Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

motar gombe akaja suka kama hanya gabaki d'aya
tayi ligis kafufunta sun kukkumbura don ita bata taba tafiya irin na yau ba, shiyasa sai zare ido take, tana kallon mutane, suma suna kallonta sauran abincin data saima kulenta yaci ya rage shitasamu ta afa a bakinta jin yunwa na shirin kasheta.


Har dare suna kan hanya basu isa ba, ga dare ya fara rabuwa wasu har bacci suke Amma banda Nnenna dake zaune rungume da bakkon ta, suna gaf da shiga garin gombe, kamar daga sama sukaji karan bindiga tauuutauuutauuu sai sukaji tayan motarsu ya fashe, musulmai dake cikin motar ne suka fara Ambaton Allah, yayin da Christoti na ihu suna kiran jesus, Alamudai sun shiga riskun yan Fashiiiiiii






✨Ruqeenjalal✨




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

Free page🀧

*EXQUISITE WRITER'S FARUM*


page 1⃣5⃣&1⃣6⃣
Nnenna kam jikin ta rawa ya fara ganin yanda hankalin jama'ar motar ya tashi don ita ba fahimtar kome tayi ba tadai san Tabbas akwai abinda ke faruwa.

Motar ce ta tsaya a take barayin suka saitasu da bindiga tare da basu izinin fitowa daga motar, ba musu duk jama'ar motar suka fifita harda Nnenna.

Ashe basu kadai aka tare ba ga mototi da yawa har biyar, kallon wata mata Nnenna tayi da mijinta da gani dai musulmai ne masu arziki matar na d'auke da ciki babba, haihuwar yau koh gobe ga mijinta a kusa da ita sai rokon barayin yake akan suyi hakuri akwai kudi a mota, Amma karsu cutar masa da mata.

Wani daga cikin sune ya daga ma su Nnenna tsawa akan su kwanta, kamar sauran babu musu duk suka kwanta, mutumin kuma wani ya buga masa gindin bindiga a kafad'a.

Matar ganin Halinda mijin ta ya shiga a take hankalinta ya tashi nakuda ya ballo mata sabo, Salati take sauran matan dake gefen tane suka fahimci haihuwa zatayi da sauri wata ta miki zata nufe ta ganin tana nakuda kuma a zaune.

Tsawa suka kwadawa matar akan ta koma inda take mijin ma jansa akai gefe aka bar matar ita kadai tana ta fama da azaba.


Caji suka fara daga mota har jikin mutane An samu wasu da kudi sai a ware su a gefe wanda ba'a samu kome agun saba Harbesa ake, Hakan yasa wasu da dama mutuwa tun ma ba'azo kansu ba suka hadeye rai suka musu.

Nnenna karan kanta Hankalinta ya tashi don ta fahimce Abinda ke faruwa a wajen watoh bakin rai bakin fama, Allah sarki mai nakuda nan nata fama da wahala kowa agun saida ya tausaya mata kuma da gani haihuwar fari ce.

Gaskiya Yan fashin nan basuda imani suna gani matar nan ta haihu Amma koh a jikinsu daker suka bari wata tsohowa ta yanke ma jaririya Cibi, Uban yarinyar ne ya roke Alfarmar a barsa yaga yarsa, Amma barayin nan haka suka ki.

Nnenna dake gefe a kwance Wani kato yazo kanta yana lalubar ta aiko banda naira dubu uku dake hannunta bai samu kome ba, janta yayi ita da bakkon ta gefe tare da bada izinin akai masa ita ciki tunda bata da kudi dole su fanshe kaya.


Kamata wasu sukayi wani yaja bakkon ya yar a take kulenta ya bayyana, Fizgo kanta Nnenna tayi da gudu ta nufi matar dake kwance cikin jini ga jaririyar a gefe dukawa tayi ta d'au jaririyan tare dama matar magana da turanci akan zata kai mata yarta har inda suke ta fad'a mata inane garin su?

Da mamaki barayin da mutanen wajen suke kallon Nnenna ita kamma koh a jikinta babu Alamun tsoro koh tashin Hankali, wani daga cikin sune ya harzuka da sauri ya nufi wajen da Nnenna ke duke tana jin maganar da matar ke fad'a mata, ga jakanta purse data bata akan inta shiga gombe sai ta binciki jakan tare da bata d'ankwalin kanta ta sanya jaririyar a ciki.

Ba musu ta Amsa daida lokacin barawon ya daga bindiga da karfi zai buga ma Nnenna akai cikin hanzari ta gauce ba tare da ya dame taba.

"Karka kuskura ka fusatani nama mahaifina Alkawarin xan danne xuciyata karka hasalani" tace tana nuna mutumin da hannu.

Hannu kawai yasa ya kwasheta da mari tau saida ta fadi a kasa daga tsungune, mikewa tayi da jaririyan a hannunta sai kuma ta daga kanta da karfi jin yana mugun sara mata.

Bata dawo hayyacin taba saida taji guje gujen mutane Ana ihu ana gudu daga maza har mata ga karan harsashe kamar ruwa, d'ago kanta tayi cikin matsanan cin Nauyi tana kallo dishi-dishi kamar dai Nnennan da babu glass.

Bata Ankara ba taji An kama hannunta da sauri an jata sun kama gudu Ashe wai yan sandane suka diro suke musanyan wuta da yan fashi.


Tsungunawa tayi da gudu ta sabe kulenta da jinjira a haka suka ringa gudu bata masan wanene ya riketa ba, ga jaririyar sai kuka take kamar ranta zai fita dole tasa suka tsaya a wani wajen ganin sun tsira sunyi nisa da Dajin.

Su biyune da bawan Allanan da zaikai shekara 40 jijiga yarinyar Nnenna kiyi Amma ina yarinya taki shuru mutumin ma ya karbeta ya jijiga Amma ina kuka take bilhakki da gaskiya abin ya kwabe musu sun rasa yaya zasuyi da ransu Ga dare ga kukan yarinya.


Mutumin ne ya mike hade da cewa Nnenna bara ya dubo koh ruwane a samu a bata tunda kamar sun shigo kauyukan Gombe babu musu tace masa toh.

Yana tafiya yarinya sai kuka take harda had'a gumi sosai ta bawa Nnenna tausayi tunawa da tayi ana baiwa jarirai nono yasata saurin kwantar da yarinyar a cinyanta ta sauke kulenta ta aje a gefe.

Riganta ta matsar kasa kad'an hannu tasa ta zaro breast nata manya kuma tsayayu, babu wani tsoro ta kafawa yarinyar nipple a baki, jikin yarinyar har bari yake ta kama da sauri sauir take jan maman.

Duk da babu kome a cikin nono babu ruwa Amma hakan baisa yarinyar ta sake ba, sai ma Nnenna da zafi ya dameta ta zare bakin nonon ta, aiko yarinyar cinyara kara tayi da karfi, Nnenna ma da sauri ta maida mata tana rumtsa ido saboda zafi.

A haka har yarinyar tayi bacci mutumin bai dawo ba ita ma bata damuwa ba ta maida kirjinta ciki, tana mai tausaya ma jaririyar, sai da ta sake jimawa sosai kafun mutumin ya dawo d'auke da ruwa a tundi.

Da mamaki yake tambayar Nnenna ya haka yarinyar tayi bacci, Amsa kawai ta basa da yarinyar ta gaji da kukane har tayi baccin, ruwan ta karba shima ya cire rigansa ga baiwa Nnenna tana tsomawa a ruwa tana gogewa yarinyar jiki harta gogeta ta fita kamar yanda yace tayi.

A wajen suka kwana yarinyar ta farka da dare haka Nnenna ta damka mata nono a cikin duhu ba tare da mutumin ya gane ba a tunaninta batasan shikam yasan me take ba, washe gari mutumin ya fita bakin titi ya tare musu motar suka shiga har cikin gari.


Tunda Nnanna ta shigo cikin gombe take bin koh ina da kallo duk da bata kallo garau Amma tana iyya gani dishi dishi, ji take kamar ta shigo sabuwar duniya gata rike da kule da jaririya ga riganta a bace kaca kaca station mutumin yace su nufa gudun matsala.

Report mutumin ya shigar akan suna d'aya daga cikin matafiya da aka ma fashi daren jiya a mashigar gari, daman yan sandan sunsan da fashin, jakan hannunsa daya d'auka wanda matar ta baiwa Nnenna ya bude ID card na matar ya fitar ya baiwa yan sandan, tare da musu bayanin jaririyar.

Akan su nema musu matar ga jaririyar ta a hannun su koh wani yan uwan ta kona mijinta, babu musu yan sanda suka karba aka fara bincike basu bar Station in ba saida aka samo Iyayen matar ashe ma ba boyayyu bane manyan mutane ne, karbar jaririyar su sukayi suna ta godiya, jin Abinda Nnenna tayi, wasu sai kuka suke don tun jiya hankalin su yake a tashe gashi basu san halin da yarsu da mijinta suka shiga ba, daman garin su mijin suka fitoh.

Nnenna kamar tasa kuka don haka kawai taji tana son jaririyar Amma ya ta iyya haka ta basu yarsu, kakan jaririyar kudi ta baiwa Nnenna masu yawa akalla zai kai 500k kin karba tayi sai da mutumin yasa baki kafun ta karba tana musu godiya.

Mutumin ya mata sallama zai tafi sai kuma ya dawo ya tsaya ganin yanda ta rike kudi a hannu sannan tana bakke da kule ta tsaya a gefen station.

Tambayar ta yayi lafiya take tsaye bataza ta tafi gida ba?

Kuka Nnenna ta sake cikin jimami take sanar dashi ita bakuwa ce kuma bata san kowa ba takarda kawai baban ta ya bata ta taho wajen uncle nata daga Enugu, kuma yanzun bata gani sosai, bata da glass a ido.

Karban paper mutumin yayi yana dubawa sai kuma yace mata tazo suje kudin ma karba yayi yasa A Aljuhunsa ba musu ta bisa a baya, Abinci yasai mata a tsallaken titi Amma taki ci sai kulenta kawai yaci don batacin nama sam koh Abinci mai nama, ya sai mata medicated glass a wani shago ta sanya a idanunta.


Keke napep mutumin ya tare musu suka hau ba musu tana ta binsa.

Sunyi tafiya mai d'an nisa kafun suka iso wani unguwan talakawa har kofar wani gida sukayi packing,mutumin sauka yayi kamar d'azun ya zaro change daya saya mata abinci ya biya mai machine in tare dama Nnenna iso a cikin wani kwarmadeden gidan jan kasa.......




*********************
Lahab yana d'aki a kwace bayan ya rufe kofar dakin su, yanajin lokacin da Anwar ke ihu har zuwan su Addayiya da Abbu yana cewa yaga bakin Anwar in, sai kuma yaji Rahab nace wa ashe ba hakorin sa bane yacire, bakine da Goshi ya fashe duk yanajin Ana ta hidimar Anwar har kaisa asibiti da akayi da irin zagin da Mamu da Addayiya keyi Amma koh a jikinsa kofar ya sama kwado.

Ranan Rahab ma a dakin su Uxaifa ya kwana, washe gari da Asuba Lahab koh a jikinsa ya fita da asuban yaje masallaci agun ya hadu dasu Abbu Ga bakin Anwar ya sunduma gwanin tausayi, Lahab kam koh a jikinsa yayi kamar ma bai gansu ba.

Daga masallaci gidan su adewale ya wuce suka fita jogging, sai 8:00pm suka dawo,gidan su nabeel ya shiga yayi wanka ya sanya kayan sa da yake bari a gidan su nabeel wata rana in yayi wanka a gidan.

Adewale gida ya koma ya ibo musu abincin karyawa a kula lafiyayye suka karya daganan suka shiga gari yawo.


Bashi ya dawo ba sai yamma ya kamo hanyar gida don duk rashin jin Lahab baya wuce mangariba a waje haka baya fita koh ina da dare shiyasa suke kara godewa Allah baya yawon dare iyyakar sa rana.

Turo kofar falon yayi ya shiga ciki har yayi rabin falon sai kuma ya tsaya ganin mamin sa zaune a falon tana hira da Addayiya, tsayawa yayi yana kallon Addayiya da mamaki ganin yanda take washe baki, kamar ba ita ke zagin mamin su ba kullum.

Mami dake kallon sa ita ma tun shigowar sa jin baiyi sallama ba yasa ta nuna masa kofa ba tare da tayi magana ba, shima baice kome ba ya koma bakin falon ya tsaya amma baiyi sallamar ba, meya tunane oho ya juya ya zagaya ta bayan ginin flat nasu, ya shigo sashen su ta d'ayan kofar falon su.

D'aki ya wuce yayi wanka abinsa wando yasa 3quater sai Armless, jin an kira sallah yasasa yin Alwala ya fita masallaci ta kofar da ya shigo ana idar da sallan shagon mai Abincin tsallaken titin su ya shiga yasai abinci Agun ya zauna yace har isha'i yayi sallah ya shigo gida kamar d'azun yabi kofar baya.

Kwanciyar sa yayi abinsa yana chat gabaki d'aya hankalin sa nakan wayar sa.

Mami dake bakin kofar dakin hannu tasa ta tura kofar da sallama ta shigo, da sauri Lahab ya mike zaune daga kan katifar sa yana kallon mami sosai cikin sa ya duri ruwa ganin fuskar ta babu koh digon walwala.

Wallahi Lahab kabi duniya a Hankali Lahab kaji tsoron bakin jama'a lahab ina rabaka da Halima da yaranta, Lahab bakama jin Abinda nake fad'a maka koh? inka ma Addayiya koh yayan ku Umar su naka ne babu yanda suka iyya,hakuri ya zamo musu dole Amma wallahi ina rabaka da Halima(mamu)da taba mata yara don baka da hankali zaka d'aukar mata kudi har 300k sannan ka buga mata fuskar yaro sai da ya kumbura, Anwar Abokin wasan kane, bafa cousin naka bane d'an yayan kane akan me zakayi wasan banza dashi.

"Habba mami nifa bani na d'auka mata kudi ba, wani munafukin ne ma yaje ya sanar dake wannan sharbeben karyan"?

Ungo naka?mami ta masa dakuwa.

Kumbura fuska yayi "nifa mami ban d'aukar mata kudi ba"

Rufe mini baki in bansan halinka bane sai na yarda baka d'auka ba, wallahi Lahab ka shiga hankalin ka ka jima yaro ciwo Amma bazaka iyya zuwa ka duba sa ba, bare ma ka basa hakuri koh neman yafiyarsa.

"Kai mami" yace yana kallon ta

Duka mami ta kaimai da karfi a baya ji kake domm, ihu ya sake yana sosa bayan sai kuma da sauri ya sauko a katifar.

Bar kallona rasa kunya beran danga, wuce muje ka duba Anwar in kuma wallahi ka basa hakuri.

Ba yanda ya iyya haka yanaji yana gani mami ta saka sa a gaba har d'akin Anwar da sallama suka shiga d'akin.

Zaune yake a bakin gado ga abinci a gabansa saman center table, Amma ya kasa ci inka gansa sai ka tausaya masa kofar ta buge fuskar sa sosai ga goshi ya kumbura, Amma lahab koh a jikinsa tsayawa yayi a gefe yayin da mami ta nemi kujera dake dakin ta zauna tana kara ma Anwar ya jiki tare ba basa hakuri Akan rashin Hankali da Lahab ya masa.

Murmushi kawai yayi cikin sanyin jiki yake sanar da ita babu kome, kome ya wuce wallahi sai a lokacin Lahab yaji tausayin d'an-d'an uwansa, Jin yanda yayi maganar gwanin tausaya, takowa yayi a hankali ya matsa wajen da Anwar ke zaune a bakin gado shikam tsungunawa yayi a gaban Anwar in ya kama hannunsa, Cikin wasa yace "Son Am so sorry for what uncle do it for u, nasan Abinda ke damunka kar fa'iza ta ganka haka da kumburarun lebuna koh, tace a sauke sartin biki"? Ya karasa maganar yana dariya

Shima Anwar d'an dariya yayi a hankali saboda bakin sa, jin turancin da Lahab ya masa kamar wani d'an primary, kaga koh Lahab shiyasa nace ka koma makaranta turanci babu dadi.

Dariya lahab yayi daman shima burinsa kenan yaga Anwar ya sake jikinsa, hira suka soma akan budurwar Anwar fa'iza, Abincin da aka kawo wa Anwar lahab ya d'auka yaja kujera ya zauna yana bawa Anwar kadan kadan A baki ganin haka yasa mami yima Anwar sallama jin mijinta yazo zasu tafi.


A ranan tare Da Anwar lahab ya kwana gado d'aya, da safe ma shiya taimaka masa yayi brush harda karyawa ya basa a baki dayake bazashi Office ba, lahab ma zama yayi a dakin ya d'auko wani English novel yana karanta wa Anwar duk jaraban Mamu saida ta barsa.....



*************
Nnenna na bin mutumin A baya har suka shigo cikin gidan da sallama a bakin sa.

amsa masa wasu yara dake zaune a tsakar gidan sanye da uniform Suka mike da gudu suna oyoyo baba, jin Abinda yara ke cewa yasa matar gidan saurin fitowa daga bayi hannunta d'auke da buta.

Fuska ba walwala take kallon mijin nata sai kuma ta kalli Nnenan dake gefe kama baki tayi hade da cewa mijin nata, kai shayibu menene haka zaka shigo gida daga kai sai wando da vest duk datti ga wata Arniya da guntun riga tana binka a baya wanan shegen kulenfa uban me yasa aka shigo mini dashi cikin gida?

Girgiza kai mijin yayi yana kallon Ma'u, haba ma'u ya daga dawowa na koh waje baki bani na zauna ba baki bani ruwa koh wani abu da zansha na dawo hayyacina ba, zaki tareni da irin wa'innan xantuka, keda tun daren jiya nace miki ina hanya Amma kika ga shuru ban dawo ba, koh a jikin ki?

Eh koh a jikin nawa wani abin kake tsinana mini ne da in ka dawo zan damu sannan wacece wannan tace tana nuna Nnenna.

Bai bata Amsa ba sai kallon yaransa da yayi wa'inda suka sakesa da sauri suka koma kusa da Nnenna suna lakutar jikin kulenta sai kuma su ruga da gudu su koma baya suna dariya, sai kuma su sake dawowa su taba duk sun cika gidan da ihun su, daka musu tsawa ma'u tayi, kai shegu ku rufe mana baki kun cika mini kunne?

Kai ma'u Allah ya shiyeki nace miki banason kina zagen yarana da shegu Amma baki ji, sanan meya hanasu zuwa makaranta har yanzun suna zaune da uniform a jiki?

Tsaki ta sake hade da kallon su, kai me ya dawo daku ku fad'a masa da bakin ku? Ba musu suka sanar da baban su an koresu kudin petiA ne basu biya ba aka korosu.

Girgiza kai kawai yayi don kudin kwata kwata naira 100 ne, koh wani mutum daya shi kuma yau koh sisi bai dawo dashi ba dan kudin daya tara a kudun ma gashi ya hadu da iftilahi.

Kallon Nnenna yayi cikin turanci yake ce mata ta zauna bara ya ibo mata ruwa sai tayi wanka koh, gyada kai tayi ta nemi gefen dakali ta xauna shima boket ya d'auka da sauri ya nufi kofar gida.

Cikin masifa ma'u tace kai shayibu ban gane ba?me nake ganin yarinyar nan ta aje min gindin ta a dakalina?

Wa'iyyazu billah dake ma'u da rashin iyya magana, toh zama zatayi bakuwa ce tare muka samu iftikahin barayi a hanya?


Bata da gidan yan uwane da bazata tafi ba zata biyoka gida?oh na gane watoh sabon iskanci ne kenan daka saba xa'a kawo mini har gida toh wallahi bazata zauna mini a gida ba, sai dai ka zaba koh ni koh ita, wannan daga ganinta ma karuwa ce........... .







✨Ruqeenjalal✨




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

Free page🀧

*EXQUISITE WRITER'S FARUM*

page1⃣7⃣&1⃣8⃣
Juyawa shayibu yayi yana kallon ma'u, shikam Allah ya gani rashin kudi da bin umurnin Iyaye,sune silar da yake hakurin zama da ma'u Amma wannan karon zai nuna mata ikon Miji akan matar sa, Ma'u baki da hankali a gaban yaran ki babu kunya kike irin wannan magana, toh bara na gaya miki koh kibi Abinda nace koh kuma ga kofa ki tafi duk inda yafiye miki nan.

Waro ido tayi tana kallon shayibu sannan ta maida kallon ta gun Nnenna dake xaune gabaki d'aya kanta a duke duk da ba Hausa takeji ba, Amma daga Kaga muhawaran da suke kasan fad'a ne, toh wallahi bara kaji xama kam daram dam, in ma burinka kenan na tafi na barmaka gidan kuji dadin iskanci toh bazan tafiba tace tana shigewa daki Abinta.

Shima bai kara magana ba ya d'auki jamfansa a igiya ya saka, ya fita bai jima ba sai gasa da ruwa a boket d'aya hannun nasa d'auke da sabulu sai take Away a Abinci.
Da sauri Nnenna ta mike ta karbi boket inda ke Hannun sa ta aje a gefe,nuna mata bayan gida yayi cikin turanci yace ta kai ruwan ciki ba musu takai ta aje.

Yaran sa kam kulen suka tasa a gaba suka maida abin wasa,Abincin ya mikawa Nnenna yayi yace mata taci, ba musu ta karbi take Away in tana budewa da sauri yaran suka rugo zuwa inda take alamu dai suma ba karyawan sukayi ba, Aje laidan Nnenna tayi a kasa ta bude, shinkafane da miya sai nama d'aya akai da sauri ta kauda fuskar ta, iba tayi a laidan takeAway in ta mikawa kulenta sauran ta baiwa yaran Shayibu.

Da mamaki yake kallon ta sai kuma ya kasa hakuri ya tambaye ta dalilin da yasa batacin duk abinda ya sai mata?girgiza kai tayi sai kuma a hankali tace masa ita batacin nama koh abinci mai nama.

Da mamaki yake kallon ta sai kuma ya wuce d'akin matar sa, zani da riga ya d'auko harya fitoh da sauri ma'u ta biyosa da gudu tazo ta fizge kayan kuma tace Nnenna bazata saka mata kaya ba.

Fita yayi bai jima ba sai gasa da siket da riga na gwanjo har guda hudu, ya baiwa Nnenna ta shiga wanka, Alele ya sayo mata ba musu taci ya nuna mata dakin yaransa akan ta shiga ta kwanta tunda jiya basu samu bacci ba, ba musu ta shiga ta kwanta abinta sai bacci.

Bata farka ba sai kusan 3:00 na yamma nan ma masifar Ma'u ne ya farkar da ita akan bazata ci Garin kwaki ba yau ta gaji sai dai ya bata kudi ta sayo musu Shinkafa a dafa koh dafa duka ne(jalof).

mikewa tayi ta fitoh a d'akin jin ma'u ta shiga ciki kallon Shayibu tayi sai kuma tace, "sir pls in zamana ne Bataso sai na tafi"?

Murmushi yayi watoh mutun koh baya jin yare Allah ya basa baiwar gane abinda ke gudana, haba Nnenna bafa akan xamanki bane?

"Toh akan menene sir tunda nazo kuke fad'a"?

Kudi ne takeso na bata ta sai Abinci ni kuma bani dashi shiyasa kinji ki koma daki koh?

"sir haba ka d'auki kudin dake hannunka kasai abinda ya dace"

taya zanna taba miki kudi, badon bani dashi ba da dasafen nan ma hidimar ki duk ni zan d'auka basai na taba kudin ba?

"No sir nikam na bar maka kudin ka rike a hannunka ni damuwata kawai ka kaini wajen uncle nawa"?

Sosai yaji dadin girmama sa da Nnenna tayi gashi dai yarinya kirista tana da Hali mai kyau da tunani, ok kawai yace yana fita a gidan tsintsiya Nnenna ta d'auka ta share musu gidan kwanuka masu datti data gani a watse duk ta had'asu waje d'aya haka ta wanken babu omo, tana cikin wanke wanken sai ga shayibu ya dawo da laida baki ajewa yayi yana kallon Nnenna da mamaki, Daughter kece haka da aiki?

"Ba kome sir is my pleasure"

Ma'u ma'u yana kwalawa matar tasa dake d'aki kira, Amma tayi biris dashi koh Amsawa batayi ba gashi yaransu sun dawo makarantan Allo sunyi jigon-jigon a gefe duk yunwa na damunsu ga mangariba ya kusa.

Fitowa tayi tana yamutsa fuska, gani lafiya kaketa kwalamin kira haka?

Kedai kika jiyo da halinki ga shinkafan nan saiki d'aura mana da wurwuri akwai wake yaran nan yunwa sukeji?

Ita wannan menene Amfaninta da bazata d'aura ba, sai ni zan daura ita kuma tana yawo da siket kai ba dankwali kana kare mata kallo, ta karasa maganar da nuna Nnenna dake xaune tana d'aureye kwanuka.

Amma dai kinsan yarinyar nan yar Kudu ce koh? Abincin mu daban da nasu haka ma yanayin girkin mu sannan koh da ace ta iyya ai bai dace ki sata aiki ba bayan wanda take miki.

Dakata shayibu banason maganar banza abinci ne nace bazan iyya girkawa ba.

Ya miki kyau kawai yace yana wucewa madafan Gawayi ya kunna daker lokacin ana kiran sallan mangari ba ya samu ya fara kamawa, wucewa yayi zuwa masallaci da yaransa maza biyu macen ma buta ta d'auka tayi Alwala ta shimfida sallaya tana sallah.

Nnenna sai kallonta take don Abin sabo ya xamo mata kauyen su babu musulmin da xaiyi sallah a sarari haka suna kallo, Asalima inka musulunta koranka ake a kauyen.

Ruwan xafi ta d'aura a gaushin ganin ya kama, sai ga shayibu ya dawo tire ya d'auka yana gyaran wake yayinda Nnenna ya bata dakan barkono yaransa na gefe da kule, gabaki d'ayan su suna zaune har bayan isha'i ya gama girkin, xubawa Nnenna yayi a kwano d'aya da yaransa ya zubawa kulenta a wani tsohon kwano ya xuba nasa daban ya xubawa Ma'u nata babu kunya tazo ta d'auka tayi daki.

Suna gama cin Abincin Nnenna tayi wanka yace musu su tafi daki su kwanta, suna shiga Nnenna ta tambaye yaran takardun makarantan su, firfitarwa sukayi tana ta

Please Login or Register in order to submit comment