kuka ta saka tare da rimtsa idanunta gudun kar ya shigar mata ido.

Kara papa ya sake ganin wani ya kunna leta tun daga nesa ya jifo mata, Amma abin mamaki wutan na faduwa a cikin petur kawai ya musu, sun gwada hakan yafi sau biyar Amma wuta yaki kamata.


Wani daga cikinsu ne ya zaro sharbebeyar wuka cikin zafin rai yake cewa tunda bazaki kama da wuta ba wallahi sai nayi ajalinki jinin sister na bazaki sha bulus ba, da gudu yayi kanta baiyi wata wata ba kawai ya d'aga wukar ya burma mata, kara ta sake da karfi ganin wanda wukar ya caka shima yaron ihu ya sake hade da kama kansa ganin abinda ya aikata wa............................







✨Ruqeenjalal✨




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

Free page🀧

*EXQUISITE WRITER'S FARUM*


page1⃣3⃣&1⃣4⃣
Papane wukar ya caka a ciki ashe lokacin da wannan guy in ya tinkare Nnenna papa ya rugo da gudu unexpected ya shiga gaban Ta, wukar ya sauka a cikinsa.

Ihu Nnenna ta sake da karfi a take tayi tsalle ta fizge igiyoyin dake jikinta, a take suka tsintsinke, cikin hanzari ta taro papa dake kokarin kaiwa kasa.

Kuka take cikin yare take magana, pls papa karka tafi ka barni bani da kowa sai kai, me yasa baka bari An kasheni ba kai kayi rayuwar ka Meyasa??meyasa?? tana maganar tana kuka.

Cikin magagen mutuwa papa ya kama hannunta yasa mata paper dake hannunsa, a hannunta cikin Azaba ya soma mata wasiya, Nnenna ke ya dace ki rayu bani ba, don ni tawa ta kare wannan Address na d'an uwa nane yabar kauyen nan shekaru da dama ki bar garin nan ki tafi wajensa, sai kuma tari ya sarke masa.


Sai da ya sakaita kafun ya cigaba da magana jini na biyo bakinsa, ki rike Addininki kinga AREWA zaki tafi, zakiga abubuwan da suka sabawa Al'adun mu ki iyye bakin ki aduk inda kika tsinci kanki, kiyi hakuri da rayuwa sannan ki xamo mai kawaici domin fushin ki Ajalin wasu ne, naso na sanar dake koh da wani abune a game dake kafun nabar duniya Amma hakan baxaiyu ba lokaci na yayi, Amma nasan wata rana zaki san kome koh bajima koh ba dade, in jesus name?

"Emeen papa bazaka mutu ba asibiti zan kaika" ta karasa maganar hade da kokarin kamasa ya mike tsaye, Amma ina rai yayi halinsa.


Ihu ta sake da karfi sai da ya Amsa amo kuka take da karfi tana rungume da papa.

Inyamuran nan basu wani ji d'ard'ar ba, suka sake yunkurin d'aureta Amma abin mamaki duk wanda ya taho gareta sai dai kawai aga yana faduwa macece yayin da ita kuma ke duke cikin tsananin bacin rai.

Ganin abinda ke faruwa yasa sauran mutanen gudu sosai, kauye ya kashame da guje guje, yayin da Nnenna ke tsungune a gindin bishiyar rike da papa har lokacin kuka take tana maijin wani irin ciwo da fushi a ranta.

Dafata taji anyi da sauri ta d'ago domin ganin wanda ke tsaye a kanta, tsohowar d'azun datazo ta sanar da papa za'a kasheta ne, tsaye tana hawaye, Nnenna kiyi hakuri kinji rayuwa haka take tafiya da kaddara iri iri abinda yafi miki ana shine kiji maganar Obinna kibar garin nan ki tafi inda ya turaki.

D'aga mata kai Nnenna tayi tana mamakin kallon matar da take zarzar tunda aka cakama papa wuka ta koma kallo kamar kowa gashi ba glass a idanunta"bani da kudi ki dubi kayan jikina akwai petur bazan iyya tafiya a haka ba "?

Ina zuwa kawai tace, ta koma cikin kauye, ba'a jima ba sai gata da kaya dogon riga ta had'a da kudi 10k ta mikawa Nnenna, gashi kisa kayan wannan kudi kiyi kudin mota.

Karba Nnenna tayi sai kuma ta kara kallon matar, momy ni zan jira a binne papa dani kar abar gawansa a wulakance"?

Karki damu daughter ki tafi na miki Alkawari gawan papan ki zai kwanta a mutunce?

Mikewa tayi a hankali ta juya ta kama hanyar fita a kauyen gabaki d'aya, daman sun riga sunyi nisa tana kuka tana tafiya rike da kaya da kudi a hannu sai da ta kusan fita a kauyen kafun ta shanja kaya, kudin ta saka a Aljuhun rigan har lokacin warin petur take.

A haka ta ringa fasa hanya zuwa lokacin At least 5 na yamma zaiyi tana fita bakin titin ta samu machine mai kafa biyu, ta tare akan tanaso ya fitar da ita zuwa tasha, shikam mai machinen haka kawai yaji shakkan ta da tsoron d'aukar ta ganin kyau inta yayi yawa karfa yaje ya d'auki Aljana gashi hanyar ba mutane.


Ganin kamar bazai d'auke ta ba yasa ta zaro masa 2k ta nuna masa akan zata biyasa mundin ya kaita, inyamuri da kudi ba musu yace ta hau, harta hau machine zai ja da mamaki kawai taga kulenta a gindin machine a zaune yana kallonta ita harga Allah ta manta da zancen kulen ma tsabar tashin Hankali.

Da sauri ta sauka ta ciccibesa ta hau suka ja, basu suka isa tasha ba sai 6 gashi babu mototi kowa ya tashi kudi ta biya mai machine in ta koma wani rumfa ta xauna a bakin shagunan wasu masu manja da suka kulle.

Har dare ya raba tana wajen a zaune koh motsawa batayi ba har aka fara yayyafi kamar wasa aka fara zuga ruwan sama sosai tun baya samunta har ya fara tabata.

Ruwa akayita jugawa har 9 na dare zuwa lokacin gabaki d'aya tashan babu kowani maluki sai ita kad'an ta kowa ya kara gaba ga sanyi ga yayyafi.

Tana zaune kanta a duke sai digar da hawaye take tana tuno Abubuwan dake faruwa a rayuwar ta, wai menene laifin ta meyasa sai ita kad'ai Abubuwan nan ke faruwa da ita, avinda ke yawo a ranta kenan, jikawai tayi an haskata da touch, Amma koh d'ago kai batayi ba tanajin sahon kafar mutane, Amma hakan baisa taji koda d'an tsoro ba, don zuciyarta yanzun yariga ya kekashe duk wani tashin hankali, gani take kamar ta riga ta gama ganinsa a kauyen su, tunda har wanka da petur aka mata za'a cinna mata wuta.

Kamar da wasa taga maza hudu akan ta dagani dai irin yan iskan nan ne, kama mata hannu dayan yayi cikin maganar yan kwaya yake cewa, kai baby ya haka naji kina warin petur Amma dai duk da haka bamu damu ba, zamu iyya a hakan ma.

Fizge hannunta tayi kawai ta mike tsaye kulenta ta d'auka, Zata kara gaba da sauri d'ayan ya sha gabanta hannu yakai zai taba mata kirji, ai ji kawai yayi anyi sama dashi an buga a kasa ya sake kara da karfi jin kamar kafarsa ya karye, ita karan kanta a tsorace take ganin abinda ya faru duk da a duhune, tsere suka shigayi ita da yan kwayan ana rige-rige kowa gudu yake don ita ma arcewa tayi, bata tsaya ba sai gonan wani dake yankin wajen ta shiga ta kwanta a cikin ciyayi.

Har asuba Nnenna idanunta biyu, yau dai idanunta sun koma kallo kamar ko wani mai lafiyar ido, sai kuma ta tsinci kanta da rashin jin bacci kwata kwata koh tashin Hankali ne yasa ta kasa baccin ne oho.



****************
Lahab basu dawo daga ball ba sai kusan 6 na yamma, bai saya bin gidan su nabeel ba direct ya nufi gidan su, haka ma adewale gidan su ya shiga, da sallama ya shigo babban falon sai kuma ya saya yana bin kowa da kallo ganin gabaki d'ayan su a tsatsaye alamu dai shi ake jira ya shigo.

Basarwa yayi kawai ya shigo falon irin koh a jikinsan nan ya kama hanyar bangaren su.

Lahab!!!Abbu ya kira sunan sa tsayawa yayi yana kallonsa ba tare da ya Amsa ba, jin abinda Abbun ya cigaba da fad'a, Lahab ka d'auko card in Halima ka bata sannan ka fitoh mata da kudin ta?

Hade fuska yayi sosai ya tamke tamau irin ba wasa a cikin nan"A gaskiya a gidan nan ana mini abinda bai kamata ba, ace ni shikenan an mai dani agola nida gidan ubana bani da sakat, yanzun rabona da cikin gidan nan tun yaushe Amma a rasa wanda za'a d'aurawa sata sai Lahab saboda an mai dani barawo"?

Da sauri Addayiya ta cebe zancen ai barawon ne, koh karya aka maka baka sata?

"Karki kara cema d'an uwana barawo Addayiya kikiyaye bakin ki? tayaya zakuce shiya d'auka mata abu batare da anyi bincike ba, kuma taya ma zai d'auki ATM nata Alhalin baisan pin in ba, ai sai a tuhume ni da yaranta tunda muke cire mata kudi bashi ba?

Da mamaki kowa ke kallon Rahab kiri kiri Lahab xaiyi abu Amma haka xai goya masa baya kuma sun tabbatar lahab ne kad'ai xai iyya aikata abin nan.

Kuka mamu ta sake da karfi tana nuna Lahab, cikin masifa take cewa, wallahi kai zaka aikata tunda naga Rashida tace mini zata tafi bayan shigan ka kitchen zuciya ta ta rayamin kaine zaka sace mini kudi?


Da mamaki shareef yace mamu me kike nufi bamu gane ba?

Kwashe yanda sukayi da Gogoji mamu tayi ta sanar dasu, salati abbu ya sake ya farama mamu holo akan abinda tayi da wasa da rayuwar wasu wannan ai rashin imani ne taya d'an mata na cikin Ciwo tazo a taimaka mata Amma har tana mata barazana da rasa aikin ta, aiko kyauta yaci ta baiwa gogoji tayiwa d'anta jinya, sosai fad'a ya koma kan mamu maimakon Lahab da ya baro ta.

Sosai taji bakin ciki da kara tsanar Lahab a ranta fiye da da, especially da Abbu yace su shirya bayan isha'i suje su duba yaron gogoji su bata kudi tayi hidimar jinya.


Lahab cikin murna ya cinna mamu ya wuce d'akin su yau koh holo bai Amsa ba, wanka yayi ya ibi abincin da Rahab ya kawo masa yaci abinsa bayan isha'i sukaje asibitin, sun samu jikin yaron da sauki, Abbu ma ya bawa gogoji kudi sosai haka ma ummu da Addayiya, tare da sanar da ita babu zancen kori a tsakanin su sun zama d'aya ai tsawon shekaru ba wasa bane.

Itama bata fad'a musu Lahab ya bata kudi ba.

Suna dawowa lahab ya xauna a falon su yana kallon ball, don ya manta da wayan sa a gidan su nabeel, gabaki d'aya ya tattara hankalin sa akan kallon.

Anwar daya fito dakin sa sanye da rigan bacci da wando, hannu yasa ya d'auki remote ya chanja tasha zuwa news, da mamaki Lahab ke kallonsa ganin ya zauna yana wani abu isa-isa,mikewa yayi yana kallon Anwar ya mika masa hannu hade da cewa"bani remote"?

Innaki baka fa sai me?

"Sai kowa ma ya rasa"lahab ya basa Amsa

Au haka koh toh a rasa kace koh? karamin mara kunya d'an iskan karya wallahi tarawa nake ina jiran uncle muzammil ya dawo ya mana maganin shege.

"badai shege ba kace shegu, kuma inya dawo in sai me mala'ikane shi da zanji tsoron dawowar sa koh gidan ubansa ne"?

Kama Baki Anwar yayi, ubansa ka zaga lallai abin naka nayi ne lahab wallahi kadaiji kunya baza'aje boko ba baza'aje arabic ba ahaka dai za'a kare

"Inna kare a haka uwarka ce ta kare"

Jin Amsar da lahab ya basa yasa bacin ransa karuwa akan nada, don yaji haushin abinda lahab da rahab suka ma mahaifiyar sa, da kunyatata da sukayi a gaban kishiyar ta da surkuwar ta ga yara, gashi kowa baiga laifin saba saina mamu, hannu yasa zai tsinke lahab da mari.

Da sauri lahab ya cabe hannun Anwar hade da wurgarwa, da gudu ya b'anb'ara, sanin da yayi koh ya saya in zasu daku ma shine zaiji a jikinsa, shima Anwar da gudu yabisa.

Gudu Lahab keyi Anwar na binsa harya nufi kofar d'akin su da sauri yasa kafa ya bangaje kofar ya shiga, cikin sauri ya maida kofar zai rufe daidai lokacin shima Anwar ya kawo kai zai shiga, buga masa kofar Lahab yayi a fuska ji kake kauuu sai salatin Anwar dake tashi da karfi yana innalilahi Lahab ya cire masa hakoriiiiiii



*******************
Nnenna sai da asuba ta mike a hankali jin muryoyi na tashi a tasha, bakko mai datti ta gani a gonar d'auka tayi ta tsunduma kulenta a ciki ta fita a gonar ta nufi tashan, Abinci ta saya hade da kifi ta baiwa kulenta itakam ta kasa cin kome don mutuwar papa ya shiga jikinta bana wasa ba.

Duba takardan da papa ya bata tayi wanda jiya ta cusa a Aljuhun riganta, budewa tayi tana dubawa gani tayi ya rubuta mata Gombe state da kuma unguwa da address na gida hade da sunan mutumin Coulis Appa, nunawa masu motar tayi akan tana neman motar gombe?

Bata samu ba sai dai sunce ta shiga a sauke ta a wani state, ta hau wani mota ba musu ta shiga ganin wannan ya amince zai kaita don wasu mutanen koh magana ta musu sai dai suki kulata haka mai abinci ta koreta wai tana warin petur karta jaza mata masifa, wasu yarane ta roka suka sayo mata, haka motar ma tana shiga mutane suka ringa toshe hanci wasu na tufar da yawo.

Ganin haka yasa driver ce mata ta sauka, kuka ta sake tana basa hakuri daker ta samu ya yarda Amma sai dai ta zauna akan injin mota daman bus ne.

Ba musu haka ta zauna tana maijin azaba bad'an kad'an ba,kafun mita ya cika, karshe dai da taga za'a tada motar Kawai tace zata koma boot cikin kaya ta zauna agun bazata iyya zaman kan inji ba, da murna mutanen motan sukace ta shiga boot in, a haka akayi ta tafi sai kusan 4 aka sauke su a wani gari wanda itama batasan ina bane agun inyamuri mai motar ya had'ata da wani akan zata gombe.

Tana bakke da bakkonta ta shiga

Please Login or Register in order to submit comment